Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dan haka WUTSIYAR RAKUMI tayi nesa da ‘kasa nida ke! A rayuwa bana hangen na sama na, Banda ma soyayya bata shawara da kai, Ina ke ina ni Afrah? A ture wannan ma, wallahi tallahi Ko na aure ki bazaki ji dadin auren ba, wallahi Afrah bazan iya soyayya ba ko burbushin soyayya babu a zuciata wallahi, idanma akwai to ba irin ta auratayya bace, Ina miki soyayya irin wadda yaya yake yiwa kanwar sa, Ina miki soyayya irin wadda dan uwa musulmi yake yiwa y’ar uwar sa musulma, Ina miki son so a matsayin ki na ‘ya mace, domin duk duniya bayan son da nake yiwa fiyayyen halitta sai wanda nake yiwa kaina da mahaifiya ta da iyaye na da yan uwa na, Toh fa sai mata, domin duk mace ko mai kankantar shekarun ta abar ‘kima ce wallahi, Dan haka ki dauki ‘kimar ki da darajarki ta diya mace, dan Allah Afrah na ‘dauke ki ‘kanwa wallahi, Dan Allah kiwa zuciyar ki Adalci! Ki tsaya a matsayin ki, Mulki ko sarauta, kudi da malantaka duk basa siyan soyayya, Insha Allahu rabbi mijin ki yana nan tafe, na gari mai komai da addini ya tanadar, kyakkyawa dan babban gidah irin ki! Wanda yafi ni komai, sa...”

Kasa karasa wa yayi saboda wani marayan kuka da Afrah ta saki mai tsuma zuciyar duk wanda ya saurara, ta riko hannun sa, cikeda sheshshek’a tace,

*“KAI MIN HALACCI* Shamsudden, wallahi na amince bata biyu ba, ko ata hudu ne, a shirye nake dana aure ka...!”

Shiru yayi yana kallanta, a yanzu yadda take yasan ba zata fahimci abinda yake son ta fahimta ba, cikin jan numfashi tare da zare hannunsa data rik'e yace,

“Afrah kona aureki ba zan yi miki amfanin komai ba, wannan dalilin ne yasa kikaga bana kula mata saboda bani da sha'awar mace an cire min duk wani feeling, Saboda wani ciwo da nayi, ke in takaice miki abin haihuwar dake jikin nan ma an cire shi ki gaya min idan na aureki ta yaya zan sauke nauyinki dake kaina? Idan na baki abinci na baki gurin kwana ai kinsan basu kadai bane hakkin aure ko? Shi yasa nazo baki hakuri dan Allah ki lallashi zuciyarki kice mata ta dena son wanda bashi da wani amfani.”

Wannan itace sabuwar dabara da shahararriyar ‘karyar da Shamsuddeen yake tunanin zai yi amfani da ita wajan yin rejecting d'in duk wata da zata kawo mishi zancen soyayya. Wani irin kuka ya kwacewa Afrah da alama bataso jin wannan mummunar kaddarar ba wadda ta afkawa sahibinta, kanta yana sunkuye taji yana cewa,

“Na gode da nuna soyayyarki gare ni Princess Afrah.”

Yana kaiwa nan ya tafi yana murmushi dan yasan babu ta yadda za'a yi yarinya da ranta da lafiyar ta aure shi a haka....
*ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE, DAN GIRMAN ALLAH MAI SO YA KARANTA, YA BIYA DUKA BIYAR DIN DARI 5 NE. SUNE KAMAR HAKA*

*BURI DAYA*
MAMUH GEE

*DAURIN BOYE*
SAFIYYA HUGUMA

*WUTSIYAR RAKUMI*
BILLYN ABDUL

*SAUYIN KADDARA*
HAFSAT RANO

*KAI MIN HALACCI*
MISS XOXO

*MASU SON SIYA, ZASU IYA TUNTUBAR LAMBOBIN MU KAMAR HAKA;*

08030811300
07067124863


*WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER;MISS XOXO🧕🏼*

*27....*

Gabaki d'aya Fa'iza jikinta rawa yake yi hankalinta ya tashi tayi saurin ajiye wayar tare da dafe kirji, Saboda barazanar fad'o mata da taji yana yi, wannan abin da ta gani shine ya hanata fahimtar lectures har suka tashi, gaba d'aya tsoran Raheenah ya mamaye zuciyarta koda zasu fita sallah ce musu tayi suyi gaba zata taho. Tana zaune a bakin gate tana jiran Aliya zuciyarta banda bugawa babu abinda take yi bakinta ya kasa dena furta innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, mutanan da suke wucewa sai kallansu take yi tana ganin tamkar zasu gano abinda ta gani hakan yasa da kyar take hadiyar yawu.

Wayarta ce ta fara ringing saboda a rud'e take yasa ko tsayawa ta duba sunan mai kiran ba tayi ba kawai ta kara a kunne bakinta na rawa tace,

“Hello..”

“My soulmate.”

Yana fad'ar haka ta gane ko waye, wato Muhamman S kasan cewar haka yake kiranta, cikin rashin nutsuwar zuciya ba tare da ta san ma ta amsa masa ba tace,

“Na'am.”

Wani irin dad'i ya kama Muhamman S dake kwance akan kujera a d'akinsa tare da sakin wani k'ayataccen murmushi, tabbas ya fara kamo zuciyar Fa'iza dan gashi nan ya kirata da sunan da kullum take cewa karya kuma kiranta da shi har sai ya bayyana kanshi, idanunsa a lumshe yasa hannu yana shafar kwantaccen gashin dake hab'arsa yace,

“Ya school, kun dawo gida ne?”

“A'ah ina jiran Sissy.”

Yadda yaji muryarta ne yasa gwiwarsa yin sanyi ya tabbatar bata cikin nutsuwa hakan nema kila yaji tana bashi amsa kai tsaye ba tare da taja ba kamar yadda take yi,

“Meke damunki naji muryarki haka?”

“Ba..b..ba..komai.”

Tayi maganar bakinta yana rawa cikin rarraba kalmomin, zaune ya tashi tare da kurawa center table ido tamkar Fa'izan ce a gurin yace,

“A'ah akwai ki gaya min me yake damunki.?”

“Kaina ne yake ciwo”

Ta fad'a a takaice saboda ya rabu da ita bata son magana a wannan yanayin da take ciki,

“Toh menene ya janyo miki ciwon kai?”

“Lectures ne kawai.”

“Toh ki tashi ki tafi gida mana ki kwanta ki huta.”

“Zan tafi ai Sissy nake jira.”

“No ki tafi ta taho tunda bakya jin dadi, bana son ki zauna kar ciwon ya tsananta please kiyi tafiyarki

“Bazai yiwu ba ai, itama tana jirana kaga idan muka fara 'yar haka da ita toh zamu raba kai abinda Baba baya so kenan.”

“Toh shikenan ni bari na kyaleki idan kinje gida na kiraki bye.. lo...”

Bata bari ya karasa ba ta katse kiran dan bashi take muradin ji ba, tana son jin kalmar ne daga cikin zuciya ya fito daga bakin Shamsuddeen ba wai na wani ba wanda ma yake b'oye mata kansa. Karar shigowar sako taje (message), kamar karta bud'e dan ta san shine sai dai ta daure ta bud'e dan tana son ma wani abun yazo mata wanda zai sa ta manta da videos din da ta gani gashi sunki barin cikin idanunta har yanzu gane take tamkar yanzu ta bud'osu,

“Yes I m selfish..thats why I care for u..thats why i’m scared to lose u, thats why I miss u every moment..thats why I cry for u in your absence, thats why I pray to god for your happiness..thats why I always wish that one day u wud be mine. Yes I m selfish, because I love u my soulmate..”

Lumshe ido tayi bayan ta gama karantawa tana ta faman tunani wanda ta rasa gano na menene ma bare tasan akan abinda take yi, duk kwanyarta ta tsaya da aiki har Aliya da Nawal suka karasa wajan bata sani ba sai da Aliyan tasa hannu ta dafo kafad'ar sannan Fa'iza tayi saurin d'agowa cikin firgici,

“Tunanin me kike yi haka?”

Kai ta rike tare da mik'ewa tsaye, kafin tayi magana motar Nawal dasu Nour suka fita da ita tun d'azu shine sai yanzu ta dawo ita da Lamfat da Daddy abokin Lamfat d'in. Kallanta kawai Nawal tayi fuskarta a matuk'ar b'ace, hannu ta kawai ta mik'awa Nour wacce ta bud'e k'ofar barinta, suma su Lamfat suka fito tare da dorawa Nawal car key d'in a tafin hannunta, cikin d'an b'acin rai Nawal tace,

“Wannan shine karo na biyu da kina karb'ar motata kije kisha zamanki a inda kika tafi, ki gaya min tunda kika tafi sai yanzu kika dawo duk an gama lectures, shin mene amfanin kawoki school d'in?Chilling? Ko mene?”

“Wallahi Nawal ba abinda kike tunani bane, munje gidan sister d'in Lamfat ne ta haihu shine fa ta rik'e ni ta hanani tafiya, yanzu ma sai da nace mata zan kawo mota shine ta barni na taho, please sorry ba zan sake dadewa ba daga yau.”

Wata banzar harara Nawal tayi mata tare da bud'e motar ta shiga, su Aliya ta yiwa nuni da su shigo amman Aliya ta kad'a kai tare da matsawa gurinta tace,

“Kiyi tafiyarki kawai Nawal zamu hau napep mungode.”

“Dan Allah ku shigo karku batamin rai kuma.”

“Allah bazamu hau ba, bari kiji na gaya miki indai har za'a dinga d'aukar motarki ana zuwa wani gurin wanda zai dasa zargi wallahi ba zan sake shigarta ba, idan ke kina ganin babu wata matsala ni a gurina babbar matsala ce, kawai ki tafi mun gode.”

Tana kaiwa nan ta yiwa Fa'iza magana suka tafi, hakan kuwa ya tayarwa da Nawal hankali, kenan idan aka gano abinda akeyi a motar ta haka kowa zai juya mata baya? Lallai akwai matsala dole ne ta gyara manufarta akan mutane, dole tayi takatsantsan itama. Da wannan tunanin ta fita daga gate lokacin har su Aliya sun tari napep sun shiga.

Tunda suka fara tafiya Aliya ba taji ko tarin Fa'iza ba hakan yasa ta kalleta tare da kura mata ido tana tambayar ta,

“Sissy wai meke damunki ne naga sai tunani kike?”

Fa'iza taja numfashi ba tare da ta kalli Aliya ba saboda mai napep tace mata,

“Bari sai munje gida.”

“Okay Allah yasa dai lafiya, kuma Allah yasa ba Muhamman S bane ya b'ata miki rai.”

Ba tace komai ba har sukaje gida, wanka sukayi sannan suka ci abinci basu samu damar tattauwa maganar ba domin d'akin gwaggo Aliya ta tafi suna ta gwabzawa akan Aliya tace dole sai ta kwanta akan cinyarta amman gwaggo taki sai faman tureta take yi, hakan kuma yasa Aliya turo baki tare da cewa,

“Shikenan tunda bakya son na kwanta akan kafarki, nasan da ace Mamana tana raye komai nace tamin sai tayi min shi, Allah sarki maraici mutuwa mai raba 'ya da uwa harma da uba.”

Nan da nan kuwa jikin gwaggo Talatuwa yayi sanyi, cikin nuna kulawa tasa hannu ta janyo ta zuwa jikinta tana shafar bayan ta tace,

“Ke baki san wasa ba da anyi miki abu sai ki fara zancen maraici, sai kiyi ta kwanciya ai idan kika kumburata ai Baban kune zai yi wahalar siyan magani.”

Murmushi Aliya tayi k'asa-k'asa domin tana sane ta fadi haka saboda tasan idan ba hakan tayi ba toh gwaggo ba zata bari ta kwanta a cinyarta ba, bayan ita kuma tana jin dad'i tare da jin farin ciki a duk lokacin da taji ta a kafar gwaggo sai taji tamkar suna tare da Maman ta. Daga haka gwaggo na bata labari tayi bacci, Fa'iza ta leko d'akin taga tuni Aliyan tayi bacci, d'an tsaki taja tare da karasawa wajan tasa hannu tana tashin ta gwaggo tace,

“Kibarta mana ko wani abun zaku yi?”

“A'ah gwaggo so nake tazo muje mu kwanta wallahi yau tsoro nake ji bazan iya kwana ni kadai ba.”

“Toh kema kizo nan ki kwanta ni ku tayani kwanan.”

Hakan kuwa aka yi Fa'iza taje ta kwanta akan katifar gwaggo, gabaki d'aya ta kasa bacci da ta rufe ido zata hango videos din cikin wayar Raheenah, ganin ta kasa bacci ne yasa ta mik'e ta fita daga d'akin ta koma na Umman su wacce take zaune tana shafa maganin zafi a k'afarta saboda tayi tsami wajan zaman d'inki. Shirun da taji Fa'iza tayi shine yasa ta d'aga da kai tana kallonta, gabaki d'aya taga ta kurawa wata atamfa dake can gefe ido kai kace makauniya ce, cikin mamaki Umma tace..

''Fa'iza lafiyar ki kuwa?'”

Cikin firgici ta waigo kirjinta sai duka yake yi ta daure tace,

“Lafiya lau Umma kawai na kasa bacci a can dakin.”

“Ahh! Ina ita Aliyan?”

“Umma tana d'akin gwaggo kuma harma tayi bacci.”

Kad'a kai Umma tayi tare da cewa.

“Toh ki shiga ciki ki kwanta, kiyi muku addu'a.”

Toh kawai ta fad'a tare da shiga d'akin, sai da ta gyarawa k'annanta kwanciya tayi musu addu'a sannan ta kwanta itama, ko wayarta bata d'akko ba a can d'akinsu ta barta.

Wajan karfe goma Aliya ta farka daga kan pillow din da gwaggo ta d'ora mata kanta, tashi tayi lokacin itama gwaggo tayi bacci, Aliya ta fita tare da komawa d'akin su zata canza pad, tana shiga taji wayar Fa'iza na ringing taje ta duba, Muhamman S ta gani kamar karta d'auka sai kuma ta d'aga dan ta sanar dashi cewar Fa'iza bata kusa, tana karawa a kunnanta taji yace.

“My soulmate.”

Wani irin dum! Aliya taji a kirjinta domin kamar muryar Yaya Sahal d'inta taji, bakin ta yana kyarma tace.....

*SWITZERLAND 🇨🇭*
*UNIVERSITY OF ZURICH*

Successfully su Shamsudden suka ‘kare karatun su na MBA, A satin da akai convocation dinsu, suka ‘dora da PGDIPIL, wato ‘post graduate diploma in professional international Law’ for a period of 6-9 months, maximum of a year....

Lalle Allah qadirun ne ala manyasha’u, Domin shi d’in mubawayi ne gagara misali, Lalle Allah ahadun samadu ne, Mamallakin kowa da komai, Mai raya wa mai kashewa, mai azurtawa mai talautawa, Sarkin da babu wani sai shi, Kamar yau ne Shamsu Gaja ya tafi ‘kasar Switzerland yin karatun degree na farko, wanda dan siyasar unguwar su ya ‘dauki nauyin karatun su kyauta, Allah mai d’aga wanda yaso a rana tsaka, Ya azurta Shamsu tun yana yaro karami yake sana’ar rake, ya dawo ta y’ar kiosk/container/canteen/ Shago. Daga nan ya shiga kiwon baru da sauran su, Rana tsaka Allah ya ‘daga shi zuwa ‘kasar Switzerland domin ‘karo karatu! Wanda da karatun boko shine abunda shamsu yafi tsana a rayuwar sa, baya gaban sa baya burge shi, ya tsani duk wata harka inde ta jajayen fata ce ma gaba d’aya, Amma sai dai me? Alkalamin qudra ya riga da yazo da shamsu sai yayi karatun boko, sai ya ‘karu da boko, domin mafi yawan alkhairin kasuwancin sa yafi riba daga boko! Umma ta kance Allah dai ya zaba maka abunda yafi alkhairi Shamsu! Domin bakasan inda abincin ka yake ba, Toh gashi Allah yasanya mafificin alkhairin sa daga bangaren boko ne!

Yau ga shamsu mai rigar ‘yar shara, Mai shago, mai charging waya, Mai baru, Mai rake, Mai hatsi da soya bins (soy beans) ya zama wani abu a rayuwa, Ina abokan sa dake mai dariar sana’ar sa? Yau ina Aliya dake gasa mai maganganu don ta raina ajin sa? Kada ka rena sana’a komai ‘kan’kantarta! Domin Allah yana sa albarka a cikinta, harka hab’aka a rayuwar ka, Ya halatta kasuwanci yai hani da riba, Shi arziki ko dukiya ba sai kayi boko ba, Toh abun dai sai hamdalah kawai! Domin Shamsudden a yanzu yanada matakin, Bachelor of science degree in international relations, yanada MBA (Master of business administration), And successfully yanxu ya gama PGDIPIL(post graduate diploma in professional international law).

*SHIN WANENE SHAMSUDDEN AL’AMIN BUHARI?!*

Shamsudden Al’amin Buhari yana d’aya daga cikin ‘ya’yan Malam Al’amin Buhari da Malama Bintu Muhammad, Su biyu Allah ya albarkarci iyayen su dasu, Na fari shine Muhammad Garzali sai na biyu kuma Shamsudden, kuma shine auta, daga kansa Allah ya tsayarwa hajia Bintu haihuwa, Malam Al’amin Buhari Ardo, ‘Dan asalin garin yola ne ‘Njamboli Fulani, Mahaifan sa sun rasu, sai rik’on sa ya dawo kano wajen ‘kanwar mahaifiyar sa, anan ya tashi har ya kai minzalin karatu, ya fara primary anan kano inda ya nufi Sumaila Local Govt nan ya fara karatun gaba da primary (junior/secondary school) a makarantar Gwamnati dake garin. Anan Allah ya had’ashi da Bintu Muhammad, lokacin da ta kai tallan alala makarantar su, Nan dai suka kulla zumunci mai aminci da ita, har ya kai su ga aure, A lokacin bayan ya gama makarantar ya koma kano yayi NCE, a Sa’adatu Rimi collage of education dake kumbutso LG. Ya koma ya nemo auren ta, Malama Bintu Muhammad ‘yar kauyen Sumaila ce, unguwar ‘kofar fada dake kauyen na Sumaila, Mahaifin ta Malam Muhammad Ubale malamin Allo ne dake koyarwa a makarantar Allo, Mahaifiyar ta kuwa marigayiya malama Hadiza itama y’ar asalin kauyen Sumailan ce, Malam Ubale kuma almajiranta ce ta kai shi kauyen na Sumaila, Amma usulin sa ‘dan Bornu ne, Abun dai sai sam barka kawai!

•••. •••. •••. •••.

Filin jirgin dank'am yake da al’umma wad'anda sukaje taryar 'yan uwa da kuma ma'aikatan gurin, kowa ka gani cike yake da nishad'i da walwala. A hankali jirgin dake tsaye a saman filin jirgi na tashi da sauka na malam Aminu kano dake jiran a gama saita mishi inda zai sauka ya tsaya, sannu a hankali ya fara sakkowa yana bud'e tayoyinsa wad'anda zasu temaka masa wajan zama da k'afafunsa. Sai da ya gama saisaita kansa a filin jirgin sannan kofar da za'a fito ta bud'e a hankali har ta gama bud'ewa. Janye ya fito da ‘dan karamin akwatin sa, ya rataya wata jaka a bayan sa mai ‘dauke da tambarin designer na Dkny(Donna Karan New York), Sanye yake cikin ‘kananun kaya, Samfarin Italian Switz Suit Royal blue color, takalmin sa da jakar duk kalar kayanne, Wutsiyar hannun sa na dauke da agogon Rolex Gold, dan yatsan sa na tsakiya kuwa azurfa ce, ya saka portal white glass ‘kirar Pablo, daka ganshi kasan jin dadi na tattare dashi, Kallo d’aya za kai masa kasan a duniya dai yagama dacewa da komai, Fari ne ‘kal kamar bature, Yanada tsawo sosai, Sannan ba shida kib’a kuma bai cika rama ba, kana iya hango 8packs dinsa ta zatin ‘kirar jikin sa, Kyakkyawa ne na ajin k’arshe, yanada wasu irin sihirtattun idanu tamkar mai bacci, gasu dara-dara TubarkAllah, zamu iya kiran su da sexy sleepy eyes, ‘kwayar idanun sa brown color ce! Hancin sa tamkar shiya zana shi don tsini, bakin sa ‘dan karami ne pinkish color, yanada dimples, Dan koyaya ya yamutsa fuskar sa sai sun lotsa, yanada kwantaccen gashin kai(curly) da cika, kamar na larabawa, hakan ya samo asali ne ta tsatson fulanin rugar kakan sa Ardo, girarsa cikakkiya ce domin ta kusa had’ewa, yanada saje da gashin baki, da bature kewa laqabi da side burns and beards, Kai alkalami yayi kad’an wajen zayyano zati da haiba ta Shamsudden, Shamsudden ya zarce tunanin mai karatu, Gaba d’aya tashin ‘kamshin turarukha yake yi, kai abun dai ba sauki, yana zuwa passengers lodge ya hango Yaya Garzali tsaye yana zuba idanun ta Ina zai hango ‘dan uwan nasa, gefe d’aya kuma Ummah ce tana zaune da carbi a hannun ta, gaba d’aya sai kallo ya dawo kan Shamsudden, duk hankulan yan matan dake wajen kansa suka koma, kobi takansu bai yiba, cikin sauri Shamsudden ya nufi wajen Ummah, bakin sa har kunne, ji Ummah tai kawai an rungumeta ta baya, cikin zakuwa yace,

“First love! I love and miss you..”






_Toh jama’a Shamsudden ya dawo, Yanzu labari ya fara💃🏿a hayye nanaye😹_ #Asha hutun Sunday lapia😍❤🏽🤝🏽🤝🏽


_ALLAH JIKAN IYAYEN MU DA RAHAMA🤲🏻

*WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER;MISS XOXO🧕🏼*

*28/29*

“Ba ita bace Aliya ce 'yar uwar ta, please dan Allah wanene kai? And meyasa kake b'oye mata kanka?”

Shiru Sahal yayi jikinsa yayi wani irin mugun sanyi shima sai yaji tamkar ta gano shi, amman yana fatan kar Allah yasa hakan kasan cewar bai fiye yi mata magana ta irin wannan yanayin ba. Amman yanzu da take yi masa wannan tambayar mai zai ce mata? Babu abinda zai iya ce mata domin bashi da amsar bare kuma kwarin gwiwar yin magana, hakan ne yasa ya dinga ce mata,

“Hello... Hello... Hello, Soulmate ko kinyi bacci najiki shiru? Hello..bana jinki ko bacci kikai? Good night love! may angel wishes watch over your sleep tonight.”

Yayi maganar a zuwan baya jinta kwata-kwata sannan ya katse kiran, sakato Aliya tayi tana bin wayar da kallo, lallai wai daman haka ake soyayya?shin me yasa ita Yaya Sahal bayayi mata irin wad'annan kalamai masu dad'i da sanyaya zuciya, haka Muhamman S yake yiwa Fa'iza kalaman kauna ita da bata son shima, me yasa suda suke son juna ita da Sahal amman koda wasa bai tab'a yi mata kwatankwacin furucin kauna ba, lallai akwai gyara a cikin lamarin soyayyarta da Sahal dan tafi kowa buk'atar jin kalaman kauna, wato abin sauyawa yayi ita take yiwa Yaya Sahal furucin kauna yayin da ita kuma Fa'iza Muhamman S yake mata ita kuma kullum budar bakinta bata sonshi musamman ma da yake b'oye mata kansa.

Ajiye wayar tayi taje ta d'auki pad ta nufi toilet, jikinta ta gyara sannan ta koma d'akin su ta janyo wayarta itama, tunani take ko ta turawa Yaya Sahal text tunda shi yaki ko kiranta bare suji muryar juna. Murmushi tayi tare da tunanin kila aiki ne yake yi masa yawa shi yasa baya kiranta da dare sai dai ita ta kira shi, kai koda safe koda ranar itace take nemansa amman shi sai dai idan zaizo gidan su sannan yake kiranta yaji suna gida, ta shiga gurin rubuta sako ta fara rubuta masa good night text,

_'I was waiting the night to see the moon it didn't appear, so I called the sky 2 ask where the moon is? It told me the moon is reading your sms, good night and sweet dreams my Habibi.'_

Sai da ta sake karantawa kafin ta tura masa tana murmushi kamar ita ya turowa, tashi tayi taje tasa phone d'in a charge ta koma ta kwanta gefe d'aya zuciyar ta kasa manta muryar Muhamman S da taji a waya. Shirun da taji Fa'iza bata dawo d'aki ba shine yasa ta mik'e itama ta nufi d'akin Umma dan ganin ko tana can, tana zuwa kuwa ta ganta kwance cikin su Hidayya tana shak'ar baccinta, itama ta rab'a gefenta ta kwanta, ranar dai duk a can suka kwana daman Umma tana d'akin Baba Suleiman hakan yasa bata san Aliya ma ta koma d'akin ta ba sai da asuba da ta shiga.

Da safe suna breakfast Aliya ta gaya mata cewar Muhamman S ya kira ita kuma ta d'aga so ita tana jinshi shine baya jinta dan haka har abinda ya fad'a saida Aliya ta sanarwa da Fa'iza sannan ta karkare da cewa.

“Ke yanzu Sissy daman haka Muhamman S yake kashe ki da dad'ad'an kalmomi? Gaskiya Sissy kinji dad'i wallahi ni Yaya Sahal bai tab'a ce min koda I love you ba, kullum nice nake gaya masa haka.”

Numfashi Fa'iza taja tare da cewa,

“Kema Sissy kin matsawa bawan Allahn nan, tuntuni na gaya miki akan ki rabu dashi ki kama wani ga samari nan Allah ya baki kamar zasu kasheki amman kin wani nace masa ba dole ya dinga yi miki rashin mutunci ba, ni wallahi haushi kike bani ma.”

Aliya ta d'auki Jakarta tare da sanya takalmi tana cewa,

“Sissy ke baki san love bane shi yasa kike ganin kamar ina shirme, amman bari kema ki fad'a tarkon soyayya wallahi sai na yi miki dariya.”

Fa'iza tayi murmushi cikin ranta tana cewa, 'Aliya kenan ni tun kafin nasan meye so nake soyayya ballantana kuma yanzu da nake jin tafi ta da zafi duk da na rabu da ganin wanda nake so d'in.' Amman a fili itama jakar ta d'auka ta zura takalmi da hijjab tana cewa,

“Sannu wadda tasan so, nima ina yin nawa ai kawai kece baki sani ba.”

Dariya Aliya tayi saboda bata yadda da maganar ba, sallama suka yiwa gwaggo Talatuwa sannan suka yiwa Umma suka fita daman Baba Suleiman ne zai rage musu hanya dan haka shi a cikin mota suka gaida shi ya basu transport money, tun a cikin motar yake taja musu kunne akan su kula da tarbiyar da suka basu karsu biyewa kawaye musamman maza, sosai sukaji yana taja musu kunne akan duk abinda suka san yana faruwa a cikin jami'a har suka rabu akan idanunsa suka shiga napep shi kuma ya wuce inda zashi. Fa'iza na son yi mata zancen Raheenah amman tana tsoran kar Aliyan taje ta tare ta da maganar hakan yasa ta had'iye son gaya matan da kyar domin abin yana damunta tana son fitar dashi daga zuciyarta. Tun akan titin tarauni kowacce ta hau Adaidaita sahun ta, Saboda Aliya zasu tsaya a kano poly suyi assignment tukun, Akan hanyar Fa'iza ta zuwa Old site ne taji mota ta tsaya a gefenta, kamar karta kalla sai kuma taga tabbas gurinta aka zo hakan yasa ta tsaya.

Zuge glass d'in aka yi anan taga Husnah, murmushi tayi kafin tayi magana Husnah ta rigata ta hanyar cewa,

“Shigo Yaya Sahal ya karasar damu munyi late yau sauran 'yan mintuna Mr Adewale ya shiga.”

Babu yadda Fa'iza ta iya dole ta bud'e baya ta shiga ta zauna, ba tare da ta kalli Sahal d'in ba ta fara gaida shi, shima kamar kar ya amsa sai dai ba zai iya ba dole yasa shi amsawa yana satar kallanta ta cikin mirror d'in dake gabansa,

“Fa'iza kinyi aikin nan kuwa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment