Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yan s.i.d ɗinta.gaba daya tsoro ,firgici da tsantsar mamakin abinda ke faruwa yasa sun kasa koda motsine agurin ,bare suyi wani abu.
Sun ƙanƙame juna jikinsu yana wani irin bari,nanny Banda sunan Allah ba abinda take ambata"innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, meye wannan ke shirin faruwa haka,tareeƙ kana ina bana ganin komai fa " nanny ta faɗa tana ƙanƙame tareek dake kusa da ita.
Shi kansa tareeƙ jikinsa rawa yake ,sam ya kasa magana sai rungume mahaifiyarsa da yayi sosai ajikinsa.

Ƙaran rashad ne ya karaɗe dakin ,cikin wani irin sauti na azaba,wanda kana jinsa kasan wanda ke wannan karan yana cikin azaba da halin ƙunci.
Kuka kawai amma ta sanya ,dan tasan yau kam ɗan ta sai abinda hali yayi,shikenan yau abinda ake shukawa agidan ya dawo kansu.

Ahankali ɗakin ya fara washewa daga tsantsar duhun da yayi ,kusan minti uku suna cikin halin tsoro da razani kafin ,suka fara ganin komai tar-tar .

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shine abinda Dukansu suka haɗa baki wajen faɗa,sakamakon ganin wani narkeken maciji mai girman gaske nannade da Rashad ,Wanda kallo ɗaya zakayiwa Rashad kasan cewa ba alamun numfashi atare dashi.
Kallon kallo ake tsakanin mutanen dake cikin dakin,wanda suka shiga tashin hankali fiye dana farko,dan kuwa ba Adeeb aɗakin sai wannan narkeken macijin,wato dai Adeeb shine ya zama wannan macijin.
Jikin nanny Banda rawa ba abinda yake ,haka ammi da amma,jakadiya da Zulaihat wacce tuni ta jiƙa jikinta da fitsari,tana tsaye ƙanƙame da amma wacce itama ta ƙanƙame Zulaihat ɗin.
Sun kasa magana sai kallon ikon Allah suke.
Macijin nan yana tsaye nannade da Rashad ya fasa kai yana wani irin huci da fesar da wani irin bakin abu daga bakinsa.juyi ya farayi da ƙarfi kafin ya maka rashad ajikin bango,ji kake timmmm!!Rashad ya baje akasan tyles,tuni jini ya fara zubowa daga kansa.hakan bai ishi macijin nan ba ya kara zuwa ya nannade Rashad tare da kara makashi jikin bango.
Ihu suka farayi ganin macijin nan na ƙoƙarin tarwatsa kasusuwan Rashad.
Da gudu jakadiya ta juya tayi waje tana ihu ,ta nufi part ɗin mai martaba,tana faɗuwa tana mikewa,gaba ɗaya bata cikin hayyacinta.
Zulaihat ma silalewa tayi agun ba alamun numfashi atare da ita.

"Wayyo jama'a ku taimaka min ,zai kashemin yarona,wayyo Allah na na shiga uku ku taimaka min"amma ta faɗa cikin ficewar hayyaci,dan tsabar tsoro gadan gadan take nufar cikin dakin gurin da Rashad ke kwance ayashe, aikuwa kafin ta ƙarasa kaiwa inda Rashad ke kwance, saijin wani abu tayi mai kama da bulala ya fyadeta a gadon bayanta,wani ihu amma ta kurma tare da faduwa sakamakon azabar raɗaɗin da taji gadon bayanta ya ɗauka.da rarrafe ta koma inda take tsaye. Jikinta na rawa .
Ammi fa tsoro ya gama kasheta,dan ko tsayuwar kirki ta kasayi, sam batayi tsammanin haka abin yake ba,ashe dai da gaske mutum yana iya komawa wata halittar ta hanyar asiri?lallai yau taga abinda ya fi ƙarfinta , sam bata tsammaci abun haka yake ba, amma dole tayi wani abu dan gudun zargi.dan haka cikin bugawar zuciya da tsananin tsoro ta fara takawa zuwa gurin da Adeeb ke tsaye yana zagaya Rashad yana huci.

"A...a.ddd..ee.e.bbb."ammi ta kira sunansa cikin tsinkewar numfashi, shikuwa baiko kalli inda take ba ,burinsa kawai yaga Rashad yayi motsi ya kara karairaya masa inda bai gama lalacewa ba.
"Ka nutsu Adeeb ɗana,.n...i.cce ammin ...ka, ka ...ka...ji."ta faɗa tana matsawa cikin tsoro da firgici.

Ai kuwa jin takunta da adeeb yayi ,afusace ya juyo tare da kai mata tsafka, cikin sa'a kuwa ya damketa,ihu ta farayi tana neman taimako,"wayyo Allah na taimako jama'a taimako"ammi ta faɗa lokacin da Adeeb ke nannaɗeta kamar buhun goro.saida yagama naɗeta sannan ya fasa kansa saitin fuskar ammi yana huci.tsabar firgici tuni ammi ta sume ,kura mata ido Adeeb yayi kafin ya fara dakinta ahankali ,ta faɗa kan gado.

Gurin fattu ya koma tare da hawa gadon bayanta, nade ta yayi tare da mirgina ta ta juyo rigingine,kallon fuskarta yake wani irin farin Ruwa na zubowa daga idanunsa ,kwanciya yayi akan cikinta yayi lamo yana mai juya kansa ,tare da yin wani irin ƙara yana bude bakinsa.
Al'amarin yayi matuƙar tsorata dukkan wadanda ke cikin dakin,dan nanny ma tuni ta sume ,amma ce kawai mai ƙarfin hali ,dan tana zaune riƙe da bayanta da tasha bulala.
Tareeƙ kuwa hawayene ke zuba daga idanunsa.yana matukar tausayawa yallabai ɗin nasa.
Ana cikin wannan halin ne,abie ya shigo dakin tare da waziri da manyan faɗa ,sai Shaikh lateef ,babban malamine dake koyar da ilimin addini sannan masani akan abinda ya shafi jinya da maganinta, ya ƙware sosai wajen magance abun daya shafi sihiri.
Lokacin da jakadiya ta kaiwa abie labarin,shikuma suna tare da su waziri suna ɗan tattauna wata magana mai muhimmanci,shine suka garzayo gaba ɗayansu, ɗan ganin abinda ke faruwa.

Ba ƙaramin kaɗuwa abie yayi ba,lokacin da ya wannan kumurcin macijin amatsayin Adeeb ɗinsa,hawaye ne kawai ke zuba cikin idanunsa, ya ƙurawa Adeeb ɗin ido.tunanni kawai yake ,waye wanda yayiwa adeeb wannan aika -aikar?me yatsarewa wanda yayi masa haka?ace yaro mai gata dan sarauta kamar Adeeb yana zama maciji?duk yadda Adeeb ya kasance mai tausayi da taimakon al'umma ,amma ashe wasu suna can suna shirya masa mugunta.lallai dole ya tsaya tsayin daka ,wajen bawa yaronsa abin sonsa kariya ta ko wacce siga.yasan ammi na ƙoƙarin wajen yiwa adeeb addu'a ,kuma tana sawa ayi masa kamar yadda take faɗa amma dole shima ya dage ta bangarensa.

Abie ne ya kalli Shaikh lateef,cikin damuwa da zubar hawaye yace "Shaikh kaga Adeeb ga ,kaga halin da yake ciki,menene abinyi ?abie ya faɗa yana mai share kwalla.
Shaikh lateef kuwa wanda tun shigowar su yake kallon Adeeb,kallo na tsinake,sai lokacin yayi ajiyar zuciya kana ya kalli abie,yace" ranka shi daɗe lallai Adeeb yana cikin tsaka mai wuya ,da tuggun maƙiya ,amma In Sha Allah komai yazo ƙarshe,yanzu dai ayi ƙoƙarin diban bayin Allah dake kwance dan akaisu ga likita,sannan sai musan abinda ya kamata muyi"Shaikh lateef ya faɗa yana mai kallon abie.
Nan da nan kuwa aka kwashe su ammi da nanny,Zulaihat ,sai dai ko yaya akayi yunƙirin zuwa inda Rashad ke wance kamar gawa,take macijin nan zaiyo kan mutum afusace.

Ganin haka ya sanya abie cikin ƙarfin hali ya tunkari Adeeb dake fagen fattu yana fasa kai,ya kasa ya tsare,
Ahankali abie ke kallon Adeeb da idanuwansa masu fidda hawaye kafin yace"habeebee kayi hakuri adauke dan uwanda,dan asuba lafiyarsa, koma me yayi maka nine nan,zan ɗaukar maka mataki,bazan taɓa yarda da zalunci ba"Abie ya faɗa cikin sanyin murya yana kallon Adeeb.
Huci kawai Adeeb keyi yana kallon Abie kafin ya maida kansa ga fattu yana kallonta,sannna ya ɗago kai ya kalli abie,
Jinjina kai abie yayi cike da fahimtar Adeeb ɗin yace "na fahimta habeebee,dole zan ramawa yarinyar nan abinda rashad yayi mata,dan kasan ba'a zalumci amasarautata" abie ya faɗa yana mai ƙara sawa kusa da Adeeb ɗin ahankali ya sanya hannunsa yana shafa bayan Adeeb.

Shikuwa Adeeb sai huci yake yana guri da wata iska mai matukar zafi.haka aka samu aka lulluɓawa Rashad Abu ajikinsa kafin kayi waje dashi, amma duk yadda akayi ƙoƙarin ɗauke fattu Adeeb ya hana ,dan hatta mai martaba ,da yayi yunƙurin daukar ta saida Adeeb ya kai masa tsafka.haka suna ji suna gani ba yadda suka iya,sai lulluɓe mata jiki da sukayi itama ,dan kuwa yaƙi barin jikinta ma.

Shaikh lateef ne zaune gaban Adeeb yana karanto wasu addu'oi yana tofa masa,lokaci guda jikin Adeeb yayi laushi, gaba ɗaya baya ko kwakwkwaran motsi,sai huci da yake fiddawa ,ya dora kansa akan ruwan cikin fattu dake lulluɓe,jikinsa sai wani bakin hayaƙi ke fita.
Ci gaba Shaikh lateef yayi da addu'ar sa yana tofawa Adeeb,yayin da su abie ke gefe guda suna kallon ikon , Allah,dan zuwa lokacin murƙususu kawai macijin nan keyi,kafin wannan hayaƙin ya turnuke dakin,baka iya ganin komai tsabar duhu.
Su abie suma addu'a suka fara,lokacin da suka ga wanan hayaƙin,dan Shaikh lateef yace karsuji tsoron komai ,duk abinda zasu gani kawai suyi addu'a.

Can kusan wucewar mintuna biyar suna ta addu'oi ,dakin ya fara haske yana washewa har ya gama washewa tar, kamar ba shine yayi wannan duhun ba.

Adeeb ne durƙushe agaban wannan table ɗin da fattu ke kwance,kansa har lokacin yana kan cikin fattu.

Hamdala Abie da su waziri sukayi,ganin Adeeb ya dawo asalin halittarsa, dan abie yayi matuƙar tsorata, kar ace ahaka Adeeb ɗin zai zauna.
Ahankali Adeeb ke buɗe idanunsa ,da har zuwa lokacin basu gama komawa normal ba.

Kanshi ya daga da gyar yana ɗan yatsine fuska tare da dafe kan,dan ciwo yake masa sosai.
Sai kuma yayi saurin zabura ya mike tsaye "Hulwa" shine abinda ya faɗa cikin daga murya yana waige waige,

" Habeebee ka nutsu kaji ga hulwar taka nan kusa da kai "abie ya faɗa yana mai mikewa shima tare da riko kafadun Adeeb.
Sai lokacin Adeeb ya ga su abie aɗakin,kallon abie yayi kafin ya kalli inda abie ke nuna masa,zaro ido yayi ganin hulwarsa kwance kamar gawa,"Hulwa " Adeeb ya faɗa yana mai girgiza fattu,amma ina Hulwa tayi nisan zango.
Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungumeta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsanani ciwo da zafi.irin kukan da Adeeb keyi kaɗai zai fahimtar da kai yadda yake jin Hulwa da kuma ciwo acikin ransa.

"Rashad !
Rashad !!
Rashadddd!!!ka tabka babban kurkuren ƙoƙarin tabamin mata,kayi kurkure,idan Hulwa ta mutu"yayi shiru yana mai goge hawayen dake kwatanta cikin idanunsa,kafin ya ɗago idanunsa da suka yi wani irin mugun jaaa,ya kalli Abie sannan yaci gaba"wllh billahi,saina kashe Rashad ,idan har matata ma mutu sanadin sa"Adeeb ya faɗa cikin karfafa murya da nuna gaskiyar abinda yake fadi har cikin ransa.

Kallonsa kowa keyi acikin ɗakin,dan kuwa sun zama speechless,matarsa yake ta kira,kodai yarinyar nan amatsayin matarsa take?ko kuma yana nufin ita zai aura?
Shine abinda yake ta yawo cikin zukatan su Abie.
"Ya kamata akai yarinyar asibiti yanzu,nikuma zanje gida domin yin bincike akan larurar prince ranka shi dade"cewar Shaikh lateef yana mai mikewa tare da shafa kan Adeeb,dan yana tausayawa yaron sosai.

" Haka ne Shaikh bari akaita asibiti yanzun nan " cewar abie yana mai kallon Adeeb dake ƙankame da Hulwa kamar zai maidata cikinsa.

Kafin su ankara tuni Adeeb ya sungumi fattu yayi hanyar barin dakin da ita." Habeebee kayi hakuri akai yarinyar asibiti,kaima fa ba cikakkiyar lafiya gareka ba" cewar abie kenan ,ganin Adeeb na ƙoƙarin ficewa daga ɗakin.

" Ba wanda zai kara tabamin mata abie ,domin itaɗin mallakina ce mata tace ta Sunnah,hakkin kula da ita yana kaina,dan haka bana bukatar taimakon kowa,karka manta ,likitanci bangarenane" yana faɗin haka yayi waje da fattu rungume aƙirjinsa.

Kai tsaye fart ɗinsa ya nufa da fattu ,yana zuwa ya shimfiɗeta akan lafiyayyen gadonsa, kallo yabi jikinta dashi,cikin wani irin zafi da ƙunar zuciya,gaba ɗaya glasses sun maƙale ajikinta ,jini duk ya bata mata jiki.hatta fuskarta baka ganewa.

Gimbiya suhaimat ce tsaye tana bin Adeeb da kallon sabe da yarinya akafadunsa,haka kawai gabanta ke tsananin bugawa,so kawai take taga yarinyar,
Ko menene ya sameta oho?ahankali ta juya taci gaba da tafi zuwa dakin ammi,dan su basu san abinda ke faruwa ba.
Zuciyarta gaba ɗaya taki samun nutsuwa ,ba abinda take son gani sama da wannan yarinyar,gaskiya bazata iya jurewa ba dole taje taga yarinyar,sannan ta san meke damunta?me yasame haka gaba ɗaya jikinta jini...



Masu karatu ku biyoni dan jin gimbiya suhaimat zata je ganin fattu ne ko yaya?
Taku anty mammy

Mrs babi 💘💘


Share and comment fisabilillah.

More comment more typing
[8/23, 9:06 PM] +234 813 465 3007: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄


MACIJI NE 🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚


Free book

Page 57/58





________________Gimbiya suhaimat ta gama tsara cewa data huta zataje part ɗin Adeeb dan ganin yarinyar nan,
Saidai shigarta part ɗin ammi da yanayin da taga ammin yasa ta saurin,ƙarasawa cikin dakin ,cikin damuwa take faɗin"ukktee meke damunki? Yana ganki akwance?gimbiya suhaimat ta faɗa tana kamo hannun ammi ,wanda ba'a daura mata ruwa ajikinsa ba.

Ahankali ammi wacce tayi nisa cikin tunani ta buɗe idonta tana kallon gimbiya suhaimat,kafin ta sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido ta buɗe" ke dai bari suhaimat,yau naga abinda ban taba gani ba arayuwata,nan ta bata labarin abinda ya faru,saidai ta boye mata asalin labarin fattu,sai cewa tayi wata baiwa ce Rashad ɗin yayiwa fyade,dan ita atunanninta Rashad yayiwa fattu fyaɗen.

Sosai gimbiya suhaimat ta tausayawa yarinyar,sannan tayi Allah wadai da halin Rashad,zuciyarta na tsananin bugawa ,har cikin ranta take jin tausayin yarinya.kuma tayi alwashin ,saitaje taga yarinyar nan kafin ta bar ƙasar.

Rashad kuwa kai tsaye aka wuce dashi,lafiyayyen asibitin dake masarautar,emergency akayi dashi,cikin gaggawa likitoci suka duƙufa akansa dan ceto rayuwarsa.
Dan da dama cikin likitocin , sunyi tunanin hatsari ya samu mai muni.
Karon farko ruwa suka fara ɗauka masa,kafin suka fara bincikarsa,karayama kusan biyar ce ajikinsa, bayan munanan raunuka dake jikin sa,sannan since kansa ya bugu ,dole sai sunyi bincike akwakwalwarsa, dan tabbatar da lafiyarta.

Amma kuka take sosai cike da tarin damuwa da baƙin ciki ,meyasa Rashad zaiyi mata haka?me yasa gaba ɗaya halayyar Rashad ta sauya ne?da ɗan ta mai hankaline da nutsuwa ,sannan yana bin maganarta,amma daga baya ya fandare ya zama gagararre,yanzu ga irin abinda ya jama kansa.karaya har biyar ajikin mutum.Nan dai taci kukanta ta ƙoshi,tana zaune gefen ɗan ta.

Nanny ma ta farfaɗo ,hankalinta amatukar tashe ,tana zaune hawaye na zuba cikin idanunta,yayin da tareeƙ ke rarrashinta cikin kwantar da murya.
"Kayya tareeƙ abinnan na magajin faɗa,ya isheni yaron nan tun yana ƙuruciya yake haɗuwa da tuggun maƙiya,har zuwa girmansa,yaushe ne zai sami salama shima,kadufa wai Adeeb ne ya zama wannan ƙaton macijin,wanda idan awani gurin ka ganshi,sai inda ƙarfi ka ya ƙare wajen ceto rayuwarka.
Yanzu idan haka ta faru dashi awani gurin yunkurin kasheshi fa zasu yi"nanny ta ƙarasa cikin kuka tana fyace majina.

Hannunta tareeƙ ya kara damƙewa cikin nashi,kafin yace " wai ummeee yaushe zasu sanar da gaskiyar da muka jima da sanine?yaushe zamu taimakawa yallaɓai mu haska masa hanya danya gane irin haɗari dake bibiyarsa arayuwa?na gaji da boye gaskiya ummeee kiyi wani abu"tareeƙ ya faɗa cikin damuwa.

"Tareeƙ baka san masarautar ya take ba,idan baka iya kama ɓarawoba ,to shi zai kama ka,dole mubi komai asannu,akwai lokacin bayyana gaskiya kaji?kayi hakuri"nanny ta faɗa tana mai shafa kan ɗan nata.
Yanzu ya jikin ɗiyata yake ?shikenan yanzu yaron nan ya lalata nata rayuwa?ya karbi budurcinta awulaƙance sannan tana cikin al'ada ?kai ban taba ganin fajiri irin Rashad ba,Allah ya saka miki ɗiyata"nanny ta faɗa cikin kuka sosai,tana tausayawa fattu.
Tareeƙ ma runtse ido yayi zuciyarsa na masa zafi,dan kuwa yasan ahalin yanzu Adeeb yana can cikin bakin ciki da damuwa,saidai shikam yana ganin kamar Rashad ɗin bai sami damar yiwa fattu fyaɗen ba suka karaso, yana kuma fatan Allah yasa hasashensa yazama gaskiya.

Akan gado Adeeb ya shimfida fattu,wacce ke kwance kamar gawa,bata ko motsi,gaba ɗaya jini ya wanke mata fuska,jikinta ko ina raunine ,dan kuwa ba ƙaramin azaba Rashad ya gana mata ba,lips ɗin ta sun bushe idanunta ya kumbura sosai.
Runtse ido Adeeb yayi lokacin da idanunsa suka sauka kan wuyanta zuwa ƙirjinta ,fasassun kwalabe duk sun soketa, zama yayi abakin gadon,cikin wata irin karaya da zafin zuciya.ji yake kamar yaje ya kama Rashad yayi gutsin-gutsin dashi,
Hannunta ya kama na dama ,ya riƙe cikin nashi,gam-gam .jikinsa sai rawa yake ,yama kasa aikata komai akanta.wai hulwarsace kwance agabansa kamar gawa.
"Why Rashad ?why ?duk matan dake cikin fadar nan sai matata?me yasa zaka aikata haka agareni?Adeeb ya faɗa afili yana mai kaiwa bango naushi, ji yake kamar zuciyarsa zata kama da wuta.
Da sauri ya mike tare da ɗauko first aid box ɗinsa, dan Adeeb cikakken likitane akan fannin lafiya yayi karatunsa .

Farar vest ɗin fattu data yage kaɗan daga sama ya kama,wacce ta rine da jini, ya cire mata ahankali,nan da nan albarkatun ƙirjinta suka bayyana,cikin faduwar gaba Adeeb ya kawar da kansa ga barin kallonsu,zuciyarsa na ci gaba da bugawa. haka ma ya zare wannan dogon wando dake jikinta ya ajiye gefe,ya rage daga ita sai pant Wanda shima gaba ɗaya yayi stairs saboda yadda jini ya ɓalle mata ,tsabar yadda ta shiga ruɗu da razani.

Hannun Adeeb karkarwa yake ya kasa aikata komai,dan haka cikin sauri ya janyo ƙaton bargonsa ya lulluɓe fattu dashi,iya saman ƙirjinta zuwa kanta ya bari abuɗe.

Sosai ya tausayawa fattu lokacin da yake cire mata kwalaben nan,dan kuwa taji ciwo da yawa,ko yaya ya taba gurin da kwalbar take saita zabura kamar zata farfaɗo.

Haka dai ya gama cire mata kwalaben nan,tas yayi mata dressing ɗin duk inda ya kamata, ya sami ruwan zafi da towel ya goge mata jikinta .sai dai kuma ba wani kayan da pant da kuma pad ɗin dazai canja mata.
Dan haka rigarsa ya ɗauko fara ƙal ,doguwar ya zura mata, kafin ya dauko mata kayanta,dan kuwa yana tunanin ta dawo nan part ɗinsa da zama kenan. Ƙarin Ruwa ya sanya mata ,kafin ya nufi ƙofa, kai tsaye ya kulle ƙofar ya fita zuciyarsa kamar wuta haka yake jinsa,ya nufi part ɗin nanny.

"Tareeƙ na roƙeka kada kace zaka sanar da magajin faɗa komai ahalin yanzu,dan kuwa bamu da kwararan hujjoji akan hakan ,ka bari nan da lokaci kankanin shida kansa zai gano komai,zamu nuna masa hanya ta yadda zai fahimci abubuwa da dama" nanny ta faɗa tana rike da hannun tareeeƙ.

Umme wllh zuciyata zafi take,Aduk lokacin dana ga yallaɓai cikin wani halin,yana zagaye da maƙiya ,amma bai sani ba,shi yana zaune dasu zuciya ɗaya ....

"Su waye maƙiyan nawa?sannan wace gaskiyar ce ake boyemin?"
Suka tsinkayo Muryar Adeeb yana faɗin haka cikin sautin da ba wasa acikinsa.

Da sauri suka juyo gaba ɗayansu, dan basu tsammanci ganin Adeeb ɗin awannan lokacin ba.

"Magajin faɗa yaushe ka shigo?ya jikin naka?ina ɗiyata take ?"nanny ta faɗa cikin inda-inda da son n kawar da zancen.

Ƙura mata ido Adeeb yayi cike da tuhuma ,gaba ɗaya ta daburce.da alama akwai abunda take boyewa ita da tareeƙ .kallonsa ya dawo dashi kan tareeƙ wanda kansa ke ƙasa ,shi yaji dadin jinsu da Adeeb yayi,fatansa ɗaya ayi komai yau akare.

"Tareeƙ, what wrong me kuke ɓoyemin? Dama akwai Abinda zaka iya boyemin tareeƙ ?na dauke tamkar kanina da muka fito ciki daya,why tareeƙ?" Adeeb ya faɗa yana kallon tareeƙ.
Kallon nanny tareeƙ yayi,yana jin ba dadi cikin ransa,dama yasan watarana hakan zata iya faruwa,shi baiga amfanin biye boyen ba , amma suna haɗa ido da nanny tayi saurin girgiza masa kai,alamun karya ce komai.

"Tareeeƙ,am tolking to you me kuke hidden mini?kada kusa na fara zarginku fa,Please nanny,bayan ammina da abie, ku kadaine mutanen dana yarda dasu arayuwata,ku kaɗai ne waɗanda nake ganin bazasu taba cutar dani ba,karki karyamin zuciya nanny, Please me kuke ɓoyemin?" Adeeb ya faɗa cikin wata kalar murya mai cike da tsoron kar ace nanny da tareeƙ suma suna daga cikin maƙiyansa .

"Ka kwantar da hankalinka magajin faɗa,wllh har abada bazamu taba cutar da rayuwarka ba,saidai mu bata kariya, amma kasani akwai mutanen da kake kallo matsayin maƙiyanka,saidai sam,ba haka abin yake ba. azahiri kake ganinsu matsayin maƙiya,amma abaɗini sune masoyanka na haƙika.
Su kuma wadanda kake kallo matsayin masoya,suke son ganin bayanka, sune waɗanda suke cin dunduniyarka,Adeeb ka kula kazamo mai lura da mutanen da kake tare dasu " nanny ta faɗa tana mai riƙe da hannun Adeeb,fuskarta ɗauke da damuwa.

Kallonta kawai Adeeb keyi,tunda ta fara maganarta ,me take nufi kenan?su waye ya yarda dasu ,kuma suke cin dunduniyarsa?
Sannan suwaye yake wa kallon maƙiya ,alhalin sune masoyansa na asali?kallon nanny yayi cike da tarin tambayoyi zuciyarsa na harbawa da gudu.

"Nanny ban fahimceki ba,me kike nufi da kalamanki? Please kiyimin bayanin da zan gane"Adeeb ya faɗa yana kallon nanny,idanunsa sun kada sunyi jajur dasu.

Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe mai ƙarfin gaske,sannan tace magajin faɗa ,idan baka manta ba,shekaru kusan sha takwas mijina da kuma gimbiya nazli sunyi haɗari suka mutu,sanadiyyar wuta data kama motar da suke ciki,harda yaranta mata su biyu,nanny ta faɗa tana kallon Adeeb,

Runtse ido Adeeb yayi da mugun ƙarfi,har abada bazai taba mantawa da wannan baƙar rana ba ,ranar data zamo mafi muni arayuwarsa.

Bude idonsa yayi wanda suka cika da kwalla yana kallon nanny kafin cikin rawar murya yace " tabbas nanny bazan taɓa mantawa da wannan rana ba,domin itace rana mafi muni arayuwata" ya faɗa yana mai lumshe idanunsa hawaye suka ziraro sharrrt.

"To kasani wannan haɗarin ba afkuwa yayi ba ,shiryashi akayi" nanny ta faɗa tana mai kallon Adeeb ,

Azabure Adeeb ya bude idanunsa,da suka gama zama jajur dasu,kallon nanny yake cikin kiɗima da ruɗewa" nanny kamar ya ban gane ba,me kike nufi da shiryashi akayi?waye ya shirya?kuma meye dalilin shiryawa?"Adeeb ya faɗa aruɗe.

Kamo hannunsa nanny tayi ta zaunar dashi akan kujera dan kuwa gaba ɗaya jikin sa rawa yake.
"Tareeƙ maza jeka kulle mana ƙofar nan"nanny ta faɗa cikin damuwa.
Ahankali tareeƙ ya nufi ƙofar tare da kullewa, yana jin sanyi aransa,koba komai yau zasu sauke nauyin da yayi musu bake bake acikin zuciya.

" Nanny kiyi saurin sanar dani, domin zuciyata gab,take da tarwatsewa,dan kaɗuwa" Adeeb ya faɗa cikin tsantsar zaƙuwa .

Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace " ina son ka saurari maganata da kunnen basira ,sannan kayi min kyakykyawan fahimta,kasani bazan taɓa cutar da kaiba, kuma duk abinda nayi nayine don tsiratar da rayuwarka" nanny ta faɗa hannunta riƙe dana Adeeb.
"Please nanny go street to the point kina kara sani cikin wasi-wasi" Adeeb ya faɗa cikin muryar damuwa ,jikinsa na rawa ,ba abinda yake son ji sai wanda ya shirya wanann haɗarin.

Mikewa nanny tayi tare da zuwa jikin window ta tsaya ,kallon Adeeb take tare da karantar yanayinsa, kamar yadda shima yake kallonta cike da ƙosawa.

Ahankali ta buɗe baki tace"ba kowa bane ya shirya wannan hadarin face ..........


Wayyo masu karatu cajina ya kare ,amma karku damu mu tara anjima,
Nice dai anty mammynku.


Mrs babi💘💘

Share and comment fisabilillah.

More comment
More typing.
[8/23, 9:06 PM] +234 813 465 3007: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄


MACIJI NE 🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)


Elegant online writers📚📚


Free book

Page 59/60




________________Ahankali nanny ta ke kallon Adeeb,kafin ta sauke ajiyar zuciya,tunani take ta yadda Adeeb zai karbi wannan magana,ta yaya zata sanar dashi cewar,amminsa itace silar faruwar komai?shin zai amince da abinda zata faɗa masa ko yaya? Wane irin kallo zai musu idan yasan cewa amminsa ce ta kashe sarauniya Nazli da yaranta tare da baban tareeƙ,kuma abakinsu?anya kuwa basu barowa kansu aiki ba?
"Nanny kiyi magana mana kinyi shiru, ki sanar dani wake da hannu akan hadarin nan?"

Da sauri nanny ta dawo daga dogon tunanin data tafi,kallon tareeƙ tayi cike da karayar zuciya ,amma cikin ƙarfafa gwuiwa tareeƙ ya kalli nanny yana mai jinjina kai da nuna alamun ,kwantar da hankali.
Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe Tana mai kallon fuskar Adeeb,kafin ta fara magana.
"Magajin fada kamar yadda na faɗa maka,wasu abubuwan muna kallonsu ne ba a yadda suke ba,ka sani abinda zan faɗa maka ba ƙarya ,ba kuma cutarwa.shiru ta ɗanyi tana jinjina maganar kafin taci gaba"ba kowa ya shirya wannan hadarin ba, face Amminka"nanny ta faɗa tana mai kure Adeeb da ido.

Da wani irin slow Adeeb ya mike tsaye bakinsa bude,zuciyarsa na wani irin bugawa kamar guduma, ji yayi kunnensa ya ɗauki wani ƙara ƙuuuuuuuu!!!
Sai yake jin maganar ta nanny Tana rarrabewa,kamar baiji me take faɗi daidai ba,jikinsa rawa ya kama,ta yadda yana mikewa tsayen yaji kamar zai fadi dan haka da sauri ya koma ya zauna,idanunsa ƙuri,akan fuskar nanny,
Cikin in-ina ya ke cewa"na...nan.,...y mek....Ike ..son....f..a...ɗ..I n..ee." ya faɗa numfashinsa na rarrabewa,ji yake kamar zuciyarsa zata fito tsabar yadda take bugawa.

Da sauri nanny ta ƙaraso kusa da Adeeb ta zauna ,cikin nutsuwa take shafa bayansa tare da kallon fuskarsa cikin tausayawa,dole yaji maganar tazo masa kamar saukar aradu."ka nutsu Adeeb domin Abinda nake faɗa maka yana buƙatar nutsuwa,tabbas Amminka itace ta shirya wannan hadari,tare da taimakon wani ma aikaci dake cikin gidan nan,mai kula da harkokin motocin gidan"nanny ta faɗa cikin sanyin murya tana jin zafin rashin mijinta da uwar dakinta kamar yau abin ya faru.

Kallonta Adeeb yake cikin wani irin yanayi na mamaki ,al'ajabi,tsoro,ruɗu dakuma firgici,ji yake kamar zuciyarsa zata iya fashewa ako wane lokaci,wannan wane irin magana nanny keyi?anya kuwa tana cikin hayyacinta?yaushe nanny ta koma maƙiyarsa ta hanyar hade kai da amma?dan su shiga tsakaninsa da amminsa? Dan kuwa yana tabbatar da cewa wannan shirin amma ne,lallai duniya ba tabbas .cikin zuciyarsa yake wannan maganar,kafin a fili ya kalli nanny ,sannan ya kalli tareeƙ,sai kuma yayi murmushi wanda yafi kuka ciwo ,sannan ya miƙe tsaye yana mai sanya hannunsa cikin aljihu,sannan ya fara magana bayan ya juya bayansa yana kallon bango" ban taba tsammanin cewa matar data raineni tun ƙuruciya zata iya hade kai da makiyana,ɗan ganin sun shiga tsakanina da ammina ba ,yau na
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment