Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gida”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan”.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Ummi muje in kaiki gida”.
Kai ta gyaɗa kana ta miƙe.
Suka fita da kallo Abba ya bisu cike da tausayawa.

Moddibo kuwa yana ajiye Ummi agida kai tsaye makarantar Malam Arɗo ya nufa yana isa yayi Parking tare da fita ya nufi harabar makarantar iska na kaɗa shi kai tsaye Office din malam Arɗo ya Murɗa handle din ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama.

Anutse Malam Arɗo dake duba wani littafi ya ɗago kansa tare da sauƙe Idanunsa akan Moddibo ganinsa cikin wani irin yanayi yasa yayi saurin miƙewa tare da riƙe hannun sa kana yace.
“Moddibo ya dai?”.
Kai Moddibo ya Girgiza cikin sanyin murya yace.
“Bakomai”.
Kujera Malam Arɗo yaja masa ya zauna kana shima ya koma mazauninsa.

Cike da kulawa Malam Arɗo yace.
“To ina ƴan biyun naka?”.
ƙasa yayi da kansa tare da runtse Idanunsa kasancewar sa ba mai saurin kuka ba ya tabbata da ace yana da saurin kuka da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zaiyi kuka ko hakan zaisa ya samu sassaucin abinda yake ji Aransa ya sake damƙe lip ɗin sa da ƙarfi wanda zuwa lokacin ya sake kumbura kana yayi ja sai sheƙi yake.

Ido Malam Arɗo ya tsira masa kana yace.
“Ya dai Aliyu mai yake faruwa da Jameelu tun jiya da yamma naji ana raɗe-raɗin wai ba agansa ba nayi ta kiran wayarka baka ɗauka sannan shi kuma idan na kirasa akashe ina Jameelu da gaske ne babu shi!??”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago kansa still yana taune da lip ɗinsa kana cikin raunin murya yace.
“Babu J”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Na sani Aliyu ka nutsu ka dawo hayyacinka Aliyu na sani babu Jameelu sannan na gaskata tunda har naga kai kaɗai kazo nan na tabbata do min idan anganka tamkar anga wata ne dole za'aga zara”.
Ya faɗa tare da miƙewa ya dafa kafaɗar sa.
Runtse Idanu Moddibo yayi

“Yanzu ya ake ciki?”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da shafa ƙirjinsa dake bugawa da ƙarfi kana yace.
“Nima kaina ya kulle a duniya bansan me zanyi ba bansan ya zanyi na ganni da J ba?”.
Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Toh yanzu wani mataki aka ɗauka akan lamarin!?”.

Cikin raunin murya yace.
“Babban matakin da aka ɗauka shine addu'a da faɗawa Ubangiji abinda yake faruwa”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi tare da faɗin.
“An ɗauki mataki mai kyau, da girma wanda ya dace da dukkan Musulmi yanzu mu shiga cikin makaranta mu faɗawa yara su tayamu da addu'a Ubangiji Allah ya tsare malam Jameelu ya kuma bayyana sa aduk inda yake”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace.
“Toh Nagode Allah ya saka da alkhairi”.

Hannunsa Malam Arɗo ya riƙe bayan ya mike suka fita kai tsaye bangaren ƴan primary suka fara shiga Ajinsu Ramadan da Raudat yaran na ganinsa suka miƙe cike da farin ciki suna cewa Moddibo Moddibo Kusan a tare Raudat Ramadan da wasu ɗalibai uku suka ce Moddibo ina Malam Jameel munyi kewar ku bakwa zuwa.
Lumshe Idanunsa da yaji suna masa zafi da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zuciyarsa zata buga da masifar ƙarfi tsayuwar sa ya gyara agaban ajin tare da cewa.
“Ina ɗaliban Malam Jameel?”.
Baki ɗaya yaran suka ɗaga hannu suna tsalle tare da cewa gamu nan Moddibo ina yake munyi kewarsa bakwa zuwa yanzu, dan Allah kace yazo muna san ganinsa.
Kasa furta komai Moddibo yayi hakan yasa ya jingina bayansa da jikin bango yayi ƙasa da kansa yasan yanda J ɗin sa ke son Yara da kuma wasa da su wanda a ra'ayinsa baison koyar da yara amma saboda yanda J ɗin sa ke son Yara Yasa yake shiga koyar musu ganin haka yasa Malam Arɗo yayi gyaran murya Atake duk yaran suka nutsu tare da tsirawa Malam Arɗo ido.
A hankali Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin.
“Kuna jina?”.
Kai suka gyaɗa masa.
Ya sauƙe numfashi tare da cewa.
“To zaku yiwa Malam Jameel din ku addu'a Allah ya bayyana shi?”.
Aruɗe yaran suka ce Malam Jameel ya ɓata ne?."
Kai Modibbo ya gyaɗa musu cike da damuwa.
Cikin zare ido Raudat tace.
“Malam Jameel din mu ya ɓata kuma to ina yaje?”.
Ramadan kuwa miƙewa yayi tare da zuwa gaban blackboard ɗin cikin yanayin damuwa sosai ya riƙe hannun Moddibo da har zuwa lokacin Idanunsa ke lumshe yace.
“Moddibo ina Malam Jameel ɗin mu yaje dan Allah ka kira wayansa kace ya dawo Muna so sa”.
Kasa cewa komai Moddibo yayi sabida zulumi.
Gyaran murya Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Kuyi masa addu'a Allah ya bayyana shi idan kunyi sallah kuyi addu'a Allah ya bayyana Malam Jameel sannan ku faɗawa iyayenku suma suyi masa addu'a Allah ya karesa ya kuma dawo dashi cikin aminci da salama”.
Hawaye Ramadan ya fara zubdawa tare da cewa.
“Toh Malam zamuyi masa addu'a zan faɗawa Mommy da Addah Khausina suma zasuyi masa addu'a Allah zai dawo dashi”.
Ahankali Moddibo ya shafa kansa tare da cewa.
“Yawwa Ramadan kuyi masa addu'a ayanzu babu abinda Malam Jameel yake buƙata awajen mu face addu'a”
Cikin rauni sosai yaran suka ce zamu yi masa.
Cikin sanyin jiki Malam Arɗo da Moddibo suka fita zuwa bangaren Secondary bayan sun fita anan suka shiga ɓangaren na naziri saida suka gama zagaye ko wani aji suna sanarwa Ayiwa Malam Jameel addu'a Ubangiji Allah ya bayyana shi cikin tashin hankali ɗalibai suka shiga masa addu'a.

Bayan sun fito Moddibo ya nufi hanyar gate
Cikin kula malam Arɗo yace.
“Moddibo baza ka shiga office din ku ba?”.
Kai ya girgiza tare da cewa.
“Um-um bazan shiga ba zan tafi bazan iya zama babu J ba”.
Ya faɗa tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Abban M Jameel ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama A inda ya fita yabar Abba anan ya dawo ya sameshi zaune still wayarsa na gabansa ya zubanusu Ido da alama tun bayan fitarsa ko motsawa baiyi ba.

Ahankali Abba ya ɗago kai tare da zuba masa ido cike da tausayinsa baki ɗaya ya rame ya canza idanunsa sun sake girma da ja kana idanunsa sun faɗa, Ahankali Moddibo ya ƙaraso ya zauna agefensa aƙasan Capet Cike da tausayawa Abba yace.
“Aliyu ba kayi wanka ka sauya kaya ba”.
Siririn tsaki Moddibo yaja tare da yin ƙasa da kansa kana yace.
“Abba har yanzu basu sake kira ba!?”.
Kai Abba ya Girgiza tare da cewa.
“Har yanzu basu sake kira ba gani nan ina zaune tamkar gadin waya nake sai tsumayin kiransu nake amma basu kira ba, amma yanzu ka samu kaje kayi wanka ka samu kaci abinci”.

“Abba banajin yuwa”.

“Ya zamuyi Aliyu idan kaima baka ci abinci ba ai faduwa zakayi. Insha Allah addu'ar mu bazai bar Jameelu ya ta gayyara ba”.
Sai ya kuma maida kallonsa kan Hajiya Karima data shigo wacce ita ma baki ɗaya tayi sanyi ahankali yace.
“Ki zubawa Aliyu sbinci”.
Kai ta gyaɗa tare da nufar dining ta ɗauki Plate ta zuba masa jollof fice da yaji bushesh-shen kifi da namar kaza ta kawo masa.
Moddibo kuwa hannu ya daga mata alamar kada ta ajiye masa ganin ta ajiye yasa ya maida kansa jikin kushin ɗin ya jingina tare da lumshe idanunsa yace.
“Ina ma ace tare suka ɗauke Ni da J da yafi min farin ciki ina rayu dashi aduk inda yake duk halin da yake ciki ace muna tare wallahi da yafi min farin ciki akan rabani da Jameel da sukayi”.
Kallonsa Abba yayi cike da tausayawa wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji Moddibo ya kira Complete sunan M Jameel cikin raunin murya yace.
“Toh ya zamuyi Aliyu ka daure kaci abinci”.

“Abba ba zan iya cin abinci ba”.
Cikin rarrashi Abba yace.
“Haba Aliyu ka naso kasake sa kamu cikin damuwa ne rashin cin abinka dai dai yake da yiwa kan ka illah, wanda bazan so hakan ba dan Allah ka daure kasa wani abu acikin ka”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh Abba abani tea”.
Miƙewa Hajiya Karima tayi ta nufi dining kana ta haɗa masa tea cup ɗaya ta kawo masa ahankali ya karba tare da kaiwa bakinsa da ƙyar ya iya shan rabi ya ajiye Cup ɗin.
Abba bai tilasta shiba dan shima akaran kansa yasan ba zai iya saka komai acikin sa ba baya ga tea ɗin da yake sha dan raya kai, cikin sanyin murya yace.
“Aliyu kaje ɗakin Jameelu kayi wanka ka sauya kaya”.
Girgiza kai yayi cikin rawan murya yace.
“Abba bari in je gida saboda nabar Innayi ita kaɗai tun safe sannan na barta cikin damuwa”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh Aliyu ka gaisheta”.

Yana isa gida yayi Parking tare da wucewa Bedroom ɗin sa, kai tsaye toilet ya shiga tare da sakarwa kansa ruwan sanyi sai alokacin ya lura da Dick ɗin sa daya kwanta luƙui tamkar bai taɓa tashi ba tsanananin fargaba da tashin hankali da yake ciki yasa ya kasa tantance shin shi ɗin wani irin halitta ko kuma wanne irin jinsi ne shin shi ɗin namiji ne ko mace baisan matsayin da yake ba bare kuma ace sha'awa baki daya Dick ɗin sa ya kwanta tamkar babu wani abu mai suna sha'awa daya taɓa ji cikin sanyi Jiki ya gama wankan tare da fitowa ya shirya cikin Jallabiya kana ya fesa turare kai tsaye sashen Innayi ya nufa.

Misalin ƙarfe 5:00pm da wasu Mintuna bayan antaso Amakaranta motarsu Ramadan na shiga harabar gidan tayi Parking Ramadan ya ɓude tare da ficewa da gudu.
Acan falo kuwa Mommy da Khausar ce zaune suna kallon TV cikin tashar Nat geo well Suna kallon namomin daji Ramadan ya shigo tare da zama gefen Khausar kana ya langwaɓar da kansa tare da cewa.
“Addah Khausi”.
Hankalinta na kan wasu irin halittun ruwa tace.
“Na'am Ramadan”.
Cikin muryan rauni yace.
“Addah Khausi wai Malam Jameel ya ɓata”.
Cikin sauri ta kallesa tare da riƙe hannunsa kana cike da mamaki tace.
“Malam Jameel ya ɓata kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata kana yace.
“Eh Addah Khausi Moddibo da Malam Arɗo su suka shiga ajinmu suka faɗa mana Malam Jameel ya ɓata ba asan inda yake ba”.
Cike da mamaki da kuma al'ajabi Khausar tace.
“Ha'a wace iriyar magana ce wannan Malam Jameel ya ɓata ba'a san inda yake ba!?”.

Mommy kuwa cike da mamaki take kallon Ramadan kana tace.
“Ramadan ka tabbatar kuwa?”.
Kafin yace wani abu Raudat ta shigo da kuka fuskarta jage-jage da hawaye kana ta zauna kusa da Mommy tare da cewa.
“Wallahi Mommy wai ya ɓata!”.
Da sauri Mommy ta ɗauki wayarta dake hannun kujera kana tace.
“Gashi kiramin Umminsa”.
Amsar wayar Khausar tayi still da mamaki atare da ita tace.
“Eyyy aikuwa Jiya naga miss call ɗin Asma'u bana wajen daga baya kuma da nazo ina ta kiranta bata ɗaga ba”.
Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo sanye da hijabi har ƙasa kana ta zauna kusa da Khausar dake laluɓo number Ummi ya zama na sun sa Ramadan Atsakiya kasancewar kujeran 2sitter ne.

Bayan Mommy ta amsa Sallamar ta tace.
“Hajiya wai kinji abinda yaran nan suke faɗa wai Malam Jameel ya ɓata!”.
Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh dama baki ji bane aini tun jiya da yamma Aminu ke faɗa min wai yaji Amasallaci ana cewa ayi addu'a Allah ya bayyana ya kuma tsaresa ashe dama ba kiji ba?”.
Kai Mommy ta.
Girgiza fuska cike da damuwa tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Wallahi ban jiba Subhanallah ya Salam Ubangiji Allah ya tsaresa”.

Hajiya Bunayya kuwa ahankali ta saci kallon Mommy sai taga idanunta nakan Khausar data maƙala waya akunnenta cike da dabara ta sake murza turaren dake hannunta kana ta fito dashi ta ɗaura akan Ramadan tana shafa masa aranta kuwa fari fess tana cewa Alhamdulillah wannan turaren dai na samu na shafa masa saura kuma gobe in faɗawa Boka Kar'uzu na shafa masa turaren.

Khausar kuwa jin Asma'u tayi Picking call ɗin yasa cikin sauri tace.
“Asma'u”.
Cikin wata dashash-shiyar murya mai cike da rauni Asma'u tace.
“Na'am Khausar”.
Cikin alamun damuwa Khausar tace.
“Asma'u wai me nake ji?”.
Cikin muryan kuka Asma'u tace.
“Khausar an sace Yah Jameel yau kwana biyu kenan kusan na uku ba Yaya Jameel ba labarinsa”.
Atsorace Khausar ta dafe hannunta aƙirji kana tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ansace Yah Jameel Kuma?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa hawaye na bin kuncinta tace.
“Eh”,
Cikin sanyin murya tace.
“Ubangiji Allah ya bayyana shi aduk inda yake Allah ya fito mana dashi”.
Ameen Asma'u ta amsa tare da katse kiran.

Kallon Mommy Khausar cikin tashin hankali tace.
“Mommy wallahi da gaske an sace sa”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa.
“Ya Salam wallahi bamu sani ba barin idan Abbanku ya shigo zan tambaye sa muje muyi wa Umminsa jaje Ubangiji Allah ya bayyana shi Allah ya tsaresa aduk inda yake”.
Khausar kuwa kasa tsaida hawayen ta tayi cikin Muryan kuka tace.
“Ameen Mommy Ameen ya hayyu ya ƙayyum Allah ya bayyana Malam Jameel har kwana biyu kuma!?”.

Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tare da marairaice fuska kana tace.
“Hakane kam wannan duniyar ta zama abin tsoro idan kana fama da talauci ka banu idan kayi wadata ɓarayi da ƴan Kidnapping su hanaka kwanciyar hankali da nutsuwa Allah dai ya kyauta”.
Ta faɗa tare da miƙewa ta fice ranta fess.
Baki ɗaya Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yita cikin jimami da fargaba musamman Khausar ta gagara tsaida hawayen ta.

Moddibo kuwa yana fita daga sashen Innayi mota ya shiga tare da nufar gidan Abba yana isa ana kiran maghariba tare da Abba suka shiga Masallaci suka gabatar da sallah.
Acan ɓangaren Mommy kuwa bayan an idar da sallar Isha'i ta sanarwa da Lamiɗo suna san zuwa yiwa Ummi jaje nan yace ba damuwa ta kira Khausar da Hajiya Bunayya su fito bayan sun fito da kansa yayi Driving ɗinsu zuwa gidan Ummi.
Bayan sun isa.
Mommy ce agaba sai Khausar sai kuma Hajiya Bunayya bakinsa ɗauke da Sallama suka shiga dai-dai lokacin kuma maƙotansu suka fito.

Zaune suka samu Ummi kan 2sitter tana riƙe da Kur'ani Idanunta sun kumbura sun ƙanƙance yayin da Asma'u ke zaune gefenta hannunta riƙe da Carbi.

