Join Our WhatsApp Group

AUREN FANSA Complete Hausa Novel Document by AUREN FANSA


AUREN FANSA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 51160



AUREN FANSA

Reading Time: 4 Hours

Added On: 06, Oct 2023

Author: Maryam S Bello ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Pure Moment Of Life Writers

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 299.75 kb

File Type: txt

Views: 568+

Download: 239+

Last download: 5 days ago

Description/Story: AUREN FANSA 01
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
_AUREN FANSA_!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM!
Wannan shafin tukuci ne gareku members na
pure moment...!
FATY AXLAND SUHANA JANNART, AUNTY
KHADY, HUSNAH, DEEJA WAZIRI, ZEE YABOUR,
UMMUHANEEF, MOMYN SULTAN, UMMYN
YUSRAH, ZARAH SURBAJO, MOMYN KHADIJA,
UMMA YAHYA MUSA (SISIN MAMA), BIEBIE DEE,
NANA FA'AD,
FAtY MANSUR (XARAH), FATY KHALID NA
SHUKA, SHAFA ABDUL, SUMYNBASH, SALMA ALI
WADA, ROOKY KAZ, AISHA ALI GARKUWA, UMMI
HAMBALI, UMMEE GARKUWA, RUFAIDA YUSUF,
HAFSAT MUSA, SADNAF, FHARIEEDAT,
RAFEE'AT, SAMRAH, BIBA WADATA, SEEMALUV,
NEERATU LUV, AYSHA HANWA, AYSHA GANA,
UMMU SAFWAN, DELU CHOGAL, MRS FAWWAZ
(YESMEN TAFEESU), RAFI'AT DIKKO, MAMAN
IHISAN.❤️💖🌹
🌹01 🌹
Sautin kuka ne ke tashi a cikin d'akin, daga jin
mai yin kukan har cikin ranta takeyin shi, wanda
zan iya cewa koma dai menene, ta dad'e a haka,
don kuwa idanunta sunyi jajir sannan fuskarta
ma tayi ja saboda farar mace dama idan tayi
kuka fuskarta ta kanyi ja.
A hankali aka turo k'ofar d'akin aka shigo, daga
bakin k'ofa yaja ya tsaya yana k'are ma matar
tasa kallo a lokaci guda kuma yana girgiza
kansa cike da takaici. Sai da yaja numfashi ya
had'iye 6acin ransa sannan ya soma takowa a
hankali har yazo daidai bakin gadon da matar
tasa ke kwance tana kukan fitar rai.
A hankali ya dafa ta had'e da kiran sunanta cikin
wata irin sigar rarrashi.
"Hajiya Bilki."
Bata d'ago ba amma ta dakatar da kukan da
takeyi hakan ya nuna cewa taji kiran mijin nata.
A hankali ya soma magana.
"Haba Hajiya Bilki, dama ace bazaki iya d'aukar
kaddara ba? Har ki zauna kina kuka saboda
Allah ya jarabe mu? Haba Bilki! Kin bani mamaki
wallahi."
Shi d'inma k'arfin hali kawai yakeyi amma
zuciyarsa ta raunana!
Tashi tayi zaune gami da share hawayen
fuskarta tana fuskantar mijin nata da har yanzu
yake tsaye bai zauna ba. Sannan itama ta soma
magana cikin 6acin rai.
"Don Allah Alhaji ka barni, na gaji da wa'azain
nikam gaskiya hak'uri na ya k'are haba! Ta yaya
za'ayi ace mun shekara akalla sha biyu da aure
amma duk shekara sai nayi 6ari? Meyake faruwa
ne? Ka duba fa ka gani kaf danginka bak'ina
suke gani gaba d'aya sun tsane ni sun sa min
ido! Abin ya fi d'aga min hankali sai jiya da
muka je sunan gidan Hajiya Karima bakaga
yadda ake nuna ni ba! Gaba d'aya na zame
musu tamkar wata mujiya haba!"
Ta k'arashe tana cigaba da kuka. Alhaji ya
runtse idonsa yana mai jin rad'ad'i a cikin
zuciyarsa, tabbas yasan haka maganar take sai
dai kuma yasan basufi k'arfin Allah ya jarabe su
da rashin haihuwa ba, shi ya d'auki hakan a
matsayin kaddara. Don haka sai ya nutsu ya
fara magana.
"Hajiya Bilki a kullum bazan gaji da fad'a miki ba
Allah ubangijinmu mai baiwa ne sannan mai
hikima ne, kar ki manta ke d'in baiwarsa ce
sannan duk yadda yaga dama yayi dake haka
zaiyi dake, Allah yayi miki baiwa da yawa ba
dole sai kin samu haihuwa
zakiji dad'in rayuwarki ba, ki gode masa da ya
baki kyau, arzik'i ya wadata ki
da lafiya, sannan uwa uba ya barki da ranki, har
akwai abinda yafi wannan jin dad'i a rayuwa?"
Gwauron numfashi ya saki tare da zama a kusa
da ita yana kallon cikin k'wayar idonta sannan
ya cigaba da magana.
"Haihuwa ta Allah ce, idan yaga dama zai baki
idan kuwa bai ga dama ba duk dabararki bazai
baki ba, duk yanayin da kika tsinci kanki kamata
yayi, ki d'aga hannunki sama ki gode masa
sannan ki rok'e sa gafara da rahama.
Wad'annan maganganun nasha fad'a miki su ba
tun yau ba amma naga kamar ta iske suke bi.
Wallahi ki nutsu kar garin garajenki kije kiyi
sa6o, kina jina?"
Ta d'aga kanta a hankali yayin da ta sa
yatsanta ta share hawayenta. Yayi murmushi irin
nasu na manya yace.
"Bilki duk ba wannan kizo ki bani abinci yunwa
nakeji."
Ta6e baki tayi tace
"Kayi hak'uri na manta ban girka ba."
Yayi murmushi yace
"Bilki kenan ya za'ayi mijinki ya fita aiki tun
safe amma ya dawo gidansa abincin ci ya
gagare shi?"
Tace
"Haba Alhaji! Yau sati na d'aya fa dayin 6ari ya
kamata ka barni na huta mana."
Inda sabo ya saba da halin Bilki amma da yake
Allah ya zuba masa hak'uri sai kawai yayi
murmushi yace
"Haka ne Allah ya baki lafiya."
"Amin" kawai tace yayinda ta koma ta kwanta
gami da bashi baya. Tashi yayi ya fice daga
d'akin yana mai jinjina hali irin na Bilki.
D'akinsa ya fad'a kai tsaye yayi wanka yana
fitowa ya zumbula jallabiya fara ya fito ya nufi
kitchen, fura da nono ya had'a mai yawa ya
dawo parlor ya zauna had'e da kunna T.V yana
kallon tashar Aljazeera. Sai da ya gama shan
furar tas sannan ya koma ya kwanta tare da
lumshe idanu a lokaci guda kuma ya fad'a kogin
tunani a haka har bacci ya sace sa.
Awarsa biyu daidai ya farka ya duba agogon da
ke mak'ale a bangon hannunsa, k'arfe 4:19pm,
zumbur ya mik'e yaje yayi alwala yayi sallah,
bayan ya kammala kansa tsaye ya wuce d'akin
Bilki tana kwance kan gado tana latsa waya,
kiranta yayi a hankali.
"Bilki." Tana taunar chewing gum sai da yayi
k'ara k'as sannan ta d'ago ta kalleshi tace
"Na'am." Ajiyar zuciya ya sauke ya fara magana
fusakarsa ba annuri ko kad'an.
"Yanzu kina ganin bacci ya kwashe ni amma har
lokacin sallah ya wuce ki kasa tashi na inyi
sallah?"
Tace
"Kayi hak'uri na manta ne."
Girgiza kansa yayi yace
"Allah ya kyauta, zan fita daga can zan wuce na
gaida Goggo (mahaifiyarsa) sai na dawo."
Ko kallonsa batayi ba tace
"To sai ka dawo, daga nan ka siyo man nama
mana."
Fita yayi daga d'akin yaje ya sake yin wanka ya
shirya cikin farin yadi kalar kunun kanwa marar
nauyi ya fice daga gidan.
Sai da akayi sallar magriba sannan ya wuce
gidan Goggo dake cikin Layout a garin Katsina,
yana shiga ya fad'a d'akinta kamar yadda ya
saba bayan sun gaisa tasa aka kawo masa
tuwon masara miyar kuka da man shanu ya ci
ya k'oshi ya kora da fura. Nan suka d'an ta6a
fira kamar kullum sannan ta soko masa zancen
da kullum baya son shi.
"Ya maganar aure Hamza?"
Yayi dum ya kasa cewa uffan, tabbas shima
yana son k'ara auren sai dai kuma yana gudun
tashin hankalin Bilki, don haka bai ce komai ba
kansa dai na k'asa.
AUREN FANSA 02
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
Dedicated to Ummi Aisha and Zeebee💘
🌹02 🌹
"Daman nasan bazaka amsa ni ba Hamza, kuma
ni har ga Allah bazan maka dole ba. Sai dai kana
buk'atar kaje kayi tunani sosai akan maganar,
idan kana da ra'ayin aure to zaka iya yi, idan
kuma bakada shi babu damuwa."
Shiru yayi yana nazari, yana son faranta ma
mahaifiyarsa rai sannan bayason tashin hankalin
Bilki, don haka sai ya k'ak'alo murmushin dole
yace.
"Goggo zan je inyi shawara da Bilki kome kenan
zan zo na sanar dake."
Murmushi tayi tace
"Allah ya nuna mana."
Yace "Amin."
Bai bar gidan ba sai wurin tara ta wuce na dare,
gida ya wuce kai tsaye. Yana shiga ya wuce
d'akinsa yayi wanka ya sanya kayan bacci ya
fito parlor.
Bilki na zaune tana latsa waya tana kallon wani
American series, jin alamun shigowa yasa ta
kalleshi lokaci guda kuma tace
"Har ka dawo?"
Yace
"Na dawo." A lokacin da yake zama kan kujera
yana gyara zaman glass d'in idonsa. Matsowa
tayi kusa dashi tare da kwantawa bisa k'irjinsa.
Dukansu kowa yayi shiru kafin Bilki ta katse
shirun nasu
"Hamza, wai ya maganar mu ne?"
Yace
"Wace magana kenan?"
Ta zum6uro baki tace
"Ba dai har ka manta ba?"
Yayi shiru tabbas yasan maganarta bata wuce
tana son kud'i.
Tayi murmushi tana mai kashe murya had'e da
shagwa6a tace
"Kace zaka bani kud'i naje Dubai mana saro
kaya."
Shiru yayi gami da sauke nannauyan numfashi
yace
"Bilki kenan, ay mun gama wannan maganar tun
rannan kuma nace zan baki, sai dai ba dole sai
kinje ba yanzu ay inace sautu ake badawa kuma
bama haka ba, ina k'awarki da ke yawan zuwa
basai ki bata ba ta kawo maki."
Ba haka taso amma ya zama dole ta lalla6a shi
don haka sai tace
"Duk d'aya ay kuma bakomai sai na bata d'in
nawa zaka bani?"
Yace
"Zan baki dubu 100 ki fara da ita daga baya sai
na k'ara maki."
Da sauri ta tashi zaune
"Dubu d'ari kuma? Ni gaskiya ta mani kad'an."
