Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels

MACIJINE SHI🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 1

Bismillahir rahmanir rahim,Ina godiya ga Allah daya bani damar fara wannan littafi ,bayan kammala littafin soyayyata.Allah kasa yadda na fara lafiya naga bayansa lafiya ameen.

Gargadi banyarda wani ko wata ya juyamin wannnan littafi ta kowace sigar ba.

_______________Wata kyakkyawar yarinya na hango sanye da kaya irin na Fulani ,wato rigar saki dakuma zaninta,duka duka rigar da kadan ta wuce cibiyar ta,saidai kuma ta daura zanin ya rufe mata cikinta ta yadda ba wanda zai ga jikinta awaje.

Farace irin mai sirkin yallow -yellow din nan,tana da doguwar fuska mai kyan tsari dauke da dogon siririn hanci har baka,bakinta dan karami kamar gidan tsutsa,tana da irin manyan idanunnan masu kamar tana jin barci,ga gashin ido zara -zara.
Girarta kuwa ,kamar wacce aka dora Mata ita dan saiti,gaban goshinta wasu yan kananan gashine kwance lub lub kamar na jarirai.
Masha Allah yarinyar ta ko ina ta hadu ,dan doguwace marar jiki saidai fa Allah ya hore mata hips Kai kace wata babbar macece Sannan akwai alamun girma akirjinta , ma'ana dai akwai dukiyar Fulani dasuka fara tasawa akirjin nata.

Duka duka wannan yarinyar bata wuce shekara 15/16 ba ,amma kallo daya zaka yi mata kasan Allah yayi halitta agurin.

Sandace irin ta Fulani ahannunta tana dagawa sama ,da alama tana son hada kan wasu tarin sha'nun dake kiwone wani kayataccen jeji ,dan kuwa ciyawace agurin Kore sharr da ita ,sha'nun suna ta cin abarsu .

Tafiya ta farayi gurin shanun dake dan nesa da ita ,dan ita tana daga jikin wata bishiya ne tana kallon yadda suke kiwo abinsu.

Kanta ta daga ta kalli yadda garin ke hada wani irin hadari baki kirin dashi ,kuma da alama koda yaushe ruwa na iya saukowa.
"Kuzo mu tai gida abokaina kada ruwan nan ya sauko ya taba mu banin son nai mura aradu"
Cikin Yaren fulatanci take musu magana ,tana daga sandarta .aikuwa kamar wanda suke jin me take fadi suka fara yin hanyar gida .
Murmushi tayi tana mai binsu tana kara daga sandarta .

Tafiya suke cikin jajen ita kadai daga ita sai wadannan garken shanun ,sam ba alamun tsoro tattare da ita,yar wakar tama take tana daga sandar sama.

Kusan tafiyar minti biyar sukayi ,sannan na fara hango bukkokinsu dake can gaba kadan .
AHankali naga duk wani annurin dake kan fuskar yarinyar ya dauke ,nan da nan damuwa ta maye gurbin nishadi da take ,sosai naga jikinta yayi sanyi har suka karasa wata bukka dake farkon rigar da alama nan ne gidansu.

Garken shanun ta fara zuwa ta daure su tsaf sannan ta nufi cikin gidan,bakinta dauke da sallama.
Lokacin har anfara yayyafi .

Ba kowa a tsakar gidan nasu ,hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da nufar wata bukka cikin sauri.
Saidai kafin ta karasa kofar bukkar aka daka mata wata uwar tsakar da saida sandar hannunta ta fadi kasa.

Afirgice ta juyi jikinta na rawa sosai kamar dan mazari.da sauri ta karaso gurin matar data daka mata tsawar,
"Gani gwagwgo"ta fada cikin rawar murya. Kallon matar nayi sai na tarar da
matar farace saidai kuma kazanta da rashin kulawa yasa tayi wani irin baki baki fari fari,sannan tana da jiki sosai sam fuskar ta ba alamun rahama a cikinta.
Tana tsaye a kofar bukkar ta tana hararar yarinyar dake durkushe gabanta.
Cikin masifa da bala'i matar ta fara magana da hausarta marar kyau.

"Da kake kokarin shigewa dakin,ubankane zai debi ruwan?
Ko kin ajiye bawanki ne a gidan?matar ta fada cikin zaro ido.
Kan yarinyar akasa jikinta na rawa ta fara magana
"Allah hukkumu hakuri gwagwgo naga ruwa na don sauka ne shiyasa ban deboba"ta fada cikin rawar murya da tsoro.

Wani wawan mari matar ta kai mata cikin rashin imani da tausayi cewar yanzu ta dawo daga kiwo kuma ko abinci bata ci amma take kokarin sake turata rafi.

"Shegen yaro mai bakin hali wllh yanzu koke kidobo min ruwan nan dan ubanki karuwa kawai"matar ta fada tana mai hankade yarinyar .

Faduwa tayi sosai hannunta ya bugu da wani dutse dake ajiye tsakar gidan da alama na zama ne.

Kara ta saka cikin azaba tana mai dafe hannunta dake mata wata irin azabtar zafi.
"Wayyo handi ɗin boni lalashewa gwagwgo hannu na ta ɓalle" ya rinyar ta faɗa cikin azaba.

"Shege wllh dama zai karye danafi kowa jin dadi yarinya kamar aljana,ace kinfi kowa kyau arugarnan? Na tsaneka fatto saina bata wannan shegen fuskan baki.maza ki tashi kona shakeki agurin ki mutu kowa ya huta" cewar matar cikin bala'i da tsantsar nuna tsana ga dattin.

Cikin hanzarin ta mike ta zari wani boket din roba ta fice tana kuka sosai.

Tafiya mai nisa tayi kafin tazo rafin, har zuwa lokacin kuka take hannunta sai zogi yake mata, ruwan ta debo cike da sauri dan kuwa ruwan da ake ya fara karfi.

Saidai me ?tana juyawa tayi arba da wani murtukeken maciji katon gaske ya fasa kai yana huci.

Wani irin mugun tsorone ya kamata nan da nan jikinta ya kama rawa har batasan lokacin da boket ɗin ya fadi kasa ya fashe ba.

Tashin hankali kenan wanda ba'a sa masa rana ,iyakar rushewa da tashin hankali yarinyar nan ta shiga.
Hannu ta ɗora aka tana mai kara ƙarfin kukanta.

"Wayyo ni fattu bukar na mutu na lalashe ya zanyi da rayuwata nashi zai karni wayyo baffana wayyo Allah ,taimaka min"
Ta faɗa tana kallon boket ɗin dake tarwatsa,dama kuma rana ta gama cin ubansa.
Shi kuwa macijin nan ganin yadda ta tsaya tana kallon sa kuma tana kallon fasashshen boket ɗin ta ,sai taga kamar neman makami take ,dan haka afusace yayi kanta

Ihu ta kwalla mai karfin gaske tare da zubewa agurin sumammiya dan ganin yadda macijin nan yayi kanta baki bude.

Masu karatu ya kukaji?
Meye ra'ayinku akan wannan Nobel ɗin?
Ina bukatar comment dinku idan buk din nan yayi muku dadi muci gaba.

Takuce har kullum anty mammy

Msr babi💘💘

Comments
AndShare
Fisabilillah.
[7/19, 10:10 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJINE SHI🪱🪱🪱
Page 2

https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

_______________Ihu ta kwalla mai ƙarfin gaske ,tare da zubewa agurin sumammiya,dan ganin yadda macijin nan yayo kanta baki buɗe .

Hakan ba ƙaramin tsorata ta yayi ba .
Dai dai lokacin ne kuma wani katon macijin ya nufo wannan macijin da gudun gaske ,yana zuwa ya sarkeshi suka fara kaiwa juna sara .hakan shi ya hana wannan katon macijin ya sami damar karasawa inda fattun ke kwance asume.

Sosai macizan nan ke kaiwa junansu sara suna murdewa cikin jikin juna.ko wanne na ƙoƙarin illata dan uwansa.

Ahankali fattu ta fara bude idanunta da sukayi mata mugun nauyi tana kuma lumshesu,hannunta ta daga da nufin dafe kan nata,saidai wani azababben zafi da radadin ga wani irin zugi dataji hannun yana mata ,shine ya sanyata sanya kara tare da fashewa da kuka."washhhh hannuna wayyo kaina"ta fada cikin kukan tana mai dafe kan da dayan hannun marar ciwon.
Sai kuma ta zabura cikin azama ta zauna tana mai zare idanu da rarraba su,sakamakon tunowa da katon macijin da yayo kanta dazu.saidai kuma can ta hangi macizan biyu suna ta artabu,gaba daya sun jima kansu ciwo jini yana ta zuba akikkunansu,amma sunki daina fadan.

Tsoro ,fargaba ,tashin hankali da rudewa suka saka fattu kurma wani uban ihu tare da yunkurawa ta felle da mugun gudu tana ihu cikin rudewa dan ganin macizan sun zama biyu wato har fada suke akan waye zai cinyeta.

Duk da irin ruwan da ake zugawa mai ƙarfi ga iska ,haka tayi ta cin uban gudu ko gabanta bata gani.ikon Allah ne kawai ya kawota gidansu lafiya.
Kai tsaye ta danna cikin gidan da gudu ta shige dan dakin dayake amatsayin nata,cikin rawar jiki ta janyo wasu karare dogaye guda hudu ta kara a kofar,dan sune
Matsayin murfin kofar tata.

Dakin ba komai sai wata yar yaloluwar taburma ,wacce kallo daya zaka mata kasan cewa taga duniya,dan gaba daya ta ciccinye kuma tayi lakwam da ita.sai wani zani dake gefe daure ,da alama kayanta ne acikin.
Tana tsaye atsakar dakin ,har lokacin jikin ta rawa yake ,ga ruwa sai zuba yake ajikinta yararara!!!
Kallo daya zaka mata kasancewa afirgice take sai kif-kifta ido take tana kallon kofa,gani take kamar macizan nan zasu biyota.tayi kusan minti biyar acikin wannan halin ,kafin ta fara cire kayan jiki ta dake yararin ruwa."masha Allah nace,sakamakon ganin wani uban dogon bakin gashi mai santsi akanta,lokacin da take zame dan kwalin dake kanta .an raba kan biyu an daure ko wanne bangare sai kuma aka nannade ko wanne abarinsa kamar gammo.hakan da akayi shine ya hana mu ganin gashin nata tun farko.

Daurarren zanin nan ta kwance ta dauko wani zanin irin wanda ta cire da rigarsa ,saidai kayan fa sun sha jiki sosai ,sun kode sun jeme sunyi wani fari,sai wata hula baka irin ta sanyin nan ta dauko ta ajiye kusa da kayan ,sannan ta mike tsaye ta cire rigarta ta ajiye ta gefen ta barmar ahankali ta warware tsangalallen zanin shima ta ajiye gefe,ya zama daga ita sai wani kodadden pant Wanda kana gani kasan shima yaga rayuwa.kallonta nayi tun daga sama har kasa kawai nace Masha Allah.dan sura kam Allah ya halicce ta agurin fattu jikintahar wani sheki yake kamar yar masu kudi wacce ke rayuwa cikin jin dadi.

Haka ta dauki kayan ta saka ajikinta tanayi tana kuka abin kwanon ban tausayi.
Bayan ta kammala sanya kayan ne kuma saita dauki wanda ta cire ta matse sannan ta makalasu ajikin karan dake jingine akofar dakinta.

Zama tayi akan yar tabarmarta ta dukunkune jikinta tana kuka.abubuwa dayawa ke dakinta ahalin yanzu,na farko tsantsar tsoron macizan data gani dan bata taba ganin irin wadannan macizan ba,dan dayan kam jikinsa mai matukar shekine da kyau,sai kuma hannunta dake mata azabar ciwo uwa uba kuma yunwa,rabonta da abinci tun safe data sha nono har kawo yanzu da magrib ta sanyin kai ba abinda taci.
Sosai take tausayi rayuwarta, tabbas rashin uwa babbar gibine arayuwa,yanzu da innarta na kusa da ita data rungumeta ta fada mata damuwarta,amma rashin dace ta daya shine sam batasan koda fuskar innarta ba ,bata sani Bama kotana raye koya mutu Allah shine masani.
Tana cikin wannan halin taji an ture kararan data rufe dakinta dashi.
Azabure ta mike tsaye tana shirin sanya ihu.

"Ke fattu nutsu mana nine fa ,nine baffanki"wani dattijo ne fari mai dan tsayi yake maganar,yana sanye da riga da wando na wani yadi mai arha sai takalmin sau ciki na roba,da hula irin mai malafar nan.ya shigo cikin dakin da wani kwano hannunsa.

Ajiyar zuciya ta sauke sakamakon ganin baffan nata ,da sauri ta karasa kusa dashi tace "baffan usee wollahi na tsorata ne"ta fada idonta akan kwanon dake hannunsa.

Murmushi yayi yace "hoo fattu akwai tsoro,sannu maza karbi wannan tuwon ka shinye nasan kanajin yunwa,kayi sauri kar hansai ta gani"yana fadin haka ya mika mata kwanon yayi saurin fita,dan kar matar tasa ta fito ta ganshi ya shiga uku.

Cikin sauri _sauri fattu ke cin tuwon nan kamar zata kware, tas kuwa ta cinye ta side kwanan, da sanda tafice tsakar gidan ta wanke kwanon ta ajiye akicin sannan ta sha ruwa tayi alwala ta koma daki.
Sallar la'asar tayi da magrib dan tuni an kira.
Har zuwa lokacin ruwa ake saidai bai kai ƙarfin na farko ba.tana zaune cikin zullumin matakin da gwogwgo zata dauka akanta ,na fasa mata boket har akayi ishsha tayi salla sannan ta kwanta tana mai karanta addu'a ,nan da nan barci yayi gaba da ita,har baffanta ya shigo ya duba ta yaga tayi barci addu'a yayi mata cikin tausaya wa halin kuncin da take ciki kafin yayi saurin fita.

Gwagwgo kuwa tana daki ita da yaranta suna ta hira suna cin gyada ,ba ruwansu da wane halin fattu ke ciki,shin ta dawo gidanma ko yaya taci abinci ko bata ciba?sam ba wanda ya damu ,kuma ba wanda yayi Sallah a cikinsu.

Can cikin dare fattu na barcinta damuwa da tsoro dan kuwa mafarkin macijin nan take ,saidai kuma ba na farkon bane yazo mata yanzu wannan mai kyakyakywan jikin ne,saidai gaba daya jikinsa jini yake zubarwa,ga wani irin hayaki da tururi dake fita ajikinsa, sai burkima yake yana wani irin kuka da wata murya mai amon sauti,kuma yana nufota da ƙoƙarin hawa jikinta .

Wani razanannen ihu ta kwalla tare da mikewa zaune afirgice ,tana mai waige waige,ba abinda take iya gani saboda duhun dakin ,hakan yasa tayi saurin komawa ta kwanta tare da karanta addu'a kala_kala,hannu ta mika dan janyo zaninta ta rufe jikinta dashi ,saidai kuma hannun nata taji ya sauka akan wani abu mai dan karen sanyi da santsi.
Cikin tsoro take shafa abun dan jin ko menene,tabbas MACIJINE dan kuwa ta tabo har kansa ....

Masu karatu badai macijin ne ya biyo fattu da gaske ba?

Wane hali fattu zata shiga ?

Muje zuwa yaki ce dai anty mammy

Mrs babi💘💘💘

Share and comment fisabilillah.

More comment
More typing.
[7/19, 10:10 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJINE SHI🪱🪱🪱

Na manya kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 5/6

https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share

________________Hawa macijin nan yayi kan ruwan cikin fattu ,daidai kan fuskarta ya tsaya tare da fasa kansa ,ya tsaya ƙuri yana kallon fuskar Tata, wacce tuni idanun fattu ke rufe tayi mutuwar kwance ko nunfashi ta kasa shaƙa cikin salama.

Shikuwa macijin nan ganin bata koda motsi saiya sauƙo daga ruwan cikinta ya tsaya saitin fuskar tata tare da fasa kansa yana huci ,.matsowa yayi sosai jikin fuskar tata yana hura mata iska daga bakinsa,sannan ya ɗan ja da baya ya tsaya yana kallon ta.

Ahankali fattu ta ɗan buɗe idanunta dan ganin shin me kuma macijin nan ke shiryawa ?ta yaya yake tsara kasheta itama,saidai tana buɗe idanta suka sauka akan na macijin nan ya ƙureta da idanunsa.

Cike da tsoro da fargaba fattu ta kafe shi da nata idanun,dan tsintar kanta tayi da kasa daina kallonsa,abubuwan mamaki take gani tare da macijin,sam kwayar idanunsa ba irin ta macizai bace,sak!irin ta mutane ce saidai gurin farin yayi wani irin kala kala , blue yellow pink ,Amma asalin kwayar baƙace ƙirin.
Sai kuma taga hawaye na zubowa daga idanun macijin kamar mutum yana kuka.

"Innalillahi wa'inna ilahirin raji'un, Allahumma ajirni fi musibati waaklifni kairan minha,la'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin"shine abinda fattu ta fara karantawa cikin zuciyarta jikinta na wani irin tsuma da karkarwa, tunda take bata taɓa ganin irin wannan macijin ba sai yau,ya maciji zai kasance da idanun mutane? sannan kuma jikinsa akwai banbanci sosai dana macizai,dan shi yana da wani irin jiki mai ban mamaki yadda kalar idanunsa ta kasance haka shima jikinsa yake .sannan kuma bai kai girma irin na macijin jiyan nan ba amma yana da girma shima sosai,kuma dogone na gaske.

Kallon kallo kawai ake tsakanin fattu da macijin nan,inda ahankali ya fara hucewa daga kumbura da fasa kan da yayi ,fattu na kallonsu harya koma normal jikinsa ya daidaita ,sannan ya fara ƙoƙarin barin ɗakin ta wata yar hanya dake jikin katangar karan ,wacce ita fattu sam bama tasan da ita ba sai yau,da alama dai shi yayiwa kansa hanyar.
Saida yaje gab da hanyar tasa saikuma ya juyo da kansa yana kallon fattun,shi bai tafiya ba kuma bai dawo ciki ba.

Sosai jikin fattu ke rawa tana zubda hawaye ,dan yau kam lamarin ya kulle mata kai ,wai wannan wane irin MACIJINE ?shin macijin ne ma kokuma wata halittar?sannan maiyasa yaƙi yi mata komai,sai dai ƙoƙarin ceto ta da yake atsammaninsa na ko bata numfashi?haƙiƙa akwai abin dubawa dan gane da wannan macijin.

"Fattu ! fattu!!kin tashine kinyi sallar lokaci yana ja fa"ta tsinkayo Muryar baffa daga wajen ɗakin yana mata magana .
Jin muryar baffa da fattu tayi sai hankalinta ya ɗan kwanta cikin ɗaga murya tace "baffa kazo ka taimaka min gwogwgo bata motsi"ta faɗa cikin Muryar kuka tana kallon macijin.

Cikin sauri da azama baffa ya shigo ɗakin yana faɗin"subhanallah me kuma ya sami Hansai din?
Cikin kuka fattu ta kalli baffa sannan ta kalli inda macijin nan yake ,har lokacin yana tsaye yana kallon ta,
"Baffa bansani ba kawai ta shigo tana dukana sainaga ta faɗi ƙasa"abinda fattu ta tsinci kanta kenan da faɗa murya na rawa.

Ahankali macijin nan ya juyar da kansa ya bi ta yar ƙofar nan ya fice.
Sai lokacin hankali fattu da nutsuwarta suka dawo jikinta ,cikin ƙarfin hali ta yunƙura ta tashi zaune ,har lokacin akwai alamun tsoro da firgici akan fuskarta,dan jikinta sai rawa yake.
"Washhhh hannuna"ta faɗa ahankali tana mai runtse ido,dan sosai hannun ke mata mugun ciwo.

Ruwa baffa ya ɗebo mai sanyi wanda ya taru na sama,yana zuwa ya kwarawa gwogwgo ruwan cikin moɗa .aikuwa azabure ta tashi zaune tana ihu"wayyo Allah na maciji zai kasheni malam kawo ɗauki ,fattu tayiminn turen maciji,wayyo wuyana ,wayyo hannuna na shiga uku na lalace"abinda gwogwgo hansai ta farka dashi kenan,maimakon ambaton sunan Allah .

"Kayya hansai ki nutsu ba wani maciji ana fa nine bukar wannan kuma fattu ce ɗiyarki"cewar baffa kenan a ƙoƙarin sa na kwantar mata da hankali.buɗe ido gwogwgo tayi sosai ta kallesu kafin tace "kuturin bala'i Allah ya kiyaye wannan sheɗaniyar ta zama ƴata mayyace fa,wllh ture tayimin yanzun na wani maciji ya kusan hallakani,wllh sainaga bayan yarinyar nan Shegiya may.......wayyo Allah na ya dawo ya dawo"gwogwgo hansai ta faɗa sakamakon hango kan macijin nan da tayi ,ai da gudun gaske ta fice daga ɗakin tana ihu .

Girgiza kai baffa yayi yana Allah wadai da halin matar tasa ,sam baiyi dacen mata ba.kallon Fattu yayi wacce take riƙe da hannunta mai ciwon, hawaye na zuba a idanunta na azaba.

"Ashsha ashsha fattu kiyi haƙuri kinji,komai yayi farko zaiyo ƙarshe ,Allah yana sane da halin da kike ciki in sha Allahu zakiyi dariya anan gaba"baffa ya faɗa cikin sanyin murya da ƙoƙarin kwantar mata da hankali.

Ahankali ta sanya hannu ta share hawaye idanunta ,kafin tace "baffa hannu na ciwo yake min"ta faɗa tana nuna masa hannun dayake mata ciwon.

Kallon hannun yayi yanda ya kumbura yayi suntum dashi ,cikin tausaya wa yace "ayya faɗimatu sannu. Kinji maza daure kiyi sallah saina duba miki hannu kiyi haƙuri, Allah yayi miji albarka"ya faɗa yana mai taimaka mata ta miki tsaye.

"Ameen baffa "ta faɗa tana ficewa daga ɗakin .bayi ta shiga ta kama ruwa sannan tayi alwala cikin dabara kafin ta fito ta koma ɗakin ,Sallah tayi tare da karatun alƙur'ani mai girma ,da ka take karatun dan da ahaka aka koya mata ,bayan ta idar ne baffa ya shigo ɗakin ɗauke da kwarya ahannunsa ,

" Sannu fattu karɓi wannan madarar Kisha kinji,saina duba miki hannun"baffa ya faɗa yana miƙa mata kwaryar.karɓa tayi ahankali tayi Bismillah ta kafa kanta,saida ta shanye kafin ta ajiye kwaryar .

Allah Sarki fattu tasha wahala sosai lokacin da baffa ke gyara mata hannun ,dan yayi tsami sosai ,kuka harda majina,haka baffa ya gyara mata yana mata sannu.bayan ya gama gyara mata ne yace ta kwanta ta huta kafin garin ya gama wayewa.haka ta kwanta tana ajiyar zuciya ,ba jimawa kuwa barci yayi gaba da ita ,abinka da wanda bai sami barci ba dama.
Ficewa baffa yayi daga ɗakin ya nufi nashi cike da tausayin ƴar tashi dayake matuƙar ƙauna.

Ko minti talatin batayi ba tana barcin ta tsinkayo muryar gwogwgo tana kiranta "Ke gantalalliya mayya fito dan ubanki ,ko uwarki ce zata miki aikin?Shegiyar yarinya aljana wllh bakici bulusba yadda kika sa macijin nan ya lagartamin jiki to wllh saina rama ,fito ki ɗebomin ruwa yanzun nan .

Afirgice fattu ta tashi daga barcin ta fito da gudu tazo tana rawar jiki ,Dan bala'in tsoron gwogwgo take kamar ranta."gwogwgo dame zan ɗebo ruwan "ta faɗa kanta asunkuye.

Da ubanki zaki ɗebo ruwan kinji ?kije ki nemomin kuɗin da zaki biyani bokatina inyaso ki ɗebomin ruwan aciki"gwogwgo ta faɗa tana daga ɗaki,dan taƙi fitowa waje kartaje macijin nan ko ajikin fattun yake.

Masu karatu har zuwa wannan lokacin fa yaran gwogwgo hansai suna kwance aɗaki suna barci.
Amma take ƙoƙarin tura fattu ɗiban ruwa da wannan safiya,alhalin bata da lafiya.dan lokacin da baffa ke gyara mata hannun tana jin ihunta.lokacin tana kwance akan gado tana hucin azabar da macijin nan ya gana mata,"Shegiyar yarinya Gara kemaki ɗandana azabar dana sha ,Allah yasa hannun ya karye ma kowa ya huta.

"Dan Allah gwogwgo kiyi haƙuri wllh bansan inda zan samo kuɗin ba kiyimin rai "fattu ta faɗa cikin kuka.

"Dan kan ubanki tashi ki ɓacemin da gani,wllh kome zakije kiyi bai dameni ba Indai zaki kawomin murtala uku da raina gomata."ta faɗa tana rarumo wani busasshen kwanon tuwo aɗakin ta cillowa fattu shi.
Allah ne ya kare fattu da tuni kwanon ya sauƙa akanta ,tayi saurin ficewa da gudu daga gidan.
"Shegiya da kin tsaya ai"cewar gwogwgo tana mai kwanciya ba ko sallar safiya.

Koda fattu ta fita daga gidan kuka take sosai ,batasan inda zata nufa ba ,ina zata samo Murtala uku da Naira goma?waye zai bata waɗannan iyayen kuɗin? Kodai gurin jauro zataje tace ya taimaka mata da Murtala uku da Naira goman?kai a'a bazataje ba, dan jauro ba mutumin kirki bane ,ranar nan ma hannunta yake ƙoƙarin kamawa wai yana sonta,kuma baffa yace maiyin hakan ba mutumin kirki bane.

Kusan minti biyar tana saƙa da warwara,kafin ta yanke shawarar kawai ta tafi bakin rafin ta zauna ko Allah zai sa ta sami abun ɗiban ruwan.

Tafiya take ahankali ,wanda kallo ɗaya zaka mata kasan batajin daɗi,hannunta mai ciwon kuwa ta rikeshi da ɗayan hannun.haka ta nufi rafin dake can bayan gari cikin jeji.

"Hai jauro wai kuwa kaga Abinda nake gani"?
Cewar haroji kenan wanda suke zaune akan wata bishiya shida jauro can kusa da rafin da fattu ta nufa.

"Wanda aka kira da jauron ne ya ɗago kanshi dake duƙe yana zuƙar sigari yace "me ka gano mana"?

"Wllh fattu ce kuma ita kaɗai kaganta can ta nufi rafi"ya faɗa cikin ɗoki da zumuɗi.

Da sauri jauro ya kalli gurin da harojin ke nuna masa ,aikuwa fattu ya hango ,cikin hanzari ya fito daga kan bishiyar yace "wayyeee huuhuuu ,yau kam mun fito

Please Login or Register in order to submit comment