Cikin sauri Khausar ta ƙarasa kusa da Asma'u tare da riƙe hannun ta kana tace.
“Asma'u da gaske wai dagaske ansace Yah Jameel!?”.
Cikin zubda hawaye Asma'u ta gyaɗa mata kai kana tace.
“Khausar da gaske ansace Yah Jameel tun randa kikazo ya maida kin nan, har yanzu babu labarin sa yanzu kusan dare na uku kenan za ashiga”.
Khausar ma cikin zubda hawaye ta damƙe hannun Asma'u tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Kallon Ummi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ayyah Ummin Jameel Ashe abinda ya faru kenan toh Ubangiji Allah ya tsare Allah ya bayyana shi”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.
“Ameen ya Allah Nagode”.
Mommy kuwa kafaɗar ta ta dafa kana tace.
“Ba komai Ummin Jameel kiyi haƙuri ki daina kukan nan ki riƙa yi masa addu'a Insha Allah Ubangijin zai bayyana shi”.
Cikin sauri Ummi ta share hawayenta kana tace.
“Nagode Mommyn Khausar Nagode³”.
Cike da tausayawa Mommy ke sake ƙarfafa mata guiwa.
Ahankali Khausar ta juya tare da kallon Ummi cikin Muryan kuka tace.
“Ummi Allah ya bayyanar da Yah Jameel insha Allah ba zasu samu nasarar cutar da shiba zamu tayi masa addu'a Allah ya karesa”.
Miƙewa Hajiya Bunayya tayi kana tace.
“Bari mutafi Alhj na jiran mu awaje yace a gaidaki".
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Nogeda Allah ya saka”.
Sannan suka fita a coumpund suka haɗu da wasu matan sun shigo yiwa Ummi jaje bayan sun koma gida.

Baki ɗaya Khausar ta kasa nutsuwa kafin ta kwanta taje tayi alwala kana ta ɗauki Kur'ani tana ta karatu tare da tawassali dashi da niyyan Ubangiji ya bayyana M Jameel aduk inda yake.

Misalin ƙarfe goma na dare kamar lokacin da aka dauke M Jameel Moddibo dake gefen Abba ya miƙe da niyyar tafiya Akuma dai-dai lokacin wayar Abba dake gabansa ta hau ruri.
Atare Abba da Moddibo suka kalli wayar cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnensa.
Daga ɗaya ɓangaren akace Alhj Bashiru mahaifin Jameel ko!?”.
Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da cewa.
“Eh nine nayi ta kiran layinku baya shiga”.
Cikin fusatacciyar murya Mutumin yace.
“Dama ce maka mukayi idan ka kira zai shiga?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da faɗin.
“A'a to menene sharaɗin ku na biyu kaga ban faɗawa kowa ba!”.
Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.
“Kuɗin fansa zaka biya shine sharaɗin mu na biyu”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“To nawa kuke buƙata?”.
Kai tsaye mutumin yace.
“Milion ɗari biyu”.
Atsorace Abba ya dafe hannunsa aƙirji kana ya zare ido cikin tsanananin firgici yace.
“Milion ɗari biyu!?”.
Atare Hajiya Bunayya da Moddibo da maganar ya dakesu suka haɗa baki atare wajen cewa.
“Milion ɗari biyu?”.
Cike da gadara Mutumin yace.
“Toh idan ba zaka bada ba sai ka shirya karɓan gawar ɗan ka!”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.
“Kuyi hakuri dan Allah dan darajar Annabi kada ku kashe wayar”.
Cikin Yanayin ɓacin rai Mutumin yace.
“To ai mun riga mun faɗa muku abinda ake buƙata idan ka shirya gobe zamu sake kiran ka muji ko ka shirya”.
Yana gama fadar haka ya katse kiran...!






By
*GARKUWAR MARUBUTA*


[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ne ba free book bane 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci kada ki karanta na sata na Allah ya isa. 0661110179 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group ɗina*


Cappande. Acikin tafin hannunsa ya ɗebo sulallan Gwal ɗin da wasu yan guntu-guntun sanduna tare da birbiɗin yashin kana ya shiga jujjuyasu, ahankali ya maida kallonsa kan Innayi data gyaɗa masa kai alamar ya fito dasu hannunsa ya zura acikin tukunyar yashiga kalato salullan wanda na ainihin Gwalne aƙalla sun kai guda ashirin, karkaɗe yashin yayi tare da fitowa dasu kana ya ɗaura su akan rigarsa tare da gyara zaman sa abakin ramin ya tsura mata Ido Innayi ma ido ta zuba masa ganin yanda ya zauna yasa tashiga maida yashin ta rufe ramin kana ta sanya duwatsun ta rufe tare da tura fantekar kan ramin kallon Moddibo dake binta da kallo tayi kana tace.
“Ɗaura min randan nan akai”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe still Idanunsa na Kanta cikin sanyin murya yace.
“Innayi wannan kamar Gwal?”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Eh Gwal ne”
Still ba tare daya motsa ba ya sake kallon Gwal ɗin kana yace.
“Ina kika same su Innayi?”.
Girgiza masa kai tayi kana tace.
“Wannan ba lokacin tambayar ina nasamu gwala-gwalai bane. Moddibo lokacine daya kamata ace ka lissafa su muga adadin su kana musan nawa za'a samu mu haɗa mu karɓo Jameelu yanzu tashi mubar wajen nan mushiga ɗaki kaga dare ya tsala”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Toh”,Kana yabi bayanta tare da tsira mata idanu cike da ɗumbin mamaki tare da tarin tuhuma ahankali ya sake kallon sulallan Gwal ɗin dake haɗe da waɗanan sanduna guntaye aciki asaman laɓɓansa yayi sallama tare da shiga ɗaki.
Wutan ɗakin Innayi ta kunna Atake haske ya zagaye ɗakin bayan Moddibo ta ratsa tare da rufe kofar ɗakin kana ta dawo kusa dashi ta tsaya tare da sanya hannunta ta tsistsince ƴan guntulayen sandar ta shiga haɗawa kasancewar akwai wajen haɗawa ajiki Moddibo kuwa Idanu ya zuba mata cike da mamaki.
tana cigaba da haɗawa ga mamakinsa sai yaga ya zama sanda irin wanda manyan Limamai ke riƙe wa suna tafiya dashi sanda ce mai masifar kyau da tsari wacce da ka gani kasan mai tsadace.

Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.
“Wannan sanda ce samansa inda ake riƙewa ne kaɗai keda Gwal sai kuma ƙasan sa inda ake dogara wa amma wannan bazan baka shiba saboda ba zaiyi daraja sosai ba. Saboda ahaɗe yake da sanda kana sandar kuma bazan siyar ba, sulallan dai zaka haɗa ka duba sai dai sunzo mana alokacin da bashine ba saboda sulallan baki ɗaya sun ƙare”.
Ido kawai Moddibo ya zuba mata still da shock atare dashi.
Innayi ta cigaba da cewa.
“Baki ɗaya nauyin karatunka.
Cin mu, shan mu, suturar mu, tun kana ƙarami da duk wani abinda ya kama su nake ɗauka in siyarwa Alhaji Hashim mai sayan gwala-gwalai shiyasan farashin sulallan duk yanda suke zan faɗa masa adadin da suke yazo ya siya muyi lissafi muga nawa za'a samu”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan”.Yayi mgnar tare da lumshe idanunsa, baki ɗaya damuwarsa asamu kuɗin bawai tunaninsa ya tambayi ina tasamu gwala-gwalan nan ba sannan bashida kuzarin da zai iya tambayar ta, sandar na menene, kana bashi da ƙarfin zuciyar jin mai yasa baza asayar da sandar ba, ayanzu burinsa bai wuce asamu ahaɗa kuɗaɗen akarɓo J ba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon Innayi kana yace.
“Toh zan tafi dasu ɗakina”.
Kai ta gyaɗa masa kana ya miƙe ya fita yana jin confidence da farin ciki yasan Gwal nada daraja duk da cewa ƴan ƙananun sulallane amma yasan da izinin Ubangiji zasuyi daraja.

Acan gidan Abba kuwa bayan tafiyar Moddibo Hajiya Karima ta kalli Abba daya zurfafa acikin tunani kana ta ɗan ya mutse Fuska tace.
“Alhji wai yanzu baza ka sake ƙara neman ragi ba? yanzu sai ka ɗauki Million ɗari da hamsin ka basu mai kake tunanin zai faru gaba idan sunji daɗi za'a sake ɗaukan ƴaƴanka ne fa!”.
Anutse Abba ya ɗago kansa tare da kallonta kana cikin sanyin Murya yace.
“Karima to me kike tunani?”.
Ba yabo ba fallasa tace.
“Ka nemi ragi”.
furzar da iska mai zafi yayi still Idanunsa na kanta kana yace.
“Karima kamar baki ji me yace ba, cewa fa yayi muddin aka nemi ragi akan rayuwar Jameel”.

Cikin sauri tace.
“Bafa za'a kashe Jameel ba, kawai Alhj idan zaka nemi ragi ka nemi ragi, sai kace baka sha zafin neman kuɗin ba zaka ɗauka agabtale ka basu kamar ba kasan darajar suba, amma babu yanda zaka ɗauki wannan maƙudan kuɗin ka bayar akan Jameelu!”.

Cike da mamaki Abba ya kalleta kana cikin ɗaga sautin murya yace.
“Karima to idan ban bada kuɗi akan Jameelu ba akan wa kike so in bayar? Shin Karima anya Karima?”.
Wani irin kallo ta masa kana cikin sauri tace.
“Anya me?”.
Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo baki ɗaya ta hargitse babu walwala afuskarta ta kalli Hajiya Karima kana tace.
“Ai dai kam abin nata da mamaki, idan bai ɗauki kuɗi ya bayar akan Jameelu ba akan wa kike so ya bayar?”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Abba da idanunsa ke lumshe kana tace.
“Aini Alhj naga ƙoƙarin ku ma da har kuka iya neman ragin da suka rage muku, kuma ai sunyi ƙoƙari ni dai anawa tunanin kada ku kuskura kada ku sake yin batun ragin wasu kuɗin, suje su kashe mana yaro abanza idan aka kashesa mai son sa keda asara wanda bai sonsa kuma bai damu ba”.
Ta ida maganar hawaye na ciko kwarmin Idanunta.

Hajiya Karima kuwa wani kallo ta watsa wa Hajiya Turai tare da cewa.
“To mekike nufi?”.
Taɓe baki Hajiya Turai tayi kana tace.
“To ai gaskiya ne duk mai son Jameelu ba zai so ace za'a sake neman ragi ba”.
Taɓe baki Hajiya Karima tayi tare da watsa mata kallon banza kana tace.
“Kenan kina nufin Ni bana son Jameelu?”.
Hannu Hajiya Turai ta buɗe kana tace.
“A'a wannan ke ki kafaɗa da bakin ki amma dai shawaran da kika kawo ba shawara me kyau bace”.
Hannu Abba ya ɗaga musu tare da kallon Hajiya Karima dake kumfar baki kana yace.
“Bana son hayaniya ya isheku.
Dan Allah kubarni inji da abinda ke damuna”.
Kai Hajiya Turai ta gyaɗa tare da tsuke bakinta alamun itama ba hayaniyar take soba.
Cikin sanyi ta kalli Abba tare da cewa.
“Alhj ga Million biyu a Account ɗina zan bayar ahaɗa”.
Wani shegen kallo Hajiya Karima tabi Hajiya Turai dashi kana cikin taɓe baki tace.
“Hmmm munafurci dai da neman gindin zama haddasu kaza acikin cin danƙo”.
Cikin sanyi Abba yace.
“Nagode Turai Allah ya saka da alkhairi ayanzu kyauta koda na Naira biyar aka bani ita ina buƙatar ta, xansa acikin tumunin kudin da za'a karɓo Jameel”.
Cikin sauri Hajiya Karima tace.
“Nima Allah ya bani in bayar”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Ameen”.
Juyawa tayi ta fice Hajiya Turai kuma ta zauna gefensa tana sake tausansa.

Acikin kwanaki biyu Moddibo ya saida gwala-gwalan da kuma motocinsa dana M Jameel Yayi total ɗin kuɗin sun kama Million ashirin da biyar ya turawa Abba cikin account ɗin sa Alhamdulillah yanzu akwai Million casa'in da biyar acikin account ɗin Abba Aɓangaren Abban ma yana cigaba da fafutuka ganin ya samu kuɗi.
Acikin kwanakin baki ɗaya abubuwa sun kankama baki ɗaya sun sake maida hankalinsu kan neman kuɗin suga sun samu sun haɗa yau ya kama kwanan M Jameel goma kenan awajen Kidnappers din kana yau kwana biyu rabon Abba da Moddibo suyi waya da M Jameel Misalin huɗu na yamma Moddibo ya bar gidan Abba ya nufi gidansu bayan sun sake tattauna wa.

Acan ɓangaren Boka Kar'uzu kuwa Hajiya Bunayya da

1 Comments On SAKAYYAH
avatar
fatima-8-5-3

1 month ago

Reply

Allah ya qara basira

Please Login or Register in order to submit comment