Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

SIRADIN RAYUWA Complete Hausa Novel Document by SIRADIN RAYUWA


SIRADIN RAYUWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 36961



SIRADIN RAYUWA

Reading Time: 3 Hours

Added On: 30, Sep 2023

Author: Hafsat Rano ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Zafafa Biyar

Author Phone : 09033181070, 0903ย 234ย 5899

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 213 kb

File Type: txt

Views: 2381+

Download: 1226+

Last download: 3 hours ago

Description/Story: *SIRAD'IN RAYUWA*




*_Wannan littafin na kudine,kuma amana ce a hannun duk wadda tasiya,idan kina da buqatar a dama dake,nemi wadan nan lambobin ki saya ki karanta ta hanyar data dace cikin nutsuwa da kwanciyar hankali,babu cigiya,babu a dauko mana_*

*Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki*๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*

_saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)_๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

ย 0903ย 234ย 5899

*IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU*๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡


09033181070

_akwai yiwuwar ganin sabbin qirqirarrun sunayen garuruwa da gurare_



1995


*Tushen Labarin*




Malam bilyaminu usman,haufaffen bafulatanin nijer a haihuwa da yare,ta wani fannin kuma d'an qasar *KAISA* kuma bahaushe magidanci mai halayya da dabi'u da al'adu irin na wasu daga bara gurbin hausawa,wadanda basu gama fahimtar abinda addini yayi magana akai ba kan iyali da haqqoqinsu dake bisa wuyan dukkan wani magidanci,walau saboda jahilci ko kuma sun take ne da gangan bisa son zuciyarsu da soye soyen rayuka.

Haifaffen agadez iyayensa dukkaninsu suka kasance xallar fulanin niger,fatauci da neman kudi yakawoshi qasar kaisa,wanda a yanzun ita tazame masa mazauni na dindin.


Shiga da saninki kusan shine laqabin da mutane suka yiwa gidansa bayan da halayyarsa tafito qarara na auri saki,mutum ne ma'abocin aure aure,wanda har hakan yazame masa jini da tsoka,bai kuma daukeshi a wani abun aibu ko abun Allah wadarai ba,ya auri mata aqalla da suka doshi goma,wanda mafi yawa daga cikinsu kowaccensu tana da yara a gidan,walau maza ko mata.


Yana da tarin yara da suka kusa su ashirin da biyar,wanda dukkaninsu warin takalmi ne,mutum biyu uku uwarsu daban,harda masu mutun d'ai d'ai da uwarsu ta haifesu su daya tak cikin wannan gurguxu zuga da harqalla ta gidan,kamar yadda BILKISU take 'ya daya tilo da mahaifiyarta tahaifa cikin gidan.


Kusan dukka wadan nan tarin yara nashi yara mata sunfi yawa,saidai mazan da aka soma haifa masa na farko farko mutum uku daga ciki sun tasa,babu wani batun samun sauyi salama ko tallafi daga tasawar da sukayi,domin suma kowannensu takanshi yakeyi,ci sha sutura ko muhalli mai kyau bai cikin tsarinsa bare akai ga jigo kuma uwa uba ilimi,hasalima za'a iya cewa baisan kwana da tashin wani cikin iyalinshi ba,kowa yana riqe ne da kanshi.


Saidai kash,dukka wadan nan halayen nasa hakan bai hana a bashi aure ba,a duk sanda tabusa mishi,ko ranshi ya raya masa,yayi katari da budurwa ko bazawarar da ranshi ya kwanta mai da ita,tofa bazaiyi qasa a gwiwa ba wajen zage qwanjinsa da qarfin aljihunsa koda qarfin aljihun wasunsa ta hanyar cin basussuka yakashe mata kudi yakawota gidanshi.


