Join Our WhatsApp Group

KADDARAR RAYUWA Complete Hausa Novel Document by KADDARAR RAYUWA


KADDARAR RAYUWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 50308



KADDARAR RAYUWA

Reading Time: 4 Hours

Added On: 06, Oct 2023

Author: Mai Dambu ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 293.56 kb

File Type: txt

Views: 1262+

Download: 654+

Last download: 2 days ago

Description/Story: a: *QADDARAR RAYUWATA*
       _SHUKRAH_

Mai_Dambu

    Sadaukarwa ga
_Ummyn Yusra_
_Zulaihat Rano_
_Aunty Raliya_
_Um Nass_
  ¥Ummul Ilham_

بسم الله الرحمن الرحيم

  Shafin farko

Zaune yake a ofis ɗinshi duk da aikin da yasha gaban shi be hanashi tunanin halayar D'an Uwanshi Maina ba yana mamakin yanda ya rufe idanun shi yake saɓawa Ubangijii shi ko goro baya ci balle akai ga giya ko zina asalima shi baya iya ɗago idanun ya kalle mace inda Ba kanwarshi Ubaedatu bane ko Autarsu zuhra duk da sun ɗin sun fitone daga gidan sarautar Katagum.

          Karan wayarshine ya dawo da shi daga duniyar tunani ɗaukar wayar yayi ya kara a kunenshi cike da ladabi da biyayya dan da alamu da babba yake wayar.

        "Na'am Abba, wayyo ba kowa a gidan key yana hanun ku jirani na zo na buɗe muku don Allah ganin nan"

       Miqewa yayi jikinshi na rawa yace.
" Ni Mashkur naga takaina Idan Abba yasame Maina yana tare da yarinyar nan a.,"

        Suran key ɗin motarshi yayi ya fita da sauri Yaranshi sojoji suka mara mashi baya tsuke fuska yayi ya ɗaga musu hanun komawa sukayi ya shiga mota yabar Basic na airforce dake gubi gari dake jahar bauchi.

     Gudu yake sosai kaman zai tashi sama,

    bak'in alkalami ya bushe dan me martaba sarkin katagum Alhaji Husaini Muh'd da tawagarshi sun isa gidajen manyan sojoji da yake maiduguri byy pass har sunyi parking sun gani motar maina a kofar gidan yasa suka shiga kai tsaye ya nufi ɗakin Allah ya taimaka shi ɗayane  ya nufi ɗakin Maina sauran duk suna falo.

           Yana isa koridon da zai sadashi da ɗakin maina ya soma jiyo ihunsu da nishinsu kunci da bakin cikine ya rufeshi amma bai kasa a gwiwa ba yatura kofar ɗakin yayinda kofar ya ɗaga labulen ɗakin Maina ya hango akan yar mutane, ita kuma ta ɗaga kafarta ta zuba mashi a kafaɗa sai zunkuɗata yake.🙊

       Sake kofar yayi jada baya kaman zai faɗi ji yayi antare bayanshi kamshin turaren shine ya shaida masa waye ya tareshi...

        Tallaɓe shi Mashkur yayi yakaishi ɗakinshi ya zaunar da shi a bakin gado sannan ya koma jikin firji ya ɗauko mashi ruwan faro ya buɗe mashi ya zuba akofi ya mika mashi a ladbace yana me sunkuyar dakanshi dan abinda yake gudu kenan kuma ya faru Mashkur ji yake kaman kasa ta tsage yashige sabida tsananin kunya Abba k'in ɗago kai yayi karshe fita yayi daga ɗakin yashiga ɗakin maina yana zuwa yasamesu suna nan akan abinda suke juya baya yayi cikin sanyi murya me daɗin yace.
"
Idan kagama abinda kake kaxo Ga Abba a ɗakina, zaka mutu ba ahaife wata mace ba ma kabi duniya a sannun kasan daga inda kafito amma ko ajikinka kake aikata zina sabida sanranka idan Aure kakeso Maina akwai mata a familynmu akwai a wasu gidajen sarautar masu mutunci da kima ba kadangarun bariki ba zasu kaika subaro ka indai matane...."

      Gashi a nutse yayi magana zaka ɗauka wata macece take magana haka, fita yayi daga ɗakin ranshi a ɓace.

      Shima maina jikinkishi rawa yashiga yi sabida wannan shine karo na biyu da mahaifinshi ya kama shi da mace....

