Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

wanda har bata san lokacin da ta biye masa ba itama,duk abinda yayi mata, itama shi take masa.basu rabu da juna ba har saida Adeeb ya samu nutsuwa sosai.kafin suka daure suka rabu da jikin juna,sai lokacin fattu ta fahimci ko kaya babu ajikinsu.kunya ce ta kamata,da sauri ta janyo bargo ta rufe jikinta tare da lumshe idonta.

Murmushi Adeeb yayi yana mai gyara mata gashin kanta daya barbaje,kafin yace "Hulwa meye kuma na rufe ido?nifa bana son wanna kunyar taki,Please ki buɗe ido ki kalleni,kinji?"ya faɗa yana hura mata iska akan idanunta.
Cikin wani irin salon murya mai cike da nishadin soyayya tace "Hamma Ni wllh kunya nakeji,kayi ta gane min jiki"ta faɗa ahankali tana rungumeshi.

Rungumeta shima yayi cike da soyayya kafin yace "hulwata idan ban kalli jikin ba,jikin wa zan kalla?jikinki mallakina ne,shine abinda zan kalla ya debemin kewa dan Allah karki hanani kallon abinda ke sani nutsuwa" ya faɗa cikin salon sa na shagwaba yana ɗan turo baki.

Murmushi fattu tayi tana mai kara cusa kanta akirjinsa,cike da kaunarsa.
Gaba daya sun shagala da nunawa juna soyayya,sun manta da su, Sultan Habib dake jiran fattu,saida wayar Adeeb tayi kara sannan suka farga,kiran Abie ne dan haka cike da kasala ya mika hannu ya daga wayar,
"To Abie gamunan "kawai ya faɗa tare da kallon fattu yace "Hulwa su anty na jiranmu"ya fada kamar zaiyi kuka.

Da sauri fattu ta mike tana zaro ido,wllh sam ta ma manta da batun tafiya Ghana,gaba ɗaya Hamma ya mantar da ita komai da soyayyarsa.
Shagwabe fuska tayi tana mai faɗin"Hamma kaga kasa na manta da su inna suna jirana ko?"ta fada tana nufar toilet da sauri tana tafe tana bubbuga kafa,ciki da tabara.
Lumshe ido Adeeb yayi yana mai faɗin "wayyo hulwata,zaki kasheni da salonki"kafin ya bita toilet din,wanka sukayi tare sannan suka fito,da kansa ya shirya fattu,kafin ya haɗa mata kayan da yasan zata bukata,sannan suka fito.

Haka Adeeb da Hulwa suka rabu cike da kewar juna,Adeeb ji yake kamar yayi kuka.

Tunda fattu ta tafi Ghana,kullum sai su wuni suna waya da Adeeb,sosai yake nuna mata yadda yayi kewarta,ita kuwa tausayinsa duk ya gama kamata,ba abinda yake son ji da gani sama dashi.saidai tayi tararrashinsa,tun tana kunyar fada masa kalamai harta zo ta daina,take zagewa tana nuna masa soyayya.

Ba irin gatan da fattu bata ganiba,agurin iyaye da danginta,kowa sonta yake,yana riritata,gyara kuwa tunda suka zo innarta ke fama,an tsuma fattu sosai,ta yadda da kanta wataran take jin tana bukatar Adeeb akusa da ita.
Tayi kyau jikinta ya kara gogewa,kallo ɗaya zaka mata kasan tana cikin jin dadi da annashuwa,komai yaji ajikinta.

Satinta biyu a ghana Adeeb ya kasa daurewa ya shirya kayansa yace ya tafi Ghana.
Amagarkama kuwa,lamarin ammi ya gwabe sosai,dan kuwa zuwa yanzu bai zama lallai ka gane ta ba,wasu abubuwa take tamkar na mahaukata,tayi ta ihu kenan tana faɗin irin abubuwan da ta aikata,ƙafarta ɗaya ta lalace sakamakon ciwon da taji,banda wasu irin kuraje da suke fito mata masu tsananin karni da doyi.haka zatayi ta ihu tana yagunin jikinta.duk wanda yazo inda take,da gyar yake iya tserewa dan kuwa hauka take sosai,tana dukan mutane.hakan yasa aka kulle gurinta,saidai atura mata abinci ta kasan kofa.

