Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yadda suka saba.

Sarki ya ce, “Don Allah in Ardo ba zai damu ba, ina da wata bukata guda daya ko kuma alfarma da nake nema ayi mini.”

Jin haka sai Sarkin Fulani ya ce, “Ran Sarki ya dade ai ka wuce nan. Fadi abin da kake bukata kawai in har lallai kana da bukatar fada din, amma ko ma mene ne nina amince.”

Sarki ya ce, “Ina so ne ka aurar da ‘yarka Bingyel ga dana Bashari.”

Sarkin Fulani ya ce, “Na ba shi. To ai ni wannan kamar Karin girma ne a gare ni. ‘Yata ta auri dan mutunci kuma dan Sarki mai adalci.”

Abin ka da dattijai, nan suka yanke shawarar za a yi bikin cikin wata biyu masu zuwa. Shi ma abin da ya
sa za a dan dauki lokaci haka shi ne dalilin da Sarki ya
Www.bankinhausanovels.com.ng bayar cewa wasu daga cikin manyan bakin da za a gayyata daga nesa suke, kuma bai kamata a ba su dan gajeren ‘okaci ba, don baa san irin hidimomin da ke gabansu ba, musamman kasancewar mafi yawancinsu ba su dade da barin garin ba a dalilin nadin sarauta da suka zo.

Sarki ya yi kiran Bashari ya ce masa, “Ai sai ka ba da tukuici, babanka Sarkin Fulani ya mallaka maka Kanwarka kake ce mata ko? To za a yi bikinku cikin wata biyu.”

Bashari bai san lokacin da ya buga tsalle ba saboda tsananin murna, ya manta cewa a gaban Sarki ya ke, watakila kuma kasancewar don ya riga ya saba da su ne? Nan take ya fara zabgawa Sarki kirari da addu’a, “Hadari sa gabanka inda kake so. Allah dai Ya sa ka gama lafiya.” Ya juya wurin Sarkin Fulani ya yi godiya cike da kunya.

Sarki ya yi magana, “Yauwa Bashari sai ka je da babanka ka nuna masa gidansa?”

Sarkin Fulani da Sarki suka yi sallama, Bashari kuma na gefe ya kasa zaune ya kasa tsaye, har sai da suka fita suka nufi sabon gidan Sarkin Fulani. Bayan ganin gida sai ya rasa abin da zai ce, da Kyar Bashari ya ciyo kansa ya hau ingarman dokin da aka ba shi ya
nufi riga, don da ya ce ne sai ya sake komawa ya yi wa Sarki godiya.

Kafin Ardo ya isa gida, tuni Bashari ya kewaye a sukwane zuwa can cikin daji inda budurwarsa ke kiwo, don ya rigaya ya san cewa ba ta riga ta taso zuwa gida ba. Yana zuwa ransa a bace ya ce mata, “Kin ji wai za a yi mini aure nan da wata biyu.”

Ta ce, “To mene ne amfanin ka zo ka fada mini? Da mana gaya maka ina ‘yar Fulani mai kiwo ina dan Sarki>”

Bashari ya katse ta, “Af na manta ban yi miki albishir ba, Sarki ya yi wa babanki sarautar Sarkin Fulanin wannan kasar gaba daya, sannan kuma yanzu shi ne babban mai ba Sarki shawara na musamman.”

“Yar Fulani tana jin haka sai cikin bacin rai ta ce, “Da ma mahaifina ai Sarkin Fulani ne, kuma wannan abokantaka da Sarki babu wani amfani ko kuma tabbas ciki, don da a ce yana son sa ai ba zai hana dansa ya auri ‘yarsa ba. To ni zan fada wa babana kada ya amshi ko daya daga cikin abin da Sarki ya ba shi, kuma jibi-jibin nan za mu tattara mu bar muku Kasarku, kai kuma ka je ka auri Sarauniyar kyau ta duniya. Da ma an ce mini ku kado ba ku da alkawari amma Www.bankinhausanovels.com.ng ji ba, na ga kamar kai daban ne. Amma babu komai.” Ya jawo sarewarsa ya fara yin wata irin busa da sukan yi tare, sai ta sa hannu ta fisge, ta ce, “Kaicona da na koya maka yadda ake busa wannan abu, ga shi yanzu za ka je kana busa wa wata.”

Bashari ya Kyalkyace da dariya sannan ya ce, “Ke, ba na son shirme. Ga sanarwa ta musamman, Bashari dan Salihu kuma dan Sarki Shahzad, kado, zai auri Bingyel ‘yar Fillo a cikin watanni biyu masu zuwa. Kuma ga ta nan a gabansa tana kallon sa har an gama shirya komai tsakanin Sarki da mahaifinta.”

Murna kuma ba sai an labarta ba.

Sai ya kasance a duk ranar da babu karatu ko kuma wata hidima da zai yi wa Sarki, to Bashari yana wurin ‘yar Fulani a cikin riga suna tsimayin bikinsu. Ji suke yi kamar su jawo ranar.

Sarkin Fulani kuwa tuni ya yanke shawarar cewa sai an yi bikin ‘yarsa sannan zai koma cikin birni ya tare.

Ana nan dai har ya kasance yanzu saura kwana uku kacal a daura auren.

Bashari ya nufi riga don ganin budurwarsa, amma abin da ya tarar ya yi matukar ba shi mamaki, wato bukkokin gidan Sarkin Fulani ne gaba daya a Kone.
Www.bankinhausanovels.com.ng Ya yi tunanin samun wani Bafillatani ya tambaya amma sai ya sauya shawara don babu kowa a wurin, kuma kasancewar tsakanin gidan Sarkin Fulani kafin a sake samun wani gidan akwai tafiya mai ‘yar tazara.

Ya ji kamar zai zautu don tsananin rudewa. Ya nufi inda suke kiwo, ba kowa, ya dauko sarewarsa yana busawa ko ta ji ta amsa, amma shiru. Sai ya yankewa kansa shawarar cewa lallai duk yadda aka yi ‘yar Fulani yaudarar sa ta yi ba auren sa za ta yi ba, tun da dai ga shi sun kora dabbobinsu sun gudu. Kuma abin mamaki ita da dattijo babanta.

Ya rasa inda zai sa kansa. Ya sake komawa can riga din amma dai abin da ya bari shi ya tarar.

Daga Karshe dai ya dauki dangana.

Ya hau dokinsa don komawa cikin gari. Ya fara tafiya ke nan sai ya hango tarin wani abu a cikin ganyayyaki. Da ya matsa sai ya ga ashe Sarkin Fulani ne kwance male-male cikin jini, ya Kusa da shi kuma Harande ne dansa, Kanin ‘yar Fulani, shi wannan ma ba sai an tambaya ba, daga gani ka san ya mutu. Ya gaggauta ya dora su a kan doki ya daure ya wuce gaba yana ja har cikin gari. Ya je ya ba Sarki labarin irin wannan abin bakin ciki da ya afku. Aka dauki Sarkin Fulani aka shiga da Www.bankinhausanovels.com.ng shi. shi don fara yi masa magani, shi kuma marigayin aka yi masa janaza.

Zaton sarki yafi karfi a kan cewa ko makiyansa ne suka yi wa Sarkin Fulani wannan aika-aika don irin taimakon da ya bayar wurin jinyarsa. Suka yi zaton shi ma Sarkin Fulanin sun halaka shi ne, suka kwashe masa dabbobi, suka kashe masa da, watakila ma ita kanta yarinyar ba a nan suka kashe ta ba. Daga Karshe dai aka yanke shawarar saurarawa har sai Sarkin Fulani ya farfado don gane hakikanin wannan danyen aiki.

Kafin nan sai aka baza jarumai, Kudu da Arewa, Gabas da Yamma ko za a dace a samo dabbobin tare da kamo wadanda ke kora su kafin su Ketare kasa.

Kana ganin Bashari ka san yana cikin tashin hankali, don duk ya fita hayyacinsa. A kullum yana cikin dajin nan inda suke kiwo da ‘yar Fulani, wani lokaci ya dauki sarewa yana wata irin busa wanda duk rashin tausayinka za ta iya sa ka hawaye, in ma ba ka barke da kuka ba.

Bayan misalin kwana uku da faruwar lamarin, sai aka samu Sarkin Fulani ya farfado yadda zai dan iya magana. Aka tambaye shi abin da ya faru, sai ya rika nuna wa Bashari alama, hadi da ‘yan kalmomin da ke iya fitowa daga bakinsa cewa ita ‘yarsa ba a kashe ta Www.bankinhausanovels.com.ng ba An tafi da ita ne, kuma ba kowa ne ya aikata wannan ba ta hanyar dauko jingar miyagu, sai Jae, wato dan Fulanin nan da ke taya su kiwo. Jin wannan fa sai hankalin Bashari ya tashi. Nan take ya nemi izinin Sarki cewa yana son a ba shi dama ya je ya nemo ta duk inda take, Sarki kuwa ya amince. Aka hada shi tare da jarumai dari da isasshen guzuri. Ya yi sallama bayan an yi masa addu’ar samun dacewa.

Abin da ya fara yi sai ya koma rigar su Sarkin Fulani, daga nan sai ya wuce inda suke kiwo ya daga hannunsa ya nuna wa jarumansa Kudu ya ce, “Ina zaton ‘yar Fulani wannan hanyar aka bi da ita, saboda haka nan za mu bi.” Ya wuce gaba suna biye.

Kwana tara suna tafiya ba dare ba rana, sai dai in gajiya ta yi yawa a tsaya a huta. Kusa da kan iyakar Kasa sai suka hango shanu fululu farare fat, Bashari ya cewa jama’arsa su dakata. Ya lababa har sai da ya kai kusa da dabbobin sosai ta yadda zai iya tantancewa, kuma cikin gaggawa ya tabbatar wa kansa cewa babu shakka wadannan shanun su ‘yar Fulani ne. Sai dai kuma abin mamaki ga shanun nan su kadai suna tsaye babu kowa tare da su. Saboda haka sai Bashari ya yi zaton ko sun ya da zango ne don hutawa. Www.bankinhausanovels.com.ng ya koma zuwa ga jama’arsa ya ba su izinin yi wa yankin wurin gaba daya zobe amma cikin dabara. Shi kuma Bashari sai ya nufi cikin dabbobin shi kadai. Dan Fulani da sauran abokansa ashe duk suna kan bishiyoyin da ke wurin, kuma ganin Bashari ya nufi cikin shanu sai suka dudduro. Murna ta rufe Ja’e dan Fulani kasancewar yau ga shi ga Bashari su kadai, zai aika da shi lahira. Da ma tun asali shi dan Fulani ya rabi Sarkin Fulani ne kan nufinsa na samun damar lallaBar ‘yar Fulani ta aure shi har ya sami kusantar dukiyar, to ga shi wannan kadon ya shigo duk ya lalata masa shiri, yana neman tashi a huhun-ma’aho. Wai har kado zai aure yarinya shi kuma Ardo zai koma cikin birni. Saboda haka sai ya yanke shawarar gayyato abokansa suka zartar da wancan danyen hukunci, suka sace yarinyar suka tattara dukiyar gaba daya suka gudu. Daga dirowar dan Fulani sai ya fara surfa wa Bashari ashariya tare da cewa, “Yau kwananka sun Kare.” Amma kafin shi da mutanensa su isa wurin Bashari, tuni askarawa sun kawo kan su. Sun yi Kokarin kariyar kai wanda a sanadin haka, biyu daga cikin Bata-garin suka rasa rayukansu, aka kama sauran har da jagoransu dan Fulani. Bashari ya tambaye shi inda’yar Fulani take, amma takaici da taurin kai suka hana shi magana. Aka yi aka yi amma ina. Daga karshe dai Bashari ya tunzura ya ce su yi ta bugunsa ko zai mutu shi ake so ya mayar da jawabi ba sauran abokansa ba. ‘Yan cika aiki suka fara aikinsu, har sai da dan Fulani ya tabbatar da cewa yana gab da tafiya kiyama matukar bai yi magana ba, sai ya ce zai yi magana.

Ya ce shi dama a cikin zuciyarsa ya san cewa ba shi da wata cikakkiyar bmkata ta auren ‘yar Fulani. Kuma abin da kawai ya sa bai kashe ta ba tun farko saboda ya tabbatar da cewa in ya sayar da ita, to zai sami isasshen guzuri da Karin dukiya don tana da kyau. Ya ce kwana biyar ke nan da ya sayar da ita dinare dubu uku ga wasu fatake, kuma sun riga sun tsallake Kasa da ita. Ya nuna hanyar da suka bi.

Bashari ya ware mutum talatin daga cikin askarawansa, ya ce su kora shanun da masu laifin su kai su wurin Sarki, kuma su sanar da shi cewa shi ya shiga cikin wata kasa neman ‘yar Fulani don kuwa an sayar da ita. Aka yi wa dan Fulani daurin goro shi da abokansa hudu da suka rage, aka kama hanyar babban birni da su. Bashari kuwa da sauran jama’arsa sai suka bi hanyar da aka nuna musu, suka fara tafiya kwana da kwanaki. Kwatsam ba zato ba tsammani sai suka shiga wani yanki cikin wata kasa wanda babu komai cikin sa sai rairayin hamada. Amma tunanin cewa zai Kare da wuri sai suka yi ta kutsawa ba dare ba rana har dai guzurin ruwansu ya Kare, suka fara mutuwa da daidai da daidai. Babu damar komawa baya, gaba kuma ba a san yawan nisa ba. Kafin kwanaki kadan duk sun fadi sun mutu in banda Basharida mutane shida kawai. Baa . ma maganar dawakansu don yanzu babu ko daya. Allah cikin ikonSa sai aka yi sa’a wani dan Sarki ya Zo zai wuce ta hamadar. Ya ci karo da mutane duk sun marmace, ya ce a bincika ko akwai masu sauran shan ruwa, shi ne fa aka samu aka ceci Bashari da sauran wadanda ke tare da shi. Aka ci gaba da tafiya ana jinyar su don duk ba su san inda suke ba. Bayan sun wuce wannan hamada sai suka iso bakin wata Korama wadda ke kewaye da korayen ciyayi laya-laya. A nan suka yada zango har aka kammala jiyyar marasa lafiya, suka murmure tare da dawowa cikin hayyacinsu. Ya yi wa dan Sarkin matukar godiya tare da labarta masa dalilin fitowarsa daga gida. Dan sarki ya ce, “Ashe duk kanwar ja ce, mu ma abin da ya fito da mu ke nan, soyayya Ce. Www.bankinhausanovels.com.ng Ya fara ba Bashari labari cewa, “Sunana Amir. Ni dan Sarki me, wanda ya fada cikin wata irin matsananciyar soyayya. Mun yi alKawari ni da wannan yarinya cewa za mu yi aure bayan watanni uku, kawai sai yarinya ta Bace. Mun yi nema ni da rundunata da ‘yan leKen asirina cikin duniyar nan lungu-lungu ko za mu dace, amma ina? Mun fara yanke tsammani ke nan sai muka sami labarin cewa akwai wani shahararren Sarki a can Kasar Arewa wanda za a iya samun cikakken labari a wurinsa, don shi ma irin wannan ta faru ga ‘yarsa, ta Bata Bat. An ce wani Sarkin aljanu ne ke sace ‘ya’yan mutane kyawawa yana tafiya da su. Weannan shi ne dalilin da ya sa na karkato na fuskanto gida don in sake shiri mu tafi Kasar wancan Sarki don samo labari, daga can kuma mu wuce neman wannan barawo na ‘ya’yan mutane. Ba aljani ba ko Shaidan ne sai mun ga abin da ya ture wa buzu nadi.”
A haka ayarin Amir dan Sarki ya mika, a kwanaa tashi har suka isa garinsu. Labarin dawowarsu ya bazu ko ina a gari, mata sai rafka guda suke ta yi, babu abin da ake ji ko ina sai kade-kade da wakewake; kowa yana ta murnar cewa wani nasa ya dawo. Dan Sarki da Bashari suka wuce unguwar dan Www.bankinhausanovels.com.ng Sarki don kintsawa kafin su je gai da Sarki. Cikin lokaci suka fito suka nufi fada, in ka ga samarin nan biyu sai ka dauka wasu taurari ne saboda irin kyan da Allah Ya yi musu.

Sarki ya rungume dansa yana mai cike da murnar dawowar sa. Ya ba mahaifinsa labarin Bashari, shi kuma ya karbe shi cike da girmamawa.

Sarki ya ce, “Ku dai samarin wannan zamani al’amarinku sai ku, yanzu kowannenku ya bar yankinsu, ya shiga cikin hadarin neman yarinya? Kun san halin mata kuwa? Ko da yake yanzu dai duk a Kyale wannan zance. Shin ka yi nasara game da abin da ka fita nema?”

Yarima Amir ya ce, “A’a, Allah Ya taimaki Sarki, amma na sami labarin inda za mu iya samun labarinta. Shi ne na dawo in shirya in sake fita, an ce can kasar Arewa akwai wani Sarki wanda shi ma hakan ta faru ga ‘yarsa kuma an tabbatar cewa yana da cikakken labari. Daga wurinsa kuma sai in tsunduma duniya neman ta.” Da Sarki ya ji zancen dansa sai ya ce, “Ya kai dana, ina ji maka tsoron yawo cikin duniya, ka dai ga dan Karamin misalin abin da ya faru ga abokinka, mafi yawancin jama’‘arsa sun rasa rayukansu, kuma ga shi kai ne mutane suka sa wa ido a matsayin magajina.

HMMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE WWW.BANKINHAUSANOVELS.COM.NGYARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM’UNA CHAPTER 14 BY HARUNA USMAN
YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM'UNA BY HARUNA USMAN Jun 28, 2022 0 1 Add to Reading List


YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAM’UNA

CHAPTER 14 BY HARUNA USMAN

Www.bankinhausanovels.com.ng

MUN TSAYA

Sarki ya ce, “Ku dai samarin wannan zamani al’amarinku sai ku, yanzu kowannenku ya bar yankinsu, ya shiga cikin hadarin neman yarinya? Kun san halin mata kuwa? Ko da yake yanzu dai duk a Kyale wannan zance. Shin ka yi nasara game da abin da ka fita nema?”

Yarima Amir ya ce, “A’a, Allah Ya taimaki Sarki, amma na sami labarin inda za mu iya samun labarinta. Shi ne na dawo in shirya in sake fita, an ce can kasar Arewa akwai wani Sarki wanda shi ma hakan ta faru ga ‘yarsa kuma an tabbatar cewa yana da cikakken labari. Daga wurinsa kuma sai in tsunduma duniya neman ta.” Da Sarki ya ji zancen dansa sai ya ce, “Ya kai dana, ina ji maka tsoron yawo cikin duniya, ka dai ga dan Karamin misalin abin da ya faru ga abokinka, mafi yawancin jama’‘arsa sun rasa rayukansu, kuma ga shi kai ne mutane suka sa wa ido a matsayin magajina.

ZAMU TASHI

Sai dai kuma soyayya ta rufe maka idanu ko mulkin ma naga kamar ba ka damu da shi ba. Kuma shi mulkin nan in ka bari ya Kwace maka, to ba za ka sami wani ba, amma ita mace kana zaune sai a kawo maka ko guda nawa kake buKata.

Yanzu ma maganar da ake yi akwai wata yarinya da da na ajiye musamman don kai. Kuma na tabbata kyan ta da cikar halittarta in bai wuce na yarinyar da kake wahala a kanta ba, to ba ko zai gaza ba. Ka je yanzu bayan mun gama cin abinci ka gan ta.”



Da dan Sarki ya ji zancen mahaifinsa, sai ya yi godiya sannan ya ce, “Ya kai babana mai girma, ina fata ka yi mini gafara a game da abin da zan fada.”

Sai Sarki ya ce, “Aminci gare ka ya dana. Fadi

jawabinka.”

Dan Sarki ya ci gaba, “Godiya nake. To a cikin jawabin mai martaba ya ce akwai mata da yawa, sai dai kuma abin da Sarki ya sani ne cewa ko a cikin rigunan Sarki akwai guda daya wadda ya fiso. Haka ma dawakin Sarki da ‘ya’yansa. Haka nan ma a duk cikin abin da Sarki ya mallaka ballantana kuma cikin matansa. Saboda haka ya babana, ni yanzu hankalina yana wurin wata kuma ina ji a cikin raina cewa ban

yanke tsammani ba. Ni yanzu in ba ita na aura ba, to gaskiya ina jin hankalina ma ba zai dawo kan sarauta
ba.

Ranka ya dade ita kuma waccan yarinya da ka tanadar mini, to na gode Allah Ya Kara girma, amma Baba ka yafe ni. Ni ko ganin ta ma bazan yi ba don na san ba zan so ta ba alhali masoyiyata na raye…”
Bashari ya yi sauri ya dubi abokinsa ya kifta masa ido, yana mai masa nunin cewa ya bi a hankali, har ma a daidai nan Basharin ya katse masa magana ya ce, “A‘a, kai dai kada ka yi saurin yanke hukunci, ka bari ka gan ta mana.”



Sarki ya ce, “Yauwa, ka ji magana ke nan.” Sarki na zaton lallai in ya ga yarinyar, to dole ya ji yana son ta ko da ba kamar waccan ba, ta yadda zaa iya lallaba shi ya aure ta. Daga nan ko ba komai zuciyarsa za ta fara rage tunanin waccan da baa san inda take ba.

Aka gabato da abinci da kayan marmari iri-iri, a

kan cewa in sun kammala Bashari zai raka abokinsa su shiga su ga yarinya. AMMa al’amarin yarinya ‘yar Fulani kuwa, lokacin da Ja’e mai yi wa mahaifinta kiwo shi da abokansa suka sassari mahaifinta a gabanta suna tunanin sun kashe shi kamar yadda suka kashe kaninta, to ita sai suka daure ta suka kada tare da shanu. A kan hanyarsu suka sayar da ita ga wasu fatake a kan dinare dubu uku.
Da fataken da suka saye ta suka lura da kyanta, sai suka yi ta tattalin ta suna kulawa da ita yadda ya kamata har suka isa birnin Jagirgiri inda Sarki Mus’ab yake sarauta. Suka Ki kai ta kasuwa don wayo da kuma lura irin ta kasuwanci. Maimakon haka sai suka tsayar da shawarar tallatawa Sarki.

Suka sa Bingyel ta yi wanka sannan suka kawo sutura da kayan kwalliya irin na alfarma suka ba ta ta fece ado. Babu shakka in ka gan ta za ka ce ko watakila tana cikin kyawawan aljanun nan ne da akan yi labari. Wadannan fatake ba su zame ko ina ba sai fada, aka yi musu iso suka shiga har wurin Sarki. Ita kuma yarinya ta rufe jikinta kaf har da fuska.

Aka yi sa’a kuwa a ranar Sarki Mus’ab na matukar jin nishadi. Ya tambaye su dalilin zuwansu.

Fataken nan suka rusuna, sannan sai babbansu ya ce, “Ran Sarki ya dade, haja ce irin taku ta manyan sarakunan duniya muka kawo maka, yarinya ce balagaggiya wadda har yanzu yarinya ce ba ta zama mace ba tukuna. Kyakkyawa ce wadda za ta iya bugawa da kowace mace a bangaren kyau.”



Sarki ya umurci yarinya ta bude fuskarta, ai yana ganin ta sai ya zuba mata idanu kurui yana mamakin irin wannan kyau nata. Zuciyarsa ta fara sarke
Www.bankinhausanovels.com.ng sarken cewa, “ tsarki ya tabbatar wa wanda Ya halicci wannan kyau.”
Yace, “Nawa kuka sayi wannan yarinya?”
Suka ce, “Dinare dubu uku ne Allah Ya ba ka yawan rai.” Sarki ya ba Ma’aji umurni cewa a ba su dinare dubu goma, sannan a ba kowannensu manyan riguna goma-goma, suka fadi suka yi godiya don tsananin murna da irin wannan sallama. Ita kuma yarinya Sarki ya sa aka shiga da ita cikin gida tare da umurnin cewa kada a kuskura a sa ta aikin komai, kuma a rika ba ta abinci na alfarma da isasshen kayan marmari don jikinta ya Kara kyau da ni’ima, tare kuma da sutura irin wadda ta dace da kyakkyawa irinta. Jakadiya ta ce, “An gama, ran Sarki ya dade.”
Tun daga wannan rana da aka shiga da ‘yar Fulani cikin gidan Sarki, babu abin da ya sauya na irin halin Bacin ran da take ciki tun daga lokacin da dan Fulani ya yi musu wancan mugun alkaba’i. In ta tuna dan’uwanta da mahaifinta da a iyakar saninta ta tabbatar da cewa an kashe su a gabanta, da kuma saurayinta Bashari, duk sai abubuwa su dugunzuma su cakude mata a zuciya, sai ta fashe da kuka. A mafi yawan lokuta kuma da zarar hakan ta faru, to sai ta dauko sarewarta tana busawa, wata irin busa mai sa tausayi a wurin mai sauraren da ke da masaniyar yadda busa ke tafiya. Amma a wurin sauran gamagarin mutane, sai mutum ya ji busar kamar don sa nishadi ake yi, wanda hakan ya sa in ta fara sai mutanen cikin gidan Sarki duk su natsu suna ta saurare.

Duk abin nan da ake yi da duk lokacin nan da aka dauka, Sarki bai taba shiga inda take ba. Sai dai duk lokacin da ya ji busa, to ya tabbatar da cewa ita ce. Kuma shi kansa yana matuKar jin dadin busar.

Wannan shine al’amarin ‘yar Fulani.

Amma shi Bashari mun bar shi a fadar Sarki yana cin abinci da abokinsa dan Sarki tare da Sarkin suna ta hira irin tasu ta saraki. Sarki na ta nuna musu irin kyan wannan yarinya da kuma KoKarin tausa dansa a kan cewa ya bar wa Allah, in waccan yarinya da ya ke nema an gan ta, sai ya yi ta biyu ko ta uku da ita. Shi kuma yaro yana ta kewaye-kewaye cikin kunya. Can sai suka ji busar sarewa na fitowa daga cikin gida, sai Sarki ya ce musu, “To, yarinyar da na tanadar maka ce ke wannan busa.”

Suka yi tsit suna sauraro, shi kuwa Bashari sai tsigar jikinsa ta shiga tashi, ya tabbatar da yanayin busar kuma ya fahimci wadda ke yin ta. Ai nan take ya sa hannu cikin aljihunsa ya zaro tasa sarewar ya fara
Www.bankinhausanovels.com.ng mayar da busa.
Mamaki ya rufe Sarki da dansa, amma tun kafin su sami damar yin tambaya sai ga yarinya ta fito daga cikin dakinta a guje ta nufe inda su Sarki ke cin abinci, don ita ma ta riga ta tabbatar da wanda ke busar. Matan gida suka biyo ta a guje suna zaton ko ta zautu ne. Tana shigowa Bashari ya gan ta, ai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On YARINYA NUR DA SARKIN ALJANU SHAMUNA
avatar
abdullahi-dahiru

6 months ago

Reply

Good

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to abdullahi-dahiru

Keep following our site for more hausa adventures novels

Please Login or Register in order to submit comment