Join Our WhatsApp Group

ALLAH NE SHEDA 1 and 2 Complete Hausa Novel Document by ALLAH NE SHEDA 1 and 2


ALLAH NE SHEDA 1 and 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 10652



ALLAH NE SHEDA 1 and 2

Reading Time: 0 Hours

Added On: 17, Sep 2023

Author: Zainab Abubakar Safana ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : GOLDEN'S WRITES ASDOCIATION

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 59.88 kb

File Type: txt

Views: 2681+

Download: 1003+

Last download: 3 days ago

Description/Story: 💞💞💞💞💞💞💞💞
alhamdulillah my fans this is my new book,Ina godiya ga Allah sannan kuma Ina godiya a gareku masoya na, nagode.
An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
💕💞💕💞💕
ALLAH NE SHEDA!
💕💞💕💞💕

@GOLDEN'S WRITERS ASSOCIATION@writing by'xee"abu safana
mrs'salihu Bamalli my ustax!






Ayyah taslima kinga ajiye aikin nan kije xan karasa girkin nan kinji kinga kinyi latti xuwa school, to anty dakin bari na karasa miki kawai na kusafa,
a'a kije driver yashirya ke yake jira ki fito kawai,jeki kanwata Zan karasa ki maida hankali ayi karatu saikin dawo!
to antyna nagode saina dawo'to kanwata.
dasauri tashirya cikin school uniform dinta ta dauki baskect dinta ta fice, harga Allah tana kaunar anty tauhida saboda yadda take sonta kai kace' wata kanwarta ce alhalin kuwa babu dangin uwa bare na uba, hasalima taslima yar aikinta ce'zakuyi mamaki idan nace'muku yar aikinta ce, takewa wannan gatan harta sakata makaranta domin a lokacin da aka dauko Mata taslima a matsayin yar aiki dama tun a kauyensu ita tana karatu hakan yasa tauhida(anty) ta mayarda ita ta kuma jawota a jiki kamar wata kanwarta wacce suka fito gida daya, komai yimata takeyi, shi yasa suka shaku matuka,
around 1:30pm tashigo gidan ta kwalla Kira "antyna! antyna!!
shirun dataji yasa ta nufi bedroom din tauhida a kwance take' tana xubarda kwallar data Saba,
shiru tayi'a lokacin data sameta a wannan yanayin zama tayi a gefenta tareda dafa kafadarta tace 'antyna'
dasauri tauhida ta dago tana share kwalla tace'taslima yaushe kika dawo,banji dawo war ki bane,

anty dama bazakiji dawowa ta nasani tunda kina nan kina abunda kika Saba,ban San har zuwa yaushe ne zaki daina tunani da kukan nan ba,Allah yasani bana son ganinki cikin wannan yanayin ko kadan domin hankalina yana matukar tashi,
Allah sarki kanwata kiyi hakuri, kinfi kowa sanin Abunda yake damuna banida burin daya wuce naganni da dana! ko diyata a duniya sai dai kuma Allah bai bani ba, shekata6 kenan da aure taslima Dana samu cikin saiya zube baya zama munyi maganin asibitin munyi na Islamic din but kin daiga shiru taslima Ina tsoron Karna mutu banga,iri na ba a duniya nasan idan na mutu taslima kowa zai manta dani ne, a duniya tunda kinsan banida iyaye na,mamana da babana duk sun rasu dama ni kadai suka Haifa a duniya sai kuma suka rasu,hakan yasa na tashi a hannun wan mahaifina wato baban tauhed mijina Wanda shida matarsa suka rike ni tamkar yarsu yaransu kuwa babu wani banbanci a tsakanin mu,tin Ina karamata tauhed yake hidima dani,harna girma inda hakan yazama soyayya aka hadamu aure nida shi, so da kauna da kula babu Wanda bana samu a gurin tauhid daga baya yanayin aikinsa ne yasa baya xama a gida kinsan cewar soja ne,kuma babba Ana tura shi kasashe yayo watanni inda yake Nuna min damuwar sa akan barina dayake yi ni kuwa na nuna masa babu matsala na kuma Kara masa kwarin gwiwa akan aikin nasa,shi yasa yake alfahari dani,

rashin haihuwata ni yafi tayarma da hankali domin shi yake rarrashina, akan hakan Ina son haihuwa matuka a haka muka cigaba da addu'a akoda yaushe muna Neman zabin ubangiji a family ma duk su suke kwantar Minda hankali, haka nacigaba da rayuwa idan yayi tafiya sai kannensa suxo su tayani xama domin su ukku iyayensu suka Haifa shine babba tauhed sai saudat da muhsina, yanayin karatun su yasa na nemi a samo min yar aiki shine aka kawo min ke,naji dadin zama dake saboda kirkin ki tarbiyar ki,nutsuwa kamala da sauran su,shi yasa nake jinki kamar jinina kuma kece kika zamo mai share min hawaye a duk lokacin da suka xubo, kece madadin tauhed.......


💕💞💕💞💕💞💕💞💕ðŸ

wannan shafin kune members of Sirrinki Alkhairin ki group and Matan aure group godiya da sadaukarwa a gareku.

Allah ne sheda! by xee'abu safana




hakane anty dukda haka kisa hakuri a ranki kinji komai lokaci ne, kuma haihuwa nufin Allah ne kiyi hakuri kinji antyna!
to taslima nagode kinji Allah yai miki Albarka kije watsa ruwa kiyi sallah saiki zo muci abinci,
yawwa antyna ta uncle dina ko kefa harnaji dadi'murmushi kawai tai batace komai ba,
kwance take tana waya da tauhed yace'namesake (domin haka suke kiran junansu tace' Na"am namesake Dina,

kinga wallahi nayi kewar ki Ina so inzo inganki gaskiya ni,
dariya tayi domin cikin shaqwaba yayi maganar tace' soja mazan aiki karka tada hankalin ka Ina lapiya kuma Ina kular maka da kaina sosai da sosai, bana so kadamu kanka harkaje ka fara ramewa,
smilen yayi tareda shafa lallausan sajen sa yace'Allah sarki iyalina Allah yabrmu tare'amin mijina nakaina,

a haka suka cigaba da wayarsu taslima dake zaune, bayan tauhida ta kashe wayar tayi'dariya tare da fadin Kai Ana shan love a gurin nan anty wallahi kina son uncle dayawa shima kuma yana sonki, kuna burge ni wallahi,

Allah ko kanwata to kema zancigaba da miki addu'a Allah yabaki miji nagari kamar ki domin mata tagari ita tafi dacewa da miji nagari, shi isanya nakewa uncle dinki addu'a ko bayan ba raina Allah yabashi Mata tagari wacce zata kula dashi fiyeda ni,
haba anty ai dake zai kare rayuwar sa, insha Allah.

ohni! wai kuna bani mamaki kunsan fa rayuwar nan batada tabbas ba madawwa miya bace' tadan wani lokaci ne,
dukda haka dai anty'to shikenan ina fatan kinshirya kayanki Dan kinsan gobe ne,kikace zakije kauye gurin umma, haba anty aikin san yadda nake dokin ganin ummana yau ai bazanyi baccin kirki ba, kinsani ummana Allah sarki,
au wato taki ce ke kadai ma ko?

au sorry ummanmu!
washe gari tunda safe taslima da driver suka dauki hanyar kauyen nasu da akwai nisa hakan yasa sai karfe3 na yamma suka shiga kauyen sukayi parking a kofar gida da gudu tashiga gidan tana kwalawa ummar ta tah Kira,
ummar datake duke tana hada itace a murhu tace' wah nakeji kamar taslima, kafinta karasa taji an rungemeta dukkan su farin ciki suke kara ra, a fuskokin su,

daki suka nufa driver kuwa shigowa yayi da kayan bayan sungaisa da umma yasha ruwa yace'xai wuce.

