Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta duKar da kai ta ce, “Ai babu wuya, duk abin da mutum ya saa ransa cewa zai koya, ai zaiiya matufKar dai akwai mai koya masa a kusa.”

Jin haka sai Bashari ya ce mata, “Ai kuwa da wannan mai koyo ya yi sa‘a.”

‘Ta mika masa sarewar ta ce ya rike, ita kuma sai ta ruga cikin daji. Can bayan kamar rabin sa‘a, sai ga ta ta dawo rife da gwandar daji masu kyau sun nuna lugub-lugub, ga kuma Kokiya da tsada duk ta hada ta mikawa Bashari. Ya yi godiya a daidai lokacin da ya dauki wata tsada ya jefa a bakinsa.

“Yar Fulani ta ce, “Ya kai wannan saurayi, ni ko wani abu ne ya ke ta ba ni mamaki.” Bashari ya ce, “Ya ke ‘yar Fillo ke kuwa mene ne ke ta ba ki mamaki?”
Ta ce, “Tun ranar da ka zo sai na ji kamar wata
Www.bankinhausanovels.com.ng sabuwar rayuwa ta zo mini, don ko tunaka na yi sai in ji wani farin ciki na shiga cikin zuciyata, in kuma kana kusa da ni, duk sai in rude. Ka ga daren jiya ma na kasa yin barci saboda tunanin ka, wai mene ya sa haka ne?”



Bashari ya Kyalkyace da dariya. “Yar Fulani ta yi wani sansaraKwai tana mamakin mene ne abin dariya a cikin maganarta, don ita tana ganin iyakar gaskiyarta ta fada. Can sai Bashari ya sake kallon ta da kyau sannan ya gyara murya ya ce, “Yarinya ‘yar Fillo, wannan abu da kike ji ya nuna miki saurayi kado ya yi kasuwa ke nan. A taKaice dai wannan abu shi ake kira soyayya.”

Ta dukar da kai da fahimtar cewa lallai abin da ya fada fa haka ne, sai ta ce, “Ai ko kadan haka ba za ta yiwu ba.”

Bashari da ke kashingide jikin bishiya, sai ya gyara zama ya ce, “Ko mene ne dalilinki na cewa hakan ba za ta yiwu ba?”

Ta amsa da cewa, “Ya kai saurayi, shi so nauyi gare shi, ya fi dutse nauyi kuma ya fi teku zurfi. Yana da dadi da Kanshi da kuma haske. In kuma baayi sa’a ba, to shi so babban hadari ne, kuma ga yawan mahassada a cikin sa.

Ya kai saurayi, idan muka shiga cikin kogin so ni da

Www.bankinhausanovels.com.ng kai, to ina ganin ma abin zai yi wuya. Ka ga da farko dai kai ba dan Fulani ba ne, halayenmu da naku sun sha bamban. Mutanen gari za su rika zunden ka cewa ka auro ‘yar Kauye, sannan kuma daga ganin ka kai da mahaifinka masu wadata ne, mu kuwa talakawa ne.”

Sai ya katse ta ya ce, “T’saya kada ki yi nisa. Ke Bingyel, ba ki da hujja ko daya, zan iya ci gaba da rayuwata gaba daya a riga ko daji saboda ke, in hakan kika fiso. Zancen ni ba Bafillatani ba ne ki kau da shi, in kuma zai fi miki dadi, to ni ma daga yau ina iya zama dan Fulani.

Ya ke hasken wanda ya yi sa’a ya gan ki, maganar arziki da ki ka yi, to shi so babu ruwansa da arziki ko sarauta ko talauci, kuma ni ina ganin duk son da ya ke duba wadannan abubuwa, to ba hakikanin son gaskiya ba ne. ‘To wai ma in kina maganar arziki ne, shin kin san cewa mahaifinki da a cikin gari ya ke dole a kira shi Sarkin kudi?

Ya ke farin cikina, ina so daga yau ki sani cewa babban abin da soyayya ke bukata shi ne alkawari. Ke in takaice miki ni na sadaukar da kaina zuwa gare ki, sai dai ko in ke kika ki ko kuma mahaifinki. Ni dai sai yadda kika yi da ni.”

