Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tattara kayanshi Dikko yana zuwa ya biyoshi. Tashi na har nayi mata abinda zatayi gulma wa mijina , bayan sun gama tattaunawa tace Dikko kabar matarka ta ɗaura jigida ? Ra'ayinta ne kema kije ki sakawa mijinki. Amma ai baka san jigida yaushe ka fara so ? Da matata ta fara ra'ayin ɗaurawa sai kawai nima naji ina muradi domin tayi farin ciki. Zata sake magana yace dakata da Allah , ke "yar uwata ce matsayinki daban hurimin matata daban. Kiyi magana abinda ya shafeni dake matsala ta gida na ko gyara abinda ya shafeni da iyalina ni ba yaro bane ba nasan abinda ya kamata. Dikko kar kamin rashin kunya kaji ? Ko nayi miki dai ai nasan bana buguwa wurinki. Tou ko dukana zakayi ne ? Haba ina zanyi abun kunya in daki Yayata yayi maganar yana murmushi. Ai da irin haka namiji ke zama mijin tace , ba tare daya kalleta ba yace ni mijin kan tace ne ni. Tana so dai ta suko Sultana Dikko ya tare kuma har sukayi firarsu suka gama ta tafi ita Sultana bata sake fitowa ba.

Cike da farin ciki ya nufi ɗakin An mata. Pa - Pi na kwance wai daga nan yake bawa Mamanshi labari ita dake toilet tana wanka. Shigowar Dikko ɗakin ne yasa yace Yaya zoka nan kaji ya nuna mishi kusa dashi , naƙi inzo ba cewa kayi ka ɓata damu ba , dokina ma baiyi kyau ba ? Ai sai kayi bacci zan maida ka wurin Momy , ɗan guntun tsoki yayi yana turo bakinshi yace ai babu yuwana da wannan Momyn wayyayi ya ƙarasa maganar yana harara... Tou zo kaji. Saukowa yayi yazo inda yake tsaye , kaje kace ma Ashiru ina gaishe shi. Har ya fara tafiya yace kuma dani jakaje ? Dakai zanje mana kayi zamanka idan ka dawo bazanje dakai ba , can janjauna ce kazo ? Ey mana , kuma Pa - Pi kayyayi facci ? Kayi bacci Babana kanayin bacci ina zuwa sai kawai in saka a mota. Amma wayyayi ban zuwa wurin Momy can gackiya , nima bazanje ba kaidai jeka , da sauri ya fita daga ɗakin yana gunguni.

Lumshe idanuwanshi yayi tare da sauke ajiyar zuciya a wahalce bayan Pa - Pi ya fita. Da gudu na fito daga toilet suuuuuu na taho na shige jikinshi. Murmushi yayi amma bai riƙeni ba yace yarinya ya akayi ne ? Kawai inayin farin ciki na faɗa ina fita daga jikinshi na fara tafiya cikin salo mai ibar hankali jigida kuma ta fara ihu. Rufe ɗakinki yayi ni kuma naci gaba da kakkaɓa ƙugu , shima dariyar yayi yaɗan tako da zamarshi. Dariya na sakeyi tare da hayewa saman gado dan a tunanina ko zaimin cuta ne. Cike da shauƙi shima ya hayo gadon ya riƙeni yana shaƙar iska cike da muradi. Zuƙewa nayi ya sake riƙoni a gajiye ya rumgumeni jikinshi da yanayin ƙuruciya. Wai shi shine nake kaɗawa ganye ko ? Saiya lullusani a daren nan , wannan ƙugun da nake masa ingije dashi zai bani labari dan masu garinmu.....

A "yan kwanaki biyun nan dai ban leƙa makaranta ba , gida kawai domin yafi min daɗi saboda mun buɗe sabuwar rayuwa da muke raya kawunanmu cikin tsantsar soyayyar da bama san rabuwa da juna. Rabon da muyi faɗa ko wani yaji fushi harya ɓatawa wani rai yanzu mun daina , Dikko ya jajirce yana ta kwatanci da nuniya. Ranshi fes domin duk yadda ya bada saƙo anshewa nakeyi shi yasa yakeyin farin ciki. Mai gilashi ma a gefe tana ta ɗirkako nata bakin gwargado amma duk abin nan dai Dikko bai haƙura da Sharifa ba Dady yana ta tunatar dashi akan muhimmancin auren sati na gaba za'a saka rana , Yusra dai har yanzu babu ruwanshi da ita kuma ta sameshi har G R A domin sasanci a ranar ta auna iskancin da tunda take duniya bata taɓa ganin namiji da irin shi ba , ta tsorata dan bata taɓa ganin aljani akan namiji ba sai a wurin Dikko , saida tayi fitsarin tsaye saboda firgita , tunda ya rufeta ta inda take tura tsiraici shi yasa ta tafi gabanta gaɗi ta kama tuɓe²n kaya , tunda Yusra take a duniya ita bata taɓa ɗana ya namiji yake ba sai akan Dikko taso taji su kuma mazan ya tasu darajar take ? Anan ne fa yayi bakandamiyar shi. Tunda ta samu aka fito da ita dakel saida tayi jinyar fargaba. Wannan Yusra ba ko wace ce ba itace Yusran data ɓata Sadiyya matar Dikko na farko. Kuma ita bata san shi Dikko ya auri wata Sadiya can ba. A jirgi ta ganshi taji ya mata , nan tayi mishi bariki irin namu na mata hardai suka rabu bai bata numbershi ba. Amma da masifa saida taje ta samoshi.....

Jiddah kuwa wuta kawai take sha a gidan Yazeedu. Shidai Dikko yace ba ruwanshi , kuma bazai wani je ko yayi magana wa Yazeed ba , can suje su babbake ba abinda ya dameshi da sabgar gidan kowa dan shima baya so a shiga sabgar nashi gidan bare har a samu damar sawa matarshi ido. Taje ta sakata An mata ta wala abunta , duk wanda ya taɓota zaici ubanshi ne kawai abunshi , amma idan tayi iskanci shine zai bata wahala kuma dare yayi su shige bargo asha soyayya.

Gadon Inna kuwa suma danginta cewa sukayi ai basai an bani komai ba , dan duk abinda za'a bani ni na girmeshi inji su. Basu bani ba ko tayinshi basuyi min ba haka suka sha shagalinsu kuma suje suma kansu sukayi ma. Halima da abiyar zamanta suna can suma suna cuɗa zaman kishi , Halimatu taga ta kanta ɓarowo hannun maza.

Saida nayi sati ina hutun da babu dalili. Ranar da naje makaranta a ranar Sharifa tayo zugar karuwai suka bani kashin bala'e dakel aka ƙwaceni a hannunsu. Mai gilashi itace aka sa ta kawoni gida ita da Farisa. A waje muka haɗu da Dikko shi zai fita mu zamu shiga , fita nayi na nufi wurin motarshi ina kuka. Mai gilashi itama da kalar sherinta ta fito shima Dikko fitowa yayi cikin tashin hankali. Dakel nakejan ƙafa cikin wahaltuwa kamar zan mutu saboda bala'e , muna haɗuwa na kwanta jikinshi ina ƙara yawan kuka na , cikin faɗa yace me ne² ? Da shashshekar kuka nace karuwanka ne ta dakeni , cikin rashin fahimta yace wace karuwa kuma ? Nanfa Nana Mai gilashi ta ɓalle ta fara rattafa sharri kamar an tirke musulmin da yayi ridda. Tana bashi labari jikinta yana ƙyarma shi kuma zuciyarshi tana fin jirgin sama tashi. Dakel ya haɗe yawun ɓacin rai zufa ta tsirgo mishi da yaga jini nabin jikinta. Lokacin daya ɗago Sultana tuni ta some , wannan kenan.....

Bayan wasu shekaru.....


Wancan duka da Sharifa ta gayyato akayi min saida akayimin aiki. Dukan ya janyo min matsaloli , giccewar ɗa a ciki {{ breech }}. Zubar jini mai tsanani daya ƙi tsayawa. Bayan anyi hoton ciki wato {{ scanning }} sai likita ya sanar dasu cewa akwai buƙatuwar yimin aiki na gaggawa saboda placentar ta safko , matsalar bugawar zuciya da sama da yadda ya kamata wato {{ fetal tachycardia }} sannan kuma matsalar bugun zuciyar akwai alamun zai koma ƙasa ga yadda ya kamata wato {{ fetal bradycardia }} duk da ganin cewa lokacin haihuwa baiyi ba , nan sukayi ta allureni da alluran da zai taimaka lafiyar ɗan kafin ayi aikin. Suka kuma shirya sanya baby a kwalba da kuma ci gaba da yi mishi wasu allurai har zuwa wani lokaci saboda l b w ciki wata bakwai. Satinmu shidda a asibiti aka sallamemu muka dawo gida da wani ɗan magen yaro suka haɗomu da wanin zanin raino mukai ta fanan goya yaro ta gaba daga ni har Babanshi. Pa - Pi kuwa tunda yaga wannan ɗan mitsitsin ɗa ya daina ɗagama gidan ƙafa koda wasa. Ba'ayi taron suna ba wannan umarni daga mai gida yaro yaci sunan Baba Binna muna kiranshi da Khalifa.

A ranar da sukayimin dukan kuwa Dikko a wurin ya barni ya shiga mota cike da ɓacin rai ya tafi neman Sharifa. Mai gilashi da taimakon wasu daga cikin yaranshi suka tafi asibiti dani. Duk wanda yaji bana lafiya acan ya sameni kafin wani lokaci duk wani ɗan uwan Dikko ya bayyana idan dai yana kusa. Dikko kuwa ya nemi Sharifa harya gode Allah bai ganta ba , ita kuma daƙiƙiyar taita kiran Mai gilashi. Ƙarshe Mai gilashi cewa tayi Malam yace da zaiyi mata aiki amma daya buga ƙasa ya gano ta taɓacin amanar wata aminiyarta , wani attajiri ɗan siyasa yazo auren ita aminiyar ke kika rufe ciki wai haka yace , shine nace shin ko kin gane ko wace ce ? Iyakar tunanin Sharifa ta kasa hasasowa. Mai gilashi tace tou daƙiƙiya wannan ba ko bace nice..... Kuma nice nan na shirya komai ta yadda kika gani na rusa miki wannan auren jaka , tunin duniya nake ƙufule dake yadda kika hanani ci ga kaiwa ga nasara tunda naji kince SAI KIN AURI D ' K nace ma zuciyata idan dai ta bari kika aureshi saina rabata rayuwa da gangar jikina. Nice nan na ɗauki nauhin komai na shirya na kuma gabatar , idan kika sake kirana zan saki sauran hotunan wa duniya naki kamar yadda kema kika ɗauki hotuna na da nake a gurɓataccen yanayi kika samu nasara wurin ganin kin hana auren. Kin hana nawa kema na hana naki 1/1 sai kuma kin sake , idan kuma kika sake kirana saina shafe farin ciki daga rayuwar ahalinki tana faɗin haka ta ajiye waya.

Shi kuma a ranar har dare yana gidansu yana yayyafa ruwan rashin mutunci , waishi ko shi baya dukan An mata tunda ta samu ciki. Shine aka samu wata tsagera taje tayo gayyar ƙatti ? Waishi maza zasu dakar mishi mata ? Da ciki aka dakar mishi mata ? Har dare yana can yana abu ɗaya , Momy tace a fitar dashi ta daina ganinshi , wannan riƙo da akayi mishi da zumar lallashi shikenan ya birke ya fara sai kashe , waye yace wai a riƙe shi ne ? Yace baya so ana taɓashi kaza². Shikenan fa ya mimmiƙe ko za'a tashi duniya saiya ramawa An mata dukan nan bazai yadda ba , wai ko an faɗa musu jakace matarshi ? Sai ayi mishi abu dan cuta idan kuma yayi magana sai ace bashi da haƙuri , tou saiya rama kuma bamma gajiya duk wanda yayi mata sai yayi mishi ko waye kuma ko wacece............. Daga nan ya ɗauke.

Dady kuma tara su Ashiru yayi yace gaba ɗayansu sun cuceshi sun kuma munafurceshi. Me yayi musu sukayi mishi haka ? Bayan su sukace mishi Babanshi ya warke ya haƙura ya daina neman magani , me yasa² ? Me yasa sukayi mishi haka ne ? Wannan ce soyayyar da suke bugun ƙirji cewa suna iya bawa Babanshi fansan rayukansu ? Karo na farko daya ga cin amana zahiri. Ba kuma zai sake yadda da kowa ba. Haƙuri Ashiru ya bashi sannan ya buɗe mishi gaskiyar lamarin yadda yake cewa.

Rashin lafiyar da Mai gidansu yayi bayan ya samu sauƙi. Sun faɗa mishi abinda Mustapha yace , amma sai kuma wata matsala dashi dai Mustaphan yace. Wai asirin da mutum yaci a abinci da wanda mace tayi "yan maƙale² dashi a jiki ta kwanta dana miji wannan asirin wahalar fita gareshi wallahi. Cikin magungunan dashi Al ' Ameen ya bawa Sadiya da sunan taimako yace wannan na kayan mata ne , shine taje tayi amfani dashi kuma shi Al ' Ameen ya bawa Mai gida magani a london , sanin manufarshi da aikin maganin bamu sani ba kuma shima Mai gida bai sani ba , wannan dalilin ne yasa yace yaso ya haɗu da Al ' Ameen akwai tambayoyin da zaiyi mishi. Gadai asiri an fitar na fili amma na jiki bai daina tasiri ba , ganin bai warke ba yasa yace kawai bara ya haƙura da Hajiya yaci gaba da sabgoginshi dan yasan bazata yadda ta sake zama dashi ba , a ranar daya bar gidan gwamnati ya koma gidanshi lalurar ta tasoshi a gaba , daga nan ne ya tafi jinya bayan ya dawo ya ƙarƙare aurenshi da Hajiya Jiddah yace itama Hajiya Sultana zai jira yaji me gidansu zasu ce. Shidai Allah ya sani shima yasan tunda yake a duniya rayuwarshi bata taɓa san wata mace ba wallahi sai a kanta.

Akanta ya san soyayya kuma akanta ya farayi ma shaƙuwa kuka , itace macen farko daya sa hannu ya daka a duniya wacce bata gidansu ba , kuma itace mutum ta farko data ɗaga hannu ta mareshi , yace shi a gidansu wallahi baisan wani abu da ake kira duka ba , tayama za'ayi tunanin dukanshi bayan kowa sanshi yake amma zuwanta rayuwarshi yasa ya anshi hukunci mari daga iyaye , itace macen da ta ɗaukeshi kamar wani sa'arta kuma bata iya zuciya dashi. Shine yace a yadda suka rabu yasan har abadan duniya ta gama dashi ashe ba haka ba. Yayi alƙawari har abadan duniya ya gama aure zai jira daga gidansu ita Sultana ayi magana kawai zai haƙura da ita , yasan babu uwar da zata haƙura tabar "yarta ta zauna da shi da kuma lalurashi. Yayi kuka shi da kanshi yaji tausayin kanshi.

Kamar ya haƙura amma ya kasa. Duk abinda yakeyi zaiyi zuru yana tunani , idan zaici ko zaisha zaiyi murmushi yace ko a wane hali kike ? Ya shiga ɗimuwar rayuwa da zaucewa ganin zai ida warwarewa yasa yasha ta dubu ya tafi gidansu bayan ya fara tura Abbakar. Bayan ya dawo da itane yake faɗa mata ya warke dan abinda yasa ya ɓoye mata kila idan tasan har yanzu yana da damuwa bara ta zauna dashi ba.

Sa hannun masu sa hannu a ciki Ashiru ya faɗawa Dady , Bilki yasa aka kira mishi tana zuwa ta fara zazzaga rashin mutunci. Wai ita zai tirke ? Tou tayi taje tayi yayi maganinta , ta fara azaƙaƙura rashin mutunci nan fa gida ya ruɗe aka fara tone²n asiri , Dady yace Bilki sai ta bar mishi gida , "ya "yanta suka fara kuka Dady zai tona musu asiri. Ita kuma cewa takeyi su daina kuka ya saketa, saboda mahaukacin ɗanshi zai tara yaran Dikko a gabansu yaci mutuncinta ? Har nawa ma Dikkon yake ? Wato shi tunda baya nan bara yayi a gaban yaran Dikkon idan shi Dikko ya dawo daga duniyar ɗimuwar rayuwa su bashi labari yaji daɗi.

Har tsakar dare ana abu guda Momy ita kuma tana cewa sai an warkar mata da ɗa wallahi. Kuma shi Dady karma ya kuskura ya saki Bilki dan wallahi bata riƙe mashi "ya "yanshi , Dady yace ko bata riƙesu shi ya isa ya kula da rayuwar yaranshi. Har Dikko ya dawo ba'a gama faɗa ba , shine ya bawa Dady haƙuri akan kar yayi saki wa Aunty Bilki , Dady yace tou kinji haƙuri yake bani akan ki duk ke kinyi masa abu na rashin kyautawa. Cewa tayi wallahi idan dai akan Dikko zaiyi haƙuri ya zauna da ita wallahi ta haramta zaman aurenta dashi , nan suka sake buɗe sabuwar rigima Dady yace saboda Babanshi yayi haƙuri rigima dai da tashin hankali har aka rabu , ita bata zama albarkacin Dikko saboda bata ƙaunarshi kuma sai ta kashe Dikko ta ɗauki alƙawari a gaban Dady , dariya Dikko yayi cewa inma ki kasheni ko ki fasa lumfashi yana wurin Allah sai lokacin daya so zai tsinkeshi. Shawara ɗaya zan baki kidai bi sannu domin ni ko hassada mutum ya cikamin saiya lalace......

Jiddah ta ladaftu domin Yazeed ya zabga mata bulalar saki mai ɗan bara'un zafi. Tayi iya ƙoƙarinta a koma G R A da ita amma ina ? Nima na rama maganar data faɗa a lokacin aurena nace nima G R A nawa ne ni ɗaya daga ni sai yarana. Umar Faruk {{ Pa - Pi }} Aliyu {{ Khalifa }} DIKKO {{ Junior }} Maryam {{ Ummie }} sai ayarin gidanmu da kuma wanda naso nima nace mata Dikko nawa ne ni ɗaya. Bata ga Sharifa ba da tace SAI TA AURI D ' K yadda ta ƙare ? Taje tayi haƙuri tayi maleji da Yazeedu. Dole ta lallaɓa ta koma gidanta kuma ya rage iskancin hanaci masa abincin gida saidai shine yake auna musu kamar "yan boarding.

Mai gilashi ta rabu da tsohon mijinta tana Abuja tana aure sa'ar rayuwa dabance , wato duk iya iskancin mutum idan Allah yaso mishi jin daɗi saiya shiryar dashi.

Halimatu dai ƙanwar Hadiza bata samu kwanciyar hankali ba saida tayi waje road da ita ga miji ya samu ƙarin matsayi a wurin aiki. Ta dafe kan mijinta ram an shiga lugudan wuta.....

Amisty Mardiya Hafsa Aunty Suwaiba kowa tana can tana ansar wuta dai² da irin rayuwar data aikata a zamanin ƙuruciyarta , duk wadda bata mori rayuwar ƙuruciyarta da kyakkyawar ɗabi'a ba ƙarshen faɗan tayi makauniyar ƙarshe.

Sharifa dai har yanzu ba'a samu anyi aure ba. Ita dai Mai gilashi ta haye ta ibi filin abuja suna can sunacin duniyarsu. Tacemin kila dai tana da rabon a nunota a talabijin tunda ta auri ɗan siyasa nikam nace mata kila dai aljannun shiga talabijin gareta.

Jamila Musa gareki jinin katsinawa.

Tam Alhamdulillahi Hajiya Maryam ko nace Hajiya Sultana. Duk dai baki faɗa mana shin Mai gidanki ya warware ko har yanzu yana ta faɗar saina kashe ki........ *Sultana:•* Murmushi ni harma kin bani dariya , gaskiyar lamari Mai gida Dikko dadai sauƙi ba kamar cancan baya ba , dan mafi akasari saina ɓata mishi yake wannan ihu kuma ai kinsan yanzu ba'ayi. Gulmar Dady kukeyi ko ? Inji Pa - Pi tou bari in kirawo shi , ɗage kanshi yayi tare da cewa Ya.......................Ya........

Abun arziƙi ai yayi bari kiranshi kar yazo ya karkashemu muma a bar mutanen Qerau da jimami.......

Alhamdulillah

Masu biye da labarin kwarata anan ne ubangiji ya bani ikon dakatawa. A madadin duk wani bakatsine ko ina yake a faɗin duniyar nan muke ma duk wani daya karanta littafin kwarata fatan alkari domin nuna muku halakci da kara irin namu na katsinawan Dikko. Kai har wanda bai karanta ba kyakkyawar fata da dubun gaisuwa ta musamman data fito daga yankin jihar katsina,

Jinjina da gaisuwa gareku Kanawan dabo tunbin giwa , saƙon gaisuwa da jinjina a gareku mai kyau albarkacin Umar Sanyi.



Alhamdulillah.


🔚


Rubutawa.


*JAMILA MUSA QERAU....*



14/02/2020



Na barku lafiya. Cike da kewarku , sai Allah mai kowa mai komai ya sake haɗamu idan muna da rayuwa a cikin labarin *ƁOYAYYAR SOYAYYA...*


*JAMILA MUSA ce...*

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On KWARATA RETURN
avatar
fatima-kasim

4 months ago

Reply

Naji dadi sosai sosai Allah y kara basira

avatar
daiy

4 months ago

Reply

Replying to fatima-kasim

Ameen muma munji dadin kasancewarki anan.

Please Login or Register in order to submit comment