Inna kuwa tanajin xuwan taslima ta dauko tabarma ta shinfida a tsakar gida tanata habaici da maganganu anje karuwanci andawo shine za'a shige daka a bawa uwa Dan abunda aka samo Ana karyar aiki akaje to aidai maji magani,
tundaga umma har task in a babu Wanda ya kulata, taslima ta fito da 20k dinda anty tauhida ta bada akawo wa umman da kuma tsaraba da kayan abinci da sutura, sosai umma ke godiya tana sawa tauhida albarka sannan takara yiwa taslima nasiha ta rike mutuncin ta tabama marar da kunya,

satin ta daya amma jitayi kamar tana kurkuku saboda axabar bakaken maganganu da mugun fata irin nasu baba da inna Dan haka 1week tayi tadawo kano,tacigaba da karatun ta DA kuma aikinta,,,,,,

💞💕💞💕💞💕💞
Allah ne shaida!

xee'abu safana mrs'Bamalli

this is your page safiyya lamba Ina godiya da nuna kulawa da kaunar littatafai na jinjina yar mutanen sakwatawa,

¶¶¶¶¶

cikin kula tauhida ta dubeta tace'taslima alfarma naxo nema a gurinki?

alfarma kuma ni anty,ai babu abunda zaki nema a gurina ki rasa shi, meh kike so anty!

aikine mai wahalar gaske taslima, aikine kuma na sirri sonake yazama sirri tsakanin na dake,sai Wanda xaiyi aikin?

anty meh kike so ne haka?

kuka tasaki ta rike hannun taslima tace' kanwata yanxu haka Ina dauke da wani cikin a karo na6 kenan doctor ya tabbatar minda cewar cikin nan shima zubewa zaiyi kamar sauran saboda inada matsala kuguna(marata) bazata iya daukar Dan mutum ba mafita daya ce!
mene ne mafitar aunty?

dole saidai acire kwayoyin halitta na asaka a cikin wata indai anaso su rayu! taslima ki taimake ni, Ina rokon ki, ki amince a cire kwayoyin halitta na asama ki kirainar min su,ki haifarmin ki bani, taslima kinsan burina bai wuce Inga jini na ba, kuma inaji a jikina bawani dadewa zanyi a duniya ba,

jin maganar antyn tayi kamar saukar aradu ina bazai yiwuba, inzama bazawarar karfi da yaji alhalin bantaba yin aure ba,kuma idan mutane suka ganni da Cikin meh zance musu, mezan cewa ummana? baba da Inna suyi mana dariya a kunyata ni a idon duniya domin duk Wanda zancewa ba cikina, bane bazai yarda ba,ko a gaban ummana naje banida wata sheda,duk Wanda xancewa banyi zina ba kuma banyi aure ba,bazai yadda ba tunda dai ciki ba'a shansa a ruwa ko a shaka a iska kowa cewa zaiyi waye shaidata, to ni kuma ai nasan ALLAH NE SHAIDA sai kuma ita antyn, gaskiya bazan yarda ba,wannan ai ganganci ne da rayuwa da kuma farin cikina, take so inyi, tawani bangaren kuwa Ina tausayawa Mata matuka Ina kuma tuna alkairinta a gareni sosai,,,,
taslima kinyi shiru' kallonta nayi nace'AUNTYYYYYY!!!!
Murmushi Antyn tayi tace'taslima? Fadamin abunda ke ranki,
A kasalance tace"anty na amince, da sauri tauhida ta rungumeta tana fadin nagode kanwata ki shirya gobe muje mucewa ummanki zamuyi tafiya zamu Dade, sannan kuma namiki alkawarin babu Wanda zaisan maganar nan dagani sai ke sai ALLAH to anty! Ta fadi ita dai kam duk jikinta a maceh yake tana tsoron al'amarin,