Murna ta lullube ‘yar Fulani, ta ce, “Ya kai masoyina, ni kuma na dauki alkawari in dai muna da

Www.bankinhausanovels.com.ng rai, to babu mai raba mu. Sai dai matsala daya ce kawai nake ganin za ta iya kawo mana dan cikas.”

Ya tambaye ta, “Wace irin matsala ce?”

‘Yar Fulani ta ce, “Ina kyautata zaton, ko kuma in ce maka mun riga mun yanke shawara nan ba da dadewa ba za mu bar wannan Kasar zuwa wata, don kwanciyar hankalinmu gaba daya. Akwai kanin Sarkin kasar nan wanda ya nuna cewa wai dole in so shi ni kuma na ki, kuma ga shi yanzu shi za a yi wa sarauta. Wannan ya sa za mu tashi mu bar masa Kasarsa da zarar an nada shi, kada ya zo ya ci mana mutunci.”

Hakan ya tsunduma Bashari cikin tunanin irin rudanin da soyayyarsu za ta shiga. Ko kuma wane irin hali shi kansa zai shiga in har wani can daban ya aure ta? Ya shiga sake-sake a zuciyarsa yana cewa “In kuwa haka ne, to wannan dattijo da nake jiyya yana samun sauki za mu yi sallama in tsallake in bi Fulanin nan duk inda za su.”

“Yar Fulani ta yanke masa tunaninsa ta ce, “Ya kai saurayina kana tunanin mene ne?”

Sai ya ce mata, “Ke nake tunawa.”

Ta ce, “To ai ga ni kusa da kai. Kuma ai mun riga mun yi wa juna alkawari.”

Suka dubi juna suka yi wani murmushi a daidai

Www.bankinhausanovels.com.ng lokacin da wancan dan Fulani da aka dauka don taya ta kiwo ya iso wurin. Samun su a cikin irin wannan hali wanda ke nuna cewa akwai soyayya ya sa zuciyarsa Kuntata, ransa ya baci, ya rasa abin da ke yi masa dadi a duniya. Ya wuce dai bai ce komai ba.

Suka zauna nan gindin bishiya, ta fara koya masa yadda ake busa sarewa. La’asar sakaliya suka tashi suka koma riga cike da farin ciki da annashuwa.

Wancan dan Fulani makiyayi kuwa sai da ya san yadda ya yi ya kewaya ya je ya sami Ardo ya tsegunta masa cewa ya ga ‘yarsa tana zance da wani bako kado. Nan da nan Sarkin Fulani ya kwabe shi tare da umurnin cewa kada ya sake jin irin wannan magana daga bakinsa. Tun daga wannan rana kuwa dan Fulani ya shiga Rulle-Kulle a cikin zuciyarsa, amma fa ba Kullin alheri ba.

Dawowar wadannan yara sai suka tarar da Sarkin Fulani a wurin mara lafiya, wanda a karon farko ya fara samun sauki har an fito da shi yana jingine a jikin dannin gidan. Murna ta kama Bashari duk da cewa har yanzu mara lafiyar bai fara iya magana ba, sai dai daga hannu kawai.

Da Magriba ‘yar Fulani ta kawo wa Bashari dambu ya ci, bayan Isha’i kuma, sai ta dauko tabarmarta ta je can kusa da bukkarsa suka zauna suna ta zantawa har

Www.bankinhausanovels.com.ng dare ya fara shiga sosai kafin ta tashi ta shige tata bukkar.

Haka makamancin wannan al’amari ya yi ta faruwa, in Bashari ba ya wurin majinyacinsa, to yana cikin daji wurin ‘yar Fulani suna hira.

A haka sai da suka sami kusan watanni uku.

Yanzu Bashari ya kware sosai a fagen busa sarewa ta yadda in yana busawa, sai ka ga shanu sun kewaye shi a cikin daji suna saurara. Soyayya kuwa tsakaninsa da ‘yar Fulani sai abin da ya kara gaba.

Mara lafiya kuma ya gama murmurewa, sannan duk abin nan da ake yi bai taba gayawa Bashari ko kuma sabon abokinsa Sarkin Fulani cewa shi ne Sarkin wannan kasa ba. Wata rana suna cikin hirarsu irin ta dattijai, sai ya cewa Sarkin Fulani, “Babu shakka akwai soyayya a tsakanin dana da ‘yarka, ko mene ka gani?” Sai Sarkin Fulani ya ce, “Ai niba ni da ta cewa, abin da ‘yata take so shi nake so, don na fi son farin cikinta fiye da komai. Ita da dan’uwanta fa kadai suka rage gare ni.

Akwai dai wani abu ne da muke hange. Wato Kanin Sarkin wannan kasa tamu yana son wannan ‘ya tawa amma ita ko kadan ba ta Kaunarsa, to kuma ga shi goben nan shi za a nada Sarki, kuma na tabbata

Www.bankinhausanovels.com.ng zai kyale mu ba. Saboda haka muke ta shiryeshiryen washegarin nada shi mu kora shanunmu mu bar masa Kasarsa don kada ya tozarta mu. Ba don rashin lafiyarka ba ma da tuni mun yi nisa.

Dama ka san shi kanin Sarki yana shakkar tsohon Sarki ne saboda ba zai yardar masa da zalunci ba. To yanzu abu ya lalace, don ko shiga gari da na yi ranar kasuwa, duk mutane suna ta dari-dari kan wannan sarauta tasa. In ka ga irin mutanen da aka gayyato don bikin nadin ma kawai abin zai ba ka takaici, ko ina gari ya cika da shaidanun mutane suna ta sheKe ayarsu, kai abin babu kyau. Babu shakka mun yi rashin adalin Sarki.” Jin haka sai Sarki ya ce masa, “Ai komai na Allah ne. In niyyarsa ba ta alheri ba ce sai ka ga wani abu ya faru, sai dai kuma akwai wani abu da nake roKo ka yi, wato Kokarin halartar bikin nadin sabon Sarki, don akwai hikimar da ta sa na ce maka haka. Ni da dana ma duk za mu halarta,in Allah Ya so.” Sarkin Fulani zai yi jayayya, sai kuma ya lura da yanayin da abokin nasa ya yi masa magana. Sai ya yanke shawarar yin shiru tare da amincewa.

Sarki Shahzad ya fara tunani cewa, “Ikon Allah, yanzu har watanni uku sun cika, ashe ni lissafina ba daidai ba ne.”
Www.bankinhausanovels.com.ng
Bayan kiwo su Bashari suka koma gida. Yana kammala dauraye jikinsa sai ya shige cikin bukkarsu ya tarar da Sarki zaune yana lazimi. Bayan ya kammala, sai ya gaishe shi cikin girmamawa, shi kuma ya amsa cike da murmushi.

Sarki ya ce, “Ya kai dana Bashari zauna ina son mu yi magana ni da kai.”

Bashari ya nemi wuri ya zauna yana saurare a tsorace abin da Sarki zai ce, don shia zatonsa ko ya yi wani laifin ne.

Ya ci gaba da cewa, “A wancan lokaci da wannan masifa ta faru da ni na san wadanda nake tare da su, har suka yi Kokarin salwantar da ni, wato ba barayi ne suka nemi halaka ni ba kamar yadda mutanen gidan nan suke zato. Saboda haka ina son ka ba ni labarin hakikanin abin da ya faru tun daga farko har karshe. A takaice kuma ina son in san labarinka kai kanka.”

Bashari ya kwashe labari bai rage komai ba ya ba Sarki, tun daga fitowarsa gida har zuwa zamansu

gidan Sarkin Fulani da kuma dalilin da ya sa ya yi Karyar cewa barayi ne suka nemi halaka shi har ma don su yarda ya ce musu mahaifinsa ne.

Sarki ya ce, “Ya kai dana, na gode maka, Allah Ya saka maka da alheri, Yasaka gama lafiya.”

Daga nan sai Sarki ya ba Bashari labarinsa tare da

Www.bankinhausanovels.com.ng sanar da shi cewa gobe tun Asubahin fari za su nufi gari, kasancewar bayan Sallar Azahar ne a kan yi nadin sarautar. Ya kammala da cewa Bashari, “Sai dai kuma ina fata wannan labari namu ya ci gaba da kasancewa sirri har zuwa lokacin da za a bayyana shi.”

Suka sami Ardo suka yi masa godiya mai tarin yawa tare da sanar da shi cewa tun Asubahin fari za su tafi. Sarki kuma ya Kara jaddada roKonsa ga Sarkin Fulani a kan cewa lallai yana buKatar ya halarci wurin nadin sabon Sarki gobe.

Bashari da ‘yar Fulani kuwa har kuka suka yi saboda za su rabu. Ya yi mata alKawarin cewa za ta rika ganin sa, zai rika zuwa duk inda take.

Asuba na yi suka kama hanya. Bayan sun dan fara tafiya kadan, sai Sarki ya sauya shigarsa ya yi irin ta makiyayan daji, sannan ya kawo wani rawani ya nade kansa ruf, ba ka ganin komai sai idanu. In ka gan shi sai ka rantse cewa wani Ridahumin bakauye ne.

Suka isa cikin gari, sai suka ga an Rayata shi da tutoci da sauran kayan Kawa, ko ina ka duba sai gungun baki, masu goge na yi, masu molo da dara na yi, ‘yan caca da masu bori kuwa kowa ya baje hajarsa. “Yan daudu da karuwai sai rangwada suke suna ta kurkurdawa tsakanin jama’a suna sheKe ayarsu wai

Www.bankinhausanovels.com.ng nasu ya kama, gari ya zama nasu.

Sarki na gaba Bashari na biye da shi, ba su zame ko ina ba sai gidan Waziri, suka tarar da zaurensa a bude kuma ga dukkan alama yana ciki, saboda haka sai suka shiga. Suka tarar da shi zaune a kan buzu ya yi tagumi, cike da bacin rai. Sarki ya ce, “Salamun alaikum ya kai Waziri.”

Waziri ya yi wuf ya dubo zuwa gare su da mamaki don ya ji muryar ta yi kama da ta Sarki. Ya mayar da sallama sannan ya ce, “Ku su wane ne, kuma mene ne labarinku?”

Sarki ya warware nadinsa.

Waziri ya yi tsalle ya tsallake kujeru ya yi cikin gida a guje yana cewa, “Ni mene ne nawa a ciki za ka yi mini fatalwa? Je ka can wurin Kaninka shi ne zai haye maka karaga.”

Da Sarki ya ga cewa lallai Wazirinsa ya firgita, sai

ya zauna kan kujera tare da umurtar Bashari cewa shi ma ya zauna. Zamansu ba dadewa sai ga dan Waziri ya shigo da cikakken tabbacin cewa mahaifinsa ne a cikin zauren, amma sai ya yi arba da Sarki a zaune, mamaki ya kama shi. Ya yi tirya-tirya zai gudu, sai Sarki ya kira sunansa, “Abdallah.” Sai ya tsaya ya sakankance cewa lallai wannan Sarki ne, saboda haka sai ya yi gaisuwa.

Sarki ya ce masa, “Ka je ka cewa Waziri ina son ganin sane.” Yaro ya shiga cikin gida ya tarar da mahaifinsa wato Waziri cikin halin tsoro, yana ta kyarma.

Waziri ya tambaye shi, “Ia ina ka biyo da za ka shigo? Ba ka ga fatalwar nan ba a zaure?”

Yaro ya ce, “Baba ka kwantar da hankalinka, ba fatalwa ba ce, Sarki ne da kansa ya ce yana son ganin ka. Ina ganin gara ka je, wataKila akwai wani al’amari ne wanda muka kasa ganewa.”

Da kyar Waziri ya fita. Sarki ya ce masa, “Haba Waziri, ko dai da ace ni fatalwa ce ka san ba zan cuce ka da komai ba.” Ya dafa kafadarsa ya ce, “Kwantar da hankalinka.” Waziri ya dan sami natsuwa, ya yi gaisuwa cike da mamaki. Sarki ya dan gutsura masa labarin a taKaice Kwarai sannan ya ce masa ya tashi yanzu babu lokaci. Ya ce, “Abin da nake so da kai yanzu Waziri, ka je ka kawo mini kayan yaKi, amma fa kada wani ya sani. Kuma ka gargadi yaron nan Abdallah ya kame bakinsa.” Aka kawo wa Sarki sulke ya shige, haka nan shi ma Waziri, don ko data Baci. Jama’‘ar gari da baki, babba da yaro, mace da namiji, duk kowa ya hallara a filin nadin

Sarki. Sarkin Fulani Www.bankinhausanovels.com.ng da’yarsa su ma suna cikin ‘yan kallo. Yanzu Waziri da sabon Sarki kawai ake jira don aci gaba da gudanar da harkokin nadi.

Jimawa kadan sai aka ji tambura na tashi, sabon Sarki ya tunkaro ke nan. Ya zo ya zauna, yanzu sai dai masu nadi kawai su fara aikinsu. Kuma a daidai wannan lokaci zuciyar Sarkin mai jiran gado tuni ta harzuka irin yadda wai har Waziri ne ya yi sakaci har ya riga shi fitowa. Ya Kulla a cikin ransa cewa ana

nada shi cikin jawabinsa na farko zai fara ne da sauke Waziri ya nada nasa. Wato an sami dalilin da za aba jama’‘a na sauke Waziri; komai ya zo da sauki ke nan.

Can sai aka hango wani mutum ya keto fili a kan doki ga Waziri biye da shi tare da wani kyakkyawan saurayi. Kuma shi wannan mahayi ya rufe fuskarsa, sai idanunsa kawai ake iya hangowa. Mutane sai suka rika zaton cewa wannan lallai wani babban amini ne na masarautar ya halarci wurin nadin Sarki, shi ma sabon Sarki haka ya ke zato. Saboda haka nan da nan aka ba shi kujera ya zauna a cikin tantin da Sarki ya ke. Albarkacinsa shi ma Bashari ya sami zama cikin wannan babbar inuwa.

Ita ko Bingyel ‘yar Fulani da ke can cikin taro da ta hango saurayinta sai ta fara tsalle tana daga hannu wai ko zai hangota, amma ina, saboda yawan jama’a.

HMMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE WWW.BANKINHAUSANOVELS.COM.NGYARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM’UNA CHAPTER 13 BY HARUNA USMAN
YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM'UNA BY HARUNA USMAN Jun 28, 2022 0 0 Add to Reading List


YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM’UNA

CHAPTER 13 BY HARUNA USMAN

Www.bankinhausanovels.com.ng


A JIYA MUN TSAYA

Can sai aka hango wani mutum ya keto fili a kan doki ga Waziri biye da shi tare da wani kyakkyawan saurayi. Kuma shi wannan mahayi ya rufe fuskarsa, sai idanunsa kawai ake iya hangowa. Mutane sai suka rika zaton cewa wannan lallai wani babban amini ne na masarautar ya halarci wurin nadin Sarki, shi ma sabon Sarki haka ya ke zato. Saboda haka nan da nan aka ba shi kujera ya zauna a cikin tantin da Sarki ya ke. Albarkacinsa shi ma Bashari ya sami zama cikin wannan babbar inuwa.

Ita ko Bingyel ‘yar Fulani da ke can cikin taro da ta hango saurayinta sai ta fara tsalle tana daga hannu wai ko zai hangota, amma ina, saboda yawan jama’a.

ZAMU TASHI

Sarkin Fulani ya tambaye ta dalilin daga hannunta, sai ta ce, “Dubi babban bakon can da ya zo yanzu, kusa da shi wane ne zaune?”

Dattijo ya kyalla ido sosai, ya ce, “Ai kuwa Bashari ne, yaya aka yi ya sami zama cikin sarakuna?”