    Banɗaki ya shiga yayi wanka sannan saka dan gajeren wando sannan ya juya ya tsuke fuska yace.

"Karki kuskura kifita inda bani nace kifita, kina jina ko..."

       Fita yayi daga ɗakin yashiga ɗakin Mashkur yana rakuɓe mai martaba yana zaune ya sunkuyar da kai hanunshi rike da kofin ruwa yana juyawa a nutse.

Cikin sanyi murya mashkur yace.
"Abba kayi hakuri insha Allah haka bazata sake faruwa ba Abb.."

       Daga mashi hanun yayi sannan yayi gyaran murya yace.
"Ai bakai kayi laifi ba kuma shima beyi laifi ba laifin namune da ace tunfarko haka zai koma toj da tun a lokacin muka mashi aure.Amma ina bamu hankanta ba asalima mun biyewa sun zuciyarmune domin yaranmu suyi karatu su zama wasu, Ban san wani laifi nayi Allah ya jarabce ni da ɗa mazinaci ba, ni ban taɓa shan giya ba ɓan taɓa niman mata ba asalima ni auren haɗi aka min ni da mahaifiyarka Maina duk cikin Yarana kaine kafita zakka a cikin y'ay'ana bansan laifin ba, amma ba damuwa kowannenku ya shirya  nan da sati biu za'ayi auronku, bazan so nasake kamaka da mace a karo na uku wanda nagani ma sun isa ko kashirya ko karka shirya xan haɗaka da Ubaidatu.."

       A razane Mashkur ya ɗago kanshi tsoro da farga suka ɗirka a fuskanshi juyawa yayi ya kalla Maina wanda yake rakuɓe gefe guda ranshi yaji tausayin kanwarshi ya rufeshi, dukkan yanda yaso ya boye damuwarshi haka be samu ba karshe sunkuyar da kanshi yayi zuciyarshi na tafasa yana jin zafin sosai taya za'a haɗa kamilar mace da Fasiki me lasisi irin maina yana tsaka da tunani yayi Abba yana cewa.

"Kai kuma mashkur  da Zubaidatu za'a haɗaka nasan tana sonka burinta kenan kai Mashkur dan haka kowannen ya shirya nan nan da sati biyu..."

  Yana gama faɗin haka ya mike yafita sukuma suka take masa baya yana isowa falon yace.  "muce gida yau"

    babu musu abokan tafiyarshi suka mike duk suka fita juyawa yayi yana kallon maina girgiza kai yayi yace.
" Allah ya shirya minku shiryar Addinin muslunci ba xan maka baki ba amma ina gargaɗinka da rayuwa kacigaba zaka haɗu da daidaikai..."

     Yana gama fadin haka yafita daga gidan haka suka rakashi.

     Suna tsaye motarsu ya tashi.

     Mashkur da Maina
Mashkur ɗane ga  marigayi hassan ɗin sarkin katagum kuma shine sarki a lokaci yana yana tare da matarshk kausar itama yar sarki ce daga borno, Yaransu huɗu mashkur ne babba sai sultan sai Ubaidatu, sai yar autarsu Zuhra, sarki hassan yanada shekara takwas Allah yayi mashi rasu lokacin mashkur yana da shekara sha biya sai yan majalisansa suka ce abawa Husain inyaso idan mashkur ya nime abashi kujeran babanshi sai abashi sam Abba husain baya kaunar wannan kujeran dan lokacin yana matsayin jakar naija a Sudan aka bashi dan dole ya karba amma a ranshi yana kudirin koda mashkur bai nemi haka ba shi zai bashi kujeransa.

         Maina ɗane ga sarki husain  shine Babba a yaran sarki, baya ji a rayuwanshi abu biyu maina yasani daga shan giya sai niman mata amma dukkan abinda yake yana sallah itama ba akan lokaci ba dan sai lokacinta ya wucce, maina na da kanne dan mahaifinsu yana da mata biyu, Hajiya kilishe ita mahaifiyar maina yar sarkin fika ce sai Hajiya Saude ita kam yar sarkin bauchi ne,

          a ɗakinsu maina su biyarne Akwai me bishi Abbati, sai  Bappa, Zubaidatu, sai ɗan autansu Khalil. dukkansu suna da kanmu kai amma banda maina domin shi mace kome muninta idan zai hango kirjinta a cike bayi da case zai bita.
     Bambancinshi da mashkur kenan yana da nutsiwa kamala, uwa uba mutunci, ga kamun kai yana da hakuri,amna idan aka kureshi bayi da daɗi gashi ya ɗauko kyau daga mahaifiyarshida farin fata.
          dogone  me fafaɗar kirji yana da kyau kam ba laifi haka maina,
      lalacewar maina yasame asaline lokacin da aka turashi karatun degree ɗin Thailand anan yaje ya buɗe ido da kananun yan mata da suke karuwanci acan ziyaran da mahaifinshi ya farko ya kamashi da mace, yayi masa faɗa da ya ɗauka daga baya ya watserar tundaga nan ya zama tantirin ɗan iska har yagama karatu.

     Lokacin mashkur yana nashi karatun a Uk, kusan tare suka gama sai martaba yasake turasu uk suyi degree nabiyu anan maina be bar halinshi ba har sukayi faɗa da mashkur dakyar Maina ya nime mashkur suka shirya sai dai tun daga ranar Mashkur ya haramtawa kanshi duk abinda zai fito hanun maina bayan gama karatunsune suka dawo nan sarki yake tambayansu wani aiki sukeso abin mamaki dukkansu suka ce soja mashkur sojan sama, yayinda maina ya zaɓe sojan kasa, maina aka turashi kaduna, mashkur kuma lagos

        Basu wacce shekara guda da dawowa ba daga karatu matasane Yan shekara 33,
3/4/21, 9:43 AM - Ummi Tandama: *QADDARAN RAYUWA TAH*
_SHUKRAH_
Sadaukarwa
Ummyn Yusra
Zulaihat Rano
Aunty Raliya
Mom Ahmad


*page 2*

A duniya Mashkur ya tsani halayar maina duk yanda yaso ya tank'wara shi abun ya faskara dan haka yake binshi da idanun, akwananki baya sunje cin abinci maina ne yayi odan abinci ido da ido mashkur yace
"D'an uwa ni bazanci ba kawai na koshi.."

      yana maganar hankalinshi nakan wayarshi dan kar maina ya tambaye shi dalilin sai ya tsime fuska yasa waya akunne yana magana hankalin shi kwance, murmusawa maina yayi sannan ya ɗaga kai yana karewa wajen  kallo caraf idanunshi ya faɗa kan wata budurwa, sanya take da wani riga iya gwiwa fari wanda har kana hango layin wandonta da brzs ɗinta tamatsu sosai ga wani uban gashin da ta tula akanta ga takalminta tsokale duniya daq'ar take tafiya tuni maina yaji ya fara ɗaukan chaji sosai, zubawa suranta yayi idanu yana haɗiye yawun makut, lokaci guda ya fita yanayinshi addu'a yake Allah yasa ta juye ta kalleshi, ay kuwa cikin sa'a ta ɗago kanta caraf sai idanunsu ya haɗu da juna kane mata ido ɗaya yayi take ta fara wani fari da idanunta tana kwarkwasa tana turo kirjinta gaba, ay sulalewa yayi ya bar mashkur a wajen ya ɗauki yarinyar yayi suka wacce lareema hotel.

       Bayan Mashkur ya gama wayane ya lura da maina baya cikin wajen bayi mamaki ba ya meke yafita abincin da basu ciba kenan, kai koda katin wayane mashkur baya taɓa yarda maina ya tura mashi balle kuma girki ko wani abu harta cokalin cin abinci kowa da nashi dan kyamashi yake ganin kazantarshi  maina yake gani dan shi ya tsani zina da shan giya wanda kusan ɗabi'an maina kena,

            Bayan tafiyarsu me martaba ne mashkur ya raɓa gefenshi ya shige cikin gidan,

      _Cigaban labari_
       ɗakinshi ya wucce ya shiga haɗa kayanshi babu abinda ya bari sannan ya fito ya rufe ɗakin ya koma ofis cike da ɓacin rai dan ya kudirin aniyyar rabuwa da maina.

                D'aga kafaɗa maina yayi yace
" ko a jikina zaka hucce kafin ka dawo"

        ɗakinshi ya koma amadadin ya kore yarinyar sai ma suka cigaba da masha'arsu...

              ***
4pm duk ilahirin yaran gidan sun shirya tsab sai dae mutum ɗaya suke jira kowa sai tsaki yake dan suna bakin cikin wannan ɗabi'anata,

        Cike da masifa wata mata tafito tace
"Uwar me kuke jirane da kuke tsaye kaman wanda aka dasaku maza kuwucce kafin na saɓa muku."

