Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

cikin haka dago kanda zayayi sai karaf suka hada idanu dawani Dan Dattijo, tsaye agaban wani Dan karami kiyos yana gyara kayan cikin kiyos din,

Dattijon yace' Samari kanasan wani abune ?.. Da sauri *SEERAJ* yace "eh tareda karasa wa gurin shi, kallo farko dayawa dattijon yafahimci cewa shi Baban su" *SAJEEDAH* Saboda Kama dayagani *SEERAJ* yace' sannu Baba inawuni, yace lafiya lau samari meka keso?.

Shuru yayi domin yarasa Abunda zayace' Chan San "idanun shi suka dauka akan madara, Da sauri yace' Baba madara za'abani Baba yace' wani irin za'abaka?..

Yace' ummh-ummh Baba abani kowani irin ne, yace toh Bari abaka wannan _THREE CROWNS_ shima yanada kyau,

najima "ance' idan mutun ZUCIYAR shi tanayi masa zafi, kamar irin masufama Da Ulcer din nan toh idan aka kada madarar da ruwan me SANYI sosai, akasha toh anajin saukin zafin zuciyar
Yace' toh" abani shi.

Yadauko roll din madarar tareda cewa toh guda nawa?.. eh naduka za'abani Baba yace "a ah samari ban gane naduka ba?..

Murmushi *SEERAJ* yayi tareda Sosa Kai cikin jin kunyar katobarar dayayi, yace' Baba "Ina nufin na duka wannan din za'abani, yace toh toh" nagane gashi guda biyar ne yasa 'acikin Leda tareda cewa sauren me?.. Ko abaka _Coffee_?..

Da sauri *SEERAJ* yace' eh, toh shima kamar madarar?. yace eh, bayan baba yasa madara da coffee 'acikin Leda sai Yakima masa yana cewa gashi kudin Dari uku DA hamci yakama,

*SEERAJ* yace' toh tareda Ciro wallet daga aljihun wandon shi yazaro dubu daya, yamikawa Baba yakarba tareda cewa kashhh' gashi Kuma bachanji Amma Bari nakira Sajeedu yasa mo mani.

*SEERAJ* Yace toh tareda kurawa Dan kiyos din ido, gaba daya kayan dake Ciki bazasu wuce 150 to 2000, idanu yarintse yayinda yaji wani Abu yadarsu aciki ZUCIYAR shi,
Bakomai bane illah tausayi,

A hankali yabude idanu tareda bin bayan Baba da kallo, wani yadine ajikinsa daya kode sosai har wani gashi yafatayi Saboda tsabar tsufa, saidai duk Da tsufan yadin wankakke ne tas harda Karin guga.

tsaye baba yayi ajikin fallan kwanon dayake ke waye da kangon gidansa, yana kiran Sajeed,

Ahankali *SEERAJ* yasake rintse idanu acikin RANSA kuwa fadin yake YA SALAM ashe akwai mutanan dasuke rayuwa cikin talauci haka?.

_*Nikam nace tabdi Captain SEERAJ kana cikin DAULA, koda yaushe kana keta HAZO Ina zaka sani*._

*SAJEEDAH* ce' ta amsa da cewa Baba Sajeed baya nan yatafi islamiyya, yace af aina manta toh zonan kisamo Mani chanji gurin mlm barau me shayi.

Tace toh tareda ajiye hadis din taje tadauko hijab tasa tanufi waje,

Baba ya koma gurin *SEERAJ* yace' Samari Bari yarinya tazo tasamo chanji kaji?. *SEERAJ* yace toh dai dai lokacin da *SAJEEDAH* takaraso gurin tace Baba gani,

Kanta nakasa don haka bata kula damutun agurin ba, saida Baba yace' karbi kisamo mani chanji gurin mlm barau, saikiba wannan Dari shida da naira hamsin nikuma kikawo Mani Dari uku da hamsin.

Tace to tareda karban kudi sannan ahakali tadaga Kai ta kalli Wanda zaba kudin, caraf suka hada idanu Da *SEERAJ* Wanda tun fitowar ta yake kallon ta,

Jitayi kirjinta yabuga shima *SEERAJ* haka yaji kirjinsa yana bugawa tunda tafito, da sauri tagukar dakai Cikin sanyi murya tace' inawuni?.. Cikin sauri ya amsa dacewa' lafiya lau, Baba yace' Samari Kuje tasamu chanji sai abaka, yace toh".

Tafiya *SAJEEDAH* take cikin nutsuwa *SEERAJ* yana biyeda ita, yayinda kowansu" da'abuda yake sakawa aransa *SAJEEDAH* aranta fadi take oh ni *SAJEEDAH* harnan kuma yabiyoni?..

Jitayi wata ZUCIYA tabata amsa da cewar a ah baKe yabiyo ba abudai yazo siya, can Kuma sai taji Daya ZUCIYAR tace' ke! kin batada takardan dayaba Sajeed yakawo maki?.

Eh haka ne kumafa toh kila amsar yazo karba oh ni *SAJEEDAH* toh" mezan ce" mashi?.

Shima *SEERAJ* sai zance ZUCI yake fadi yake to ta'nama zanfara mezance' mata?.. nace' jajiki ne?. sannan sai Na tambaye tane ko kaninta yabata sakona?..

Ahankali *SAJEEDAH* yajuyo
'aikuwa
Karaf Suka hada idanu wani tattausan " murmushi suka sakarwa juna,

"alokaci guda Wanda da'alama basu sanda yafito ba Da sauri ta dukar dakai Cikin nutsuwa *SEERAJ* yace?..

Aha


TEAM

FOR

_*SAJEERAJ*_


Muje zuwa


Kubiyoni

A

馃挊ZUCIYATA CE馃挊

Tareda

Alkalamin

鉁嶐煆�

馃挊LUFHAT馃挊
[8:34AM, 2/20/2018] 鈥�+234 902 288 0912鈥�: 馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊

馃挊ZUCIYATA CE馃挊

_Based on true life Story_
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊

(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)

7鈨�

WRITTEN BY

馃挊漏AMEENA UMAR FARUQ馃挊
OR
馃挊MEENAT馃挊

________________________

*_庐PEN:WRITERS ASSOCIATION_*

*_PEN THE STRONGEST WEAPON_*
________________________

*_only the exquisite and Whizkid writers are opportune to be pen writers_*



鉁嶐煆�


"Yajiki?.. ba tareda tadago kaiba Cikin sanyi murya tace' da sauki yace Allah yakara tace Ameen, Sai kuma shuru yaratsa tsakayin su"

Ahankali suke tafiya Cikin nutsuwa
batareda kowa yasake cewa da Dan'uwansa komai ba, *SEERAJ* ne yakatse shurun da cewa "ina "abokina?.. tace' yatafi islamiyya yace' KO, can kuma yace' ummm ko yabaki sako dazu, "Ina nufin Sajeed dazu nabashi takardan yakawo maki yabaki?..

Cikin sanyi murya ta mai kashe masa jiki tace' "eh yabani yace OK" so banji kince komai ba ne?.. tace toh ni me zance?..yace ah ya kamata kice' wani abu mana,

Shuru tayi batace' komai ba tunda "itadin bamai yawan magana bace' saidai Murmushi da tayi, shidin'ma Murmushi yake yayinda yakejin wani irin nishadi Marar musaltuwa,
yana ratsa jiki shi.

Ita din'ma wani irin yanayi takeji 'ajikinta tun lokacin da suka haduda shi, har zuwa yanzu bata daina jin yanayin ba Wanda tarasa gane kome Nene.

_*Nikam danake gefe nace SONE yammata lol*._

"Ahankali yace *SAJEEDAH* duk Abunda kika gani narubuta acikin takardan nan wlh bakarya harcikin *ZUCIYATA* nake *SONKI* Kuma wlh bantaba jin irin wannan Son gakowace diya' ba saike,

Fatana ki 'amince ki karbi Soyayya ta pls kinji?..
Jikinta ne yai sanyi najin yadda yake rokonta takarbi Soyayyar shi, 'aranta KO" fadi take Allah sarki rayuwa waiyau ni *SAJEEDAH* ce' akeroko Na amice da Soyayya?.
A hankali tasauke numfashi saida kuma tanaji a *ZUCIYAR* ta bazata amince da Soyayyar sa farar daya ba harsai tayi shawara,

Har take fadin Allah sarki my Besty *SADEEQAH* batan data tayani shawara, Amma koda bata nan zanyi tunane kafin Na amince,

Don haka sai tace' toh" kadan bani lokaci zanyi tunani...
Yace' kamar zuwa wani lokaci?.

