Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA


_By_
*GARKUWAN MARUBUTA*
[19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

*SAKAYYAH*
_Page 11_

_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE fa ya kusa ƙarewa*

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin.*


*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._



🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,

Cikin lumshe Ido Mommy ke cin perpesoup ɗin yayin da daɗinsa ke ratsa ilahirin jikinta,
kallonta Hajiya Bunayya dake murmushi tayi tare da ɗiban romon da cokali takai bakinta kana ta buɗe Idanunta dake lumshe.
Tace.
“Gaskiya Yaya Nagode wallahi bakiji yanda naji daɗin Perpesoup ɗin nan ba, dama sai tunanin a binda zanci nake tuntuni sai kuma gashi Allah ya kawo ki”.
Murmushi mai cike da Ma'anoni Hajiya Bunayya tayi kana ta muskuta tare da gyara zamanta tace.
“Lallai de kam aidama sanyin nan saida abu mai ɗumi da ɗan yaji-yaji”.
Yayin da aƙasan ranta wani irin farin cikine mara misaltuwa wanda har yakasa ɓoyuwa asaman fuskanta.
Ita kuwa Mommy Sosai take cin perpesoup ɗin tana mai lumshe Idanunta yayin da daɗin sa ke ratsa har ƙwaƙwalwar kanta tace.
“Yaya perpesoup ɗin nan yaji kayan yaji”.
Dariya Hajiya Bunayya tayi tace.
“Dama Alhaji nayiwa nace bari na zubo miki dan nasan zaki ji daɗin sa”.
Kai Mommy ta gyaɗa da faɗin.
“Aikam gashi yamin daɗi sosai”.

Acan ɗaki kuwa miƙewa tsaye Khausar tayi daga kan stool tare da riƙe ƙugunta ta bayan ta gama nin ke kayan asaman laɓɓannta ta furta.
“Wash Allah!, Gashi yanzu na gama gyara kayan nan, amma Raudat na zuwa ɗaukan abu ɗaya zata wargaza shi kab, ya zama kamar ba'a taɓa gyarashi, amma Insha Allah next time, Idan ta ƙara har gitsashi, sama Zan mayar dan kayanta, ta yanda idan tazo baza ta iya ɗauka ba sai ta kirani in bata yafiye min sauƙi”.
Ta Ida maganar tare da fitowa falon tana riƙe da ƙugunta da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke dafe asaman wuyanta.
Cike da mamaki take kallon Hajiya Bunayya dake zaune yayin da Mommy ta ke shan perpesoup ɗin da kaɗan ya rage asaman Plate ɗin.

Cikin yanayin tashin hankali da razana Khausar ta ɗaga Muryanta tace.
“Mommy me kike ci?".
Anitse Mommy ta ɗago kanta dan sam batasan ta fito ba sai da taji muryanta, gyara rikon Plate din Mommy tayi kafin tace.
“Perpersoup ne ko zaki cine?”.
Ita kuwa Khausar kai ta girgiza cikin rawan murya tace.
“A'a nikam bazan ciba Mommy kekam Komai kika samu sai kinci, ba zaki tsaya ki duba ingancin sa da kuma rashin ingancin saba”.
Baki Mommy ta sake tana kallon Khausar da Mamaki.

Ita kuwa Hajiya Bunayya wani mugun Harara ta galla mata cike da tsanarta tace.
“Komai ta samu saita ci ke kin isa ki hanata cine?, Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! ki kiyayeni fa”.
Ta Ida maganar tana dariya irin abin awasa takeyin sa, yayin da kuwa azuciyarta ba haka bane.
Ita kuwa Mommy taɓe Baki tayi tace.
“Yaya rabu da ita itama kanta kwaɗayin ya kawota ƙilan so take in bata”.

Fuska Khausar ta ɓata cike da damuwa tace.
“Wallahi nikam ba zanci ba Mommy kema Meyesa zakici, kema daga ganin abu saiki hau ci, batare da kin duba ingancin sa ba Allah ma dai yasa kinyi Bismillah”.
Dafe kai Mommy tayi tace.
“Aikuwa de Wallahi kwaɗayin sa yasa na shafa banyi Bismillah ba, Anma bari nayi.
Bismillahi feh Auwalihi Wa'ahirihi”.
Ta faɗa tare da cigaba da shan perpesoup ɗin.
Wani banzan kallo me cike da tsana Hajiya Bunayya ta watsa wa Khausar aranta tace, shegiyar yarinya, wannan yarinyar saina bi takan ta tukunna zata gane kurenta, bari dai ingama da matsalolin dake gabana”.
Ita kuwa Khausar kallon mahaifiyarta da har zuwa yanzu take shan perpesoup ɗin tayi tace.
“Wai Mommy ba zaki haƙura dasha haka ba?".
Girgiza Kai Mommy tayi kana tace.
“Kema Idan zaki ci ga shican akula Khausar ban hana kiba, amma wannan tambayoyin naki sun fara isata”.