Bayan an kintsa, sai aka fara al’adun da aka saba na nadin Sarki, aka kammala aka yi addu’o’i sannan aka dauki rawani wanda nada shi a kan zababben Sarki shi ne tabbatuwar sarauta. Sai suka ji wata irin tsawa tace, “Kul! Kada a nada rawanin nan.”

Duk sai hankalin jama’a ya komo ta inda tsawar ta fito, sai aka ga ashe mahayin nan ne da ya zo dazu. Nan take sai ya bude fuskarsa.


To fa, da mutane suka ga Sarkinsu ne da suke matukar Kauna, sai shewa mai cike da mamaki ta cika wurin. Wadanda ke kusa kuwa sai suka fara zubewa kasa don gaisuwa. Wasu kuma cewa suke yi fatalwa ce.

Kanin Sarki saboda rudewa sai ya jawo wata gorar ruwa da ke kusa da shi yana wanke fuska don tunanin ko idanunsa ne ke zagi. Wuri ya rude haya-haya sai Sarki ya ce, “Jama’a don Allah a saurara, akwai labari.”

Wuri ya yi tsit, Sarki ya cewa Bashari ya tashi ya labarta wa mutane abin da ya faru. Ya mike ya labarta Www.bankinhausanovels.com.ng

ba tare da rage komai ba, yana ma gab da kammalawa ne sai kawai ya hango ‘yar Fulani a cikin taro ita da mahaifinta, sai ya kira su ya nuna wa jama’a ya ce, “Wadannan bayin Allah a gidansu muka yi jinyar Sarki har na misalin wata uku.”



Da mutane suka ji wannan labari sai takaici ya kama su, wasu ma har kuka suka yi ta ribzawa. Nan fa mutane suka nemi yin hargowa suna cewa, “A ba mu su mu kashe! A tsire su! A dafa su da ransu!”

Sarki ya sa aka kama su don gudun abin da jama’a za su iya yi musu a wurin, amma da ya ke mutane sun san halinsa na tsananin tausayi da yafiya, sai nan take suka birkice a kan cewa lallai a wurin suke bukata a mika su zuwa ga Alqalin Kasar ya yanke musu hukunci kafin a ci gaba da komai don kuwa maciya amanar kasa ne.

Sarki ya rasa yadda zai yi, kuma ya tabbatar yadda hankalin jama’a ya tashi, matukar ya hana wannan bukata tasu, to komai na iya faruwa. Akan dole ya amince aka mika wa Alkali shari’ar. Shi kuma ba tare da bata lokaci ba, ya ba da umurnin a tafi da su jakara a tsire su gaba daya. Jama’’a dai ba su sakankance ba sai da dubban mutane suka bi su a baya suna tsine musu albarka. A takaice ba a kyale su ba sai da aka tabbatar sun sami masauki na dundundun a lahira Www.bankinhausanovels.com.ng tukuna, sannan aka dawo filin nadin sarauta.

Sarki Shahzad ya yi godiya saboda irin kaunar da aka nuna masa, sannan ya kammala jawabinsa da cewa, “Jama’‘a kun dai san ba ni da da, to daga yau ku shaida wannan yaro Bashari ya zama dana, shi ne magajina.” Fili sai sowa, mutane suna cewa, “Mun amince! mun amince!”

Aka fa shiga shagalin dawowar Sarki abin kamar Sallah. Bata gari kuwa nan da nan kowannen su sai Kokarin barin gari, murna ta koma ciki.

Bayan an gama natsawa sai Sarki ya kira Bashari ya ce masa, “Ya kai dana, ina rokon ka da ka kare mutuncinka a cikin wannan al’umma, wato ka kiyaye mana mutuncin da jama’a ke ganin mu da shi, kar ka yi abin da za mu ji kunya. Daga yau zan fara karantar da kai ilmi na addini da sauran harkokin yau da kullum, in Allah Ya yarda. In kuma na ga ka kware tare da gogewa game da sha’anonin mulki, to akwai abin da nake shawartawa a cikin zuciyata.”

Bashari ya yi godiya.

Sarki ya ci gaba da cewa, “Abin da nake bukata da kai yanzu shi ne, ka je rigar Sarkin Fulani ku zo tare da shi.”