Dai-dai lokacin dasuka karasa gurin mlm Barau maishayi, don haka bata samundamar bashi amsaba.
gefe *SEERAJ* yasamu ya tsaya jiranta,

Saida tagai mlm Barau sannan tace' Baba yace" kayi masa chanjin dubu daya, yace' ayya *SAJEEDAH* ba chanji tace toh tareda cewa Sai anjima.


A hankali tace' toh' yaza'ayi gashi Kuma ba'a samu chanji ba,?.. yace OK" badamuwa kimayarwa Da "Baba gudin gobe idan nazo saina karbi chanji, tace' toh' shikenan Sai anjima,
Bai ce mata komai ba,

Harta fara tafiya sai yace' Dan' tsaya kiji mana, cak ta tsaya ba tareda tajuyo ba yayinda taji kirjinta ya buga,

Cikin nutsuwa yakaraso gurin ta hartanajin kamshi turarar shi, cikin rada yace' kema kitanadi amsata, Saboda gobe idan nazo harda ita zankarba saida safe regard my friend,

Sannan yatafi da sauri tajuya tana kallon shi, dai-dai lokacin da yashige wani lungo yajuyo yana mata lallausa Murmushi tareda daga hannu, ga mamakin ta saita tsinci kanta tana mai daga mashi hannun "itama tana tsaye har yabacewa ganin ta da sauri ta sauke hannun ta tana dariya kanta sannan ta tafi.


"A hankali *SEERAJ* yake tafiya *ZUCIYAR* shi cike Son *SAJEEDAH* tareda tsananin tausayi halinda suke Ciki, aranshi yaka fadin tabbas "suna bukatar temako yakuma kamata natai maka masu",

toh Amma ta yazan taimakesu"?.. tabbas bayasan sunan koshi waye, domin shi mutun'ne wanda abun duniya baida meshiba Arzinkin da mahaifi sa yakeda shi dawanda shikansa yakedashi sambasa gabanshi,

Shiyasa bayasan 'ace shi dan Alh Abbas Harka ne saboda mutane guda-guda ne basunan Alh Abbas Sardaunan Minna ba yayisuna sosa Ya shahara aduniyar masu arzikin, shiyasa mayafi San zama a Jordan Saboda hakane mayasa bakowa ne yasanshi ba,

haka dai yaita sake-sake ta yadda zaya taimaka masu batareda sunsan koshi waye ba wanda hardai ya tsayar da yadda zayayi ya tai maka masu"

Batareda sunan koshi waye ba, amman da shiradin sai saiyayi bincike "akansu" wanda nima basan kowani irin bincike zayayiba,

_*Toh kodai ma wani irin bincike ne, mudai muna nan biyeda jikan Sale HARKA*_

Ahaka har ya'isa gida dai-dai lokacin da akekiran sallah magrba, don haka bai shiga cikin gida ba sai yatsaa yai sallah anan masallacin gidansu.

馃挊馃挊馃挊馃挊馃挊
馃挊馃挊馃挊馃挊
"A yau Monday ranace da malan bahaushe keyewa kirari da ko Bature na tsoro ta, badan komai ba saidan kasan cewarta RANAN aikiga ma'aikatan gwamnati, harma da Students wato yan makaranta.

don haka yawanci mutane sai shirye-shirye suke dan suzuwa gurin aiki hakama yan makaranta, acikin masu' shirin zuwa makaranta harda Sajeed,

*SAJEEDAH* ce' tace' Kai Sajeed kai kenan kullum cikin zuwa makaranta amakare yanzu fa 8:00, yace Aunty *JEEDAH* Ai yanzu zan tafi dai-dai lokacin da yake karasa kulle Sandal dinsa dazaran buhu,

Yace' Inna Aunty *JEEDAH* natafi, sukace toh sai kadawo, yafito gurin baba yanufa yabashi raira ashirin sannan yafi,

Dai-dai inda suka hadu jiya yauma nan suka hadu, *SEERAJ* sanye dakayan Sports irin na jiya, saidai nayau jane sabanin najiya baki, da ratsin fari,
Saidai wani abun mamaki Sajeed Sam bai kulada
*SEERAJ* ba Sai faman zumbuda sauri yake Saboda yamakara,

Gani haka ne yasa *SEERAJ* yin dariya tareda tare gaban Sajeed din yace' yeee nakama lat comes, Sajeed yadaga kai yai dariya tareda cewa Lah my friend Ina kwana,

*SEERAJ* yace Lafiya lau my friend Amma dai gaskiya kayi lat sosai, yace "eh Ai shine nake yin sauri Saboda kar'afara tare lat, yace oya toh" kayi maza katafi kajiko?.. Yace toh dai-dai lokacin da yafara tafiya,

*SEERAJ* yace Aunty ka bataje school din bane?. yace eh" bata zuwa "aimataji sauki, kuma nabata takardan nan yace OK saika dawo, Sajeed yace' toh sannan yatafi.

Bayan *SEERAJ* ya
koma gidan yai wanka Sai ya shirya Cikin riga da wandon, wani bakin yadi mai shara-sharne don har Ana hango singilet dinsa, idan kaga yadin bazaka dauka mai tsada ba ne, Saidai gaskiya kam mai tsananin ne sosai,

Cikin nutsuwa yanufi Cikin gida Sai zuba kamshin yake
Bayan ya gaida Ammi da Abba sai yasa Kai yafita abunshi ba tareda yatsaya karin kumallo ba, Saboda yau yatashi Da azumi koda yafita abinsa, bai tsaya KO "Ina ba sai kofar gidan su" *SAJEEDAH*.

Baiga kowa ba agurin tiredar don haka sai yazauna akan benci, can saiga Baba yafito hannun sa rikeda buta da'alama yake wayane,

Koda Baba yaga *SEERAJ* Sai dariya yace a ah SANNU Samari kadawo, yace eh Baba,
Nadai suka gaisa har Baba ya tambaye shi sunan sa yafada masa, suka dantaba fira sannan yakarbi madara Da coffee irin najiya, yauma dai ba chanji KO" Kuma nace' baikarba ba yace Sai gobe.

Cikin kankani lokaci shakuwa tashiga tsakanin Baba DA *SEERAJ,* kasan cewar kullum idan yage jogging yadawo yai wanka yashirya sai yanufo gurin baba suyita tafira,

idan *SEERAJ* zaya tafi gida yaita watsayama gidan "Alh Siddi harara, yace' mugun Mutum kawai da baya temakon talakawa, musamman makotan shi saiya kwaf yawuce.

Ahankali *SEERAJ* yafahimci Baba irin mutanan nan'ne da'abun duniya bai dame shiba, abudaya daya kula da Baba shidai yawa data iyalinsa.

Yayinda Soyayya maikarfi tashiga tsakanin *SAJEEDAH* Da *SEERAJ*, yadda "ake tafiyar Da Soyayyar kuwa shi idan antaso daga islamiyya da yamma, Sai 'atsaya 'ayifira da safe kuma kafin atafi sai atsaya ayifira.

Cikin sati uku Soyayya kam tayi karfi matuka atsakanisu' yayinda kowa yake jin son Dan uwansa har Cikin jinsa, Wanda sukeyi idan badaya toh" daya bazaya iya rayuwa ba,
Soyayyar *SAJEEDAH* tasa *SEERAJ* yamanta da maganar auren shida *ZUBEE*.

_*nikam nace" Anya?*_

Akwai wata Rana *SEERAJ* yaje gurin Baba sunsha firar su kamar yadda suka Saba, har zayatafi Sai Baba yace mlm *SEERAJO* wai bawata yar'sana'ane da'ake Dan tabawa?.

Murmushi *SEERAJ* yayi tareda Sosa Kai yace' Baba akwai, yace' toh me'ake tabaw?. kawai tsintan kansa yayi yana cewa Baba yana Jan babban mota ne zuwa Lagos,

Baba yace' madallah yakara dacewa dama Hutu yakeyi, toh Kuma Hutun yakare gobe mazaya koma Baba yace' masha'allah toh Allah yabada sa'a yace Ameen.