Washe gari suka shirya suka dauki hanyar kauyensu ita kam duk batada walwala domin abun yana bata tsoro,a haka sukaje Umma taji dadin ganin su barinma dataga harda tauhida,
Tauhida da kanta tayiwa ummar bayani fatan alkairi tai musu suka kwana daya suka dawo gida, ranar da za'ayi aikin sosai tauhida ta kwantarwa taslima da hankali inda taji tadan samu relief, a ranar doctor yai musu aikin, aka cire kwayoyin halittar daga jikin tauhida aka sakawa taslima, 1week sukai a hospital sika dawo gida a lokacin kuma su taslima suka fara zana jarabawar waec,
Ita kanta tana mamakin yadda Antyn ta tah take kulada ita Dan yanxu ko ruwan wanka ita take hada mata, Dan haka ta fara sakin jiki da al'amarin dukda sabon yanayi datake taji a jikinta, a haka ciki ya fara mikawa kuma sungama exam da haka tacigaba da zama domin yanxu boyeta anty takeyi a kullum tana fadin taslima' ki saki jikin ki, kinji babu Wanda zaisan wannan sirrin dagani saike sai Allah ko mijina bazai saniba har sai zuwa bayan kin haihu zan sanar masa gaskiya kinji,

To but anty inda Allah yasa ni kuma nasamu miji nayi aure yagane baisame ni a budurwa bafa mezance masa,anty kinsan duk macen data haihu to sai tazama disvargin.
Hakane amma ke aina xaba miki miji kicire wannan shima a ranki kinji nayi miki miji nagari, yanxu ki kwanta ki huta bari inshiga kitchen mezan girka miki?
Ummmmm! Dan daga Kai tayi Rana' nazari tace' tuwon dawa miyar kuka tsanwa shar kar'asamata manja! Kuma bana son asaka tarugu ko kayan miya, so nake asaka sansamin yaji a miyar,
Dariya anty tayi' tace to angama,

Kullum abunda take so take ci a gidannan Dan haka batada matsala saita tunanin haihuwa!
A haka har cikinta yakai wata 6 ciki fa yafara tsufa domin yafito sosai, har gida doctor yake zuwa yana dubata, ya kuma tabbatar musu yan'biyu ne namiji da mace' Allah sarki anty harda kukan dadi tayi yanxu a duniya babu abunda tafi so kamar cikin nan, Dan haka kullum cikin addu'ar Allah yasauki taslima lapiya take,

Around 10pm na dare kwance take tana wayada tauhid tace'namesake kasan mene ne?
Gyara kwanciyar sa yayi tareda shafa sajensa yace' a.a namecy saikin fadi,

Namesake Allah inada ciki,

Zabura yayi yace'sure, habibaty are you serious?
Am serious inada ciki harna tsawon wata shida6,
What you said 6month?
Yes 6months amma fa baya jikina wllh,
Shiru yayi yana nazarin maganar ta tah banda yasanta lapiyarta lau, da ace wani ne yai maganar da yace' lallai bayada hankali,shi baigane wannan bahaguwar maganar ba wai tanada ciki na6 months amma a jikin wani kajifa wani sabon salon hauka kuma,

Shirun dataji yayi yasa'tace wallahi mijina da gaske nake kashirya ka kusa zama uba,
Jiyayi ta Kara rikita masa kwakwalwa yace' ke tauhida karfa kibari son haihuwa ya haukata ki yakike min wani zance haka,
Dariya tayi tace'shikenan saika dawo zanmaka bayani duk yadda lamarin yake, kuma kashirya idan kadawo zanmaka aure Allah kuwa,
Oh! Shoooooooot! Ya fada yana dafe kansa yace'karki rikita min kwalwa da shirmen ki na yau kinji ki kwanta saida safe ki kulada kanki i love you ya fadi tareda manno Mata wani dogon kiss ya kashe wayarsa.
Dariya abun yabata ta tashi tashige bathroom ta dauro alwala ta tada nafila.




Shafin kune wannan @GOLDEN'S WRITES ASDOCIATION@ godiya mai tarin yawa Allah yakara hada kanmu,


Shi kuwa tauhid yana kashe wayar tsoki yayi tareda fadin xai nemi Dama a gurin aikin subarshi yaje' Nigeria yakai tauhida a duba masa kwakwalwarta da haka yayi baccin sa,

Tauhida kuwa bayan tayi nafila alqur'ani tadauko tacigaba da karantawa kallon agogo tayi taga har daya da rabi na dare tati 1:30am Dan haka ta rufe tareda yin dogayen addu'o'i taje gefen taslima dake...


Read / Download ALLAH NE SHEDA 1 and 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album