Dukkan matar daya aura takan fantama a lokuttan da take cikin amarci,takanyi yadda takeso,takumayi yadda taga dama,saidai kuma da zarar wannan dama ta subuce daga hannunta shikenan itama zata shiga sahun 'yan ci dakai da neman na wanki da wanka,wanda hakan kan sanya wasu kasa jurewa,wasunsu sukan kai harsu haihu,yayin da masu zuciya a kusa,masu qarancin haquri kan tafi da ciki su haife a gida,bayan wani lokaci su dawo masa da yaro ko yarinyar da aka samu.


Cikin dukka matan daya aura mutum biyu ne tak suka iya jumurin xama dashi,mace tafarko itace kattume,wanda itace matarsa uku daya aura,tana da yara a gidan balaifi,hakanan takama sana'a ka'in da na'in,tana daukan nauyin kanta dana yaranta,hakanan cikin yaran takan yiwa wanda taga dama,hatta shi kansa malam bilyamun wani lokaci yakanci cikin arziqinta,hakan yasanya babu ganin girma girmanawa ko ganin mutunci tsakaninsa da kattume,idan ta hadosu babu wanda bazaiji kansu ba,bata shakka ko shayin zazzaginsa,ko lafta mishi baqaqen maganganu,hakanan yake zaune da ita shima saboda wataran yakan jingina da ita,sa'annan tazama tamkar wata kujera a gidan,duk wani harqallarsa da auri sakinsa a gaban idanunta yakeyi,hakanan za'ayi zaman a gama yasallami mace yasake jajibo wata.


Mace ta biyu data juri zamanta a gidan kuwa itace maimunatu,maimunatu macen da bai taba auren matar dayaji sonta cikin jiki da zuciyarsa ba irinta,macen dayaso har zuwa randa tabar duniya,macen da haryau yake marmarinta duk da qasa tarufe idanunsa,macen da bata taba daga kai ta kalleshi ba duk da mugunyar halayyarsa.


Yakance maimunatu tayi!,saboda ta soshi,ta qaunaceshi,takuma zauna dashi,duk da banbancin ahalin,daraja,nasaba,kyau arziqi da dukiya dake tsakaninsu,tazarace mai yawa tsakaninsa da maimunatu,amma duka bata duba wannan ba,a zamanin tanunashi takuma zabeshi cikin dubban samari masu kyau dukiya da aji da take dasu a zamanin.


Mahaifinta dan kasuwane da yayi suna,hakanan ya shahara wajen arziqi,kamilin mutum mai managartan halaye,nagartarsa tasanya bai duba matakin arqizin bilyaminu ba a wancan lokacin yadauki maimunatu yabashi,duk da cewa su biyu tak Allah ya azurtashi dasu a duniya.


Duk da tarin wahala da fama da take a cikin gidan bata taba fasa halin da take ciki ba,tun mahaifanta suna da rai har Allah yadauki abinsa,hakanan taci gaba da zama dashi,sam babu jituwa tsakanin bilyaminu da qanwar maimunatu mai suna zuhriyya saboda yadda take ganin yana gasa 'yaruwarta,ita kuma bata daga kai bare ta nuba mishi bacin ranta,tsabar sanyin halin maimunatu yakawo hakan,tun zuhriyya na budurwa idan tazo gidan bata kwana,iyakarta awa biyu uku tayi tafiyarta,don tace ba zata iya ganin baqinciki da takaici ba,kusan har tafi maimunatu jin zafin abun,don ko gaisuwa bata hadata da bilyaminu,hakan yasa ya shina yake cike da haushinta,yakance
"Duk abinki dai baki isa ki raba qaunata da maimunatu ba"
"Dana isa din ai da tuni na raba wallahi da baka kai warhaka tare da ita ba".


Haihuwarta tafari tasamu Bilkisu,yarinyar data fita daban cikin ahalin gidan da 'yanuwanta gaba daya,hakan kuma baya rasa nasaba da dangin mahaifiyarta data dauko wadanda suke jinin fulani,kakarta mahaifiyar maimunatu kuma shuwa ce.


Yadda komai na halittar bilkisu yake daban tun tana qanqanuwarta,saiya zamana komai nata ma daban yake,tsafta kwalliya da ado kullum cikinsu take,maimunatu tana da tsafta gason gayu da ado,uwa uba alokacin takan samu kudi cikin gadonta da mahaifinta yabari,na gidajen da ake mata haya da sauransu.


Duk wanda yakalli bilkisu saiya kuma dubanta,komai nata tsaf gwanin birgewa,uwa uba ga kyau da Allah yayi mata,sai hakan yasake zame mata ado da qawa.


Bilkisu nada shekara shida Allah yayiwa mahaifiyarta maimunatu rasuwa,duk dacewa a sannan tana da qarancin shekaru amma ta koka sosai,har hakan yabaiwa mutane mamaki,kukan nata saiya zama wani gwanin tausayi.


Zuhriyya kusan tafi kowa jin mutuwar ba kadan ba,tayi kuka tayi kuka har taji babu dadi,mutuwar 'yaruwarta daya tilo datake gani taji dadi ta girgizata matuqa,a lokacin saura watanni aurenta,amma babu yadda ta iya hakanan ta dangana.


A sannan taso daukar rainon bilkisu,amma bilyaminu ya qeqashe qasa yace sam bazai bata ba,dama can shiri suke na,bata taba nadamar rashin jituwarsu ba irin wannan lokacin,sai taji dana sanin bata aikata dukkan abinda ta aikata din ba sabida rasa damar daukar bilkisu datayi,ta wani bangaren kuma saita sake qullatarsa dajin takaicinsa,saboda duk sanda tatuna rayuwar da 'yar uwarta tayi duk da wadatarsu wanda shine sila saita sakejin qinsa a zuciyarta.


Ta fannin dangi ma bata samu goyon baya ba,kasancewar bata da aure itama riqonta ake, hakanan bikinta gab yake,tilas ta tattara ta haqura,duk da yadda taso daukar bilkisu kamar mutuwarta,saidai kullum tana hanya tana jelan ganin bilkisun,duk da tarin wulaqanci da take gani daga wajen bilyaminu amma tashanye,ita bilkisun kawai take kalla.


A sannan yarinyar bata gamu da wata matsala mai yawa ko.matsatsi ba,saboda zuhiryya kusan kwana a gidan ne kawai batayi,idan tayi nawar duniya ta tsallake kwana daya bata je ba,duk sanda taje zata mata wanka ta gyarata,ta siya mata duk abinda ranta yakeso,tawuni da ita,ta sanyata taci abinci sosai,a haka aurenta yatashi.


To yanayin aure bazaiyiwu tadinga sakaraftu ba kullum tana kan hanya,saiya zamana duk sati take zuwa ganin bilkisun,a sannan ta fuskanci akwai 'yan matsaloli na rashin kula daga matar uba dashi ubanma gaba daya,sai tasake ninka kulawarta akanta.


Ganin haka yasanya mijin zuhriyya sake shiga maganar karbo bilkisu,nan ma bilyamu yace Allah ya kasheshi shi bazai bada diyarsa ba,a sannan har duqawa zuhriyya tayi tana roqonsa kan hakan amma yace sam,haka tanaji tana gani ta haqura,saidai taci gaba da kulawa da bilkisun har zuwa tsahon wasu shekaru,wanda a sannan bilkisun takai shekara goma sha biyar.


A lokacinne yanayin aiki yadauke anty zuhriyya da mijinta zuwa qasar brazil,wanda zasu kashe shekara shida a can.


Ba qaramin tashi hankalinta dana bilkisun yayi na gaba dayansu,saida maigidanta ya kwantar mata da hankali,yakuma tayata shiryawa bilkisu duk abinda tasan zata iya buqata na tsahon lokaci.


To,ta hadu da uba mai son abun duniya,kusan duk abinda aka aje matan shida matarsa akaci,hakan yasanya kayan basuyi wani tsahon rai ba suka taru suka qare,abinda yarage mata kawai school fees dinta,wanda shima don anty zuhriyyan taje tabiya na
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download SIRADIN RAYUWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album