    Daya daga cikin yaran ne yace
"Aunty Amarya kije kawae ay zata fito muna jiranta"

             Daga kicin ɗin waje wata babban mata fara kyakyawa kana ganinta kaga bafulata doguwa me jiki tace
"Ayya Shkurah ba zaki fito ba suna jiranki me yasa kike hakane maza fito kafin nasa akira min bilal yazo yafita dake wallahi tunda baki jin magana Ubangiji ya shirya min ke shiryar addinin islam"

           Fitowa tai sanye da doguwar riga da himar ɗinta har kasa tasaka nikka a fuskanta ɗaga nikka ɗin tai ta zabga musu harara sannan taja tsaki, unifoam ɗinta kalan marron ce haka masauran sai gashi ya dace da fatarta farace tass yar shekara sha bakwai yarinya me jida kuruciyarta da jin daɗi,

       Kincin taje ta tsaya tana kallon matar sai tura baki take can da taga bata kulata ba dan aikin abincin dare suke ita da me aikinta ɗayyiba tana yanka mata vegetables.

Ganin tana ɓata lokacine tace
"Ayya Ummana zamu makara fa baki bani kuɗin tara ba kuma coki cokina ibon da eloka da alawar madara sun kare don Allah kice Adda Aisha taimin kinji" ta karshe maganar cikin sigar shagwaɓa,


          Mikewa Ummanta tai ta ɗauki pose ɗinta ta ciro naira ɗari biu ta mika mata tace.
"Ke dasu kuraba"
     tura baki tai ta amsa tace
"Mayu kawai daman kuɗin suke jira bani ba toh muje dangin kwaɗayi"

      "Ubangiji ya shirya min ke Shkurah kuje karku makara " Umma tace masu,

                     Haka sukayi ayari sai makarantarsu amma kafin a isa sai da aka biya ta gidajen kawayenta har ɗaya daga cikin abokan tafiyar itama sa'a shkurah ce mai suna Rafi'a tace
" gaskiya kina da mugun matsala dalla malama zamu tafi ba zamu bi ko ina ba"

         raba tafiya sukayi Rafi'a da ayarinta Shkurah da nata ayarin sai da suka biya ta gidan kawayenta sannan suka fito tare dake itace Ameera makarantar suna isa bakin gater tasa aka barsu suka wucce aji rafi'a  da Salmah yar Maman suna waje ansasu wanke ban ɗakin makaranta,


             Shkurah wacce sunanta Zainab, yarinya ce me matukar shiga rai gata da niman tsokana uwa uba, bata da kunya dan bata san tsoro ba amma tasame tarbiya sosai dan Umma tana da kokarin sosai dan ganin yaronta ya zama nagari ba nata kaɗai ba har na kishiyoyinta,

      Umma wacce sunanta Habiba itace uwargidan Alhaji Sa'idu Hammayo, yan misau ne, sai me bimata Mama Rukayya sai me bin Mama Ummi Hauwa, sai Aunty Amarya Jamela daga mama har Ummi kansu a haɗe yake da Umma dan basu kishi da ita dan asalima ita take rike da yaran gidan sai Aunty amarya yar Kaltungo ce tana da zafin kishi gani take kaman Umma ta gama da yan gidan dan har mijin idan ya dawo daga kasuwa dan babban ɗan kasuwane a bauchi yana dawowa kafin ya shiga ɗakinshi toh ɗakin Umma yake fara zuwa sannan ya shiga ɗakinshi sai sauran matan da Yaran gidan su shiga sai gaishe shi.

Umma itace me yara manya Abubakar shine babba yana aiki a gidan raidiyon bauchi sai Fatima tana aure a C.B.N quarts sai Hamdiya itama tana aure a dutsen tashi, sai Bilal, yana service ɗinshi a jos yazo hutu karshen mako, sai Aisha ke binshi tana schl of Nursing  shekaranta na karshe kenan, kuma ansaka aurenta nan da wata uku ita da ɗan Abokin babanta sai shkurah auta

        Sai Mama tana da yara bakwai Khadija tana koyarwa a F.g.g.c Azare tana aure a can sai Fatima tana misau take aure itama tana aiki a asibiti, sai Safwan yana karatu kuma yana zama ashagon babanshi a central market, sai Hafiz , sai Salmah duk suna tare da Shkurah dan sa'anan juna ne.

   Sai Ummi yaranta kanana ne sabida ita Allah be bata haihuwa ba sai yanxun dan an auro amaryarsu ma...


Read / Download KADDARAR RAYUWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album