Da *SEERAJ* yatashi Sai yaje akabashi fasinjan chaina, bai dawo ba saida ya kwana biyu,

Ranan dazayaje gidansu" *SAJEEDAH* kasuwa yashiga yayomasu siyayya sosai, Baba shadda mekyau yadi goma hada takalmin lnna Kuma zan'nuwa guda biyu itama da takalmin,

*SAJEEDAH* abaya tsaddu guda uku da takalma daman shafawa da turaruka, Sajeed Kuma kayan Kati masu kyau DA tsada.

Aikam Baba yayita godiya tareda samashi Albarka, Bayan yagama godiya Sai yafara fada dacewa wannan kayan sunyi yawa, karya sake kashe kudi irin haka yaringa yiwa kansa tanadi shi dai *SEERAJ* murmushi kawai yayi.

Hakanan abubuwa ke tafiya yayinda suke tazuba Soyayyar su" Wanda har Baba yafara fahimta akwai wani Abu tsakanin su",

Wani abun mamaki Kuma shine
Duk wannan Soyayyar Da akeyi, *SAGEER* bai taba ganin *SAJEEDAH* ba saidai labarita DA *SEERAJ* yake basa.

Kamar kullum yauma sun dawo daga jogging har zasu rabu, Sai *SAGEER* yace' waikai bazaka koma gurin Aiki bane?. *SEERAJ* yace saina gama hutu, yace halan sati nawa kadauko?.
yace two months,

DA sauri yace what... bakada hankali ne? dazaka dauko hutun wata biyu, cikin jin haushin sa yace' eh daga TURU aka santoni,

Yace Allah yabaka hakuri, yace Ameen tunda nine agogo Sarkin aikin bazan Hutaba KO?. *SAGEER* yace yi hakuri maida wukar nidai yau bazan tafita gida ba sainaga wannan Lucky *SAJEEDAH,* tuni *SEERAJ* yasaki lallausan Murmushi tareda cewa aikuwa yanzu zaka gansu",
aikam bai gama rufe baki ba sai gasu" nan zuwa,

Da sauri yace yau gasunan ma zuwa, ahankali *SAGEER* yajuya don yaga wace yariyace haka mai sa'a datayi nasarar mallakar *ZUCIYAR* abokina sa,

Aikam idanun shi yasauka akan *SAJEEDAH* itada Sajeed sunufo gurin su "
Idanu naga *SAGEER* yazaro tareda doka tsalle yaboye abaya *SEERAJ* Cikin alamar tsoro da abida yagani,

Ahankali Na daga Kai don naga abinda yabashi tsoro, mamaki ne Yakama ni saka makon jidanayi yace'?..


Toh fa

muje zuwa

A

馃挊ZUCIYATA CE 馃挊

Tareda
Alkalamin

馃挊Lufhat ce馃挊
[8:36AM, 2/20/2018] 鈥�+234 902 288 0912鈥�: 馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊

馃挊ZUCIYATA CE馃挊

_Based on true life Story_
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊

(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)

8鈨�

WRITTEN BY

馃挊漏AMEENA UMAR FARUQ馃挊
OR
馃挊MEENAT馃挊


________________________

*_庐PEN:WRITERS ASSOCIATION_*

*_PEN THE STRONGEST WEAPON_*
________________________

*_only the exquisite and Whizkid writers are opportune to be pen writers_*



鉁嶐煆�


"Kutttttt wannan dince" budurwar taka?.. *SEERAJ* yajuya yana kallon shi tareda cewa "eh ita ce" meye haka kake wani boyewa abayana Sai kace' kaga DODO?..