A fusace ya tashi tsaye yace
"Toh idan har bakiso gaba d'aya a barshi mana,
ya zan baki ki raina? Gskiya ki chanza halinki."
Daga haka ya tashi ya shigewarsa d'aki yayi
kwanciyarsa maganar auren da basuyi ba kenan
don ya fusata.
Washe gari ta kama Monday, kamar kullum ya
tashi ya shirya kasancewar aikin banki yake
yasa tun asuba idan ya tashi baya komawa
bacci.
K'arfe bakwai daidai ya kimtsa ya fito daman
baya jiran breakfast don Bilki bayi takeyi ba, a
hanzarce yake komai tashinta yayi daga bacci ya
ce mata zai tafi aiki, juyi d'aya tayi tashi tace
masa "Toh" sannan ta ja bargo ta rufe har
kanta. Girgiza kansa yayi ya shiga motarsa ya
harba titi.
Wani shop ya tsaya ya sayi bread da yoghurt sai
lemo sai kuma kayan tea da biscuit don na office
d'insa sun k'are, daman ya kan aje saboda ko
yaji yunwa sai yaci kawai.
A haka ya isa office d'insa ya soma aikinsa
kamar kullum. Haka ya wuni yana juya maganar
Goggo a ransa yanata sak'e sak'e, haka dai
yake sukuku dashi har lokacin sallah sannan ya
tashi ya fice tare da sauran abokanan aikinsa
musulmai.
Kamar kullum yau ma sai kusan k'arfe 6 ya diro
gida, gajiya kam ya gaji ba kad'an ba ga yunwa
data addabe shi ga uwa uba ana zafi agarin.
Yana shiga gida ya ci karo da Bilki a bakin k'ofa
taci ado tayi kwalliya na fitar hankali ga gidan
sai k'amshi ke tashi. Taro sa tayi bakin k'ofa
tana mai aika masa da sak'koni ta ko wane
fanni, a hankali ya ture ta yace
"Kinga Bilki na gaji bari naje na fara watsa ruwa
kafin lokacin sallah yayi."
Murmushi tayi ta sake sa sannan ta koma parlor
ta zauna tana binsa ta kallo har ya shige
d'akinsa.
Sai da ya kimtsa ya fito sannan ya wuce kitchen
don neman abinda zaici. Tana kallonsa ya fito
da cup d'in tea da biscuit a hannunsa ya zauna
kan dinning yaci. Sai da ya kammala tazo ta
zauna a kusa dashi tana yatsina baki tana wani
yanga da kwarkwasa. Can kuma tace
"Alhaji."
Bai kalle ta ba yace
"Na'am."
Tace
"Alhaji daman k'awata zatayi bikin k'anwarta
shine nake so ka bani kud'i na bata guddumawa
ta..."
Da sauri yace
"Haba Bilki daga dawowata zaki tare ni da
zancen wasu kud'i ay sai ki bari na huta dai
ko?"
Murmushi tayi tace
"Haba Alhaji duk bai kai ga tashin hankali ba ka
huta sai muyi magana."
Bai k'ara magana ba illa tashi da yayi ya fita
don yaga lokacin sallar magriba ta gabato.
***
"Mummy!" Yaro d'an kimanin shekara goma ya
rugo da gudu, Maman tasa na zaune kan wata
irin makekiyar kujera tana duba magazine da
glass d'in karatu a idanunta. A hankali ta d'aga
ido ta kalli yaron da ke ta gudu kafin kuma ya
haye bisa cinyar ta yana mai hugging d'inta.
Itama hugging d'insa tayi tana kallonsa cike da
so tace.
"Lafiya ka shigo da gudu haka FARUK?"
Yaron da ta kira da Faruk yana mai tsananin
murmushi kafin ya rufe baki wani babban mutum
dogo fari ya shigo yana sanye da kayan
hausawa harda babbar riga, sai da yazo daidai
bakin k'ofar da zata sadasa da parlon yaja ya
tsaya yana murmushi, sannan kuma yace.
"Ay Faruk ya d'auko grade mai kyau, sannan ya
lashe baki gaba d'aya wato overall as always."
Dukansu suka d'aga ido suka kalli mutumin dake
tsaye ya hard'e hannayensa biyu yana
murmushi.
Matar da aka kira da Mummy ta rungume Faruk
sosai a jikinta tace
"That's my boy, haka nake so Allah ya k'ara
maka basira, toh saura na Islamiyya, idan har
kayi k'ok'ari shima akwai kyautar dana tanadar
maka ta mussaman."
Cike da jin dad'i Faruk yace
"Allah Mummy?"
Tace
"Kayi ka gani I promise."
Mutumin dake tsaye ya tako ya shigo parlon,
kusa da kujerar dasu Faruk ke zaune ma'ana
doguwar kujera, sai da ya cire babbar rigarsa
sannan ya zauna yana shafa kan Faruk yace.
"My boy aje a cire uniform ayi wanka ko sai
kazo muci abinci."
Faruk yace
"Ok Daddy."
Sannan ya tashi da gudu ya shige d'akinsa.
Matar da ke zaune kusa dashi mai suna Reemah
wadda na k'are ma kallo kyakkyawar gaske ce
fara mai yalwar gashi don kuwa har gaban
goshinta ya fito. Bana tantama ta had'a iri da
larabawa. Kamo hannun mutumin tayi mai suna
Adam tace
"Muje ka watsa ruwa kaci abinci ko?"
Murmushi yayi yana jin son matarsa na k'ara
fizgarsa sannan yace
"Muje sahibata."
Murmushi tayi sannan suka mik'e a tare suka
nufi kan bene inda hannunsu na mak'ale da na
juna...

AUREN FANSA 03
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
Dedicated to my darling Maman Ihsan (SAFNA)
much love darl💕💘❣️
🌹03 🌹
***
Daddare sai da Bilki ta k'ara tada masa da
maganar wasu kud'in inda a ranar sai da ya yi
6ata mata rai fiye da tunaninta sannan ya nuna
mata ta cika son kud'i, duk dai abubuwan da ya
dad'e dasu a ransa shekara da shekaru sai da
ya amayar mata dashi, sum sum ta tashi ta
koma cikin d'aki tsabar borin kunya.
Jingina yayi da kujerar parlon tare da lumshe
idanu don ya samu nutsuwa sai dai bai kai ga
yin hakan ba wayarsa ta fara ruri, kallon screen
d'in wayar yayi yaga sunan da ya bayyana wato
My sister, murmushi ya saki na tsananin farin
ciki a lokaci guda kuma damuwarsa ta 6ace 6at,
d'auka yayi gami da yin sallama, d'ayan
6angaren akHTTP/1.1 200 OK
Content-Type: applicatioin/OCTET-STREAM;charset=utf-8
Content-Disposition: attachment;filename="AUREN+FANSA+CMPLT+BY+09063626602.txt"
Content-Length: 301602
Server: Jetty(i-jetty 1.4.1129.gionee)

AUREN FANSA 01
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
_AUREN FANSA_!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM!
Wannan shafin tukuci ne gareku members na
pure moment...!
FATY AXLAND SUHANA JANNART, AUNTY
KHADY, HUSNAH, DEEJA WAZIRI, ZEE YABOUR,
UMMUHANEEF, MOMYN SULTAN, UMMYN
YUSRAH, ZARAH SURBAJO, MOMYN KHADIJA,
UMMA YAHYA MUSA (SISIN MAMA), BIEBIE DEE,
NANA FA'AD,
FAtY MANSUR (XARAH), FATY KHALID NA
SHUKA, SHAFA ABDUL, SUMYNBASH, SALMA ALI
WADA, ROOKY KAZ, AISHA ALI GARKUWA, UMMI
HAMBALI, UMMEE GARKUWA, RUFAIDA YUSUF,
HAFSAT MUSA, SADNAF, FHARIEEDAT,
RAFEE'AT, SAMRAH, BIBA WADATA, SEEMALUV,
NEERATU LUV, AYSHA HANWA, AYSHA GANA,
UMMU SAFWAN, DELU CHOGAL, MRS FAWWAZ
(YESMEN TAFEESU), RAFI'AT DIKKO, MAMAN
IHISAN.❤️💖🌹
🌹01 🌹
Sautin kuka ne ke tashi a cikin d'akin, daga jin
mai yin kukan har cikin ranta takeyin shi, wanda
zan iya cewa koma dai menene, ta dad'e a haka,
don kuwa idanunta sunyi jajir sannan fuskarta
ma tayi ja saboda farar mace dama idan tayi
kuka fuskarta ta kanyi ja.
A hankali aka turo k'ofar d'akin aka shigo, daga
bakin k'ofa yaja ya tsaya yana k'are ma matar
tasa kallo a lokaci guda kuma yana girgiza
kansa cike da takaici. Sai da yaja numfashi ya
had'iye 6acin ransa sannan ya soma takowa a
hankali har yazo daidai bakin gadon da matar
tasa ke kwance tana kukan fitar rai.
A hankali ya dafa ta had'e da kiran sunanta cikin
wata irin sigar rarrashi.
"Hajiya Bilki."
Bata d'ago ba amma ta dakatar da kukan da
takeyi hakan ya nuna cewa taji kiran mijin nata.
A hankali ya soma magana.
"Haba Hajiya Bilki, dama ace bazaki iya d'aukar
kaddara ba? Har ki zauna kina kuka saboda
Allah ya jarabe mu? Haba Bilki! Kin bani mamaki
wallahi."
Shi d'inma k'arfin hali kawai yakeyi amma
zuciyarsa ta raunana!
Tashi tayi zaune gami da share hawayen
fuskarta tana fuskantar mijin nata da har yanzu
yake tsaye bai zauna ba. Sannan itama ta soma
magana cikin 6acin rai.
"Don Allah Alhaji ka barni, na gaji da wa'azain
nikam gaskiya hak'uri na ya k'are haba! Ta yaya
za'ayi ace mun shekara akalla sha biyu da aure
amma duk shekara sai nayi 6ari? Meyake faruwa
ne? Ka duba fa ka gani kaf danginka bak'ina
suke gani gaba d'aya sun tsane ni sun sa min
ido! Abin ya fi d'aga min hankali sai jiya da
muka je sunan gidan Hajiya Karima bakaga
yadda ake nuna ni ba! Gaba d'aya na zame
musu tamkar wata mujiya haba!"
Ta k'arashe tana cigaba da kuka. Alhaji ya
runtse idonsa yana mai jin rad'ad'i a cikin
zuciyarsa, tabbas yasan haka maganar take sai
dai kuma yasan basufi k'arfin Allah ya jarabe su
da rashin haihuwa ba, shi ya d'auki hakan a
matsayin kaddara. Don haka sai ya nutsu ya
fara magana.
"Hajiya Bilki a kullum bazan gaji da fad'a miki ba
Allah ubangijinmu mai baiwa ne sannan mai
hikima ne, kar ki manta ke d'in baiwarsa ce
sannan duk yadda yaga dama yayi dake haka
zaiyi dake, Allah yayi miki baiwa da yawa ba
dole sai kin samu haihuwa
zakiji dad'in rayuwarki ba, ki gode masa da ya
baki kyau, arzik'i...


Read / Download AUREN FANSA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album