Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mu rasa shi kiran wayarsa muka fara rasawa Ummi, yanzu kuma Insha Allah mun samu kiran wayarsa shi zamu ƙara samu next da izinin Ubangiji”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Ameen”.
Cikin jin sanyi Asma'u tayi murmushi kana tace.
“Alhamdulillah wayar Yah Jameel ya shiga gaskiya munyi farin ciki”.
Malam Ahmad daya fito daga wanka ya fito coumpund ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Alhamdulillah Asma'u maza kawo musu abinci suci tunda mun samu wayar Jameelu ya shiga maza kawo musu abinci”.
Moddibo kuwa kallon Malam Ahmad yayi kana yace.
“Nikam ma Malam baki ɗaya cikina ya cushe baki ɗaya farin ciki ya cika min cikana”.
Murmushi Ummi tayi kana tace.
“Nima cikina ya cika baki ɗaya farin ciki nake ji”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.
“Dan Allah ku zauna kuci abinci wayarsa muka fara rasawa yanzu kuma wayarsa muka faru samu insha Allah shi ma zamu sameshi nan kusa ”.
Dai-dai lokacin Asma'u tazo ta ajiye musu abincin.
Tun ɓatan M Jameel sai yau Ummi da Moddibo sukaci abinci mai nauyi acikinsu duk da ba dayawa suka ciba.
Miƙewa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi bari naje in faɗawa Innayi ta tayamu farin ciki”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.
“Aikam dai gwara kaje”.
Ficewa yayi tare da tafiya Driving yake Cike da farin ciki har ya isa gida yana zuwa ya shiga sashen Innayi.
Innayi dake ki shimfiɗe ta miƙe kana tace.
“Alhamdulillah Moddibo naga kana cikin farin ciki da alama akwai labari mai daɗi?”.
Kai ya gyaɗa still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Innayi wayar J ɗina ya shiga yau”.
Kai Innayi ta gyaɗa tare da cewa.
“Alhamdulillah gaskiya munyi farin ciki. Allah ya bayyanar mana dashi”.
Ameen ya amsa tare da wucewa sashen sa cike da farin ciki yana shiga ɗaki ya kira layin Malam Arɗo.
Malam Arɗo na dagawa yace.
“Malam Alhamdulillah yau wayar J ɗina yashiga a cigaba da taya mu da addu'a a masallacai da makarantu”.
Cike da farin ciki malam Arɗo yace.
“Masha Allah da izinin Ubangiji zai fito Insha Allah zamu cigaba da addu'a”.

Awannan daren haka Moddibo Ummi, Asma'u Bashir malam Ahmad da Innayi suka kwana cike da farin cikin shigar wayar M Jameel.

Yayin da Aɓangaren Abba ya kwana cikin taraddadi da tashin hankali koda ya farka tsakiyar dare kuka yayi ta yi yayin da Hajiya Karima ke kuka tana basa haƙuri kana tana cewa bada niyya tayi ba.

Aɓangaren gidan Lamiɗo ma haka Khausar da Mommy suka kwana azaune da Ramadan da kansa ke masifar ciwo da zaran an bashi maganin da Lamiɗo ya kawo yasha ciwon zai ɗan lafa jimawa kaɗan kuma zai sake tashi tsakiyar dare ya farka ya riƙa kuka dole Ummi ta kira Abba ya kawo masa magani cikin ikon Allah yana sha ciwon kan ya lafa.

Washe gari; Moddibo, Malam Arɗo, Ummi Innayi duk wani makusancin M Jameel na cikin farin ciki kana duk wanda ya kira wayarsa zai shiga sai dai ba aɗagawa Wunin wannan ranan haka Moddibo yayi yana kiran layin M Jameel still ba amsa.
Zuwa yamma jikin Moddibo ya fara sanyi da lamarin ganin yana kiran wayar M Jameel baya shiga lokaci ɗaya tsoro ya fara kamashi hankalinsa ya tashi Misalin ƙarfe goma na dare yana gidan Abba zaune sun kira Jameel kuma sama da sau ashirin kuma duk kiran yana shiga, sau dai ba'a ɗagawa, su kuma masatan basu kiraba.
Yayin da idanun Abba ke kumbure alamar har yanzu jinjinsa bai sauƙa sosai ba.
Cikin mutuwar jiki Moddibo ya koma gida kai tsaye sashen Innayi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga.
Innayi dake zaune riƙe da carbi ta amsa masa cikin raunin Murya yace.
“Innayi”.
Kallonsa tayi cike da kulawa kana tace.
“Na'am”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana cikin sanyin murya yace.
“ Innayi hankalina ya soma tashi wayar J yana shiga ba'a ɗauka sannan mutanen nan basu sake kira ba”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.
“Ba komai Moddibo Insha Allah ka kwantar da hankalin ka”.
Girgiza kai yayi kana yace.
“Anya kuwa Innayi?”.
Cikin bashi ƙwarin gwiwa tace.
“Ba komai Insha Allah ka cigaba dayi masa addu'a da izinin Ubangiji zai fito yanzu idan sun sake kira kuce musu an samu kuɗin Insha Allah Million biyar bazai gagara ba koda a masallatai anemi temako za'a samu su haɗu”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh Innayi Allah yasa su kira ɗin dan yanzu kam ma cikon Million ukune”.
Cikin jin daɗi Innayi tace.
“Alhamdulillah Allah ya bamu sa'a”.
Amin yace
Sanna ya miƙe ya koma sashen sa cike da damuwa. Washe gari jin sauran kuɗin da ake buƙata, Lamido ya bawa Mommy da kanta ta kaiwa Ummi su sau dai sam basu kuma kiraba.

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya yau kusan kwana ki shida kenan duk lokacin da aka kira wayar M Jameel zai shiga sai dai ba'a ɗauka.

Yayinda Ramadan kuwa ke kwana da azabebben ciwon kai idan aka bashi magani yasha ciwo ya lafa anjina kaɗan kuma ya sake dawowa.
Ga ɗaya Mommy da kwausar sun shiga damuwa, sun kai asibiti har cikin Taraba anyi hoton kan da duk wani gwaje-gwaje amman babu wani ciwo dake kansa, dan da farima likitocin sunyi zaton brain cancer ne.
baki ɗaya yaron ya fita hayyacinsa saboda tsananin ciwon kai.
Yau kimanin kwana shida kenan da aka fara samun wayar M Jameel na shiga.
Washe garin rana ta bakwai.
Da safe bayan an idar da Sallar Asbah Moddibo na fita a masallaci ya kira wayar M Jameel.
Cike da mmki tsoro ya janye wayar a kunnenshi sabida jin ance masa Switch off.
cikin mutuwar jiki ya nufi gidan Ummi yana shiga ya samu Ummi zaune akan Sallaya hannunta riƙe da Carbi.
Cike da ladabi ya gaisheta kana cikin sanyin murya yace.
“Ummi”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Na'am Babana”.
Cikin raunin murya yace.
“Ummi na kira wayar J ɗina baya shiga”.
Ahankali Ummi ta jingina kanta da jikin kujeran falon kana tace.
“Nima na kira wayan Jameelu na baya shiga bansan Meyesa ba Allah yasa al'khairi ne”.
Cike da sanyi Middibo yace.
“Amin ya Allah in sha Allah ba komai Ummi”.
Cikin raunin murya Ummi ta lumshe Idanunta tare da cewa.
“Hmmm,Hmmm Ubangiji Allah yabamu ikon cinye jarrabawar da zai jarabce mu”.
Cikin sanyi Moddibo yace.
“Ameen”.
Miƙewa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi bari naje gidan Abba naji koshi ya kira ya shiga”.
Kai Ummi ta gyaɗa Muryanta cike da rauni tace.
“Toh”.
Cikin sanyin jiki zuciya cike da karaya Moddibo ya nufi gidan Abba yana shiga coumpund ya ga Abba na ƙoƙarin shiga falo dawowansa daga masallaci kenan.
Ƙara sawa Moddibo yayi tare da miƙa masa hannu sukayi musabaha kana cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Abba wayar J ɗina baya shiga”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye masu zafi suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar kamar ƙaramin yaro baki ɗaya ya rame cikin raunin murya yace.
“Aliyu dama wayar Jameelu da kira yake shiga. Wani sanyi ne dama hankalina ya tashi tun jiya nake kiran wayar baya shiga, dama ni banyi farin ciki da shigan wayar Jameelu ba. Aliyu inaji Ajikina kamar akwai wani abu da bamu san menene ba jikina na bani ko ina Jameelu na yaje baya cikin walwala na rasa tudun dafawa”.
Cikin sauri Moddibo ya runtse Idanunsa zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi kana cikin raunin murya yace.
“Abba insha Allah J yana cikin ƙoshin lafiya mu cigaba da masa addu'a amma nima baki ɗaya hankalina yayi masifar tashi”.
Cikin rauni da tsanananin tashin hankali suka ci-gaba da tattaunawa.

Acan gidan Lamiɗo kuwa Mommy, Khausar da Lamiɗo basu rintsaba a wannan daren.
A kan Ramadan suka kwana yanata kuka baiyi bacci ba.
Washe gari Bayan an idar da sallan Asbah Hajiya Bunayya ta shigo falon Mommy ahankali Ramadan dake kuka ya miƙa mata hannu kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da wahala yace.
“Ummah! Ummah! Kaina zai fashe kaina zai faɗi Wayyo Allah na Kaina! kaina”.
Baki daya jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu dasu yayinda idanunsa sukayi ja.
Cike da tausayawa Khausar ta ɗaura tafin hannunta na dama akan goshinsa Idanunta cike da ruwan hawaye kasa riƙe hawayen ta tayi jin yanda kan ke harbawa da masifar ƙarfi.
Kuka sosai Ramadan keyi kana cikin tsananin radaɗin ciwo ya riƙo hannun Mommy kana yace.
“Wayyo Mommy Kaina zai fashe. Mommy Kaina Wayyo zan mutu Mommy Zan mutufa”.
Wani irin miƙa Ramadan yayi tare da cewa.
“Momyyyyy zan mutuuuu”.
Cikin sauri Lamiɗo da yanzu ya shigo ya karɓesa ganin yanda idanun yaron suka juya da sauri ya fara ɗan bubbuga kumatunsa yana cewa.
“Ramadan! Ramadan!”.
Wani irin juyawa Idanun yaron yayi tare da wulƙitawa kana yaja dogon numfashi....!



*Zuwa yanzu dai mun gama ratsa tsakiyar labari babi-babi na zaren na dab da fara warware wa.*


By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA CIKIN GROUPS NA DANA BUƊE NA SAKAYYAH BAto na satane, 1k ne kacal kuɗin littafin SAKAYYAH yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kiyiwa Allah da Manzonsa ku dena fidda min littafina, in dai kin san kin sayane dan ki turawa wasu, dan Allah ki gaya min in mayar miki da kuɗinki🙏🏻🙏🏻Dan Allah nace ba dan niba*

Isrnejny. Moddibo kuwa cike da mamaki da tsoro ya maimaita 200 Millions asaman laɓɓansa, he can't believe or imagine zasu iya tambayar wannan maƙudan kuɗin how cames kidnapper zasu tambayi kuɗin fansa kamar sun sace ɗan shugaban ƙasa.
Rintse idanunsa yayi tare da cije labɓansa na ƙasa lokaci ɗaya jijiyoyin kansa suka tashi sukayi ruɗu-ruɗu dasu.
Dafe kuncin Hajiya Karima tayi da hannunta duka biyu kana ta kyale baki tare da cewa.
“Ohh Allah ya kawo mu wani zamani ka haifi ɗa sannan wasu ƙartin banza da wofi su saka kasa ke sayan sa bafa Millions biyu ba, Ba ashirin ba, Ba hamshin ba, Ba ɗari ba, har Millions ɗari biyu sai kace abin Masifa ko dan sunyi zaton Jameel ɗan Aliko ɗan Gwate ne, shi, ka haifi ɗa kasha wahalar ciyar dashi shayar dashi tufatar dashi biya masa makaranta sannan ace ka sake siyan sa”.
Dafe kai Abba yayi da duka hannunsa biyu baki ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake kar-kar-kar tamkar mazari yayin da idanunsa suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashi.
Dai-dai lokacin Hajiya Turai tashigo baki ɗaya tayi zuru-zuru da ita. Idanunta sun kaɗa sunyi jawur dasu ganin halin da Abba ke ciki yasa tace.
“A'a Alhj Lafiya Subhanallah”.
ta faɗa tare da nufar Bedroom ɗin sa ta da buɗe drawer ta ɗauko naganinsa ganin alamar hawan jinjinsa ne ya tashi tare da manna waya akunnenta bayan kamar second uku tace.
“Hello Dr Muktar dan Allah kazo yanzu ina ganin kamar hawan jinin Alhj ne ya tashi”.
Cikin raunin murya Abba ya ɗago kai ya kalleta tare da cewa.
“A'a ki bari ba sai Dr yazoba, ki bani maganin kawai”.
Kai ta gyaɗa kana cikin sauri ta zuba masa ruwa a glass cup ta miƙa masa tare da bara masa maganin karɓa yayi ya afasu abakinsa ya haɗiye.
Sannu a hankali ya fara maida numfashi sama-sama yana jin bugun zuciyarsa tare da sarawan da kansa keyi ya fara raguwa amma still hannunsa na dafe da kansa.

Ɗago Idanunsa yayi tare da kallon Moddibo daya zuba masa Idanu kana ya kalli gefen damansa Hajiya Turai ce durƙushe Idanunta cike da hawaye lumshe idanunsa yayi kana ya shiga tunani kwata-kwata kuɗin dake cikin account ɗinsa tsuran kuɗi, gaba da baya Million Sha biyu ne wanda yake tunanin da sun cika Ashirin zai bawa M Jameel saboda ya habɓaka Company daya bashi, da ƙarfi ya sake rintse idanunsa tare da dafe kansa tuno wa da yayi acikin Million Sha biyu ma akwai cikon kudin hajji nashi da na matansa da zai cika ta, baki ɗaya tunaninsa ya tushe ina yasan zai fara kai kadaransa asiya masa su cikin gaggawa kuma da daraja sannan abashi kuɗin cikin tsanananin tashin hankali yace.
_“Ya Ilahi ya lillahi ya mujibud da'awati ya hayyu ya ƙayyum bi rahma tika astaghisu lahaula wala ƙuwwata illa billahil aliyul azim”_.
Abin da yake maimaitawa kenan asaman laɓɓansa.
A hankali Moddibo ya matsa kusa dashi cike da tausayawa yace.
“Colm down Abba ka nutsu ka kwantar da hankalin ka everything will be fine by the grace of Allah”.
Cikin sauri Abba ya riƙo tsintsiyar hannun Moddibo tare da cewa.
“Aliyu Why should I find 2 hundred Millions?”.
Aliyu mai zan fitar in sayar dashi cikin gaggawa in Samu kuɗi?.
Aliyu bani da ko Million ashirin acikin account ɗina,kaji kuɗin da suka kira fa”.
Kallonsa kawai Moddibo keyi cike da tausayinsa Cikin raunin murya Abba ya cigaba da cewa.
“Aliyu kwanan nan na cire kuɗi na siya filin nan kuma shima gaba ɗaya filin dana siyeshi 25 Million ne da ace suna nan kaga kuɗin akwai ɗan gwaɓi ahannu na”.
Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da sake damƙe hannun Moddibo acikin nasa kana yace.
“Ina da kadaran da zan iya sayarwa amma ta yaya awani lokaci zan samu ace ansiya se anbani kuɗina sannan na wane”.
Kasa ƙara sa maganar yayi kawai saiya janye hannunsa dake cikin na Moddibo ya rufe fuskarsa yana mai furta.
_“Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal zhalimin”_.

Hajiya Karima dake dafe da kuncinta ta ɗago kai tare da kallon Abba kana tace.
“Alhj ai dole dama za ayi ciniki dasu idan yaso sai anemi ragi”.
Moddibo kuwa kai ya girgiza tare da kallon ta kana yace.
“Idan da ace sunzo mana da sauƙi da kuma Imani acikin zancen zamu iya hakan amma fa kiga yanda idan sunyi magana sai su yanke mana kiran baza su tsaya suji ta bakin muba sai sun kwana ɗaya ko biyu kafin su sake kiran mu”.
Da ƙarfi ya runtse Idanunsa tare da cije labɓansa na ƙasa kana ya cigaba da cewa.
“Basa tunanin shin wani irin yanayi ko hali zamu kasance aciki ba yaya zamuyi, da wannan kuɗin da suka kira”.
Ya ida maganar cikin raunin murya.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Nima abinda nake tunani kenan idan nace musu babu zasu iya yiwa Jameel Illah”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Abba kar ma kace musu babu sai muyi ƙoƙari duk yanda zamuyi mu haɗa kuɗin nan muyi ƙoƙari mu basu”.
Ahankali Abba ya furta.
“Ya Salam”.
Hajiya Turai kuwa cikin matsanancin kuka ta kalli Moddibo kana ta maida kallonta kan Abba tare da cewa.
“Ai abayar ɗin yafi Alhj duk wani abinda kake dashi ka sashi akasuwa kawai asamu asayar akarɓo Jameel meye fi maka Jameel aduniyar nan Alhj, kawai asayar da komai akai musu kuɗin akarɓo shi”.
Cikin sauri Hajiya Karima ta kalli Hajiya Turai kana tace.
“Kamar ya asaida komai Hajiya Turai kifayi tunani akan abinda kike faɗa idan aka sayar da komai muku mu murayu aya kenan?”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Abba kana ta cigaba da cewa.
“Alhj ya za ayi ɗauki irin wannan maƙudan kuɗin amulmula abasu kaga idan wa'annan ƴan Kidnapping din da suka kinnafe Jameelu sunji dadi an basu abinda suke so to wasu kuma ai sauran ƴaƴan zasu zo su kwashe”.
Ta ida mgnar tare da sauke numfashi kana ta cigaba da cewa.
“Suma sauran ƴaƴan sai aje a kinnafesu su kuma idan kuɗin da za'a fanshe su bai rage ba ya za ayi kenan.
A gaskiya wannan ba shawara bace ace za aɗauki wannan maƙudan kuɗin abasu sai kace ba asha wahala wajen ne mansu ba”.
Ahankali Moddibo ya ɗago kumburarrun Idanun sa ya kalli Hajiya Turai dake dafe da ƙafaɗan Abba tana sharɓan kuka kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima data zabga tagumi.
Girgiza kansa yayi.
Sosai hankalin Abba yayi masifar tashi yama rasa wani irin tunani zaiyi Aransa ya gaza tantance abin cewa.
Sannu a hankali idanunsa suka fara lumshewa jikinsa ya saki baya yaja tare da gyara kwanciyarsa akan 3sitter tare da lumshe idanunsa Atake Bacci ya ɗauke sa sabida magungunansa da Hajia Turai ta bashi yasha sun jiƙa sunbi jininsa.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da miƙewa kana yai musu sai da safe tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Ummi ya nufa.
Awaje yayi Parking motarsa kana ya fita iska na kaɗa ko wani sashe na jikinsa ahankali ya murɗa handle din ƙofar ya tura bakinsa ɗauke da sallama ya shiga.

Idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan Sallaya hannunta riƙe da Carbi yayin da Malam Ahmad ke zaune gefenta yana rarrashin ta.
Ganinsa yasa Ummi ta ajiye carbin dake hannunta kana ta maida hankalinta kansa,Anutse Moddibo ya ƙara sa tare da miƙawa malam Ahmad hannu sukayi musabaha kana ya koma ya zana agaban Ummi.
Jin Sallamar sa yasa Asma'u da Bashir suka fito daga Bedroom tare da zama gefe da gefen Ummi ya zamana sun sashi a tsakiya kana cikin raunin murya suka gaishesa atare zuwa lokacin shima Bashir kuka yake sosai duk yayi zuru-zuru.

Ahankali Ummi ta zubawa Moddibo Idanu kana cikin sanyin murya tace.
“Babana ya akayi sun sake kira?”.
Kai ya gyaɗa tare da sun kuyar da kansa ƙasa kana yace.
“Eh”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“Me suke buƙata?”.
Still Kansa na ƙasa yace.
“Ummi kuɗi suke so”.
Numfashi ta fesar kana tace.
“Kuɗi suke so?”.
Kai ya gyaɗa amma bai ce komai ba.
Cikin tsira masa ido tace.
“Kuɗi kamar nawa suke so?”.
Cikin rauni ya kalleta kana ya kalli malam Ahmad, Asma'u da Bashir ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ummi kuɗin suna da yawa kuɗin da suke buƙata sun wuce zatonmu”.
Gyara zama tayi kana tace.
“Toh Meye amfanin kuɗin mahaifinsa?, Meye amfanin kuɗin Babansa?,Menene amfanin duk tattalin da yake yi!?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“Ummi kuɗin sun wuce tunanin mai tunani!?”.
Ɗa gowa Ummi tayi tare da tsira masa ido kana tace.
“Kamar nawa suke buƙata Babana?”.

Cikin raunin murya da alamar sarewa Moddibo yace.
“Ummi har Million ɗari biyu suke buƙata”.
Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni, tsoro, mmki Ummi taja ajiyar zuciya kana ta maida kanta ta jingina da jikin kujeran da Malam Ahmad ke zaune tare da lumshe Idanunta kana Muryanta na rawa tace.
“Ƙarya sukeyi ba kuɗin suke so ba so suke su kashe min Jameelu lallai Mahaifinsa mai arziƙi ne amma be kai matakin da za'a matsesa lokaci ɗaya ace ya fito da Million ɗari biyuba, kawai dai yaudarace suke mana anya ma Jameelu yana raye kuwa?”.
Cikin sauri Moddibo ya girgiza mata kai kana yace.
“Yana raye Ummi ina ji ajikina J yana raye kuma na faɗa miki munyi magana dashi”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Yau da suka kira kunyi magana dashi?”.
Shiru yayi yana kallonta amma baice komai ba.

Kallonsa Ummi tayi cikin muryan kuka tace.
“Babana ka faɗa min gaskiya tsakanin ka da Allah yau kunyi magana dashi?”.
Girgiza mata kai Moddibo yayi tare da faɗin.
“Ummi ba muyi magana dashi ba, amma naji muryan J ƙasa-ƙasa yana cewa Abba abasu duk abinda suke so”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da rintse idanunsa kana tace.
“Babana ka tabbatar gaskiya kake faɗa min?”
Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin sanyin murya yace.
“Wallahi Wa rabbul Khaba Ummi naji muryan J ƙasa. yana magana bawai sun bashi bane amma naji yana magana”.
Kuka Asma'u da Bashir suka fashe da shi atare kana lokaci ɗaya suka haɗa baki wajen cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ya Allah ka kuɓutar da Yah Jameel Ubangiji kada ka basu ikon cutar dashi ya Allah kaine gatanmu Yah Jameel shine ka wakilta da isar mana gatanmu ya Allah ka karesa da karewaka”.

Numfashi Malam Ahmad ya fesar kana cike da tausayawa yace.
“Asma'u ba kuka ya kamata kuyi ba addu'ar mu Jameelu ke buƙata idan kuna kuka ya kuke so Ummin ku tayi?”.
Cikin sheshsheƙan Kuka Asma'u tace.
“Abba Yah Jameel fa Yah Jameel yana cikin mawuyacin hali Abba kaji fa maƙudan kuɗin da suke buƙata Abba ya za'ayi mu samu irin wannan kuɗin mu karɓo Yah Jameel Abba Ina tsoron kada su cutar mana dashi”.

Girgiza kai Malam Ahmad yayi cikin sanyin murya yace.
“Insha Allah da izinin Ubangiji babu abinda zai samu Jameelu, ko wani bawa da kalar tashi ƙaddaran tun kafin a haifi Jameelu Ubangiji ya zana masa ƙaddaransa muyi masa addu'ar Allah ya sauƙaƙa mana zafin ƙaddararsa”.
Jinjina kai Moddibo yayi yana jin wani irin azabebben zafi aƙirjinsa.
Kallon Moddibo Malam Ahmad yayi kana yace.
“Moddibo mai Yakamata ayi acikin wannan al'amarin!?”.
Moddibo da kansa ke ƙasa ya ɗago ya kallon Malam Ahmad a hankali yace.
“Malam abinda yakamata kawai afara cuku-cukun neman kuɗin nan sai muga abinda zai kasance”.

Girgiza kai Ummi tayi still tana jingine da jikin kujera tace.
“Babana ina zamu samu kuɗin nan Million ɗari biyu fa da ace Million biyu suka ce koni kaina ma zan bada su”.
Ta faɗa tare da ɗaukar wayarta tayi checking balance kana tace.
“Gashi yanzu anan ina da Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da hamsin da ɗaya sannan kuma ba matsala gobe in Allah ya kaimu zan tafi cikin.
Taraba zan kai gwala-gwalaina”.
Sai kuma ta ɗan tsaya, jin numfashin ta na yankewa, da ƙarfi ta fizgo numfashin tare da cije labɓanta na ƙasa hawaye cike da Idanunta murya na cike da rauni ta cigaba da cewa.
“Zan saida su inga nawa zan samu ajikinsu zan haɗa harda na Asma'u sannan, motata itama zan saidawa muga nawa zan samu awurina”.
Jingina kai Malam Ahmad yayi kana cikin sanyin Murya yace.
“Har gidan nan ma asashi a. Kasuwa asayar dashi”.
Kallonsa Moddibo yayi tare da girgiza kai kana yace.
“A Malam ayi haka”.

Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.
“Asiyar Moddibo menene Jameelu baiyi mana ba aduniyar na, kasancewar sa atare damu shiyafi mana komai”.
Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da tsira masa ido hawaye na bin kuncinta ta sani fili dai filinsa ne halalinsa mallakinsa, amma baki ɗaya ginin dake ciki Jameel ne ya musu bayan yasa an buge tsohon ginin taɓon.
Girgiza kai tayi cikin rauni tace.
“A'a ba sai anyi haka ba bari muga abinda Mahaifinsa zai samu”.
Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da kallon Asma'u da Bashir da har zuwa lokacin suke kuka a hankali ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ni dai na sadaukar da wannan gida ga.
Jameelu wallahi na yafe masa shi duniya da lahira na amince asa shi akasuwa muddin za a samu masu siya, to asa shi akasuwa mu samu muga aƙalla dai awajen mu ace an samu Million goma kuɗin zaifi gwaɓi”.
Sun kuyar da kai ƙasa Ummi tayi hawaye masu masifar zafi suka zubo mata.
Hannunta Moddibo ya riƙe cikin sanyin murya yace.
“Ummi dan Allah ki daina wannan kukan idan kina kuka muku ma ya zamuyi Ummi babu abinda J ke buƙata awajen mu face addu'a ganin ki awannan yanayin naya sake raunatamana zuciya”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.
“Sosai ma wannan kukan da kike Fatima saidai ya haddasa miki wani ciwon amma babu amfanin da zaiyi dan Allah ki daina ki cigaba da yi masa addu'a. shi kansa ba zaiso ace kina masa kuka ba”.
Kai ta gyaɗa tare da share hawayen ta kamar yarinya kana tace.
“Na daina Insha Allah zan cigaba da yimasa addu'a Ako da yaushe”.

Saida Moddibo ya tabbata ta daina kukan kafin ya mata sallama ya fice cike da tausayinsu Driving yake ahankali har ya isa gida yayi Parking kana ya fito ya rufe gate din tare da wucewa sashen Innayi bakinsa ɗauke da sallama.
Kwance ya samu Innayi cikin Yanayin damuwa gefenta da Radio tana sauraro wanda ɓatan M Jameel ake sanarwa.
Miƙewa tayi ta zauna tare da amsa Sallamar sa kana tace.
“Moddibo ya labarin Jameelu?”.
Cikin sanyin murya yace.
“Innayi sun sake kira ɗazu”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“Toh kunyi magana dashi yana cikin ƙoshin lafiya?”.
Girgiza mata kai yayi kana yace.
“A'a Innayi bamuyi waya dashi ba amma bisa duk kan Alamu J baya jin daɗin zaman wajen can”.
Ahankali Innayi ta jingina bayanta da jikin bango kana ta matsar da Radio gefe tare da cewa.
“Dama Moddibo ya za ayi yaji daɗin zaman wannan wajen. kasan yanayin da yake ciki ai dole bazai ji daɗin zaman wannan wajen ba amma me suke buƙata?”.

“Innayi kuɗi suka nema”.

“Kuɗi suka nema to aisai abasu aje a karɓe shi”.

“Innayi kuɗin da suka nema na fitar hayyacine!”.

“Kuɗi har nawa suka nema? Da zai zama na fitar hankali”.
Dafe goshinsa yayi kana yace.
“Innayi Million ɗari biyu suka nema kuma cikin ƙanƙanin lokacin fa”.
Ita kam Innayi baki ɗaya lissafin ta sincewa yayi jin maƙudan kuɗin tama rasa nawane, kallon Moddibo tayi tare da cewa.
“Dubu ɗari biyu?”.
Kai Moddibo ya Girgiza tare da cewa.
“A'a ba dubu ɗari biyu bafa Million fa Million ɗari biyu”.
Daga kanta sama tayi alamar tunani sai kuma ta kallesa tare da cewa.
“Million biyu?”.
Still girgiza mata kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Million ɗin goma, ashirin, hamsin, ɗari, ɗari da hamshin har ɗari biyu”.
Dafe kirji tayi kana tace.
“Million

1 Comments On SAKAYYAH
avatar
fatima-8-5-3

1 month ago

Reply

Allah ya qara basira

Please Login or Register in order to submit comment