Ƙwafa Hajiya Bunayya tayi tace.
“Ƙyaleta bare ma ni bazan bar mata ba ina kedai ya isheki?”.
Cikin sakin fuska Mommy ta gyaɗa kai tare da faɗin.
“Eh Alhamdulillah ya isheni”.

“Aiko buƙatar maje haji salla, ba zan bar matashi ba, tunda dai ke kinsha ai hikenan, idan tanaso ta biyoni ɗakina”.
Ta ida maganar tare da ɗaukan kularta ta fice bayan ta yiwa Mommy sai anjima.

Zama Khausar tayi agaban mahaifiyarta cikin raunin murya da yanayin damuwa tace.
“Mommy meyesa!?, Rayuwar nan fa ba yanda kika ɗauke ta da yanda zuciyarki take ace haka na kowa yake da munji daɗin duniyar nan fa, amma Mommy meyesa daga kawo miki abu zaki ɗauka kici yanzu kuma idan abin cutarwa ne fa?”.

Kallonta Mommy tayi cikin tsukr fuska kana cikin fushi tace.
“Khausar ki kiyayeni fa, bana son wannan baƙin halin da kike ɗaurawa rayuwarki fa. Ni bakiga ina nunawa matar nan baƙin hali ba haka zalika itama da zuciya ɗaya take zaune damu, zaman lafiya mukeyi babu kishi bare tsangoma ko hassada, amma meyesa zaki sawa ranki rashin yarda akan n
Me kike zaton zata cutar dani, babu abinda zata yimin dan haka ki kiyaye”.
Ita kuwa khausar hawaye da ya cika mata Idanunta tashiga ƙoƙarin mayarwa sabida takaici, mahaifiyarta ta ɗauki duk kan yarda da amana ta basu, amma sukuma da wannan damar suke amfani ganin sun cutar da rayuwarta.
Ƙasa Tayi da kanta kana tace.
“Shikenan Mommy Komai na faɗa miki ba zaki yarda dani ba, amma babu komai Ubangiji Allah yatsareki ya kuma kareki".
“Ameen”Mommy ta amsa a kufule.
Ita kuwa Khausar cikin mutuwar jiki ta miƙe tare da wucewa Bedroom ɗinta tana maijin wani irin zafi azuciyarta.
Da kallo Mommy tabi bayanta tana ayyana abubuwa da yawa akanta, tarasa ina Khausar ta ɗauko wannan halin baki ɗaya bata da yarda muddin Hajiya Bunayya zata kawo mata abu ko Haiydar saita tsaya tana musu tambayoyi akai, da faɗin kada suci kada suyi kaza da kaza.
Jin ƙiran sallah magriba yasa ta miƙe tashiga Bedroom ɗin ta dan gabatar da Sallah.

Aɓangaren Khausar kuwa tana shiga ɗaki ta lumshe Idanunta tare da manna bayanta da jikin ƙofa.
Hawaye masu ɗumi suka zubo mata jikinta na bata da wani makircin da Hajiya Bunayya ta shiryawa mahaifiyarta sam bata yarda da wannan perpesoup ɗin da takowo mata ba,
shin wai ma ta wani hanya zatabi ta fahimtar da mahaifiyar?.
Sosai ta zurfafa acikin tunanin da take har aka shiga Masallaci sai, asannan ta sauƙe gauron numfashi tare da nufar toilet cikin nutsuwa ta ɗaura alwala kana ta fito, tare da shimfiɗa darduma duk da yanayin zullumi da take ciki bai hanata tattara nutsuwarta zuwa ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ba,
bayan ta sallame ta ɗaga hannayenta biyu zuwa sama kana tace.
“Ya Allah baka zalinci sannan kai ka hana zalunci atsakaninmu ya Allah baka gyan-gyaɗi bare bacci ya Allah kada ka bawa wannan baiwar taka daman cutar damu ya Allah ka kare mahaifiyata al'farma Annabi da al'ƙur'ani”.
Kana ta shafa addu'ar tana mai zubar da hawaye har aka idar da Isha'i bata fita ba saima miƙewa da tayi ta kwanta agado lamo cike da tunanin rayuwa da haka bacci mara daɗi ya ɗauke ta.

Cikin ikon Allah haka Mommy ta kwana lafiya lau batare da wani mugun abu ba, tun Khausar na jira taji Mommy tace wani wajen nayi mata ciwo ko kuma taga zubewan cikin Mommy kamar yanda Hajiya Bunayya ta faɗa taji shiru,
hakan yasa ta watsar da abin aranta yayin da Aɓangaren Hajiya Bunayya baki ɗaya kunnenta ke sauraron jin wani labari daga bakin Mommy sai dai shiru amma tace bari ta kara jira kaɗan ta gani.

Yau kwanan Mommy uku da cin perpesoup ɗin da Hajiya Bunayya ta kawo mata tana zaune a Bedroom ɗin ta cike da kasala.
Cikin rumtse idonta ta zabura tare da dafe ƙasan maranta da yayi wani masifan murɗawa ahankali ta furta.
“Wash! Allah na”.
Sai kuma ta koma ta zauna tare da lumshe Idanunta yayin da hannunta na dama ke dafe asaman maranta sai ka ta miƙe tare da fitowa falon tana takawa ahankali.
Khausar dake zaune a asaman 3sitter Jikinta sanye da half gownt na bacci yayin da ta tura tulin sumar kanta acikin hular Net Idanunta na kan takardan Geography dake riƙe ahannunta yayin da Nahawu ke ajiye gefe ta ɗago manyan Idanunta ta zubasu akan Mommy dake ya mutse fuska alamar bata jin daɗin jikinta, zama tayi akan 1 sitter kana a hankali tace.
“Khausar har yanzu baki shiga ba?”.
ta ida mgnar tana mai cije lips ɗinta.

Ita kuwa Khausar kai ta gyaɗa mata tace.
“Eh Mommy karatu nakeyi, gobe Idan Allah ya kaimu zamu fara Exam ɗin First term, lokacin ai ya tafi amma Mommy lafiya na ganki haka?”.
Ta ƙare mgnar tana kafe mata ido.
Ya mutse fuska Mommy tayi tare da lumshe Idanunta still cikin na damƙarta tace.
“Wallahi cikina ke ɗan min ciwo Khausar”.

Cike da tausayawa Khausar tace.
“Cikin ki kuma Mommy?”.
Kai Mommy ta gyaɗa tace”.
“Eh”.
Ita kuwa Khausar ajiye takardan hannunta tayi tare da tsirawa mahaifiyarta ta Ido cikin tausayawa tace.
“Mommy kodai in faɗawa Abba Azo atafi Asibiti ne?".
Kai Mommy ta girgiza kana tace.
“A'a ai beyi tsanani har haka ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da sauƙe numfashi tace.
“Toh Allah ya sawwaƙe”.
Mommy da hannunta ke dafe asaman cikinta still Idanunta na lumshe tace.
“Ameen”
Miƙewa Mommy tayi ta koma kan 3sitter ta kwanta kamar minti biyu da kwanciyarta ta sai kuma sake miƙewa ta zauna tana yamutse fuska.

Ita kuwa khausar cikin yanayin damuwa tace.
“Sannu Mommy kode in Kira Abba ne?”.
Girgiza kai Mommy ta kumayi sannan tace.
“A'a tashi ki koma ɗaki nima yanzu zan shiga na kwanta”.
Girgiza kai Khausar tayi tace.
“A'a Mommy Zan zauna dake”.
Lumshe idanu tayi tare da cije laɓɓanta na ƙasa tace.
“Kada ki damu kije ki kwanta na faɗa miki naji sauƙi kuma nima yanzu zan shiga na kwanta”.

Cikin sanyin jiki ta mike kana tace.
“Saida safe Allah yaƙara sauki”.
Mommy ta amsa da “Ameen”.

Ita kuwa Khausar tana shiga ɗaki ta zube akan gadonta tare da faɗa wa duniyar tunanu, a haka bacci ya ɗauke ta kasancewar dare yaja batayi bacci ba ga kuma gajiya.

A ɓangaren Mommy kuwa haka ta kwana cikin mawuyacin hali tare da murƙusoso cikin matsanancin ciwon ciki.
Washe gari.
Da safe bayan Khausar na idar da Sallah tayi Azkhar ta nufi ɗakin Mommy bakinta ɗauke da sallama.
Mommy dake kishingiɗe kan darduma ta ɗago kanta tare da amsa sallamar Khausar.

Kusa da ita Khausar ta tsugunna tare da riƙe hannunta tace.
“Mommy ina kwana ya cikin naki?”.
“Murmushin Ƙarfin hali Mommy tayi kana tace.
“Naji sauƙi Khausar kije ki haɗa muku abin Breakfast kada lokaci ya ƙure”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.
“Amma da sauki Mommy kodai daurewa kike yi?”.
Murmushi Mommy tayi tace.
“Eh jeki shirya muku”.
Kai ta gyaɗa sannan ta fice kai tsaye kichen ta nufa.

Tana shiga tasa ruwa kadan atukunya yanda zai wadatar mata bayan ya tafasa ta ɗan zuba mai kana ta zuba Couscous kamar minti goma ta buɗe taga ya dahu yayi sar gwanin kyau, amfanin ɗiga man kenan.
Sauƙewa tayi sannan ta buɗe fridge ta ɗauko miyan stwe da yaji naman kaza ta ɗumama sai kuma ta dauko lunch box din Raudat, Ramadan da Haiydar da kuma nata ta zuba musu, sai kuma ta koma ɗaki tashiga toilet tayi wanka Agurguje ta fito ɗaure da towel mai ɗan girma sannan ta cirewa Raudat kayanta tayi mata wanka bayan sun fito tashafa mata mai kana ta sanya mata Uniform sannan itama ta shirya cikin Uniform da yayi matukar amsar jikinta hannu Raudat taja suka fita dai-dai lokacin da Haiydar suka fito da Ramadan cikin shiri ko wannensu ya nufi inda lunch box ɗin da yake ya ɗauka kana suka fice harabar gidan suka shiga mota.

Kamar ko yaushe motar na parking Khausar ta fito riƙe da hannun Raudat,
Sai da ta kaita ajinsu sannan cikin sauri ta juya ta kama hanyar koma ajinsu daga baya taji ankira sunan ta da faɗin.
“Lelewal ke kullum sai kowa ya riga ki shiga cikin aji ko?”.
Ahankali ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta akan Malam Isa dake tsayi murmushi tayi da faɗin.
“Ba haka bane Malam na tsaya kai Raudat ajinsu ne shiyasa”.
Kai ya gyaɗa still Idanunsa akanta hakanan yarinyar ke burgesa ahankali yace.
“To ki tafi kar araba musu questions paper ba kyanan”.
Kai ta gyaɗa tare da juyawa cikin sassarfa da sanin darajar kanta take tafiya har ta isa cikin ajin.

Aɓangaren Amina kuwa koda M Jameel yashiga class da niyyar raba musu questions paper ƙasa tayi da kanta ta amsa batare data kalli fuskarsa ba domin koda gaishesa ne ta dena tunda ta lura da baya buƙata kallon fuskanta, to shima M Jameel Sosai yaji daɗi da yarinyar ta daina gaishesa, dan ko kaɗan baya ƙaunar kallon fuskarta, bare kuma wata magana ta haɗa su.

Acan gida kuwa tun bayan tafiyar su Khausar Makaranta cikin Mommy ya tsananta da ciwo da ƙyar ta yunƙura ta miƙe tana mai rintse Idanunta jini taga yana bin ƙafafunta da sauri ta dafe cikinta da ƙyar ta iya furta.
“Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”.
Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya, kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama.

Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace.
“Yaya”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin.
“Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”.
cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace.
“Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya ɓalle min!
Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”.

Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace.
“Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”.
Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana shirin fita.
A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace.
“Yanzu Mommyn Khausar ta kirani.
Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”.
Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa.
Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya.
Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta riƙo hannun Mommy.

Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace.
“Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”.
Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na tsananin farin cikin burinta ya cika ne.

Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita,
agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy.

Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta.

Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa.
Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan rawan jikin da yake mata.
A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa amma baice komai ba.
Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace.
“Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”.
A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu abinda ke damunta.
Lumshe idanunsa yayi yace.
“Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin.
“Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya zauna”.
Kai ya jinjina amma baice komai ba.
Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.
“Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”.
Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta.

Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida, motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su
Tana shiga falo ta fara kiran.
“Mommy! Mommy!! na mun dawo”.
Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran.
“Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”.
Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace.
“Addah Khausy Ina Mommy?”.
Kallonta Khausar tayi kafin tace.
“Bata ɗaki ne?”.

Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh,
Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin.
“Mommy Mommy kina ciki kuwa?”.
Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata jin daɗi.

Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace.
“Jirani anan ina zuwa”.
ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin.
“Ummah”.
Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa.
“Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”.
Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki.
Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon Khausar.
Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa.
“Ummah ina Mommy mu?”.

Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace.
“Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”.

Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta.
Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace.
“Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya tsaresu daga sharrin mai sharrin”.
Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita.
Da sauri Hajiya Bunayya tace.
“Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”.

Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya Bunayya kana tace.
“A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”.
Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin.
“Sannan su waye ne Magautan?”.

Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin.
“Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su, domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai musu kamun talala!”.

Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace.
“Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.”

Ware ido Khausar tayi tace.
“Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”.

Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne.
Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin.
“Bari na tafi asibitin kar dare yayi”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace.
“Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”.
Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh ki gaisheta”.
Kai kawai

1 Comments On SAKAYYAH
avatar
fatima-8-5-3

1 month ago

Reply

Allah ya qara basira

Please Login or Register in order to submit comment