Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani masifar ramewa idanunsa sunyi luhu-luhu dasu yayinda sajensa ya cika fuskarsa kasancewar gashi mai santsi da laushi yasa sai sheƙi yake fuskarsa nan tayi fayau sai sheƙi take alamun a ɗan kumbure take sabida yawan kuka da rashin isasshen bacci.
Lumshe Idanu Innayi tayi hawaye masu zafi suka zubo ganin kamar daga jinya ya tashi.

Moddibo kuwa ahankali ya ɗaga kai ya kalleta jin yandata tsaresa da ido.
Cikin rawan murya tace.
“Moddibo kaga yanda ka dawo kuwa?”.
Murmushi mai ciwo yayi tare da Girgiza kansa cikin sanyin murya yace.
“Innayi bari na tafi wajen Ummi”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh baka tsaya kaci abinci ba”.
Girgiza kai yayi kana yace.
“A'a Innayi na ƙoshi”.

Kallonsa Innayi tayi Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Dan Allah Moddibo ka tsaya kaci wani abu dubi yanda ka dawo fa”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Toh shikenan Innayi ki bani tea”.
Cikin sauri ta hado masa tea ta kawo masa karɓa yayi yasha bayan yasha ya fita kai tsaye gidan Ummi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga falon.
Ummi na ganinsa tayi saurin miƙewa tare da fashewa da kuka mai cike da rauni.
Moddibo kuwa cikin sauri ya ƙarasa kusa da ita tare da riƙe tafin hannunta kana cikin raunin murya yace.
“Ummi meyafaru Ummi kuka kuma?”.
Cikin zubda hawaye ta kallesa tare da cewa.
“Babana abubuwan sun haɗu sunyi min yawa acikin kwanaki Ukun nan Ba Jameelu na sannan kai ɗinma da nake gani inji sanyi na daina ganinka. Babana kaga yanda kadawo fa”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Ummi Insha Allahu in Allah ya yarda hawayen mu ya kusa daina zuba inaji Ajikina J yana kusa damu”.
Numfashi ta fesar tare da cewa.
“Allah yasa hakan Babana dubi yanda ka dawo fa kamar wanda aka sallamo daga asibiti kana tafiya Iska na ɗibarka”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u data zabga tagumi tana binsu da kallo baki ɗaya itama ta rame ta sake zama shiru.
Cikin sanyin murya tace.
“Asma'u kawo masa abinci yaci”.
Kai ya Girgiza Asanyaye yace.
“Ummi bana jin yunwa”.
Cikin sauri da sanyi Ummi tace.
“Zafa kaci abinci matuƙar kana son hankalina ya kwanta to kaci abinci Babana”.
Cikin sanyi yace.
“Toh Ummi”.
Ahankali Asma'u ta fito hannunta riƙe da Plate ɗin dambun shinkafa dayaji Vegetables ya na fidda ƙamshi da soyayyan naman kaza akai da kwalin exotic.
Agabansa ta ajiye masa kallon Ummi yayi ganin yanda ta tsare da ido tana zuba masa, ahankali ya fara cin abinci duk da yana jin cikinsa ya cushe yaci ya kai rabi kana yasha lemon Kaɗan.
Ture Plate din yayi kana yace.
“Ummi bari Inje gidan Abba”.
Kai ta gyaɗa da fadin. “Adawo lafiya”.

Moddibo na fita kai tsaye gidan Abba ya nufa yana isa ya shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama Atare Abba da Malam Arɗo dake zaune suka amsa masa cikin sanyi Moddibo ya nufi gefen Abba ya zaune tare da Gaishe su.
Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi kana yace.
“Moddibo yau kwana uku bakai babu dalilinka sannan wayarka bata shiga shine nace bari inzo tambayi Abban Jameel ko lafiya kaddai wanda suka ɗauki Jameelu ne suka ɗauke mana kai”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Nima da ban ganshi ba gaba ɗaya hankalina ya tashi duk da cewa nasan yana gida lafiya amma rashin ganinsa ya sake tayar min da hankalin rashin ganin Jameelu na”.
Cikin sanyin murya Malam Arɗo yace.
“Toh Allah ya bayyana shi Alhj Ubangiji Allah ya bayyanar dashi aduk inda yake!”.
Cikin rauni Moddibo ya kalli Abba tare da cewa.
“Abbah basu kira ba atsawon kwana ki ukun nan”.
Girgiza kai Abba yayi da faɗin.
“A'a basu kira ba Aliyu kuma ga wayar Jameelu na ta daina shiga, yanzu sannan suma sun daina kira”.
Moddibo kuwa ahankali yace.
“Bakomai Abba Insha Allah Allah zai bayyana shi akan al'khairi Alfarman Annabi da Alkur'ani”.
Atare suka amsa da Ameen Hajiya Turai ce tashigo bakinta ɗauke da sallama bayan sun gaisa da malam Arɗo ta kalli Moddibo da faɗin.
“Moddibo kwana biyu shiru gashi babu wani labarin Jameelu Ubangiji dai Allah ya bayyana mana shi”.
Cikin sanyin murya suka amsa da Ameen kana ta juya ta fice.

Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi kana yace.
“Moddibo muje ka rakani wani waje mana”.
Kallonsa Moddibo yayi da faɗin Ni kuma?”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa masa kana yace.
“Eh”.
Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.
“A'a kayi haƙuri ni kam babu inda zanje”.
Kallon Moddibo Abba yayi kana yace.
“Aliyu kaje ka rakasa mana”.

Gyara zama Malam Arɗo yayi tare da faɗin.
“Kuma ta'aziyya ne ma zai rakani, gidan Lamiɗo tunda akayi rasuwar yaron nan yau wuni na biyar kenan ban samu naje ba, kuma kaima ya kamata kaje amatsayin ka na Malaminsu”.
Shiru Moddibo yayi tare da sunkuyar da kansa ƙasa.
Ahankali Abba yace.
“Aliyu kuje mana zama waje ɗayan nan ma bashi da daɗi”.
Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.
“Abba ni dai banason zuwa”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe da faɗin.
“Kuje mana Aliyu Ubangiji Allah yasa zuwan ya zama alkhairi”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ameen”.
Sannan ya miƙe Malam Arɗo na biye dashi suka fita.

Acan gidan su Khausar kuwa Lamiɗo ne zaune afalon tare da wasu baƙi guda biyu da suka zo daga Taraba Alhj Ibrahim da Alhj Musa suka zo yi masa ta'aziyya sai kuma Uncle Naseer dake gefe.
Mai gadi ne ya shigo bakinsa ɗauke da sallama kana yace.
“Ranka ya daɗe ga Malam Arɗo da Malam Moddibo Malaman su Ramadan sunzo”.
Kai Lamiɗo ya gyaɗa tare da faɗin.
“A'a kace su shigo harda malam Arɗo da kansa”.
Kai ya gyaɗa sannan ya fice ba dadewa Malam Arɗo suka shigo tare da zama kana suka yi Masa ta'aziyya ahankali Moddibo yace.
“Ashe Ramadan lokaci yayi Allah ya masa rahma”.
Cikin sanyi Lamiɗo yace.
“Ameen Moddibo ya mukaji da taraddadin rashin Jameelu har yanzu shiru ko?”.
Cikin sanyi Moddibo yayi ƙasa da kansa tare da matse yatsun hannunsa batare da yace Uffan ba sai kai da ya gyaɗa masa.
Da-dai lokacin mai gadi ya sake shigowa tare da cewa.
“Ranka ya daɗe ga Ɗan gidan Arɗo Ja'eh yazo yi maka ta'aziyya”.
Kai Lamiɗo ya gyaɗa da fadin kace ya shigo”.
Fita mai gadin yayi tare da sanar da baƙon.

Da Sallama Bararojin Fulanin dajin yashiga falon Lamiɗo cikin shigarsu irin ta Fulani hannunsa riƙe da sanda kusa da ƙafar Lamiɗo ya zauna kana suka gaisa sannan ya musu ta'aziyya.
Juyawa yayi ya kalli Malam, Arɗo, Moddibo, Alhj Musa Alhj Ibrahim ya gaishesu tare da yi musu ta'aziyya.

Kallonsa Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori ya Baban naka?”.
Cikin yanayin rashin wadatacciyar Hausa yace.
“Ai bashi da lafiya ne shiyasa bai samu yazo ba, na wakilcesa munji labarin Ramadan ya rasu Allah ya masa rahma”.
Baki ɗaya suka amsa da Ameen.

Ahankali Lamiɗo ya juya tare da kallon Moddibo kana yace.
“Moddibo da gaske wai har yanzu babu labarin Jameelu”.
Ahankali Moddibo ya ɗago kansa dake ƙasa ya kalli Lamiɗo cikin rawan murya.
“Eh har yanzu babu labarinsa, yanzu kam ma sun daina kira, sannan kuma wayarsa ma da ake kira ta daina shiga zuwa yanzu munsa hukuma a cikima sunyi iya bincikensu ba labari”.

Malam Arɗo ne ya gyara zamansa tare da faɗin.
“Ai wannan Zamani da Allah ya kawo mu sai dai Ubangiji ya rufa mana asiri amma an maida satan al'ummar kamar satan ƴaƴan awaki”.
Ido Ori ya zuba masa tare da sakin Ajiyar zuciya.
Malam Arɗo yace.
“Kisan rai kuma ba adaukesa abakin komai ba, ran mutum ya dawo kamar ran kishiya, baki ɗaya duniyar nan ta canza ta burkice ta koma abin tsoro, in ba haka ba kamar Malam Jameelu asace sa bashi babu labarinsa”.
Alhj Musa da Alhj Ibrahim kuwa kai suka jinjina da faɗin.
“Sosai kuwa yanzu idan kana da dukiya hankalin ka ba akwance ba, haka zalika idan kana talaka ma baka da nutsuwa, sai dai Allah ya kawo mana ɗauki amma baki ɗaya jama'ar duniyar ta canza, yanzu ma idan muka fita daga nan zamuje wajen Alhj Bashir ɗin muyi masa jaje”.
Malam Arɗo ya gyaɗa kai tare da cewa.
“Muma yanzu daga can muka fito”.
Jinjina kai Alhji Musa yayi da faɗin.
“Allah sarki Jameelu yaro mai mutunci da karamci, ga sanin darajar manya Ubangiji ya bayyana shi”.

Gyara zama Ori yayi tare da fuskantar Lamiɗo cikin rashin ingantaccen hausarsu yace.
“Hmmm Lamiɗo wato ai wannan duniyar ta zama abin tsoro kwanan nan abinda na gani acikin dajin mu, saman dutsen Membilla aƙasan wata bishiya har zuwa yau hankalina bai gama dawowa jikinaba har zuwa yanzu wanda yasan ni da ya ganni ayanzu yasan ban gama dawowa cikin hayyacinaba”.

Atare Moddibo da sauran jama'ar dake falon suka juya suka kallesa kusan a tare sukace.
“Me ka gani?”.
Girgiza kai yayi da faɗin.
“Kai tashin hankalin fa ya tsananta, muda muke daji ai munfi ku ganin tashin hankali, ku ai kuna cikin gari ba abinda kuke gani sai dai in an ɗauke muku mutum kuke ganin tashin hankali”.
Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya tsinke da masifar ƙarfi yana bada sautin dib-dib-dib cikin sauri ya sanya tafin hannunsa na dama ya dafe saitin ƙahon zuciyarsa kana ya runtse Idanunsa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ya hau kyarma wani zufa mai ɗumi ya keto Masa daga tsakiyar kansa cikin raunin murya yace.
“Amma meyafaru meka gani bawan Allah!”.
Girgiza kai Buba yayi da faɗin.
“Abinfa ba daɗin gani, domin ya wuce tunanin mutum”.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin.
“Toh Allah ya rufa mana asiri amma baki ɗaya zamani ya zama abin tsoro, to amma Ori mai kagani acikin dajin da har ya gigita ka haka, bayan ku Fulani daji kun saba ganin abubuwa!”.
Cikin sauri Ori ya girgiza kai da faɗin.
“Kai gane ganen da muka saba ba irin wannan bane! Duk abinda muke gani na yau da kullum lamuran iska ko halittun dajine”.
Alhj Musa dake fuskantarsane yace.
“To amma meka gani haka?
Ya kamata idan kunga abu irin wannan na tsoro Ku riƙa faɗa acikin gari wurin jami'an tsaro”.

Girgiza kai Ori yayi cikin sanyin murya yace.
“Uhm muna tsoro ai”.
Lamiɗo ne ya sauƙe Ajiyar zuciya da faɗin.
“To amma meka gani?”.
Gyara zama yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.
“Abinda nagani abin tsoro ne, to amma dai banga amfanin ɓoye muku ba, yau tsawon kwana bakwai kenan ina kiwon shanu na akan Dutsen Membilla”.
Duk ido suka zuba masa tare da maida nutsuwarsu kansa suna saurarensa.
Gyara zama Ori yayi kana ya cigaba da cewa.
“Ina nufar kan dutsen sabida ɗebo kanya, naji wani irin wari mai gigitarwa da fitar da hayyacin ɗan Adam Atake tsoro ya kamani na rasa wani irin wari ne wanan.
Saboda ban taɓa jin wari makamancin wannan ba!”.
Cikin sauri Lamiɗo ya kallesa da faɗin.
“To wannan wani irin wari ne!?”.
Ajiyar zuciya ya sauke da faɗin.
“Hmmm Lamiɗo nima kaina na gigice.
Saboda ban taɓa jin makamancin wari irin wannan ba a duniya!”.
Alhj Ibrahim ya fesar da numfashi kana yace.
“To amma me kagani awajen haka?”.
Girgiza kai yayi da alamun damuwa atare dashi yace.
“Ban taɓa ganin abinda ya tayar min da hankali ya kiɗimani ba irin wannan domin ina jin warin na haura na nufi wajen agindin wata Bishiyar kanya”.
Cikin zaƙuwa da gajiyawa za tsinkewar zuciya Modibbo yace.
“Uhmmm!!”.
Shi kuwa Ori runtse Idanunsa cike da damuwa ya cigaba da cewa.
“Ina haurawa kan dutsen. Naga gawa ɗaure a jikin bishiyar, da igiyoyi tako ina.
Wanda da alamu abin ya kwana biyu domin tuni mutumin ya rasu gawace aɗaure, bisa ga duk kan alamu tunda ransa aka dauresa har ya rasu domin har ya kumbura yayi dam sai wani irin sheƙi fuskarsa duk sauran jinka keyi, fuskara ɗauke da murmushi duk da ya rasu, sai kuma alamun kwaranyar hawaye a kan kumatunsa gemunsa da sajensa sai sheƙi sukeyi tamkar wanda kullum ana shafa masa maine kai in ka ganshi kace balarabene wannan warin ne kaɗai ke nuni da gawane, domin a lokacin bai fasheba jikinsa fes”.
Cikin sauri da wani irin azabebben tsinkewar zuciya Moddibo ya runtse Idanunsa tare da taune lips ɗinsa na ƙasa kana yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil”.
Malam Arɗo kuwa cike da tsoro ya kalli Ori kana yace.
“To amma kai Meyesa baka zo ka faɗa acikin gari ba!?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Tsoro nakeji domin Atake awajen na fara sheƙa amai da gudawa saboda warin dana shaka karshe ma agigice na koma gida, domin bana cikin nutsuwa ta kuma tunda na koma saida nayi kwana uku bani da lafiya ko kiwo sai ƙanina ne ya karba, kuma dole muka canza wajen kiwo saboda warin da wannan yankin keyi”.

Cikin sauri da ɓacin rai Lamiɗo yace.
“Haba Ori ya za ayi kuyi haka kuda kuke tare dani ai idan kunga makamancin abu irin wannan, sai ku kirani ku faɗa min idan yaso in tura ƴan sanda su duba ko menene ya za ayi kuyi shiru!?”.

Cikin tsoro da cikekken gaskiya Ori ya sauƙe ajiyan zuciya tare da Girgiza kai kana yace.
“Hmmm ire-iren waɗannan abubuwan gaba ɗaya mu Fulani ma zauna daji ake ɗaurawa alhakin sa, wanda bamusan komai ba banda Bautar Allah da kiwon dabbobin mu, amma baki ɗaya an ɗauki baƙin jini da tsana an ɗaura mana”.
Kallonsa kawai suke zuciyarsu na tsinkewa.
Shi kuwa a hankali ya cigaba da cewa.
“Mutanen gari na cewa Fulani sune ƴan Kidnapping, to idan mun faɗi ire-iren waɗannan abubuwan sai azo ace mu muka aikata ayi ta kamamu, shiyasa mukeyin shiru, kuma nima Aruɗe na koma gida baki ɗaya bana cikin nutsuwa ta shiyasa”.
Cike da damuwa Malam Arɗo yace.
“Allah mai iko kai wannan zamani Allah ya rufa mana asiri”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin jikinsa ke tsuma kana tun lokacin daya runtse Idanunsa har yanzu bai buɗe ba cikin sanyin murya Malam Arɗo yace.
“Amma Moddibo ka shirya muje wajen mu duba gawan waye!”.
Cikin sauri Moddibo ya buɗe Idanunsa dake rintse ya kallesa kana yace.
“Nikam bazan jeba Malam Arɗo me kake nufi kana nufin J ɗina ne?”.
Girgiza kai Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Ba haka nake nufi ba bakaji bahaushe yace idan raƙumin ka ya ɓataba ko cikin ramin allura ka duba ba to muje mu duba mana”.
Jinjina kai Lamiɗo yayi da faɗin.
“Tabbas kam ya kamata aje aduba yanzu kuje ku faɗawa Mahaifinsa Ni kuma zan kira hukumar ƴan sanda sai muje dasu”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da fesar da numfashi mai zafi kana cikin rawan murya yace.
“Nifa bazan jeba dan nasan in Sha Allah ba J ɗina bane, bakuji yace muku gawa bane kuma tuntuni ya mutu har ya kumbura ni kuma J ɗina bai mutuba inaji Ajikina in Sha Allah yana raye”.

Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Moddibo kada kiɗima yasa ka furta kalmar alamar sanin gaibu”.
Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai kana muryarsa na rawa yace.
“Astagafirullah³ amma dai inaji Ajikina kamar J ɗina yana raye”.
Cikin sanyin murya Malam Arɗo yace.
“Eh duk da haka dai muje”.
Girgiza kai yayi tare da cewa.
“Nifa bazan jeba”.
Cikin lallashi Lamiɗo yace.
“A'a Moddibo ka daure dai kuje Allah yasa ba shiɗin bane amma dai aje aduba ɗin”.
Kai Buba ya gyaɗa kana yace.
“Eh suje su duba kuma alokacin ma na samu an ajiye wayoyi agabansa da kuma goran ruwa fuskarsa ma bata wani kumbura ba dan kyanshi bai ɓaceba”.
Atsorace Moddibo ya kallesa zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi yace.
“Harda waya kuma shikenan bari Muje mu gani ɗin?”.
Ya faɗa tare da miƙewa suka fita kai tsaye gidan Abba suka nufa kana malam Arɗo ya masa bayani.
Kallon Abba Moddibo yayi cikin raunin murya yace.
“Abba ni dai inaji Ajikina in Sha Allah ba J ɗinmu bane, amma dai tunda sunce muje to muje ɗin”.
Cikin rarrashi Malam Arɗo yace.
“Alhj kayi haƙuri muje mu gani”.
Cikin sanyi da rauni kana da tsinkewar zuciya Abba ya gyaɗa kai dai-dai lokacin da folisawan suka iso tare da Lamiɗo.

Fita sukayi cikin shirin tafiya Abba, Lamiɗo malam Arɗo da Moddibo suka shiga mota ɗaya Ori kuma ya shiga motar Ƴan sanda suka tafi.

Suna isa dajin bayan sunyi Parking din Motar daga can nesa, suka fara haurawa saman dutsen.
Da sauri suka fara kallon juna sabida jin wani irin ni'imtaccen ƙamshi mai sanyin shaƙa, babu wari kamar yanda ya faɗa musu yasa Moddibo juyawa ya kalli Ori kana cikin sanyi yace.
“Ya gaba ɗaya babu warin da kace sai ma wani irin amintaccen ƙamshi”.
Kallonsa Ori yayi da faɗin.
“Toh yaufa kusan kwana takwas kenan da labarin dana baku ai dole wari ya baje dan zuwa yanzu Nasan gawar ya fashe bare kuma ruwan sama da ake ai dole zai za gonye sai dai kuma nima nayi mamakin wannan ƙamshi!”.
Cikin sanyi Malam Arɗo yace.
“Allah mai iko wannan wani irin ni'imtaccen ƙamshi ne a tsakiyar daji”.
Abba kuwa kasa furta komai yayi sai zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi yana jin wani irin masifaffen tsinkewar zuciya haka zalika Moddibo suna masu shaƙar ƙamshi.
Lamiɗo da polices din kuma sai lumshe idanu suke sabida daɗin ƙamshin da Ubangijin talikai ya wadata wurin dashi.
Yayinda suna kara haurawa suna ƙara jin ƙamshin.
Cikin tsanananin fargaba da tsinkewar zuciya suka cigaba da haurawa wajen suna gama haurawa Ori yayi saurin cewa.
“Yawwa ga can bishiyar”.
Da sauri Moddibo ya ɗaga Idanunsa tare da kallon jikin Bishiyar ganin gawa ɗaure ajikin Bishiya yayi har ya zagwanye idanunsa sun rarake sai ramuka kaɗai sai kuma maiƙo dake zube aƙasa da wani irin sassayan ƙamshin dake tashi a wurin.
Cikin tsanananin tsinkewar zuciya ya sauƙe idanunsa akasa dai-dai kan ƙafar gawar dake maƙale da takalmin cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da dafe ƙahon zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi.
Abba kuwa da sauri ya ƙarasa jikin Bishiyar dai-dai Inda goran faron ke ajiye Idanunsa suka sauƙa akan wayoyin dake wajen hannunsa na rawa ya ɗago wayar tare da jujjuyawa.
Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!”.
Juyawa yayi tare da kallon Moddibo cikin raunin murya yace.
“Aliyu wayoyin Jameelu na neeeee”.
Cikin sauri Moddibo ya juya tare da dafe saitin ƙohon zuciyarsa cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali yace.
“Abba wayar J kuma”.
Kai Abba ya gyaɗa yayin da wasu irin hawaye masu masifar zafi ke koro juna subabin kuncinsa murya na rawa yace.
“Eh”, Ahankali Moddibo ya juya ta gefen da gawar ke daure tare da tsaida idanunsa akan hannun gawar na dama da har ya bushe idanunsa ya zubawa zoben dake hannu gawar.
Cikin tsanananin kaɗuwa da wani masifaffen tsinkewar zuciya mai cike da ɗimuwa da tashin hankali Moddibo yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Abba kalli zobunnan hannunsa zobunnan hannun J ɗina ne da agogon”.
Ya ida maganar tare da yanke jiki ya faɗi babu numfashi atare dashi....!


Wannan littafin dai na kuɗi ne.





By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:42 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace.
“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.
Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.
Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.
Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.
“Uhmmm Jameelu na ne”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa.
“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”.
Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace.
“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.
_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.

Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.
“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.
Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba.
Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.
Kai Buba ya gyaɗa.
Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.
“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.
Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.

Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.
Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.
Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.
Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.
“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.
Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.
Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida.
Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.
Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.

Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.
Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.
Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.
“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.
Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace.
“Gawar Jameelu na ne!”.
Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.
“Gawar Jameelu kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.
Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.
Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.
Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.
“Shine”.
Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka.

Acan Asibiti kuwa ana kai Moddibo likitoci suka shiga bashi temakon Gaggawa saidai koda wasa bai farfaɗo ba ganin haka yasa suka dauƙo wani na'ura mai kama da Iron akafara danna masa aƙirji.
Amman ina babu alamun zai motsa, sosai likitocin suka dugufa wurin ganin sun cetoshi, a karo na biyu suka kuma danna mishi a ƙirjunshi, amman ina, Dr Lukman ne ya karɓi aikin tare da goggoga jikin na'urar ya manna masa a kirjinsa da ƙarfi.
Cikin ikon Allah yaja wani dogon numfashin sake dannawa yayi da karfi wani irin maraitaccen numfashi ya sake ja amma still bai farfaɗo ba sake dannawa sukayi akaro na biyar ne yaja wani dogon numfashi tare da buɗe idanunsa kana yace.
“Jyyyyyyy”.
Malam Arɗo da bai daɗe da dawowa daga gidan Abba bane, yayi saurin riƙe hannunsa tare da cewa.
“Moddibo kayi addu'a”.
Duk da cewa baya Cikin nutsuwarsa hakan bai hanashi maimaita duk wata addu'a

1 Comments On SAKAYYAH
avatar
fatima-8-5-3

1 month ago

Reply

Allah ya qara basira

Please Login or Register in order to submit comment