Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kuma Dikko da kanshi ya kaini. Wayarta ma a kashe. Daga gidanta gidan Inna mukaje kamar dai kullum yauma haka taita habaice² tana zagin Dikko wai bazai zauna mata a kujera ba , ƙiri² Inna ta koma wata zararra , shiko murmushi yayi kaɗan ya samu wuri a saman kafet ya zauna , nima kusa dashi na zauna. Haka taita zaliƙe²n da ita kanta bata san dalilin yinshi ba , taita zaginshi tana aibatashi saida ta gama kaf tace idan yaji fushi ya sakar mata "ya , shafa kanshi yayi ƙasa² yace ban gaji ba ya faɗa yana suɓaro baki a sakace , saida ta gama dashi ta juyo kaina tace kema ɗayar mara zuciyar kaza² nima taci gaba da sheƙeni har ta gaji tayi shiru , saida ta sauka ta gama da kanta ta rufe bakinta mukayi mata godiya mai gida Dikko ya sauke mata manya kuɗi muka wuce gidansu.

Ajiyeni yayi ya tafi huɗɗoɗin shi , Momy kuwa sai ɗan zungurar min ciki takeyi tanasan ta gano wani abu ne daga gareni akan Sharifa. Shiru nayi nidai idan ta matsa min da tambaya saidai ince mata Momy ban sani ba wallahi , wai har yanzu munayin faɗa da Dikko ? Tambaya ɗaya takemin ni kuma ansa biyu nake bata , ah umm. Gajiya dai tayi ta ƙyaleni , har ɗaya saura na dare bai dawo ba saidai ya turo Ashiru ya maidani gida , wato yau ya samu hanyar tafiya wurin "yan iskan matanshi ko ? Ita kuma Momy harma ta yadda da ƙaryar da yayi mata wai ya fita da Dady. Dan da Ashiru yazo tafiya dani sai ta kirashi wai shi yazo da kanshi ya tafi dani mana , shine yace mata yana tare da Babanshi kenan dan karta dameshi. Tun a mota nake kiranshi , shine ya turamin da saƙo wai yana meeting , danma ya ɗaukeni kidahuma. Ci gaba nayi da kiranshi ƙarshe kashe wayarshi yayi. Ashiru ka kaini wurin Dikko , lafiya ? Ya tambayeni ? Lafiya qalau shine yace ka kaini. Mai gidan ranki ya daɗe ? Tou meye a wurin da bazanje ba ? Ai banma san inda yaje ba , daga haka bai sake magana ba , nice naci gaba da cewa amma ai a wannan motar yake a ina ka samoshi ka ɗauko motar ne ? Shiru yayi ya ƙyaleni , fita nayi daga motar ba tare dana sake cewa komai ba na nufi ciki , Papi yana kwance a palon ƙasa yana bacci saman kujera. Ɗaukarshi nayi ina taɓashi ya buɗe idonshi yana shashshekar kuka , ɓata fuska yayi a hankali ya rufe idonshi yana cewa Yaya.... Kila ya dakeshi ne. Me yayi maka ? Saida ya sake sauke ajiyar zuciya da yanayin bacci ya sake cewa Yaya.....

Majalisar ɗinkin "yan matan tashi. Muji , yau da Jiddah ya fara zama sai kuka take masa wai Ya Yazeed yace zai aureta kuma tayi hidima dashi mai girma amma yana ta wani zamewa baya ɗaukar wayarta kaza׳ , shi Dikko ma daga farko bai gane wane Yazeed take magana ba saida tayi mishi bayani , tou shi Yazeed harma ya zama Yaya baida labari ? Hidimar da ta ita Jiddahr tayi ma shi Yazeed ya tambayeta , cikin inda² tace kawai dai kayi mishi magana muyi aure. Cikin rashin fahimta yace waike kece zaki auri Yazeed ? Ey , jinjina kai yayi tare da ɗan karkace kanshi ya tafi duniyar tunanin rayuwa irin ta gidan Yazeed.....

Ƙaton gidane ginin zamani , ya tsaru gidan iya tsaruwa kuma anyi mishi ado da ciyayi masu kyau. Ɗakin mai gadi da ɗakin janareto , a gefe kuma ga wasu irin zabga²n motoci masu masifar kyau da tsada an jera wanda shi mamallakin gidan ne ya ciyosu a harkar wasan danbe. Ajiyar zuciya Dikko ya sauke a wahalce yana jinjina kanshi , duk duniya shidai baya so yaga mace tana wahalar rayuwa. Baya so yaga rayuwar mace tana tangal² , kallon Jiddah yayi sannan ya gyara zamanshi ya miƙe ƙafafuwanshi yana daga saman kujera ƙafa ɗaya saman ɗaya. Wannan inji haka ake cika shi da mai safe rana da dare har gari ya waye a cikin awanni 24 haka yake aiki ba'a kashe shi saida idan za'a zuba mishi mai ko idan ya lalace , duk fitulun gidan a kunne suke suma cikin awowi 24 da wasa ba'a kashe su dare ko rana addau² haka suke amma ɗakin matar gida ko kwan fitila bata dashi , babu wata cima a gidan ita kanta matar gidan duk haɗuwar gidan da tsaruwarshi wankau takeyi tana ciyar da kanta.

Ga hausawa da wani irin hali wai sai kaje zuminchie wa ɗan uwanka amma ka tattara burinki baka kallon rayuwar gidan sai girman gidan , idan ka ɗora mata buƙatarka tace bata dashi sai zagi da gulma munafuka ta tattare komai ta hanamu , daga ita sai "yan uwanta sai iyayenta , ta shanyeshi ta hana ya bamu ko ya bata ta bamu ta hanamu , shin tana samu tana dashi ko bata da ? Kudai , a baku.........׳ kamar mutuwa. Shi Yazeed inuwar giginya ne shi , yana dashi da ya bawa matarshi gara yaje ya zuba harajin wasan danbe , gashi cikakken ɗan iska wata rana ma a gidanshi yake kai mata matan bariki , azzalimin namiji ne dan shi matarshi ta gida ma bai ɗauketa a bakin komai ba , "ya "ya ne ta kwarkwartsa mishi bi da bi a tunanin ta idan ta aihu da yawa ko zai gyara halinshi amma abun sai ci gaba yakeyi kamar ana daka mishi tsawar bakin iyaye. Ni a tunanina duk mai shi zai bada ne , kyauta dai bata kawo talauci. Haka kuma rowa bata kawo arziƙi , duk mai bayarwa baya rasawa , idan kuma ka samu kaci kai ɗaya dan kar ka bayar ka rasa ? Tou wata rana ma gaba ɗaya barin duniyar zakayi da kuɗin da duk tattalin da kakeyi karsu ƙare ko kuma ka tara da duk wani tsari naka na rayuwa , tou fa lallai duk zaka barsu ka tafi kai ɗayanka kaje wata rayuwa ta daban. Gara dai idan kun samu kuɗan taimakawa masu buƙatar taimako sai kuma Allah ya ƙara taimaka muku.

Caf Yazeed cikakken ɗan tasha ne. Baida mutunci ko kaɗan , dan ko A C ɗakin matarshi da yasa daga farko daga baya ƙwaƙwulewa yayi taci gasar danbe. Amma saboda riya yabar iyalinshi da wahalar rayuwa , ko tace baya bata abinci tana cikin wahala , sai ace bata godiyar Allah , abinci buhunna² gasu na ajiye a store taci ɗin ma ta ci ƙaniyarta dan tasan ba nata bane ba kwalliyar gidane saboda mutane su gani suce yana da kirki , bayan wani lokaci kuma ya jera mutane layi ya rarraba musu shi sadaka.

A anguwar sai zaginta akeyi ita marowaciya ne tabar "ya "yanta da yunwa sai azabar neman kuɗi kamar zataje dasu lahira. Wani faɗa da sukayi har iyaye suka shiga ciki tace har a c ya cire a ɗakinta da palo tace yasa musu fanka ya ƙiya , shine yace tana wurin gyara , ganin iyaye yasa yaje ya samo hoton a c n yazo ya maƙala mata , shima tayi magana yace ya gyaro itace ta lalace shi bata da tattali kaza² , aka haɗu aka bata rashin gaskiya , shi kuma ganin ya samu sa'a yasa yaketa gurje mata mutunci da wahala. Duk wanda ya kalli gidan Yazeed akace ansan sunan wani abu waishi wanki ko wankau ? Sai su "yan cikin anguwa sunce ƙarya ce , ita kuma tunda anguwar masu kuɗi ne take sa ana tattaro mata kaya tana wankewa ta goge tunda dama kayan "yan gayu ba wani datti yakeyi ba , haka azzaliman maza sukeyi dan rashin imani. Shine Jiddah zata shiga ? Allah ya basu zaman lafiya..... Allah ya rufawa An matarshi asiri da tana can tancin ƙaniyarta gata yarinya , wani hali nata ya tuno dan haka yayi taƙaitacciyar dariya , da tace wai ya tsalleke kabbarinta ya wuce , cikin dariya yace niɗin banza An mata , saida yasha dariyarshi Jiddah tana daga gefe tana kallon ikon Allah , shi yama fita daga wannan sabgar ya tafi kallon hotunan matarshi.

Duk hoton daya kalla zaiyi murmushi a ranshi yace An mata rigima , wai Dikko ka tsalleke kabarina kaje kawai , haba An mata kar Allah ya nunamin ranar da zaki tafi ki barni a duniyar nan , bana fatan naga ranar da ni zaki shige cikin ƙasa ki barni , ina so in rayu dake har ƙarshen rayuwata in tafi in barki ki rayu rayuwa mai cike da farin ciki , gaki ga Papi da "yar ƙanwarshi ko ɗan kaninshi , burina yanzu a duniya bai wuce in mutu a hannunki ba , ina sanki׳ ki jarumata..... Hayaniyar dake tashi ne ya dawo dashi daga duniyar kallon hotunan da yakeyi....

Salati yayi tare da fiddo duk girman idanuwan shi ganin Sharifa da wata irin bahaguwar shiga ta jahannama ga fasinja. Rankatakaf su Ashiru suna wurin , shi wallahi kunya ma abun ya bashi , gata ta shigo full battery wato cake take. {{ tana cikin maye }} tasha wasu irin zaƙo²n akaifu ansha girar ido atach har tsakiyar baya , wasu irin "yan kunne girman round insu yakai girman ɗan hannu sai ibar hayaƙi take tana barbaɗashi sama yana bin iska. Jiddah na riƙe da ita sai zazzabga mata mari takeyi wai ranar da Ya D ' K yai mata liƙi ita Sharifar wai tanayi ma ita Jiddah gwalo wai an saketa , tun ranar nake nemanki shegiya ƙazama , shine fa aka cakume rigima. Dikko kuwa lallaɓawa yayi yai layar ɓata bai yadda kowa yaga fitarshi ba. Har baya ganin gabanshi ya shiga mota dakel. Shi gaskiya bawai zaice yana san Sharifa ba , ah tunda dai zai aureta ya kamata ta kasance mai tarbiyar da kamun kai. An mata har hannunshi ta zauna kafin suyi aure amma kullum tana cikin hijabi , gaskiya yana san matarshi ta kasance mai sirrinta jiki yayin da wasu mazan da ba muharramanta ba suke a wuri. Baifa isa yace baya auren Sharifa Dady zaiyi damuwa.

Taya za'ayi shi matar da zai aura ta kasance haka ? Irin wannan dressing ai ba nan akeyi ba , ko a gidanka kayi irin shigar ai zaka saka hijabi idan mutane suna zuwa , tirr mtsww... Gaskiya zai faɗa mata ta daina yin haka shi baya so. Haka ya iso gida da tunani barkatai a zuciyarshi , bayan yayi parking yake ƙara hasko yadda ya ganta zuciyarshi na daɗa soyuwa da ɓacin rai , kai a , a gaskiya a , a , haka ya shiga ciki ranshi a matuƙar ɓace kawai dai yaji babu daɗi yana tayin damuwa har zuwa safe.

Dady kuwa an kaishi asibiti. Bayan likitoci sunyi bincike²nsu suka tabbatar wa da iyalinshi cewa ya samu shanyewar ɓarin jiki , ai uwar Hafsa cewa tayi ita bada ita sa lallen kaza ba , dan ba zata wani iya zaman jinya ba. Da sauranta zata taga gaba tayi aurenta ta gurji sauran shekarun da suka rage mata , wallahi bata zama tayi ta kwasar ƙazanta , Dady ya karkace baki yadda masu irin lalurar suke magana yace baya sakinta , tace bara ta kira inda za'a ansar mata tikitinta na saki a hannunshi tunda ba tare aka haifesu ba , wayarta ta ɗauka tana cewa zaka ga yadda za,a ansar min idan kazo musu da rainin hankali ƙarfin shari'a ba wani ruwanshi da shanyewar jiki zasu tafi dakai su calika ka. A taƙaice dai sun rabu kuma dan rashi inami ta tattara duk ɗan sauran abinda ya rage na ƙaddororinshi tayi gaba dashi wai karya cinye tattalin arziƙin kuɗi "ya "yanta su tashi a hoto , yadda ya nannaɗen nan idan ta zuba mishi ido sai ya cinye kaf kuɗin a wurin jinya.....

Haka taje asibitin da Amisty take ko tausayin Amisty bataji ba , ta ɓanɓare abun ƙarin lumfashin , Amisty ta fara rawar kyarawa , Momy tace kuɗina suna ina ? Faɗamin gidan uwar da kika kaimin kuɗina ko ki tafi lahira tsaye....... Ha׳ Amisty keyi , dariya Momy tayi cikin rashin imani tace rayuwa ko mutuwa.....? Amisty ta nuna rayuwa watom ta mayar mata da abun , mayarwa tayi tare da jaddadawa Amisty kwana biyar ta bata ta haɗo mata kan dukiyarta idan ba haka ba zataje gidan yari , akwai wani sabon d p o da aka kawo acan sabon gari police station inyamuri ne zata haɗata dashi , zatace idan ya anshi kuɗin ya ɗauki one miliyon haba kundai san inyamurin mutum da kuɗi.....

Halima mijinta da sauƙi sosai anma sallomoshi ya dawo gida , yana dawowa kuma da zancen ƙarin aure yazo , fitina ya tashi da rashin kunya nan fa ta tattara ƙawaye ana neman mafita. Kowa da irin shawarar da yake kawowa gashi lokaci ya ƙure ita tanayin mamaki a inama ya haɗu da matar da har zasuyi aure.......? Ɗaurin aure ranar juma'a yau saura kwana 4 , wace ce zai aura.......? Wace ce.....׳ ita..........??? A iya sanin da tayi mishi bashida budurwa dan kullum saita zindire wayarshi tayi bincike amma ba wani alamar soyayya , ashe suma maza sun iya munafurci....? Hmmm maji dai.

Hafsa abun yaci tura alhamdu ta kakarewa malam. Itama tana can sun jagalgaleta sun kaita asibiti saboda ciwon hannunta. Sai masifa takeyi itafa lafiyanta qalau duk wanda ya taɓa mata magani zatayi ma mutum uwar watsi..... Gata nan dai suka watsar a asibiti kamar asarar noma , muje gaba daga baya maji me likita yace..........?

Jiddah data ishi Yazeed da kira cewa abokanshi yayi ya tafi hutun honey time , ƙaraurawar nasararshi ta doka zaije ya buga lamba tara ya dawo.......

Shi kuma mai gida Dikko da yayiwa Sharifa faɗa dan toshewar basira sai taje ta faɗawa uwarta Mai gilashi , raɗa ta ƙara yiwa Sharifa tunda ita daƙiƙiya ce. Mai gilashi tace ta dage karta sa shakku fatan nasara.

A tsagina kuwa , yau tunda na tashi jikina yayi min wani irin sanyi , gani nan dai ni ba mara lafiya ba kuma ba lafiyayya ba , yau komai ya kasa shiga cikina saidai in bi wannan kujera inbi gado. Gajiya nayi nacewa Papi yaje yace Yaya banda lafiya. Babu wani ɓata lokaci shi yazo , Pa-Pi kuma bai dawo ba.

Gabana ya tsuguna ya riƙe cikina da duka hannayenshi cike da tausayi yace meye ne ? Yayi tambayar yana kallona. Fashewa nayi da kuka tare da ɗora fuskata a saman kanshi nace nidai banajin daɗi inajin wani abu yanamin babu daɗi kamar zan rasa wani abu a rayuwata , murmushin ƙarfin hali yayi sannan ya da dawo kusa dani ya zauna. A hankali ya jawoni jikinshi yace babu wani abu da zai faru sai alkairi , ummm ? Ki daina biyewa tunanin zuciya zataje tasa ki shiga ruɗun rayuwa , ba gani ba ? Ya nuna kanshi Kalli kuma ina tare dake , meye zai faru ne ? Munayin zaman lafiya kuma ni nakine ke kaɗai. Tou tayama kike tunanin zaki rasa wani abu mai muhimmanci bayan ni ina tare dake , ai kinsan bazan taɓa rabuwa dake ba har abadan duniya , ki kwantar da hankali ki daina wahalar saƙa tabarmar kabar da bata dace da zamanki ba gimbiya Sultana. Idan kinayin kuka hankalina tashi yake tsikar jikina duk ta mimmiƙe , hawaye basayin kyau a wannan kyakkyawar fuskar. Kuka bai dace da rayuwarki ba. Ke kiyi shiru bara ni in miki kukan tunda kina so kiga hawaye a fuska yana zuba. Ah ai sai inyi ke ki huta , baki san ba'asan mai ciki tanayin damuwa ba ? Ko so kikeyi ki haihu ne ? Yayi maganar cikin sigar zaula. Nace ey , hmmm kima ƙara dagewa kina da sauran kwanki zai kai 90 da Allah kiyi shiru ya ƙarasa yanamin hararar so, tou naji kawomin wayata , tashi yayi ya ɗaukomin wayar , bayan ya bani ya zauna ya sake riƙeni. Kowa dai daga ni harshi muna saƙa wani abu a zuciyoyinmu. Wayar Inna na kira babu daɗewa ta ɗauka , bayan gaisuwa mukayi fira da ita lafiya lau babu wani zage²n nan , kuma na haɗata da Dikko shima suka gaisa cikin mutunci , tace ina Pa-pi ? Yace ya fita yanzu. Wai jiya ba'azo dashi ba.

Me yasa shi ba'asan kawoshi ne wai ? Dikko yace insha Allah Ashiru zai kawoshi bayan la'asar , har sai wannan lokacin ? Kubar shi bana so tunda ba zaizo min yini ba. Ashirun ne baya nan idan ya dawo zasu zo insha Allah , har suka gama wayar babu wani alamu na rashin mutunci kowa ya ajiye waya da farin ciki.

Ni kuma kuka naci gaba dayi , yace bari fa ganin ina baki haƙuri ni kinsan abu kaɗan yake ɓatamin rai kodai kiyi shiru ko in tafi ko kuma ke kibar ɗakin nan sai ki zaɓa , nidai gaskiya bazan yi shiru ba , kasan yadda nakeji ne wai ? Sannu yaimin tare da tashi ya fita nima na miƙe nabi bayanshi har ɗakinshi......









*ZAINAB ABBAKAR MATAWALLE. Ina godiya sosai da saƙo uwar gidan KWARATA...*






06/02/2019






*JAMILA MUSA...*
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA RETURN...*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_


Rubutawa...
*JAMILA MUSA...*



*SAI NA AURI D ' K*



🅿 ------ 9




A palo na sameshi zaune saman kujera. Ci gaba nayi da kuka na nufeshi. Hankalinshi yana saman wayanshi yace so kike dai in zaneki ko ? Kusa dashi na zauna nace baka san ya nakeji ba. Riƙoni yayi da hannun da wayar take riƙe cikin tausasassar murya yace baki so in zaneki ne ? Yayi tambayar yana kwantar da firgitaccin idanuwanshi masu saukar da kasala. Kaɗan na kalleshi a kasalance na ɗaga mishi kaina alamar ey. Yace to shikenan jeki ciki ki kwanta ina zuwa. Miƙewa nayi na riƙo hannunshi ina janshi , ba tare daya kalleni ba yace ya wai meye kuma ? Ban bashi amsa ba naci gaba da jan hannunshi , taƙaitaccen kallo yayi min sannan ya tashi muka shiga ciki tare.

Cike da farin ciki Yazeed ya isa gidan Rabiya. Yau ciki aka shiga kasancewar ita matar gida bata nan. Yazeed kuwa tun a waje ya ɓalle botiran gaban rigarshi yana nuna yanayin haɗama. Kai tsaye ɗakin da aka bawa ita Jiddah a ɗakin ta wuce da Yazeed , suna shiga ya rumgumeta suuuu suka sulale saman gado gaba ɗayansu sunayin farin ciki tare da nunawa junansu kowa yayi maraicin kowa.

A gaggauce dai aka shiga gabatar da wasa. Ya nemi yaddar gado da kuma sa'ar makoma sai addu'a na gaba ya samu nasara mai girma. Danshi a tunanin shi a filin wasa ake. Wasan yau yafi ko wane wasa martaba da mutumci a wurin Jiddah , kasancewar an samu wadatuwar fili da tsaftatuwar muhallin da akeyin wasan. Yazeedu kuwa ya ɓata manyan awowi kuma ko wace awa minti da seconds ya bada lafiyayyen naushi mai zama a zuciya har abada. Jiddah ma ta mayar da martani domin ita dama tuni Yayanta ya gogar da ita kuma ta ɗauki karatu.

Rabiya kuwa tunda Yazeed da Jiddah suka shiga ita ta iso gidan , biyosu tayi tana lafiya ? Ina ne zataje da namiji ? Duk babu wanda yaji bare kuma yasan tana magana , suna shiga suka turo ƙofa garam har aka bige ma "yar sa idon banza goshi. Ai bawai Jiddah taji kunya ba ita Rabiya itace taji kunya dan haka ta koma ɗakinta tana neman mafita.

Taya zata iya furtawa Momy wannan zance ? Shedar zina wahala gareshi. Shin wai waye ma yace mata suna aikata saɓo ? Kuma ita bata kamasu sunayi ba , tou dan kawai sun shiga ɗaki ? Ta yuwu wani abu ya faru , sai saƙawa takeyi tana warwarewa lokaci² kuma tana kallon agogo kamar mara aikin yi har Yazeed ya fito , sai yanzu ta gane Yazeed. Shi ɗaya ya fito Jiddah bata biyoshi ba , tou meya faru ? Me sukeyi a ɗaki tsawon awowi 2 har zuwa 3... Ta shiga 3 zafa a samu matsala.....

Saida Yazeed ya wuce itama ta fito ta nufi ɗakin Jiddah. Kwance ta sameta riƙe da wayarta tana ta latse². Da hannunta ta nuna da yanayin karta shiga haƙƙinta cikin warwarewar haruffa tace am Ji-dd- , ah Jiddah am dama nace lafiya naga Yazeed ya fita ? Ba tare da Jiddah ta kalli Rabiya ba tace lafiya qalau kawai kaina ne yake min ciwo ta ƙarasa maganar tana nuna kanta. Ɗan yatsina fuska tayi tare da ajiye wayar ta taci gaba da cewa gashi gida ba kowa kawai sai nayi ma Yaya D ' K waya ina buƙatar magani , shine fa ya aiko abokinshi ta ƙarasa maganar tana watsa hannunta....

A ɗan tsorace Rabiya tace Dikkkkkkkkkko ? Ta kira sunanshi da mamaki cikin jan kalmomi wurin faɗar sunan tare da warware kaf ilahirin gininta. Ummm Jiddah ta faɗa tana jinjina kanta alamar gasgatawa. Rabiya tace taf Dikkon ? Jiddah tace shifa. Fuuu Rabiya ta fita , murmushi Jiddah tayi tare da cewa ai nasan idan na shigo dashi a tafiyar dole zai fito yayi masifa ya tilassa ayi auren , ba jiya naje muyi magana ba shine ya basar dani yana waani dariyar banza , An mata rigima , rigimo. Dariya ta sakeyi kaɗan tare da nunawa da "yan yatsunta sati biyu cif zanyi nayo waje. Wata 3 idda a cikin wata na huɗu zamu tare a sabon gida. {{ G R A }} a wata na biyar kuwa Caca zata kama gabanta , Pa-Pi zai zama nawa , wama ya sani ko jinina ne aka kai can.....? Da yanayin tunani tace babu shakka Pa-Pi nine uwarshi shine yake ƙwaƙwata , oho dai hakan ma bazai hana in kasheshi ba.......

A tsagin Rabiya kuwa tunani takeyi , meye tsakanin Dikko da Jiddah ? Wane irin magani ne ya bada a kawo ma Jiddah ? Ciwon kan ƙaniyarta ? Karfa su maida ita wata gwanjon bisa titi , tana can tana huɗɗoɗinta suyi ta wucewa ba tare da tasan so adadin da ake wucewa ba. Anya Dikko yana da gaskiya ? Kardai zagayewa yakeyi idan bata nan.....? Har zata kira Momy ta fasa kawai ta kira Dikko. Babu daɗewa ya ɗauka ko gaisuwa babu tace yazo yanzu²n nan tana nemanshi. Magana yayi sannan ta bashi amsa da cewa kawai kazo nace idan kuma ni inzo tou... Magana ya sakeyi ita kuma tace shikenan kayi sauri ina jiranka.

Dan Allah kaje tare dani. Cikin faɗa yace wai ina ne zanje dake ? Saida nayi kalar ban tausayi da marainiyan murya nace dan Allah. Baimin magana ba ya ɗauki wayoyinshi , shikenan tunda bara ka fita dani ba Allah yasa ka dawo ban..... Bakiyi me ba ?
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On KWARATA RETURN
avatar
fatima-kasim

4 months ago

Reply

Naji dadi sosai sosai Allah y kara basira

avatar
daiy

4 months ago

Reply

Replying to fatima-kasim

Ameen muma munji dadin kasancewarki anan.

Please Login or Register in order to submit comment