Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

bai san lokacin da ya tsallake Sarki da gudu ba ya nufi inda take ya tsura mata idanu. Kafin ka ce mene ne wannan, dukkan su sun yanke jiki sun fadi a sume saboda tsananin mamaki da kuma rashin zaton yadda hakan ta kasance a gare su.



Aka zuba musu ruwan randa mai sanyi suka farfado, shi kuma dan Sarki sai ya fara labarta wa mahaifinsa cewa wannan yarinya da aka tanadar masa ita ce abokinsa ya fito nema, kuma Allah Ya sa abokin nasa ya dace. A nan Sarki ya sake hakikance cewa lallai soyayya ba Karamar aba ba ce.

Bashari ya gabatar da abokinsa Amir dan Sarki ga ‘yar Fulani da irin taimakon da ya yi masa lokacin da suka fito neman ta. Ya kuma shaida mata cewa mahaifinta bai rasu ba yana nan yana samun sauki.

Amir dan Sarki ya ce, “To ai faduwa ta zo daidai da zama ke nan, yanzu sai in kammala shirina na tafiya Kasar Arewa kawai. In na je na kai Bashari da ‘yar
Www.bankinhausanovels.com.ng Fulaninsa gida, sai in wuce.” Bashari ya ce, “Haka daidai ne, amma maganar ka wuce ba ta taso ba, don kuwa in mun mika ta gida hankalin iyayenmu ya kwanta, to Kafata-Kafarka za mu je neman taka budurwar. A cikin hankalina ba zan taba samun natsuwa ba irin alherin da ka yi mini da kuma yanayin yadda Allah Ya Kaddara yanke wahalata sanadinka sannan kuma a ce in kyale ka ka tafi kai kadai alhali kuwa na san matsayin soyayya.”

A haka rundunar dan Sarki ta mutum dubu ta motsa zuwa garin su Bashari. Aka fito taryar su har da Sarki da Sarkin Fulani don yanzu ya sami sauKi. Bingyel ta ga mahaifinta, ta ruga ta rungume shi suna kukan barka da arziki.

Bayan sun sauka sai aka kawo Ja’e dan Fulani da sauran abokansa aka yi musu shari’ar fashi da makami da kuma kisan kai. Laifi ya tabbata a kansu, aka sa hauni ya dauke musu kawuna.

Bashari ya ba Sarki labarin abokinsa yarima Amir da irin taimakon da ya yi masa tare kuma da labarin cewa shi ma yarinyar da zai aura ce ta Bata. Kuma yanzu zai wuce Kasar Arewa neman labari, yana son zai bi shi in ya so in sun gano yarinyar, sai su dawo gaba dayaa fara hidimar biki.

Sarki ya ce, “Ni ban Ki ka raka abokinka ba, amma

Www.bankinhausanovels.com.ng da sharadi, muna iya gaggauta daurin aurenku da Bingyel tukuna, bayan biki da kamar mako daya sai ku yi tafiyar ku.” Dole suka amince.

Aka daura auren Bashari da ‘yar Sarkin Fulani, aka yi gagarumin bikin da a iyaka tarihin Kasar wanda aka sani, ba a taba irinsa ba. Sai dai kuma wani babban abin bakin ciki, ana gobe amarya za ta tare sai kawai aka ga wani abu ya zo ya sungume ta ya yi sama da ita, masu ihu na yi, masu jifa na yi, amma kafin ka ce haka, yarinya ta bace a cikin sararin samaniya aka daina ganin ta.

Labarin bakin ciki da Bacin rai kuma dai ba sai an tona ba. Surutai suka cika gari iri-iri, wasu na cewa ai yarinyar Kashin tsiya gare ta ba ta da sa’a ne, wasu kuma cewa suke yi ai kyanta ya yi yawa ne, shi ya sa aljanu za su aure ta. Maganganu dai ba kai ba gindi.

A karshe dai Sarki ne ya yi ta rarrashin Bashari da Sarkin Fulani a kan cewan Allah Ya so yadda aka ga yarinyar da farko haka ma za a sake ganin ta. Aka yi ta addu’ar Allah Ya bayyana ta tare da tona asirin

wancan aljani mai sace ya ‘yan mutane. Yanzu kam tafiya zuwa Kasar Arewa ta tashi daga matsayin rakiya a wurin Bashari ta zama ta dole. Aka Kara musu runduna ta mutum dubu suka nausa,

A kwanaa tashi cikin wata uku da kwana goma sha bakwai suka isa kusa da gari, suka aike wa Sarkin Kasar cewa su bakinsa ne, kuma ga su nan Karasowa.

Kasancewar Wazirinsa ba ya nan ya tafi rangadi, sai aka turo wasu manyan hakimai suka tarbe su aka sauke su a gidan saukar manyan baki na Sarki. Su kuma tawagarsu suka yi tantuna a wajen gari, aka aike musu da shanu da awaki da sauran kayan abinci da na sha don su huta sosai.

Bayan dan Sarki Bashari da abokinsa sun kintsa, sai suka tafi fada don yin gaisuwa, Sarki ya tarbe su cikin mutunci da girmamawa.

Kowannen su ya labarta wa Sarki labarinsa tare da cewa abin da ke tafe da su shi ne don su sami labarin wancan aljani wanda aka ce a wurinsa ne kawai za su
samu don shi ma hakan ta faru ga tasa ‘yar.

Hawaye suka shiga gangarowa daga idanun Sarki shar-shar har sai da suka rude suna mamakin abin da zai sa dattijo kamar wannan kuka. Sai ya ce musu, ) “Ya ku ‘ya’yana, kun fama mini ciwon da ke cikin zuciyata ne, amma fa ba na ce kun yi laifi ba ne, don kuwa matambayi ba ya bata. Kuma gaskiya ne kamar yadda kuka sami labari cewa ni ma ‘yata tana can wurin wannan aljani ya sace ta. Allah dai Ya karya
Www.bankinhausanovels.com.ng Sarkin aljanu Sham’una!” Nan Sarki ya kasa mallakar kansa, ya sake barkewa da kuka su kuma suka rika ba shi hakuri har sai da hankalinsa ya dawo tukuna. Daga nan sai yace musu, “Ku koma masaukinku, in Allah Ya so yau Wazirina zai dawo, shi ne zai ba ku cikakken labarin wannan maridi.”

Suka yi sallama suka fita suna tausaya masa. Suka je bayan gari wurin jama’arsu, kowanne ya warware ‘yan matsalolin da suka taso, sannan da yammaci suka koma masaukinsu. Shigowar su gari sai suka ji gari ya rude da sowa da murna, da suka tambaya sai aka shaida musu cewa Wazirin gari ne ya dawo lafiya daga rangadi.

Waziri ya shiga wurin Sarki ya yi gaisuwa. Bayan sun gama ganawa sai Sarki ya ce, “Waziri muna fa da bakin wasu ‘yan Sarki su biyu, sun zo ne don neman bayanin mugun aljanin nan da ya sace mana ‘ya. Su ma hakan ce ta faru gare su, saboda haka gobe in Allah Ya kai mu sai a shirya liyafa, ka yi hira da su don na ga samari ne tsarorin ka.”

Waziri ya ce, , Allah Ya taimaki Sarki.”

Da gari ya waye, dan Sarki Bashari da abokinsa yarima Amir suka nufi fada suka yi gaisuwa, suka koma gefe suna ta ‘yar tattaunawa. Can sai ga Waziri
Www.bankinhausanovels.com.ng
ya zo don yin gaisuwa. Sarki ya gabatar da Wazirinsa ga ‘yan Sarki, ai Waziri na waigawa don gaisawa da su sai kawai suka yi ido hudu da Bashari sai ya ce, “Bashari.”

Bashari ya ce, “Na’am, Habu.”

Sai suka rungume juna cike da farin ciki. Waziri ya labarta wa Sarki cewa wannan dan’uwansa ne wanda suka fito neman ilmi tare da shi. Ana cikin haka sai ga wani sakon ya shigo fada cewa ga wasu bakin nan sun zo, Waziri ya sa Madaki ya je ya tarbo su, suka shigo suka yi gaisuwa, kuma ga alama su ma neman labarin ne ke tafe da su. Sai jagoran bakin ya ce, “Don Allah Bashari ne da Habu ko kuwa idanuna ne ke yi mini gizo?”

Waziri Habu ya ce, “Ba gizo ba ne, gaskiya ne idonka ya nuna maka Yahaya.”

Bayan duk an kammala gabatar da juna, sai Sarkiya ce, “Lallai yau babbar rana ce a gare mu, saboda haka a buga tambari akwai Kasaitacciyar walima.”

Sarki ya gode musu sannan ya alKawarta musu cewa matukar dai Allah Ya fitar da wadancan ‘yan mata daga hannun Sham’una, to zai halarci garin kowannensu don a yi biki da shi.”

Ran nan ba su yi barci ba, haka suka zauna suna ta hira. Waziri Habu yana labarta musu abin da ya sani

Www.bankinhausanovels.com.ng game da aljani Sham’‘una da irin Karfinsa da kuma cewa tunkarar wannan aljani ba nasu ba ne, sai dai su yi ta addu’ar Allah Ya bai wa dan’uwansu Idrisu nasara a kan haka.

Kowannen su ya gamsu. Sarki ya umurci Waziri Habu da ya yi musu rakiya don komawa garuruwansu.

Yanzu kam kallo ya koma sama, kowa nasarar jarumi Idrisu ya ke saurare. Don dole sai dai a ce saurare din, ko kuma zato, don qalubalen ba gama garibane…

LOKACIN da Sarki Zulkiflu da Wazirinsa Habu suka sauke jarumi Idrisu dan Hamidu a gabar teku sai ya shige cikin dajin da ke gabansa ya ci gaba da ketawa, kuma kasancewar irin wannan tafiya ba bakuwarsa ba ce, sai abin ya zo masa da dan sauki.

In ya gaji sai ya saki Jagora shi kuma ya nemi wuri ya huta, bai tsayawa ko ina sai dai in akwai matukar bukatuwa zuwa ga hakan. Yi ya ke ta yi ba dare ba rana har ya iso bakin wani Katon kogi.

Babu hanyar hayewa, kuma ba wasu manyan itatuwa ballantana ya dan sassaka jirgin da zai iya daukarsa shi da dokinsa, saboda haka sai ya karkata dama ya yi ta tafiya ta gefen rafin har na misalin yini sannan ya yi sa’a ya iso wata gaba wadda a kusa da ita akwai wani dan Kauye, kuma abin kamar an shirya aka dace jirgin ruwan da kan zo sau daya a kowane mako don ketarewa da jama’‘a zuwa daya gabar ya iso. A cikin wannan dare masu jirgi suka ce za su juya,

Www.bankinhausanovels.com.ng Idrisu ya yi cinikin Ketarewa da shi da dokinsa, aka daidaita suka shiga aka mika, a haka suka yi ta yi har sai da suka yi tafiyar kwana uku sannan suka iso wani tsibirl mai matukar ban sha’awa. Ko ina a tsibirin ciyawa ce kake gani koriya shar ko kuma ka ga wani irin yashi fari sal, ga itatuwan dabino da inabi ko ina barjak, kan hanya ko ina ka duba sai inuwa linkim, don itatuwa ne ta kowane gefe suke sa kowace hanya a tsakiya. Tsuntsaye launi daban-daban kowanne da irin kukan gidansu.

Wata irin iska mai sanyin dadi da ke kewayawa a tsibirin dole ne a ambace ta musamman irin yadda kowane lokaci take hadewa da Kanshin da kan fito daga furannin da ke kofar kowane gida suna ba da gudummawar wani irin tabbaci na natsuwa da cikakkiyar lafiya ga duk wanda ya tsinci kansa a yankin.

Yawancin abincin mutanen wurin ‘ya’yan itatuwa ne wadanda suke da su, sai kuma zuma, nono da cukui da ake kawo musu. Allah Ya yi musu arzikin ma‘adinaina KarKashin Kasa da kuma na gefen ruwa.

Wani babban abin ban sha’awa game da tsibirin shi ne mutanensa, masu kyawawan halaye, girmama juna, kula da addini da kuma son baki, kowanne ka gani babba da yaro, mace da namiji ta bangaren ilmin
Www.bankinhausanovels.com.ng addini sai abin ya ba ka mamaki.
Sai dai kash, akwai wani abu da ke matukar damun su a tsibirin. Wato wani irin dodo ne, shi ba mutum ba shi kuma ba dabba ba. Kansa kawai ya kai girman akawalin doki, kuma yana da idanu hudu, daya a goshi, daya a keya, daya a kasan kunnensa na dama dayan kuma a saman kunnensa na hagu. Kowane kunne ya fi matsakaiciyar tabarma fadi kuma yana da bakuna guda biyu, daya a baya dayan kuma a gaba, kuma kowane baki zai iya hadiye Kato komai girmansa.

Wannan dodo dai yana da hannaye guda hudu wanda kowanne yana iya daukar babban dutse da shi, kafafuwansa kuwa kamar wasu manyan itatuwan rimi, cikin sa Kato wanda ko da wasa ba za a iya misaltawa da na toron giwa ba. Jikinsa kuma rabi da gashi daya rabin kuma babu, sannan yana wani irin doyi mai tsananin tayar da hankali. Ba kananan dabbobi irinsu kaji, talo-talo da awaki ba, kai hatta dawaki da rakuma in suka ji doyinsa ba duka ne suke rayuwa ba.
A dabi’a, a duk shekara wannan dodo kan fito daga cikin ruwan rataye da wani irin akurki mai girman katon gida, ya yi ta farautar mutane yana jefawa a ciki sai ya cika shi taf da mutane sannan zai juya ya nufi

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE WWW.BANKINHAUSANOVELS.COM.NGYARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM’UNA

CHAPTER 15 BY HARUNA USMAN

Www.bankinhausanovels.com.ng

MUN TSAYA

Sai dai kash, akwai wani abu da ke matukar damun su a tsibirin. Wato wani irin dodo ne, shi ba mutum ba shi kuma ba dabba ba. Kansa kawai ya kai girman akawalin doki, kuma yana da idanu hudu, daya a goshi, daya a keya, daya a kasan kunnensa na dama dayan kuma a saman kunnensa na hagu. Kowane kunne ya fi matsakaiciyar tabarma fadi kuma yana da bakuna guda biyu, daya a baya dayan kuma a gaba, kuma kowane baki zai iya hadiye Kato komai girmansa.

Wannan dodo dai yana da hannaye guda hudu wanda kowanne yana iya daukar babban dutse da shi, kafafuwansa kuwa kamar wasu manyan itatuwan rimi, cikin sa Kato wanda ko da wasa ba za a iya misaltawa da na toron giwa ba. Jikinsa kuma rabi da gashi daya rabin kuma babu, sannan yana wani irin doyi mai tsananin tayar da hankali. Ba kananan dabbobi irinsu kaji, talo-talo da awaki ba, kai hatta dawaki da rakuma in suka ji doyinsa ba duka ne suke rayuwa ba.
A dabi’a, a duk shekara wannan dodo kan fito daga cikin ruwan rataye da wani irin akurki mai girman katon gida, ya yi ta farautar mutane yana jefawa a ciki sai ya cika shi taf da mutane sannan zai juya ya nufi

ZAMU TASHI

wani dutse da ke cikin tekun, kuma wani abin takaici ma shi ne tun daga wurin farautar ya ke fara cinye wasu, ka ji yana taunar mutum garas-garas kamar yana cin risga.

Ta yin la’akari da irin girmansa da aka bayyana ya sa kowa ya ke tsoron tunkarar sa ballantana a buga. An taba gayyatar jarumai misalin dubu daga garuruwa mabambanta don su halaka shi, amma Karshe dodon bai taba samun ganima irin ta wannan shekarar ba, don kuwa su ya kame kawai ya juya ya koma cikin ruwa abinsa. Wata shekarar kuma an taba hada wata wuta ganga-ganga da nufin in ya zo ya fada amma a banza, don kuwa komawa cikin ruwa ya yi ya guntso ruwa ya zo ya fesa mata ta bice. A Karshe dai mutanen yankin suka dukufa zuwa ga rokon Allah a kan Ya raba su da wannan fitina.
Yanzu shekarar dodon ta takwas ke nan da ya gane wannan tsibiri.



Amma in ba don wannan masifa ba, to ko kai wane ne ba za ka so tafiya daga wurin ba. Kuma da ma in kai bako ne da zarar mutanen tsibirin suka ga lokacin zuwan dodon ya karato, to za su yi KoKarin sallamar ka ko kuma gargadin ka gaggauta tafiya don kada dodo ya hada da kai. Lura da irin tasirin da ilmi ya yi a tsibirin da kuma

Www.bankinhausanovels.com.ng irin ni‘imar da ta linkime wurin ta sa Idrisu dan Hamidu yanke shawarar cewa zai yi wata uku don Karin neman ilmi da kuma hutawa kafin ya wuce.

Nan da nan aka isar da shi wurin wani dattijon malami wato Shehi Salim, wanda kuma shi ne Sarkin tsibirin. Ya karbe shi da mutuntawa kamar ya taba sanin sa. Idrisu ya roKe shi ko zai taimaka ya sanar da shi wani abu daga cikin ilmi na tsawon wata uku? Don shi matafiyi ne.

Sarki ya ce, “Kwarai da gaske kuwa, mu ai da ma abin da muke so ke nan. Ina amfanin kana da ilmi ka bar wa cikinka kai daya? In ba ka koyawa wani ba to kai yaya aka yi aka koya maka?”

Ba wata-wata Idrisu ya dukufa zuwa ga neman ilmi a wurin Shehin malami kuma Sarki Salim har sai da watanni ukun nan suka cika, kuma a cikin irin hirar da Idrisu kan yi da Sarki ya sami labarin wannan dodo da kuma irin sharrinsa tare da cewa yanzu sauran misalin watanni biyu ya zo ya debi na diba, mai rabon ganin badi kuma sai ya gani.



Sai Idrisu ya ce wa Sarki, “Ranka ya dade ina son zan zauna sai dodon ya zo in ga irin yadda ya ke.”

Sarki ya ce, “Kai dana rufa wa kanka asiri kada ka yi ganganci. Ka ga mu madon ba mu iya rayuwa a wata

Www.bankinhausanovels.com.ng Kasar ne in banda nan, ba don haka ba da ko kare ba za kasamu ba.”
Da Idrisu ya ji zancen Sarki sai ya ce, “Ranka ya dade ina rokon ka yafe mini in ga wannan maridi, kuma na yarda in Allah Ya Kaddara cewa a nan zan mutu babu yadda zan yi, kamar dai karatun da muka yi dazu da kai, Akaramakallahu.”

Sarki ya ce, “Tun da yadda kake so ke nan, to Allah Ya kiyaye mu baki daya.” Idrisu ya ce, “Amin Allah gafarta malam.”

A kwanaa tashi lokacin zuwan dodo ya yi, Sarki ya sa aka yi yekuwa cewa duk wanda ba dan gari ba, to ya gaggauta tafiya, duk kuma wanda ke rike da hakkin wani bako, to ya gaggauta sallamar sa tun kafin dodo ya iso. Baki suka yi ta shiga cikin jiragen ruwa, kuma kafin ka ce mene ne babu kowa sai mutanen tsibirin nan kadai sai kuma Idrisu da ke zaune gidan Sarki wanda mutane suka yi ta mamakin rashin gudunsa.

Bayan kowa ya shirya, masu neman wurin buya sun tanada sai can aka fara jin doyin dodon, wanda hakan ke tabbatar da cewa cikin kwanaki biyu zai iso. Mutane suka fara shigewa maboyarsu ta Karkashin kasa, dawaki da sauran dabbobi kuma tuni sun fara

mutuwa, amma shi Jagora dokin jarumi Idrisu sai

Www.bankinhausanovels.com.ng ‘harbin iska ya ke yi yana wata irin haniniya ta nishadi.

Can sai aka fara jin wani irin Rugi da Karaji mai Karfin gaske da ban tsoro. Ruwan ya dauki zafi kamar ana dafa shi, wanda hakan ya sa Kanana da matsakaitan halittun ruwa fara mutuwa.



Lura da haka sai Idrisu ya shiga kayansa na yaki, ya dora sirdi, ya rataya takobinsa, ya rike mashi. Ya yi tsalle ya haye Jagora, wanda shi kuma kamar jira ya ke yi. Idrisu ya nufi bakin ruwan ta bangaren da ya sami labarin cewa ta nan dodon ke fitowa ya tsaya abinsa.

Can sai ya ga wani abu yana dagowa daga cikin ruwan nan kamar tsauni, yana buga ruwa da hannayensa, yana furzar da wani abu mai kama da wuta daga bakunansa, yana matsowa yana wani irin Karaji. Idrisu ya tabbatar wa kansa cewa lallai wannan mugun maridi ne.

Ga akurkinsa nan rataye a kafadarsa, na jefa mutane in ya kama.

Lokacin da dodo ya kusa abin mamaki sai Jagora dokin Idrisu ya Kara tsawo da fadi. Idrisu ya zaro takobinsa, shi ma abin mamaki wurin fitowar takobin daga kubensa sai ka dauka Karar aradu ce, kuma kammala fitowar takobin ke da wuya sai ya
kara tsawo yana wani irin hayaki kamar an fito da shi Www.bankinhausanovels.com.ng daga cikin wuta.

Da dodo ya hango su sai ya yi wani irin Kumayji ya nufo su da cikakken tabbacin cewa ga wadanda zai fara somin tabi da su nan cikin sauki, amma Idrisu da dokinsa Jagora ko gezau, hasali ma lokacin da dodon ya zo gab-da-gab sai Idrisu ya riKka kewaya shi kasancewar shi dodon ba ya iya juyawa da sauri, sai dai kuma da ya ke yana da ido ta kowane Bangare yana ganin Idrisu din, ya rikKa daga manyan hannayensa yana kai bugu shi kuma dokin yana zamewa ba ya samun su, can ya dago hannaye biyu ya yarfo, shi kuma Idrisu sai ya sa takobi ya datse su, habawa! Jini kamar wasu manyan idanun ruwa ne suka Balle, ga hannayen dodo kuma kamar wasu manyan itatuwa a Kasa.

Dodo fa sai Karaji ya ke yana tsalle-tsalle don tsananin Zafi, itatuwa sai faduwa suke ta yi, ya fusata gaba daya ya nufo Idrisu, shi kuwa sai ya zame ya sa takobi ya sare masa cinya guda daya. Ya girgiza mashinsa ya auna tare da sakar masa a cikin idonsa na gaban goshi, nan take sai wuta ta kama baki daya, Idrisu kuma ya janye mashinsa ya koma gefe yana kallo.
Dodo ya yi ta Karaji yana motsawa ita kuma wuta tana ta cin sa har sai da ya kasa motsi ya Kone Kurmus.



Www.bankinhausanovels.com.ng ‘Tokarsa ma kawai kamar wani tsauni. To in ba ka sani ba bari ka ji yadda nauyin mashin nan na jarumi Idrisu dan Hamidu ya ke, wato matukar dai in ba shi Idrisu din ne da kansa ya girgiza shi ba, to nauyinsa kan koma kamar na wani babban tsauni ne, kuma babu mai iya daga shi sai jarumi Idrisu kadai, ko da yake shi a wurinsa yana jin nauyin ne kamar na kowane irin mashi.

Bayan yi wa dodo irin wannan kisa na wulaKanci sai ya koma cikin gari yana kiran mutane don su fito daga wuraren da suka boBboye, amma ‘yan kadan ne

kawai suka fito, su ma,a tsorace.

Da mutuwar dodo ta tabbata sai gari ya rude da sowa da murna, Sarki ya sa aka shirya biki irin na tseren kwale-kwale da sauran wasanni iri-iri cike da murna irin wadda ba su taba yi ba.

Aka zabi wasu Katti daga cikin matasa aka ba su alhakin daukar kwanduna da kwashe tokar dodo sannan kuma su kona hannayensa da Kafarsa wadanda Idrisu ya sare. Cikin sa’a uku suka kammala suka share wurin kamar babu abin da ya taba faruwa.

Da aka natsa Sarki ya sa aka tattara mutane ya gabatar da Idrisu ga wadanda ba su rigaya sun san shi ba, gaba daya aka yi masa godiya kuma suka roKe shi akan ya amince ya zauna tare da su.

Www.bankinhausanovels.com.ng A wurin ma Sarki ya ce ya ba shi ‘yarsa don ya aura.

Jarumi Idrisu ya mike ya yi musu godiya saboda karamcinsu, ya kuma sake yi wa Sarki da mutanensa godiya saboda yarinya da aka ce za a ba shi aure, ya ce shi yanzu ba shi da lokacin yin aure don irin babban aikin da ke gabansa wanda kuma bai san hakikanin ranar da zai kammala ba ma, in ma har ya yi tsawon rai zuwa ga kai wa ga nasara ke nan.

Ya ce musu daga nan yana nufin danganawa da bayan duniya ne don saduwa da Sarkin aljanu Sham’una, barawon ‘ya’yan mutane.

Suka ya gamsu da bayaninsa, suka kuma yi masa addu’a da fatan samun nasara. Wani dattijo a cikinsu ya yi wa Idrisu gargadi cewa a kan hanyarsa ya yi hankali don kuwa zai ratsa ta garin wata Sarauniya mayaudariya, sannan kuma ga ta jaruma, komai Karfin jarumi, to kuwa za ta iya kashe shi don ta kashe sun fi a Kirga. Ya kuma sanar da shi cewa dukkan fadawanta mata ne, jarumai na Kin Karawa. Sannan kuma tana da wasu macizai guda biyu da suke bauta wa, abincinsu shi ne mutane, kuma mazaje.
Dattijo dai ya ci gaba da bayanin cewa, “Su wadannan macizai tsawon kowannensu ya fi kamu hamsin, kaurin jikinsu kuwa kamar kaurin babban

Www.bankinhausanovels.com.ng jaki.ne Dafinsu kuma idan suka tsartawa mutum, to lallai ba zai kai rabin sa‘a daya ba zai zagwanye.

Ita wannan Sarauniya kuma dai tana da wani sihirtaccen ruwa mai dafi wanda in har ka sha shi, to za ka koma ba ka da sauran laka a jikinka sai yadda aka yi da kai. Ba a taba samun mahalukin da ya taba nasara a kanta ba, hasali ma an ce har aljanu shakkar ta suke don ana hasashen Shaidan ne ya daure mata gindi.

‘Tana da abubuwa uku wadanda take saurin samun rinjaye da su, na farko tana da wani irin doki da babu mai irinsa, na biyu akwai tsafaffen takobi, na uku kuma shi ne ba ta da na biyu a fannin kyau da cikar halitta. Kana ganin fuskarta sai jikinka ya mutu a kama ka kamar kaza. Kai sai kaza ma ta fi ka wahalar kamawa.”

Dattijo ya Kara da cewa, “Ya kai Idrisu tun da ka taimake mu har Allah Ya raba mu da wannan babbar masifa ta dodo, to mu ma za mu dan taimaka maka da irin abin da Allah Ya huwace mana. A duk fadin duniyar nan babu inda maganin dafi ya ke kamar wannan tsibiri namu, ni kuma wannan ilmi shi ne babban abin da nake tinkaho da shi na gadon gidanmu.” Dattijo ya sa hannu a cikin wata ‘yar jaka da ke Www.bankinhausanovels.com.ng
rataye a kafadarsa ya dauko wani Kullin magani ya ce wa Idrisu, “Ga wannan magani ka sha kai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAMUNA
avatar
abdullahi-dahiru

6 months ago

Reply

Good

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to abdullahi-dahiru

Keep following our site for more hausa adventures novels

Please Login or Register in order to submit comment