Waziri kuwa,an yanke masa hukumcin daurin shekaru arba'in agidan yari, yayi nadama sosai kullum cikin kuka yake da neman gafara.

Rashad kuwa zuwa yanzu jiki alhamdullah,dan sosai yaji sauki walwalarsa ta dawo, Amma ma hankalinta ya kwanta sosai take kula da abie,abin sai godiyar Allah.

Ranar da Adeeb ya sanar da zuwansa Ghana,ba ƙaramin farin ciki fattu tayi ba,murna sosai takeyi har saida innarta ta fahimta,shiri akayi mata na musamman,cikin shiga irin ta ya'yan sarakuna, tayi matukar kyau kamar kasace ta ka gudu,sai ƙamshi take zubawa,gashi tadanyi kina kwanin sha'awa.

Wani kayataccen daki aka sauki Adeeb,ko ina yayi fes sai ƙamshi ke tashi,an jere masa kayan ciye- ciye,amma ko ruwa ya kasa sha,burinsa kawai yayi tozali da hulwarsa.

Wani sihirtaccen kamshine ya bugi hancinsa,wanda ya sanya shi saurin ɗago kai,cikin hanzari ya mike tsaye tare da kafe fattu da lumsassun idanunsa,wadanda ke cike da tarin gajiya da bukatar fattun tare da kewarta.

Murmushi take sakar masa cike da shaukin ganinsa.tana takawa kamar wata tarwada.

Cikin wani irin salo da zaƙuwa Adeeb ya bude mata hannayensa,alamun ta taho gareshi,da sauri ta ƙaraso tare da fadawa jikinsa,shikuma ya mayar da hannunsa ya rungumeta tsammm.


Muje zuwa masu karatu.

Mrs babi ce💘💘

Share and comment fisabilillah.

More comment
More typing.
[8/28, 1:34 PM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄



MACIJI NE🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚



Free book

Page 87/88




_______________Cikin wani irin mugun bugawar zuciya, abie ya bude bakinsa dake rawa yace "wa.....z..ii..rr"sai kuma ya kasa ƙarasawa, sakamakon numfashinsa daya dauke.nan ya zube gurin asume.

Cikin hanzari Adeeb da su Sultan Habeeb,sukayo kansa.
"Abie !abie!!Adeeb ya kira sunan Sultan yana jijjigashi.amma ko motsi bayayi,da hanzari suka zareshi suka nufi part dinsa dashi,suna zuwa likitocinsa suka rufu akansa.

Zulaihat ma asibitin cikin masarautar aka nufa da ita kai tsaye,sosai ta galabaita,dan jini sai zuba yake ta bakinta,kamar ma aman jinin take,

Queen Suhaimat,na riƙe da hannun ɗiyarta gam, dan bazata ƙara bari,fattu tayi nisa da itaba in Sha Allah.
Amma ma tabi su Adeeb dan ganin ya jikin Sultan ɗin.
Dan haka nanny ke tura keken Rashad suka fice daga ɓangaren Ammi,kai tsaye bangaren Sultan suka nufa suma,dan hankalinsu yaki kwanciya,suna buƙatar ganin ya jikin nashi.

Cikin ikon Allah kuwa aka samu Sultan ya farfaɗo,saidai banda hawaye ba abinda idanunsa keyi.
Damuwarsa ta ninka ta farko,wannan cin amana da me yayi kama?ace dan uwanka ma baka wuce ya cutar da kaiba,yanzu dama za'a iya hada baki da waziri acutar da rayuwarsa,dashi ake ƙoƙarin kashe masa gudan jininsa?lallai yau da iyayensu suna raye tabbas ba abinda zai hana zuciyoyinsu bugawa.
Duk irin so da ƙaunar daya nunawa waziri,amma ƙarshen halaccin da zaiyi masa kenan?yana tare dashi, komai nashi waziri,ko wace shawara dashi yake,ashe shikuma yana amfani da wannan damar ne yana cin dunduniyarsa?kai rayuwa Allah ya shige mana gaba.

Adeeb ne ya,zauna kusa da mahaifin nashi, tare da riko hannunsa yana kallon idonsa,cikin tattasan lafazi yake rarrashin Sultan"abie dan Allah ka kwantar da hankalinka,Ni dama najima ina zargin uncle,kuma koda muka shiga part din Ammi,Ina kallon lokacin daya zare jiki ya bar part din,Dan haka nayi saurin bada umarnin akamoshi dan dama tuni na shirya komai,yanzu haka yana hannu"Adeeb ya faɗa cikin sanyin murya yana murza hannun abie cikin nutsuwa.
Ajiyar zuciya Sultan ya sauke tare da lumshe ido,kafin ya buɗe su.
"Habeebee mutanen dana yarda dasu,su suka cutar dani,nayi dana sanin kasancewarsu makusantana,kuma na gode Allah dayasa bani da zuri'a da Ammi,da ta gurbatamin zuri'a da mugun iri,Allah Sarki matata Nazli,Allah ya jiƙanki yayi miki rahama,tare da yarana da kuma amintaccen driverna"abie ya faɗa cikin zubda hawaye yana jin zafi cikin zuciyarsa.

Haka su Adeeb da baban fattu sukayi ta rarrashinsa akan ya kwantar da hankalinsa,karya sanya damuwa cikin ranshi har yazo ya samu matsala babba.

Barcine ya dauke Sultan,dan haka suka fito zuwa babban falo,suka zauna dan tattauna yadda za'ayi.

Fattu na zaune kusa da mahaifiyarta,ta ɗora kansa akan cinyar innarta,wani irin nishaɗi da jin dadi takeji cikin ranta,wai yau itace tare da mahaifanta, lallai duk wanda ya mika lamuransa ga Allah,to tabbas zai ga daidai arayuwarsa.
Queen Suhaimat ma cike take da farin ciki,zuciyarta fess,ahankali take shafa kan fattu cike da tsantsar ƙauna,itakam tayiwa Allah godiya da wannan ni'ima da yayi mata,yau gata ga zaranta bayan shuɗewar shekaru masu yawa,ita dama bata taɓa cire rai da tsammani ba.
Suna nan zaune saiga su Adeeb sun fito daga cikin dakin,yana tura keken da Rashad ke kai,dan suna zuwa falon shima ya shiga gurin mahaifin nasu.
Tunda suka fito idon Adeeb yana kan fattu,kamar yadda itama take kallonsa,tana jin wata irin kaunarsa na ratsa dukkan sassan jiki da jininta,haƙiƙa Adeeb ya zame mata alkairi,haduwa dashi nasarace,kuma in sha Allah zata kula dashi,zata nuna masa soyayya ta gaskiya cikin amana da girmamawa.

Murmushi Adeeb ya sakar mata tare da dan shagwabe fuska,irin na nayi kewarki ɗin nan,itama murmushin ta sakar masa tare da lumshe ido alamun rarrashi,kamar yadda yake mata.
Zama yayi kan kujerar dake saitin wacce Queen suhaimat ke zaune,ta yadda zai rinƙa kallon fattunsa.
Duk abinda sukeyi nanny na kallonsu,murmushi kawai tayi tare da girgiza kai.
Queen Suhaimat ce tace "ya jikin Sultan ɗin?"
"da sauki jikinsa kam,yanzu haka yayi barci ma"Adeeb ya bata amsa cikin girmamawa.
Wayar Adeeb ce tayi ƙara, ta jikin agogonsa, dagawa yayi tare da cewa ku "shigo dashi ciki"
Ya kashe wayar.
Ko minti biyar ba'ayiba saiga wasu dakarun fadar sun shigo da waziri yana gaba suna binsa abaya,yayi tsilli tsilli da ido,kunyar duniya ta gama lalata masa zuciya,
Durkushewa yayi atsakiyar falon kansa aduƙe,yana jin kamar ƙasa ta tsage ya shige ciki.
Kallonsa kawai suke cike da alhini da jinjina rashin amana irin na waziri.
Adeeb ne ya miƙe cikin nutsuwa ya nufi gaban waziri,tsayawa yayi tare da sanya hannu cikin aljihun wandonsa, ya kafe waziri da ido,na tsawon lokaci kafin ya nisa ya fara magana"uncle ka bani mamaki,ka sanya zuciyata tunanin cewar lallai mutane ba abin yarda bane,uncle me muka tsare maka arayuwa?me nayi maka kake son ganin bayana tare da mahaifina?uncle me ka nema agurin mahaifina bai maka ba?uncle yanzu da kai za'a hada baki ɗan ganin bayan dan uwanka? Uncle why ?yaushe kazama haka?yaushe ka bari shaidan yayi nasara akanka?har idanunka suka rufe kake cutar da wanda ya aminta dakai sama da kowa?"Adeeb ya faɗa cikin salon sa mai sanya mutum shiga taitayinsu.

Kuka kawai waziri ya sanya tare da kamo ƙafar Adeeb"kayi hakuri dana,ka yafemin wllh sharrin zuciya dana shaidan ne suka sanyani aikata wannan abubuwan,da kuma kwadaituwa da son hawa karagar mulki,dan Allah ku gafarceni"ya faɗa cikin kuka sosai yana riƙe da kafar Adeeb.

Lumshe ido Adeeb yayi zuciyarsa na masa zafi sosai haƙiƙa abubuwan da su uncle suka aikata shida Ammi,sun cancanci hukunci,dan haka dole ahukuntasu.

Cikin salon sa na haɗe rai yake kallon uncle kafin yace "menene gaskiyar al'amari akan asirin zama maciji da akayi min ?"cewar Adeeb kenan yana kallon waziri.

Ɗago kai waziri yayi cikin zubda hawaye,yace "tabbas bazan boye maka ba,nine nan nasa akayi maka asiri ka zama maciji,domin farko nayi niyar ka auri yata Zulaihat,inyaso inbata guba ta sanya maka cikin abinci kaci ka mutu,sai kuma ka nuna rashin amincewa da auren Zulaihat,wannan shine ya kara tunzurani,naje gurin boka aka hada maka zazzafan asiri da kalolin macizai na duniyoyin aljanu da ban daban,wanda idan ka bar fadar nan,shikenan ka barta har abada,kuma nine da kaina na daukeka na kaika can yankin Nigeria,dan ko ganin ka bana sonyi kusa da fadar nan"waziri ya faɗa yana hawaye.

Salati gaba ɗayansu suka dauka,kowa yana Allah wadai da waziri,saboda son zuciya da abin duniya,yake kokarin hallaka dan dan uwansa.
Runtse ido Adeeb yayi cike da kumar zuciya,yama rasa me ya kamata yayi.
Daga bakin ƙofar dakin abie sukaji magana yana faɗin"waziri ka cuceni ka ci amanata ka yaudari soyayya irin ta yan uwan taka,me nayi maka haka da zafi ?kake son ganin bayana?duk irin kulawa da soyayya irin ta yaya da ƙani dana nuna maka,amma yau kaine ke son ganin bayana?kaje dan kanka,duniya zata koya maka hankali,kuma ko yanzu kasan Allah shine ke da iko akan kowa,dan gaka a ƙasa Ni kuma da iyalina muna samanka"abie ya faɗa cikin zubda hawaye yana dafa bango.

Da sauri Adeeb yayi gurinsa tare kamo hannunsa ya zaunar dashi akan kujera.
Cikin kuka waziri ya rarrafo gurin mai martaba yana bashi hakuri,
Suna cikin haka Tareeƙ ya shigo cikin dakin da sauri .
Duk waigawa sukayi suna kallonsa,
Cikin girmamawa yayiwa Sultan sannu da jiki,kafin ya isar musu da saƙon mutuwar Zulaihat .
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,shine abinda Dukansu suka haɗa baki gurin faɗa.
Shikenan Zulaihat ta riga mu gidan gaskiya,Allah ya yafe mata kurakuranta.
Waziri kuwa daskarewa yayi azaune jin labarin mutuwar ɗiyar tasa guda ɗaya tilo,
Ihu ya sanya tare da faduwa agurin yana birgima...


Mu hade anjima.
Mrs babi ce💘💘

Share and comment fisabilillah.

More comment
More typing.
[8/28, 7:54 PM] +234 906 568 0805: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄



MACIJI NE🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚



Free book

Page 91/92






_____________Cikin wani irin salo wanda ke nuna tsantsar farin ciki da zaƙuwa,Adeeb ya bude hannayensa,alamun fattu ta taho gareshi.
Da sauri fattu ta ƙaraso gareshi,cikin takunta mai jan hankali,tare da fadawa jikinsa tana murmushi.
Maida hannunsa yayi ya kulle tare da rungume fattu tsamm,ajikinsa.

Atare suka sauke ajiyar zuciya,wacce ke nuna tsantsar kewar juna da sukayi.
Banda ajiyar zuciya ba abinda Adeeb ke saukewa,kamar wanda yayi wasan tsere.
Ahankali cikin murya mai tattare da shauki yace "I miss You so much Hulwa"ya faɗa yana kare matseta akirjinsa,kamar zai maidata cikinsa.
Kusan minti biyar suka dauka ahaka,kafin Adeeb yayi karfin halin ɗago da fattu daga jikinsa yana kallon kyakykyawar fuskarta.gani yake kamar ba fattunsa ba,kamar wanda aka sauya masa ita,tayi kyau matuka,ta kara gogewa kai kace acikin ƙanƙara tare rayuwa.

Fattu ma kallonsa take cike da jin zazzafar kaunarsa na ratsa jini da tsokarta,dan gani tayi yayi mata kyau sosai,ya ɗanyi kiba kaɗan ya kara fari,ga sajen da ya kara ajiye wa yayi matuƙar ƙawata fuskarsa.

Ahankali ta kai hannunta tare da shafa gefen fuskarsa,lumshe ido yayi yana mai jin sanyi cikin ransa.cike da son nunawa Adeeb yadda tayi kewarsa ta kai bakinta kan nashi,ta fara kissing dinsa,kawai sai jin bakin fattu yayi cikin nashi.

Ai kamar mayen karfe haka Adeeb ya karbe lips din fattu ya fara sha kamar ya sami lollipop.
Tun abun yana karami har yazama babba,dan sun kasa rabuwa da juna,ganin suna neman faduwa ne yasa su zubewa akan lafiyayyar kujerar dake kusa dasu.adeeb bai bar wannan dama ba ,saida ya kara angoncewa, sosai ya shiga ruɗu da gigita,ɗan jin fattu yayi kamar bai taba ma saninta matsayin ya mace ba,sosai ya nishadantu da ni'imarta,ya rikice mata sosai haka yayi ta sunbatu yana hawaye.albarka kuwa fattu ta shata ba adadi da kyaututtuka kala kala.
Saida suka sami nutsuwa kafin Adeeb ya samu yaci abinci.anan dakin sukayi wanka tare,gaba ɗaya Adeeb ya kara kwarewa fattu,ko yaya tayi motsi hankalinsa na kanta,wani irin so yake mata marar misaltuwa.fattu duk da taji zafi amma haka ta daure bata nunawa Adeeb raki ba.nan suka shantake suna nunawa juna so da kauna,dama tuni Adeeb ya mika gaisuwa ga Sultan Habib da innar fattu.
Dan haka salla ma acikin dakin nan yakeyinta. Fattu kuwa ranar ta yabawa aya zaƙinta,dan ta tabbatar da cewar Adeeb yayi kewarta,kuma shidin jarumi ne na gaske.

Washe gari suka tashi daga Ghana zuwa Nigeria,da tareeƙ akayi tafiyar,dan dama tare suka zo da Adeeb,shiya sauka a masauki na daban.
Kai tsaye a Jos suka sauka,kafin suka nufi kauyen su fattu cikin dalla dallan motocinsu.
fattu da Adeeb cikin mota daya suke,yana rungume da ita ajikinsa,motar su ce agaba,ko kaɗan fattu bata manta hanyar kauyen nasu ba,dan haka tana lura da inda suke nufa.

Sai motar Sultan Habib shida innar fattu dasu zayyad.

Kauyen yana nan inda fattu ta sanshi, ba abinda ya sauya.gidansu ta fara hangowa,cike da doki take nunawa Adeeb gidan"Hamma ga gidanmu can,yanzu zanga baffana,Hamma bazan iya kwatanta irin farin cikin da nake ciki ba"fattu ta faɗa tana rike hannun Adeeb cike da murna idanunta ya cika da kwalla.
Murmushi yayi,dan shima saiya tsinci kansa cikin farin ciki, ganin yadda Hulwarsa ke farin ciki.
"Nima ina farin ciki Hulwa zataga baffanta,saidai anya kuwa zai gane ki?Adeeb ya faɗa yana kallonta da murmushi.
Cikin doki da dariya fattu tace "wllh zai ganeni,ko me nazama na tabbata baffana zai ganeni kuma zaka gani"ta fada daidai lokacin da sukayi facking akofar gidansu fattu.

Da hanzari fattu ta buɗe kofar motar ta fito,bata ko tsaya sauraron Adeeb ba,burinta kawai tayi tozali da baffa.da sallama ta shiga cikin gidan tana rarraba ido dan ganin ta inda zataga baffanta.
Ba kowa cikin tsakar gidan,gaba ɗaya gidan yayi datti,ko ina kazantace cikinsa.jin sallama yasa gwogwgo hansai fitowa daga cikin dakinta,tana ta soshe soshen kwarkwata.
"Waye yau agidan nan nawa?rabon da naji wani yazo gidan nan,harna manta,kodai Hau......maganar gwogwgo hansai ta makale sakamakon ganin wata balarabiyar yarinya da tayi tsaye fuskarta ɗauke da murmushi.
Cikin rawar jiki gwogwgo hansai ta fara fadin"maraba lalle baiwar Allah,daga ina?wa kike nema kodai gidan mai gari kike nema?"gwogwgo hansai ta fada cikin rawar jiki tana kallon fattu.

Dariya fattu tayi tana kallon gwogwgo Hansai,duk ta rame tayi baki sosai gashi ta tsufa,kallo ɗaya zakayi mata kasan tana cikin wahalar rayuwa.
"Gwogwgo,baki ganeni ba ?nice fa,nice fattun baffa"fattu ta faɗa tana kama hannun gwogwgo Hansai ba tare da gyama ba.
Galala gwogwgo tayi tana kallon fattu,cike da ƙaryata abinda fattun ta fada,saidai kuma wa yasan fattun awani guri?bare yazo yayi mata wasa.cikin rawar murya tace "fa....t.t.tu,kece haka ?kece kika zama kamar balarabi?ina kika je kika zama mai kudi haka?ta fada tana shashshafa fattu.
Dariya fattu tayi kafin tace" nice gwogwgo tare muke da iyayena fa da hammana,suna waje bari nace su shigo,wai ina baffana ne tunda na shigo nake nemansa"fattu ta faɗa cike da doki tana nufar waje.

Lokacin da ta fita atsaye ta tarar da itayenta da Adeeb,mutanen garin sun zagayesu suna kallonsu da shafa motar da suka fito daga ciki.
Bata damu da mutanen gurinba tacewa su Adeeb su shigo.
Murna take sosai kamar wacce akayiwa bushara da gidan aljanna.

Gwogwgo Hansai jiki na rawa ta shimfida musu wata rubabbiyar tabarmar kaba.ko kaɗan basu nuna mata gyamaba suka zauna.
Bayan gaishe gaishene, gwogwgo tayi ta kuka tana bawa fattu hakuri,itadai fattu burinta daya taji ina baffanta yake.
Nan gwogwgo Hansai ta sanar da ita duk abinda ya faru da baffa,ranar da suka bar garin.
Kuka sosai fattu ta sanya,tana jin wani irin kunci cikin zuciyarta,ina zata ga baffa?mutumin daya tallafi rayuwarta ,ya bata kulawa,wayyo Allah.haka fattu tayi ta kuka,ajikin Adeeb yana rarrashinta.
Gwogwgo Hansai cikin nadama take faɗin"bayan tafiyar malam,gaba ɗaya lamari ya lalace garin nan,kowa abinda yake so shi yakeyi,haka inaji ina gani,yarana mata sukayi cikin shege,yanzu haka bansan duniyar da suka shiga ba,shima namijin tuni ya zama rikakken barawo,yayiwa yar mutane fyade shine ya gudu,ya bar rugar nan.mai gari yana nan ya zama gurgu,jauro kuwa abarsa ta lalace har yanzu bata da amfani,haka haroji yana na da fuska kamar ta dodo,saidai yaje Bara cikin gari,dan Allah fattu ki yafe mana ,nasan hakkinkine ke bibiyarmu"gwogwgo Hansai ta fada cikin kuka.
Haushin ta sosai Adeeb yakeji,dan yasan kadan daga cikin mugayen halayenta.
Tashi sukayi domin barin rugar,dan bawani amfanin zamansu,tunda wanda suka zo gurinsa baya nan.

Kudi mai yawa sultan habib ya bawa gwogwgo hansai,sai murna take tana godiya,haka ya tabawa mutanen kauyen ma kafin suka bar garin.

Kuka sosai fattu keyi ajikin Adeeb,ta shiga damuwa mai tarin yawa,haka yayi ta rarrashinta,har suka iso cikin garin jos.

Wata babbar motace tayi faci akan tsakiyar kwalta,hakan ya haddasa go slow agurin,suna tsaye cikin mota,masu bara sai zuwa suke suna Bara.
Wani dattijone cikin shiga ta almajirai,kallo ɗaya zakayi masa kasan yana shan wahala yazo jikin motar su fattu yana Bara,kasancewar gilas din motar irin mai duhun nan ne,yasa na waje baya ganin na ciki.

Fattu ce tayi firgigit tatashi daga jikin Adeeb tana kallon tsohon dake barar.
Wani dan ihu ta sanya tana mai ƙoƙarin buɗe kofar motar.kira take
"Hamma baffana,baffana"tana faɗa cikin rawar jiki tana kokarin buɗe motar.
Da sauri shima Adeeb ya kai kallonsa inda fattun ke nuna masa.
Tabbas baffa ne kuwa.gana ɗaya fattu ta rikice tana kici kici buɗe kofar Amma tsabar farin ciki tama kasa,budewar sai kira take"baffana,baffana"
Hannunta Adeeb ya riko yace "ki nutsu hulwa,karkije kiki ciwo kinji bari muje gurin baffan"ya faɗa yana bude kofar motar.
Da sauri fattu ta fito daga cikin motar ta nufi gurin mutumin da yayi dan gaba dan zuwa wajen wata motar ya sami sadaka.
Da sauri ta kamo hannunsa tana faɗin "baffana kaine,haka ?"cikin azama baffa ya juyo sakamakon jin Muryar da akullum saiyayi kukan rashin ta,kuma duk kuɗin da yake samu na bara tarawa yake,dan yayi ta zaga garuruwa yana neman fattu,yasan watarana zasu hadu.
Jifa yayi da dan buhun dake hannunsa,wanda yake tara kudin barartasa ciki.
"Fattu,kece"baffa ya faɗa cike da shauki.
Kuka fattu keyi tana kallon baffa,kafin ta rungumeshi ajikinta tana kuka.shima baffa kuka yake cike da godewa Allah,yau gashi ga fattunsa,shikenan burinsa ya cika.
Sultan habib,da innar fatyu ma,fitowa sukayi,dan kobasu tambaya ba,sunsan wanna shine baffan fattunsu.
Adeeb kansa saida yaji kwalla ta cika masa ido,dan tausayin tsohon da yadda ya koma.

Horn din da motoci ke musu ne ya dawo dasu cikin hayyacinsu,dan tuni an janye motar data haddasa go slow ɗin,dan haka cikin hanzari suka shige mota dan ba mutane hanya.
Motar su fattu baffa ya shiga,su Sultan ma suka koma cikin tasu ,sannan suka bar gurin.

Kai tsaye gidan da suka sauka suka koma,dan yau suke don komawa Ghana,
Fattu sai murna take daga ga baffanta.
Wanka kawai suka bari baffa yayi,aka bashi wasu kayan ya sanya,kafin suka daga sai Ghana....

Masu karatu bari muyi musu rakiya zuwa ghanar muma.



Ina kuke
Masoya anty mammy?

Albishirinku,ina mai farin cikin sanar daku,sabon littafina mai suna RAINON DAWA,yana nan akan hanya,da zarar mun kammala MACIJINE,hmmmm
Daga jin sunan kinsan ba magana.

Karku bari abaku labari.
Ga mai bukata ,zai iya biyan kudinsa tun yanzu,domin nan da kwana uku zaku fara samun wannan kayataccen labarin na RAINON DAWA.

akan fashi mai sauki,

Normal group 300

Special group 500

Sannan akwai manyan mata dake son atura musu private to kuma ga naku farashi,1000
Dan haka saina jiku,

Acc. No.
Saratu kabir
A.u.b
2215749011


Saiku nuna shadar biya ta wannan no.
08148360851


Saina jiku,masoya.

Show ne your love akan novel ɗi Nan,
😍😍😍🥰🥰🥰🥰

Mrs babi ce💘💘
[8/29, 10:26 AM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄



MACIJI NE🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚


Free book

Page 93/94





_______________Ko a cikin jirgi fattu na kusa da baffanta,wanda yayi tsuru cike da tsoron jirgin,dan kuwa wannan shine karon farko daya hau jirgi.amma haka fattu ke kwantar masa da hankali har suka ƙarasa Ghana.
Part guda aka warewa baffa wanda ke dauke da duk wani kayan more rayuwa.baffa ya cika da farin cikin ganin irin rayuwar jin dadin da fattunsa keyi.abinci kala kala aka ajiye masa,har yama rasa wanda zaici.haka fattu keta zuba masa abincin tana tura masa.

Saida ya huta sosai nutsuwarta ta dawo jikinsa, sannan aka taru apart din da aka saukeshi, har Sultan Habib.godiya suka farayiwa baffa,bisa irin taimakon da yayiwa rayuwar yarsu,sannan suka ce suna bukatar yayi zamansa anan gurinsu,tunda bashi da kowa acan Nigeria.
Kuka kawai baffa keyi na gani yadda bayin Allah nan ke karramashi, suna son ya kasance tare dasu,amma wadanda ya taso cikinsu,haka suka koreshi korar kare bayan sun karbe masa dukiya.
Fattu ce ta dan turo baki tana kallon innarta da mahaifinta,kafin tace "Ni gaskiya ban yarda baffana ya zauna anan ba,tare zamu tafi dashi can gida,bana son yayi nesa dani,kuma shima yafi son zama kusa da fattunsa ko baffa"fattu ta faɗa cikin salon shagwabarta.

Murmushi baffa yayi,yace kwarai kuwa fattun baffa,duk inda kike to Nima Ina can koda kuwa cikin dokar dajine"baffa ya faɗa cikin murmushi.
Dariya sukayi suma,kafin mahaifin fattu yace "wato dai zara kin kwace mana baffanki ko?"ya faɗa da murmushi akan fuskarsa.
Dariya fattu tayi kafin tace "Allah ba haka bane daddy nayi kewar baffana,kuma nima inason in kula dashi,kamar yadda ya kula da rayuwata abaya"
Jinjina kai sukayi gaba ɗaya,suna ayyana irin kaunar dake tsakanin fattu da baffanta.

Kafin su bar kasar Ghana saida mahaifin fattu ya mallaka wa baffa kanfaninsa na ƙera takalma da jakunkuna,ya maida sunan sa akan takardun kamfanin,sannan ya bashi gida,wanda idan yazo zai rinka sauka aciki sannan ya damkawa fattu takardun gida dana kamfanin,harda mukullin sabuwar mota yar yayi.
Kuka sosai baffa yayi yana godiya,fattu ma tayi matukar murna sosai.adeeb kam godiya yayiwa Sultan habeeb,haka innar fattuma ba'a barta abaya ba,dinkuna ta sanya aka yiwa baffa,na gani na faɗa, masu kyau da tsada.sosai baffa ke yaba karamcin iyayen fattu,ba abinda zaice saidai Allah ya saka musu da aljanna.

Washe gari kuwa jirginsu ya daga zuwa Misra,fattu harda kukan rabuwa da yan uwanta,haka innarta ta cika ta da kayan gyara kala kala.
Wani ƙayataccen bangare su fattu suka sauka,wanda bayan tafiyarta Ghana ,Adeeb sanya aka kera musu.tsyawa fadar irin tsaruwar da bangaren yayi abune mai matukar wahala.kallo daya zakayiwa gurin kasan an kashe kudade makudai.

Baffama bangare guda aka ware masa inda zai zauna.haka yasha kyaututtukan gurin iyalan Adeeb,sannan shima Adeeb ya ba baffa kanfaninsa na motoci,baffa neman zaucewa yayi da irin wannan kyautukan da ake ta bashi.
Sosai ake girmama baffa cikin fadar,dan kowa yasan shidin waye.
Cikin lokaci kalilan baffa ya wanke yayi fes dashi,masha Allah kyakykyawan bafillatani,yayi kiba ya koma Alhaji sosai.ba jimawa suka shirya shida Adeeb da fattu dasu nanny sukaje suka sauke farali.
Sun dawo da kwana uku aka shirya gagarumin taron nadin Adeeb matsayin sarki.sannan ranar za'a gudanar da bikinsu shida fattu.
Anyi taro na ban mamaki wanda saida ya girgiza duniya,taron daya hada sarakunan hasashe daban daban,daga turawa,larabawa zuwa hausawa,ba kalar mutanen da babu agurin.
Taro yayi taro,an nada Adeeb matsayin sarkin misra,SULTAN ADEEB MUHAMMAD ASHRAF.
haka aka kammala taro ya tashi lafiya,kuma ranar Adeeb ya mallaka fattu dankareriyar mota mai shegen tsada
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment