Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jan baƙi M Jameel na tafsiri ƙarfe shida dai-dai suka tashi.

Anutse suka fito daga cikin masallacin suka shiga mota akuma dai-dai lokacin wayar M Jameel ya hau ruri cike da nutsuwa ya gyara zamansa tare da ciro wayar daga aljihun sa Sunan Abban sa ke yawo a screen ɗin kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe yayi yace.
“Kaga Abba ke kira”.
Ya ƙara sa maganar tare da Amsa kiran yakai kunnensa tare da cewa.
“Assalamu Alaikum”.
Daga ɓangare Abba yace.
“Wa'alaikum Salam Babana”.
M Jameel Yayi murmushi tare da cewa.
“Na'am Abba na”.
Gyaran murya Abba yayi kana yace.
“Nikam laifin me mukayu mukune da kai da Moddibo da baza kuzo mu samu ladan baku buɗa baki agidan nan ba”.
Murmushi M Jameel Yayi yace.
“Ayyah Abba na laifin me zaku mana mukam a duniyar nan gama A.J ɗin yana jinka”.
Ɗan Matsawa kusa da M Jameel ɗin Moddibo yayi kana yace.
“Abbah mai zaku mana A duniya ko kun yi mana abu baza muyi fushi da kuba waye zaiyi fushi da iyayensa?”.

Murmushi Abba yayi yace.
“Toh tun da akayi azumi baku zo kunsha ruwa a gidan nan bafa, abin yana damuna yau fa kwana goma sha uku kenan da baku zo kunsha ruwa agidan nan ba fa”.

Dariya M Jameel Yayi yace.
“Abba ka dai manta mun zo ranan da akayi azumi biyar agidan muka sha ruwa fa”.
Gyara zaman wayar Abba yayi akunnensa kana yace.
“To ai bana nan ba asha ruwan dani ba yau dai so nake kuzo musha ruwa tare”.

Gyara zama Moddibo yayi yace.
“Abba baza mu bari sai gobe ba?”.
“A'a yau nakeson ganinku kuzo musha ruwa anan”.
Cewar Abba.
Jingina kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Toh shikenan Abba zamu zo insha Allah amma bari mu fara zuwa gida”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.
“A'a karfa ku makara kuzo komai ya kammala ku kawai ake jira ga kun lokacin ya ƙarato”.
Atare suka haɗa baki wajen cewa.
“Toh shikenan Abba ga munan zuwa”.
Kallon Moddibo M Jameel dake Driving Yayi kana yace.
“Muje?”.
Moddibo kuwa Idanunsa dake lunshe ya buɗe yace.
“Eh muje mana J”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana ya juya akalar motar zuwa Unguwar su Abba ba abinda ke tashi acikin motar face ƙira'ar Alkur'ani acikin Suratu Yusuf tare da Sanyayyar ƙamshin tularensu, Wayar Moddibo dake gaban aljihu ne ya hau ruri Anutse yasanya lallausan tafin hannunsa mai zagaye da gashi ya ciro wayar tare da kallon sunan mai Kiran Malam Arɗo amsa kiran yayi tare da kai wa kunnensa.
Daga ɗaya ɓangaren Malam Arɗo yayi gyaran murya kana yace.
“Wai kai baza kazo kasha ruwa agidana ba ko sau ɗaya ne Moddibo?”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi tare da shafa kwantaccen Sajensa kana yace.
“To Malam ka gayyace mune ai baka gayyace mu shan ruwa ba”.
Da sauri Malam Arɗo yace.
“To na gayyace ku xo yanzu”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Toh ba yau ba dai sai gobe”.
Da sauri Malam Arɗo ya zare Ido tare da cewa.
“To duk abubuwan da nasa aka dafa muku kuma fa?”.
Murmushin gefen baki Moddibo ya kuma yana imagine fuskarta malam Arɗo kana yace.
“Ka bawa mutanen gida suci ba rabon mu bane
gobe kuma Idan Allah ya kaimu kama na namu kuma ayi da mutanen gida duka”.
Cikin sauri Malam Arɗo yace.
“Wato dai kai ko yaushe sai ka kawo min sabon tsari acikin al'amari na ko”.
Murmushi M Jameel yayi shaƙuwar dake tsakanin Moddibo da malam Arɗo ya wuce zaton mutane.
Moddibo kuwa ɗan Murmushin dake ƙarawa fuskarsa kyau yayi kana yace.
“Ai dole dai kam”.
Dariya Malam Arɗo yayi yace.
“Dama gobe ka tabbatar lokacin shan ruwa yana yi na ganka, ba sai na kira ba ka gaishe da Jamilu kar ku cinye min kati na”.
Ya ida maganar tare da katse kiran.
Murmushi M Jameel Yayi kana yace.
“Malam Arɗo ko?”.
Murmushi kawai Moddibo yayi yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake.

Cikin mintunan da baza su gaza biyar ba suka isa ƙofar katafaren gidan Hong M Jameel Yayi mai gadi ya buɗe musu Anutse M Jameel ya cinna hancin motarsa gidan tare da yin parking a inda aka tana da danyi Parking ɗin motoci.
Cike da nutsuwa suka nufi sashen Abban M Jameel, bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga tamfatsetsen Falon nasa daya gaji da tsawuwa yana fitar da sanyayyan ƙamshi.
Tsaye suka hangosa yana gyara ɗaurin agogon hannunsa fuskarsa da damshi da alama Al,wala yayi.

Kallonsu yayi tare da sakar musu da murmushi kana yace.
“Ku shiga kuyi al,wala kunga muna shan ruwa sai mutafi masallaci”.
Kai suka gyaɗa sannan M Jameel ya nufi toilet dake Falon kana ya kalli Moddibo da faɗin.
“A.J kashi ga toilet ɗin ciki kayi al,wala”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a kashiga na ciki ni zan shiga wannan”.
Kallon Moddibo Abba yayi kana yace.
“Wato shi yashiga ɗaki na kai ba zaka shiga ba ko? To ai kaima ɗana ne kashiga babu komai Moddibo”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan Abba”.
Sannan ya wuce Bedroom ɗin Abba ahankali ya saki murmushi ganin komai na Bedroom din tsaf-tsaf akimtse Aransa yace ashe de J gadon tsafta yayi awajen Abba shima komai nashi tsaf-tsaf ajiyar zuciya ya sauƙe tare da shiga toilet ɗin nan ma komai atsaftace Al'wala ya ɗaura kana ya fito atsaye ya samu M Jameel da Abba Kallonsu Abba yayi kana yace.
“Ku ƙaraso mu isa dining”.
Kai suka gyaɗa tare da nufar dindin ɗin da aka ƙawata da kayan ciye-ciye na alfarma wani irin kwando ne na kayan marmari ne kama daga, Inabi, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo, Ruman, Tuffa, Mangoro.
Sai kuma wasu Warmers masu kyau dake ɗauke da pride rice da yaji kayan lambu,sai daga ɗaya gefen kuma wasu jug ne masu kyau ɗaya kindirmo ne mai sanyi adame ɗayan kuma kunun shinkafa ne sai Flaks dake ɗauke da ruwan tea da kuma kofina daga gefensa kuma gongomin madara ne dana Bounvita sai kulan ƙosai sosai dining din ya ƙawatu.
Anutse suka zauna akan kujeran Abba ya zauna daga ɓarin kudu Moddibo ya zauna daga ɓarin yamma yana fuskantar gabar M Jameel kuwa daga ɓarin gabas ya zauna yana fuskantar yamma.
Anutse Moddibo ya ɗauki dabino guda bakwai ahannunsu idan yaci sai ya sanya ƙwallon ahannunsu na hagu bayan yaci sai ya ɗauki inabi yaci M Jameel kuwa dabino uku yaci tare da apple haka ma Abba.
Sai.kuma suka sha kankana da inabi kana suka ɗan ɗaura da ayaba.
Kallon su Abba yayi cike da so da ƙaunarsu kana yace.
“Toh kuci abinci”.
Girgiza masa kai sukayi kana atare suka ce.
“A'a Abba sai mun dawo daga masallaci”.
Kai ya gyaɗa musu kana suka miƙe atare suka tafi masallaci suka idar da sallah bayan sun dawo M Jameek ya ɗebi Pride rice Kaɗan da tsokokin kaza. Modibbo kuwa kindirmon da aka dama ya ɗiba a Cup Abba kuwa chicken peper da pride rice shima ya ɗebi yana ci.
Fara cinsu babu daɗewa aka turo ƙofar aka shigo Idanun Hajiya Karima bai sauƙa ko ina ba sai kan Moddibo dake riƙe da kofin kindirmon kana da plate ɗin da Abba ya sa mishi pepper chicken and vegetables da fork a samansu.

Cike da tsanarsa ta watsa masa wani wulaƙantaccen kallo kana tace.
“Toh acire tsatsan haƙori anan, kaska raɓi mai jini wato ko zuwa shi kaɗai ya samu ya keɓe da mahaifinsa ba za'a bari ya samu damar hakan ba ko?
Oh ni Kareeme tunda nake a duniya ni dai ban taɓa ganin mutum mai shegen nacin tsiya irin kaba, sam baka da godiyar Allah ba zaka tsaya amatsayin ka ba shin kai wani irin Jarabebben mutum ne Aliyu?!”.
Cikin wani irin fushi da ɓacin rai Abba ya mike ahasale ya dubeta kana yace.
“Hajiya Karima mai kikeyi haka ne?
Wai meyasa ne ke baki da hankali ne? kinsan abinda kike faɗa kuwa!”.

Fuska ta ɓata kana tace.
“Toh Alhaji gaskiyane ya barka kaida ɗan ka kuhuta mana kuyi shawara acikin sirri”.
Afusace Abba ya katseta tare da faɗin.
“Me kike nufi shiɗin ba Uwa da Ubane suka haifeshi ba shima ɗana ne”.
Sheƙeƙe Hajiya Karima ke Kallonsa kafin cike da Isgilanci ta kallesa kana tace.
“Yaushe ka haifesa bamu da labari?,yaushe ka auri uwarsa har ka haifesa bamu sani ba?”.
Cikin tsananin fushi Abba yace.
“Kifita anan ki fita Karima bana son ganinki tun da ke kince baki da ɗa'a baki iya Mu'amala da mutane arayuwarki ta duniya ba, bana son haka, Bana son haka kar ki sake yin haka na yi miki kashedi na ƙarshe wannan shine last warning Hajiya Karima!, Kada ki sake yimin haka.
Domin kuwa koda Mahaukaci Jameel ya ɗauko ya kawo wannan gidan wallahi yafi min ke daraja, saboda nasan koda mahaukacine Jameel zai nuna masa cewa ni mahaifinsa ne kuma na tabbata zai mutunta ni”.
Cikin fushi ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da Iska kana ya cigaba da cewa.
“Na tabbata ko Mahaukaci Jameel ya kawo gidan nan zai mutuntani, kuma zai ɗauke ni da daraja fiye da yanda ke ki ɗaukeni ban isa da keba, misali ga yadda idan na baki umarni kike fatali dashi, ba zakiyi amfani dashi ba.
Dan haka ko kin san Jameel ya fimin komai.
Jameel da kike gani shine Komai nawa a Duniya akan farin cikin Jameel ina iya yin komai dan haka tun wurima ki kiyayeni!
Kifita idona in rufe Hajiya Karima!!.
Ki kiyayeni kada inci miki mutunci!!!”.
Ya ida mgnar tare da buga jikin kujerar dining ɗin kana yaci gaba da cewa.
“Na tabbata kare idan Jameel zai kawo gidan nan sai yamin biyayya fiye da yanda ke kike min biyayya. Kare dai nasan idan Jameel zai kawo min gidan nan bazai tsaya yamin irin haushin da kike min ba!”.
Sai kuma ya watsa mata Kallon mai cike da fushi kana yace.
“Kare idan Jameel zai kawo gidan nan kare mai ɗa'a da biyayya zai kawo min ba karen da zai kunya ta min baƙi na ba amma ke kullum baki da hankali. idan Jameel ɗan kine da kika haifa acikin ki zaki yi masa haka ne?”.
Kasa cewa komai Hajiya Karima tayi sai huci da take tamkar zakanya.

M Jameel kuwa ƙasa yayi da kansa cike da jin daɗi karo na farko kenan da mahaifinsa ya burgesa a kanta daya buɗewa Hajiya Karima wuta akan abinda ta keyiwa Moddibo domin kullum idan ta wulaƙanta Moddibo sai sunbar gidan kafin yake mata faɗa akan ta daina, amma yau yaji daɗin faɗan da Abba yayi mata agaban Idon Moddibo saboda Moddibo zaiji daɗi sannan zai san cewa yana da daraja da kuma kima awajensu.
Moddibo kuwa kansa ya sunkuyar ƙasa da cike kunya sam baiji daɗin ɓatawan mata da Miji adalilinsa ba, yayi dana sanin zuwa gidan, yasan cewa duk lokacin da yazo gidan sai yayi sanadin da za'a samu hatsaniya, sannan ya riga daya sani tun yana yaro matar nan bata sonshi bata ƙaunar ganinsa da Jameel sai dai ya fahimci ba wai shi ta tsana ba tana fakewa da guzma ne ta harbi karsana.
Cikin sanyi murya ya ɗago kansa tare da furzar da iska mai zafi kana yace.
“Abba kayi haƙuri dan Allah dan darajar Annabi”.
Juyawa Abba yayi ya kallesa kana ya ɗaga masa hannu da faɗin.
“Yi shiru ba maganar ka Aliyu barni da ita haka take yimin, ba kai kaɗai ba, duk baƙon da Jameel zai kawo gidan nan sai taci masa zarafi, duk mutumin da zata gansa da Jameel saita nuna min ba mutumin kirki bane!”.
Sai kuma ya juyo Afusace tare da kallonta har zuwa lokacin tana tsaye cike da ɓacin rai ya tsira mata idanu kana yace.
“Mai Jameel ya tsare miki?, Jameel tun tasowar yana ƙarami biyayya yake miki bai taba Musa Miki ba duk da kinzo kin samu yana da shekara goma sha huɗu na tabbata baki yiwa Jameel wahala ba amma yana karramaki sannan yana mutuntaki kamar yanda yake mutunta mahaifiyarsa”.
Zazzafan iska ya furzar kana still muryarsa cike da ɓacin rai yace.
“Amma ke kullum baki da buri daya wuce kici masa zarafi, Idan kin zauna ki riƙa faɗa mun magana kinyi zaton cewa bana son Jameel ne?.
Shin inada wani ɗa aduniya daya wuce Jameel ne?”.

Cikin tsananin fushi da ɓacin rai Hajiya Karima ta nuna kanta kana tace.
“Ni ka ciwa zarafi akan yaro ɗan maƙota dan yana abokin ɗan ka, sannan dan na faɗa maka gaskiya, kai baka ga yadda yake liƙewa ɗan nakaba duk ya hana sa tattalin arziki sannan ya hanasa ya tara abin kansa”.
Cikin wata fusatacciyar tsawa daya amsa ilahirin falon yace.
“Ki fice min anan Karima bana son ganinki”.
Afusace ta juya kamar zata tashi sama tana wani irin huci tare da jin tsanar Moddibo da M Jameel fiye da komai arayuwarta!.

Anutse Abba ya juya ya kalli Moddibo kana cikin sanyi murya yace.
“Dan Allah Aliyu kayi haƙuri kada ka damu da abinda tayi maka, sannan bance ka ɗauki wannan amatsayin wani mataki da zai hana ka zuwa gidan nan ba, aduk sanda kaga dama zaka zo”.
Murmushi yayi kana yace.
“Babu komai Abba ai ita mahaifiya ce agurin mu dan tayi mana haka ba zai zama wani aibu ba”.
Jinjina kai Abba yayi tare da cewa Ubangiji Allah ya al'barkaci rayuwarku”.
Atare suka amsa da.
“Ameen”.
Juyawa M Jameel yayi tare da kallon Moddibo Cikin sanyin murya mai cike da so da shaƙuwa ya numfasa kana yace.
“Dan Allah A.J kayi haƙuri”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Laa babu Komai J. Yanzu dai tashi muje mu bata haƙuri”.

Da sauri Abba ya kalli Moddibo kana yace.
“Baza ku bata haƙuri ba ku zauna kuci abinci”.
Kai suka gyaɗa sannan suka zauna baki ɗayansu, basu wani ci abincin kirki ba, domin ko kowa da irin damuwar dake ransa, bayan sun kammala suka miƙe tare da yiwa Abba Sallama haƙuri Abba ya sake bawa Moddibo.
Murmushi Moddibo yayi kansa aƙasa yace.
“Ayyah Abba Allah babu komai”.
Sannan suka juya har sun kai ƙofa Abba ya ɗan ɗaga sautin muryansa tare da cewa.
“Yau kam ba zamu kwana anan bane?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Abba idan mun kwana anan Innayi ita kaɗai zamu bari acan”.
Jinjina kai Abba yayi kana yace.
“Eh kam ya kamata gida babu namiji ba gida bane kuje”.
Godiya suka masa kana suka fice.
Suna cikin mota aka kira Isha'i kai tsaye masallacin da suke limancin suka nufa kamar ko yaushe Moddibo ne yaja Sallar bayan sun idar sukayi Asham kana suka wuce gida.

Suna shiga gida kai tsaye sashen Innayi suka nufa zaune suka sameta riƙe da carbi ahannun Asma'u kuma tana riƙe da Alkur'ani mai girma tana karatu.
Batare da sun ƙarasa shiga ba Moddibo yace.
“Innayi Barka da shan ruwa”.
Anutse ta kallesa kana tace.
“Yawwa yau ina kuka tsaya ne baku dawo da wuri ba, nace Asma'u ta kira min ku inji kuma ashe wayar ba kati”.
Murmushi M Jameel Yayi kana yace.
“Ayya Innayi Abba ne ya kiramu wai muje mu sha ruwa acan shiyasa kika jimu shiru”.
Kai ta jinjina tare da kallon Moddibo tace.
“Fatan duk suna lafiya?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa mata kana ya sake labulen tare da faɗin.
“Innayi akawo mana abinci”.
Ya ida mgnar tare da zama akan shimfiɗar dake barandar Asma'u Innayi ta ƙalla kana tace.
“Ɗauki abincin ki kai musu”.
Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta ɗauki lemun tsani ta yanka ta matsa kaɗan akai kana tayi slinzing ɗin ƙwoyi kana ta zuba musu wadataccen man gyaɗa da kuma dakekken yajin barkono sai Cucumber da Cabbage ta Kai musu.
Sosai suka Moddibo da M Jameel suka ci ɗan waken tare da 5alive, bayan sun kammala kai tsaye ɗakinsu suka wuce tare da watsa ruwa, kana suka sake shiryawa tare da feshe jikinsu da turaraku masu daɗin ƙamshi.
Cikin nutsuwa suka fito aharabar gidan suka samu Innayi da Asma'u sun fito buɗe bayan motor sukayi suka shiga sannan Moddibo ya shiga mazaunin Driver yayin da M Jameel yashiga gefen mai zaman banza, kai tsaye masallacin suka nufa har suka isa ƙira'a na tashi amotar suna parking Innayi da Asma'u suka shiga sashen mata suka ma suka ƙara sa sashen su.

Yau ma kamar kullum gaba ɗaya cikin masallacin da harabar sa cike yake da ɗumbin jama'a cikin tsantsar nutsuwar daya zame musu jiki suka nufi wajen zamansu cikin sanyi mai cike da kamala da kuma kamun kai Moddibo ya ajiye System ɗin sa kana ya zauna tare da ɗan jingina bayansa da jikin kujeran ya lumshe Idanunsa tare da motsa laɓɓansa alamar tasbihi Shikuwa M Jameel zaman microphone da aka dasa masa ya gyara tare da buɗe System ɗin sa Lokaci ɗaya cikin masallacin ya gauraye da ƙamshin sanyayyan turaren su yayin da hasken Fararen glob ɗin ya haskaka hasken farin fuskarsu na fitar da sheƙin annuri yayin da baƙin sajensu ya kwanta luf-luf komai nasu kusan ɗaya yake tamkar tagwaye.

Cikin nutsuwa M Jameel ya lumshe Idanunsa tare da gyara zaman Microphone kana Yayi gyaran murya cikin Sanyayyar muryarsa mai cike da kamala yayi gyaran murya kana yace.
_“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi billahi min shuriri anfusna wamin sayyi ati a'amalina manyah dillahu fala hadiyala waman yudil fala mudillalah Wa'ash hadu Allah ilahalillahu wahdahu lasharika Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu Ya Ayyuhal lazina amanut taƙullaha haƙƙu tuƙatihi wala tamu tunna illah wa'antum muslimun Ya ayyuhan nasu taƙu rabbakummalazi halaƙakum min nafsi wahida wahalaƙa minha zaujuha wabassa min huma rijalan kasiran wa Nisa'a wattaƙullahal lazi tasa aluna bihi wal arhama innalaha kana bikum raƙiba, Amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_.

A tare jama'ar dake cikin masallacin suka amsa da.
“Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.
A hankali M Jameel ya fesar da sassayan numfashi tare da lumshe idanunsa kana a hankali yace.
“A yau muna sha huɗu ga watan Ramadan a cigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma da muke acikin masallacin mai Martaba sarki Bashiru acikin Suratu An-Nisa'i ayau zamu tashi akan aya ta Cassa'in da huɗu wala Allah kuma bazai wuce da biyar zamu tsaya ba, sai kuma shekara mai zuwa idan Allah ya bamu aron rai da lfyar”.
Sai kuma ya sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa.
“Tun daga kan aya na cassa'in da biyu muka shiga babi akan kashe ran mumini, da kuma hakkin ran Muminai, ayau Insha Allah zamu cigaba, amman kafin nan zamuyi duba i zuwa kan dukkan ayoyin Alkur'ani dake mgna kan ran muminai”.
A hankali ya buɗe kwayar idanunsa, sabida jin yadda masallacin ya cika da kabbara.
Gyara system ɗinshi yayi kana yace.
“Insha Allah ayau Aramma zai zaƙulo mana Ayoyin da Ubangiji yayi magana akan hakkin kashe ran mumini, domin tunatar wa da kuma jan hankali da kuma fito da darajar ran ɗan Adam Dan kiyaye lalacewar zamani da kuma tunatar da hakkin ran musulmi amatsayin ba komai ba”.
Cikin yanayin kamala ya juya tare da maida kallonsa kan Modibbo da idanunsa ke lumshe ajiyar zuciya sauƙe kana yace.
“Aramma bamu ayoyin da Ubangiji yayi magana akan kashe ran mumini”.
Anutse Moddibo ya gyara zamansa tare da ɗan ture system ɗin sa gefe kana yayi gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryarsa ya fara kamar haka.
Surah Al-ma'idah Aya 32
مِنْ أَجْلِ ذَٰلِكَ كَتَبْنَا عَلَىٰ بَنِي إِسْرَائِيلَ أَنَّهُ مَن قَتَلَ نَفْسًا بِغَيْرِ نَفْسٍ أَوْ فَسَادٍ فِي الْأَرْضِ فَكَأَنَّمَا قَتَلَ النَّاسَ جَمِيعًا
Ya ƙare jan karshen ayar da fesar numfashinsa da ya riƙe domin fidda cikekken haƙin ko wanne harafi,
Yayin da Al'ummar Annabi dake cike a masallacin kuwa, sukayi sit suna masu samun cikekkiyar nitsuwa ta mu'ijizan jin karatun Alqur'ani mai girma kenan.
M Jameel kuwa cike da raunin murya ya fara fassara ayar Allah madaukakin sarki nacewa-:
“Sakamakon haka ne muka wajabta akan 'ya'yan Isara'ila cewa, duk wanda ya kashe wata Rai ba tare da ita Rai ɗin ta kashe wata ba, ko kuma yayi ɓarna a kan ƙasa (ta'addanci, Fashi da makami etc) toh kamar ya kashe mutane ne gaba ɗaya na Duniya kuma ubangiji zai hukunta shi dai-dai da laifinsa”.
Shiru masallacin yayi baki ɗaya, kowa jiki nai a mace, yayinda manyan dottaɓai dake ciki kuwa, suka zuba M Jameel da Modibbo ido suna nazartan yadda akayi akalar tasirin ya sauya daga kan Suratu An-Nisa'i ya koma kan duk ayar da ke mgn kan kisan kai.
Shi kuwa M Jameel juyowa yayi ya kalli Modibbo tare cewa.
Aramma koma cikin suratul Al-ma'idah akwai ayar da Allah ke mgn kan rayuka”.
Cike da ƙwarewa da cikekkiyar hadda mai ɗauke da kaifin basira, Modibbo ya lumshe idanunsa da yakeji suna cika da rauni cike da zaƙin murya ƙira'a mai sa nitsuwa ya kawo ayar
Surah Al-ma'idah Aya 33 إِنَّمَا جَزَاءُ الَّذِينَ يُحَارِبُونَ اللَّهَ وَرَسُولَهُ وَيَسْعَوْنَ فِي الْأَرْضِ فَسَادًا أَن يُقَتَّلُوا أَوْ يُصَلَّبُوا أَوْ تُقَطَّعَ أَيْدِيهِمْ وَأَرْجُلُهُم مِّنْ خِلَافٍ أَوْ يُنفَوْا مِنَ الْأَرْضِ.
Cike da nitsuwa ya dire ƙarshen ayar,
M Jameel kuwa gyara zamansa yayi tare da fara fashin baƙin.
“Allah madaukakin sarki nacewa-:
Lallai sakamakon waɗanda suke yaƙar Allah da Manzo nai, kuma suke yaɗa ɓarna a doron ƙasa (ta'addanci, Fashi, ƙwamushe Garkuwa Da mutane etc), shine a kashe su, ko a giciye su”.
Sai kuma ya fesar da sassayan numfashi tare da lumshe idanunsa wanda tuni suke sheƙin ruwan hawaye, murya cike da rauni yaci gaba da cewa.
“Ko a yanke Hannayen su da Ƙafafuwan su a saɓani (hannun hagu da ƙafar dama, ko kuma Hannun dama da ƙafar Hagu), ko kuma a kore su daga Garin.”.
Zuwa yanzu shar-shar hawayensa ke kwaranya yayinda tuni muryarsa ke rawa, haka yasa da yawa mutanen suke zubda hawaye.
Haka dai Modibbo ya rinƙa zaƙulo dukkan ayoyin Alkur'ani dake mgna kan ran mumini, M Jameel na fassarawa, yayinda gaba ɗaya zuƙata jama'ar masallacin ya cika da rauni.
Kasan cewar gobe ne, Modibbo da M Jameel ɗin zasu wuce ƙasa mai tsarki, damin yin Umrah Ramadan, yasa dole a ranar aka rufe tafsir ɗin. Bayan jero Addu'o'in wa al'ummar musulmi dama kasa baki ɗaya.

Washe gari ranar 15 ga watan Ramadan misalin ƙarfe tara na dara dai jirgi su Modibbo ya tashi daga cikin Taraba zuwa ƙasa mai tsarki...!



Daga yauwa ɗin nan Laraba mun gama free page, in kina son ci gaban littafin SAKAYYAH to ki biya ki karanta cikin aminci. Littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Ki biya ki karanta ba haƙƙin kowa a kanki.


By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[19/07, 8:57 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

*SAKAYYAH*
_Page 17_
*LAST FREE PAGE*
_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*DAGA WANNAN PAGE ƊIN FREE PAGES SUN ƘARE, IN MA KIN SAKE GANIN LITTAFIN SAKAYYAH A WAJE TO. NA SATANE NA ALLAH YA ISA ne, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal yar ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 kiyiwa da Annabi in dai kin san kin sayane don ki fitarmin da littafin na kiyi min mgn in mayar miki da kuɗinki. In kuma kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina, wasu Groups ɗin, kiyiwa Allah da Manzonsa ki bar kuɗinki na yafe cinikin bana buƙatar sa*


Alhamdulillah su Moddibo sun sauƙa lfy a ƙasa Mai Tsarki cikin ikon Allah Mabuwayi gagara Misali sunyi Umarah sun samu goma shabiyar na watan acan cike da ɗumbin farin ciki.
Yau yakasance ranace ta Sallah angama azumi lfya. Al'ummar Musulmai na duniya sun cika da farin ciki kowa kagani fuskarsa ɗauke da yalwataccen farin ciki, kana kowa yayi shiga ta haiba da kamala.
Alhamdulillah bayan an saƙƙo daga sallar idi ko wani gida kashiga zaka samesu cikin farin ciki da shiga ta kamala kana da Lafiyayyan abinci.
Kamar yanda ko ina na faɗin duniya ya cika da farin cikin wannan ranan haka yakasance Agidan Lamiɗo.
Acan falon Mommy kuwa hallare suka gaba ɗayan su Khausar ce tsaye riƙe da waya ahanununta cikin shiga ta alfarma da kamala wani rantsatstsen less ne Blue da ratsin fari ne ajikinta ɗinkin riga da skirt yayin da skirt ɗin ya fitar mata da shape din ƙugunta rigan kuwa tayi ɗass ajikinta ma dai-dai-tan dukiyar fulaninta sun cika fam yayin da tayi ɗaurin ƴar Minister ta zubo yalwataccen sumar kanta zuwa baya daga gaban goshin kuwa ya kwanta luf-luf wuyanta maƙale da sarƙan Gwal da ɗan kunnensa kana fuskarta ɗauke da simple make up daya sake ƙawata kyawun

1 Comments On SAKAYYAH
avatar
fatima-8-5-3

1 month ago

Reply

Allah ya qara basira

Please Login or Register in order to submit comment