(Toh nima dai banga abun tsoro ateda *SAJEEDAH* balle Sajeed, domin kuwa uniform din jikin suma sabo ne Wanda *SEERAJ* yadinka masu kwana biyu da suka wuce ")

meyau *SAGEER* yahadiye jikake kut sannan yace' Kutumar Uban Kai! bagara naga DODO ba dai-dai ace' Mani wannan Ugly girl dince" budurwar ka,

Da sauri *SEERAJ* yace' what.. kasan Abunda kafada kuwa?.. kafin *SAGEER* yabashi amsa harsu" *SAJEEDAH* su karaso gurin,

Sallam sune yasa suka juyo gaba daya Sajeed yace Lah my friend yaushe kadawo? munata wucewa ranan amma bamu ganin KO Aunty *JEEDAH*? "Ina kwana murmushi yayi tareda cewa jiya nadawo, lafiya lau yakake? yace'
lafiya,

*_kasan cewar tun_* *_Lokacin Da yace_* *_wa_*
*_Baba yana Jan_* *_mota zuwa Lagos_* *_Toh" sai yanayin kwana biyu baije gidansu ba_.*

A hankali yadaga Kai ya kalli *SAJEEDAH* tareda sakar mata lallausan Murmushi,

Itama Murmushi tasakar masa mairatsa jinida jijiya, sannan ta dukar dakanta kasa Cikin jin kunya tace' Yah *SEERAJ* antashi lafiya? wayi irin sanyi yaji har Cikin *ZUCIYAR* shi,

"Aransa yake fadin *ALLAH kasan Ina SON* baiwarna taka har ciki JINI da *BARGO Na, ALLAH* kamallaka Mani ita amatsayin Matata,

Yace' Lafiya lau natashi I hope kema kintashi Lafiya? tace Lafiya lau, yace Alhamdullah,

Sannan ta dubi *SAGEER* Wanda yake mata wani irin kallon kana gani kasan Na walakanci ne da raini, tace Ina kwana? Ina kwana?.

Banza yayi da'ina tareda dauke kanshi yanuna irin baima San Allah yayi ruwan tsiyar taba, jikin tane yai sanyi ganin yadda yai mata banza don haka sai ta dukar dakai kasa,

Yayinda ran *SEERAJ* inyayi dubu yabaci don haka cikin bacin rai yace' bakaji ana gaishe kabane? Da sauri *SAGEER* yace "Oh Lafiya sannan ya kauda Kai,

Tsakin mtsww *SEERAJ* sannan ya kalli agogon hannun shi yace yau kunyi lat why?

Cikin sanyi muryar ta tace Sajeed ne yace' Sai muntsaya munsha kunu, yace toh" yanzu kunsha kunun kenan? Sajeed yace "eh munsha, yace Gud toh" Ina nawa?..

"A hankali tadaga hijab dinta tafito da kunu Cikin dan karamin cup din, roba mai marfi tamika masa, (kasan cewar tun wata Rana dasukace' masa sun tsaya San kunu shine yace' toh" shima akawo masa shikenan tunda DA wannan lokacin take kawo masa).

Bayan yakarba sai yace toh" Oya kuyi maza kutafi, sukace toh" dai-dai lokacin da suka bita gefensu suka wuce,

Saida *SAGEER* yaga shigarsu *SAJEEDAH* lungu sannan ya kece Da wata mahaukaciyar dariya, dariya yakeyi sosai harda rike Ciki,

Yayinda *SEERAJ* yake masa kallon
mamaki,

Saida *SAGEER* yayi dariya mai'isarshi sannan ya tsaya,
*SEERAJ* ya kalle
shi ran abace, yace' waka keyiwa dariya
Haka,

*SAGEER* yace' Kai DA waccan kuchakar budurwar taka, See you fa yanuna shi, yace kamar ka "ace duk kyawawan yammatan hadu masu "aji dasuke binka da wayanda suke bibiyata akan suna sonka,

Amma karasa wadda zaka zaba "acikinsu sai wannan ugly din?.. Shame gaskiya kaji kunya Kuma kabada *MAZA*, sannan kaci *BAYA* walh,

Cikin bacin rai *SEERAJ* yace "eh duk naji kasan "ance abinci wani *GUBAN* wani, su yammatan daka kefadi kyawawa ba'abunda yada meni da kyaunsu domin basa gabana ba,

ita din Kuma dakace mummunan ce" haka nagan ta naji tayi Mani,

Sannan kasani su ba sukai matsayin da zasu mallaki *ZUCIYATA* ba, har
kana fadin wainaji kunya naci' baya KO?..toh" Allah yasama BINDI naci ba baya ba, naji a hakanan nakesan *SAJEEDAH* Domin itace kadai kedai matsayin mallakar *ZUCIYATA*,

Sukuma *MAZA* dakace nabada su" indai akan *SAJEEDAH* ne aiban badasu" ba tukun, yanzu zafara musamman ma irinku dabasu San *SO NA GASKIYA* ba, yakai karshan maganar shi dayin tsaki mtswwwww yajuya zaya tafi.