Nan da nan Bashari ya zaburi doki sai rigar Fulani.



Www.bankinhausanovels.com.ng Ya ko yi saa ya tarar Ardo Jumare zai fitake nan, ya – gaishe shi cikin girmamawa.

Ardo ya ce, “Bashari amma ku mutanen birnin kuna da wayo, ashe Sarki ne muka zauna da shi na tsawon wata uku amma bamu sani ba?”

Shi dai Bashari bai iya cewa komai ba sai dai murmushi kawai.

Bashari ya ce, “Allah Ya taimaki Ardo, mai martaba Sarki ne ya ce don Allah yana da bukatar ganin ka.”
Sarkin Fulani ya ce, “Yaro, waye zai Ki kiran Sarki?”

Bashari ya fara shafa keya yana cewa, “Kafin ka kintsa bari in dan shiga daji in duba kanwata a wurin kiwo, mun kwana biyu ba mu gaisa ba.”

Sarkin Fulani ya ce, “E ita ma ko dazun nan take ta maganar ka, ashe dan halas kana tafe.”

Shigar Bashari daji fa ya ga ‘yar Fulani sai hira ta sarke, bai farga ba sai da rana ta fara shigowa cikin inuwar da suke, sannan firgigi ya ce, “Ke! Na bar yana can yana ta jira na za mu tafi wurin Sarki da shi. Kin ga kin sa na zama mara kirki ko? Na bar tsofaffi suna ta jira.” Suna cikin haka sai ga dan Fulanin can mai taya ta kiwo ya zo, ya yi niyyar daga sanda ya sheme Bashari sai dai wata zuciya ta hana shi. Ya wuce dai bai ce Www.bankinhausanovels.com.ng komai ba. Ardo da Bashari suka rankaya zuwa gidan Sarki a birni. Suka yi gaisuwa ya amsa musu da irin murmushin nan nasa mai ban sha’awa kuma mai cike da Kauna. Ya taso daga kujera ya rungume Sarkin Fulani, ya ja shi don su zauna kamar yadda suka saba yi a riga lokacin da ya ke jinya. Idan ka gan su sai ka dauka wa ne da Kani. Ga su farare, masu fararen gemmiai da saje. .

Bashari ya nemi izini ya fita daga waje. Bai yi nisa ba don ya san zaa iya neman sa. Sarki ya dubi Sarkin Fulani ya ce, “Ardo.” Ardo ya amsa, “Ran Sarki ya dade.”



Sarki ya ce, “Ardo daga yau ina son in sanar da kai cewa ka zama dan’uwana, tsakanin ni da kai babu iso. ‘Tun lokacin da na zauna da kai na fahimci cewa kana da ilmin addini da mutunci da karimci. Saboda haka na ba ka amanar kaina, matukKar ka ga na yi wani abu wanda ya kamata a ce an kwaba mini amma ka kyale ni, to ban yafe maka ba.
Ni da ‘yan majalisata mun zauna mun yanke shawarar nada ka Sarkin Fulanin wannan Kasa baki daya, maimakon Sarkin rigarku kawai. Sannan kuma yanzu kana daya daga cikin ‘yan majalisar Sarki. Za a yi nadin ne ba da dadewa ba, kamar

Www.bankinhausanovels.com.ng Juma‘a mai zuwa. Kana da ikon dawowa gari da zama duk lokacin da ka ji hakan ya yi maka dadi.

Na riga na sa an shirya maka gidanka yadda ya kamata. Kuma akwai wasu kayayyaki da na tabbatar cewa za su dace da kai na sa an shirya su yanzu, in za ka koma zaa bikadasu.”

Sarkin Fulani tun yana godiya har ya koma ya yi

shiru, ya zura wa Sarki ido kawai kuru. Can sai suka koma suka ci gaba da hirarsu kamar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAMUNA
avatar
abdullahi-dahiru

6 months ago

Reply

Good

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to abdullahi-dahiru

Keep following our site for more hausa adventures novels

Please Login or Register in order to submit comment