Da sauri *SAGEER* yasha gabana yace dakata young palot ita *ZUBEE* din kuma fa?.. *SEERAJ* jiyayi gaban sa yafadi, shikam tsakani DA Allah yamanta da maganar wata *ZUBEE* can,

Daure fuska yayi yace' au kana nufin auren *"ZUBEE* shine zaya hanani auren *SAJEEDAH*?.. Hmmm yallabai Idan harkana wannan tunanin ne toh" garama kadai Na,

zaya sakeyin magana da sauri yakatse shi dacewa
Dalla malam bana son iskanci kaji don haka bani hanya nawuce kanaji?

Matsawa gefe yayi tareda kallon cup din dake hannun *SEERAJ,* fuska ya yamutse sannan yace yanzu shan wannan jagwalgwalon zakayi?

batareda ya kalle saba yace' babu 'abunda yada meka kuma DA wannan, baki yatabe yace haka fa Mtsww toh" Allah yasa wake,
Yace Ameen naga ba kenan Domin shi wannan yariga yaru,

Hakan nan suka rabu ran *SEERAJ* abace, Saboda maganganun DA *SAGEER* yafada masa akan *SAJEEDAHR* sa.

Aranan kam wuni yayi ransa bace
Don haka nema baisamu zuwa guidance su *SAJEEDAH* ba,

馃挊馃挊馃挊馃挊馃挊
Washegari *SEERAJ* bai samu zuwa jogging ba don haka dawuri, yashirya yanufi gidan su" *SAJEEDAH*,

Da alama wannan zuwa Na musamman ne Domin kuwa me baro nagani yana biye dashi abaya, kayan masarufi ne cike acikin baron,

Baba Yace' a ah mlm *SEERAJO* Kaine yau tunda sassafe?..yace eh Baba nine in kwana? yace Lafiya lau kadawo lafiya?.. yace' lafiya lau, Baba yace "aiji kaninka baki abun magana Sajeedu yace' Mani kadawo yace "eh fa nagansu" zasu tafi islamiyya,

Idanun Baba ne yasauka akan me baro, yace "a ah *SEERAJO* wannan kayan daga Ina haka?..yece Baba nakane kawo maka,
Idanu baba yazaro Cikin mamaki Yace?..

_*Pls kuyi hakuri DA wannan bayawa*_

_*Amma fa akwai badakala*_

Muje zuwa

A

馃挊Zuciyata CE馃挊

Tareda Alkalamin

鉁嶐煆�

馃挊Lufhat ce馃挊
[8:38AM, 2/20/2018] 鈥�+234 902 288 0912鈥�: 馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊

馃挊ZUCIYATA CE馃挊

_Based on true life Story_
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊

(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)

9鈨�

WRITTEN BY

馃挊漏AMEENA UMAR FARUQ馃挊
OR
馃挊MEENAT馃挊

_*WANNAN page NAKUNE MASOYA ZUCIYATA CE WlH KUNADA YAWA, SABODA HAKANE BAZAN IYA LISSAFO SUNA YENKUBA, SABODA HAKA NE NASA DAUKAR DA PAGE,AGAREKU KUYI YADDA KUKESO DASHI NAGODE SOSAI DA KAUNARA KU , KUMA ADDU'ARKU TANA ZUWA GARENI ANA MUGUN TARE DIN'NAN,*_馃拫馃拫馃拫.





________________________

*_庐PEN:WRITERS ASSOCIATION_*

*_PEN THE STRONGEST WEAPON_*
________________________

*_only the exquisite and Whizkid writers are opportune to be pen writers_*



鉁嶐煆�


"A ah Kai! *SEERAJO* duk wannan din daga "Ina kafito dasu haka?..

Yace' Baba Uban gidana ne yafitar DA ZAKKA shine nakarbo maka,

Cikin mamaki Baba yasake cewa Kai! *SEERAJO* dukka gaba daya buhun shin kafa kanta taliya katan makaroni katan lndomin harda galon manja Da mangyada Kai *SEERAJO* kayan sunada yawa Kuma duk ni kadai?

Yace "eh Baba zakkace ai wannan manjan da mangyada Nina siyo makashi ahanya, ahankali Baba yazauna akan benci kamar zayayi kuka domin tunda yake arayuwar sa, bawani "mutum daya taba yimasa irin wannan kyau haka don hakane ma yarasa abunda zayace,

Cikin sanyin jiki Baba yace *SEERAJO* banida bakin yimaka godiya saidai nace ALLAH yai maka Albarka Allah yabiyaka, shima Uban gidan naka yasaka masa da mafificin Alkhairi yajikan magabata nandai Baba yake tasa mashi Albarka,

Bayan yagama zuba masa Albarka sai yace toh" *SEERAJo* toh" "aisai "araba kayan nan biyu idan zaka tafi can kyaunku sai katafi masu dashi KO?'... DA sauri yace "a ah 'aidaga can nake suma ankai masu masu wannan din nakune,

Yace masha'allah toh" Allah yasaka DA Alkhairi, Ameen Baba toh" Kai Dan Samari me Bari mushiga Ciki yace toh" suka nufi cikin gida.

A hankali *SEERAJ* yabi bayan sa DA kallo wani irin tausayin shine yasake Kama shi, me hadeda kaunar sa ahankali yafurta cewa "Baba karka damu insha'Allahu lokaci yakusa zuwa dazaku huta da Kai da iyalin ka,

"A haka har baba yafito sukaci gabada Da firar mutanan duniya masu Abu mamaki Da al'ajabi, tareda tausayin dakuma abinda dariya Toh ALLAH dai yasa mudace inji cewar Baba kenan, yayinda *SEERAJ* Toh Ameen,

Can sai Baba yaciro wasu kudin acikin aljihun rigarsa yace' *SEERAJ* kagani Allah ya temakini Na hada kudin makarantar kanwarka
Wato *SAJEEDATU,*

Kasan cewar yanzu Baba yamaida *SEERAJ* abokin shawaras sa, saboda ya yabada hankalinsa da nutsuwar sa, shiyasa yarda dashi yake fada masa komai nashi,
toh" KO shima *SEERAJ* din hake ne agurin sa,

_*Saidai kuma nibana San dalilin* *SEERAJ*_ *na* *_boyewa Baba koshi wane,toh kodai menene Bari mubi shi muji_*

Tunji Nasamu na karasa nahada dama Ina kiran kadawo sai kagani,
*SEERAJ* yace toh" Baba dama nima harda maganar makaranta nazo muyi, saboda gashi har second semester yakusa karewa,
Baba yace toh" wani abune haka nan dinko?

_*pls reader kar kuba laifin Baba baiyi karatuba*_

Murmushi *SEERAJ* yayi yace "eh Baba Ina nufin matakin karatun nakarshi yakusa karewa, yace oh kajiko toh" yanzu akwai matsala KO?..

yace "a ah ba komai
yace toh" *SEERAJO* kanwar takace" tana San karatu, shiyasa kullum nake Addu'a Allah yahore Mani tareda tsawon rai, nacika mata burinta,

*SEERAJ* yace Ameen Baba, nandai suka tsayarda cewa gobe Monday insha'allahu *SAJEEDAH"* zata koma ta cigaba dazuwa makaranta karda,

Can dai Baba ya mike tareda cewa Bari nakira maka kanwar taka kugaisai, yau da sukola ta tashi shiyasa bata samu zuwa islamiyya ba,
Ciki jin nauyin *SEERAJ* ya amsa da toh" Dai-dai lokacin Baba yanufi cikin gida.

Yayinda yabar *SEERAJ* yana tunani Shidai har cikin *ZUCIYAR SA* halin Baba yana bashi sha'awa, shiyasa 'akullum yakejin kaunar sa tana Kara shigarsa gashidai, talakane amma ya tsaya tsin daga yadogar DA Allah tareda neman nakashi,

Sabani wasu" talakawa da bazasu iya tashi su nemi Na Kansu" saboda tsabar muruwar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment