Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kin zuwan ta islamiya da ma kin yin sallah. Jikin shi ya yi sanyi,ya tashi da sauri ya nufo bangaran Hajjo,amma me zai gani? Wayam babu Hajjo babu alamar ta,ya bi daki daki na bangaranta,har bandaki ya duba amma shiru,tuni ya rude,hankalin sa ya tashi. Da sauri ko takalmi be iya sawa ba ya fito wajan maigadi ya na tambayar ko ya ga fitowar amaryar sa? Maigadi ya ce kai be gani ba,in ma ta fita watakila sanda ya zaga bawali ta fita din…..
DEDICATED to The Women Of Virtue💁👰🙋(group)
[16/10 21:48] .: :55am, 6/14/2015] Khadija Sidi: 👭👭👭DIYA MACE👭👭👭
6⃣0⃣
A kidime ya koma ciki,takalmin da ya sako ma hadin bauta ne be sani ba,tashin hankalin sa ina Hajjo za ta da yamma likis haka? Ko sallama be yiwa Hauwa ba ya figi motar sa dan bin sawun Hajjo. Ko da ta isa kumurya,idanun ta sun kumbura da kuka,sai tadda Indo ba ta nan sai yara,su ke fada ma ta wai Indo ta na gida dazu aka zo aka ce Baba ya kone. Nan tsakar gida ta saki jakar ta,bayan shekaru da dama sai ga ta ta dau hanyar gidan su,dan idan ba ta ga halin da Baba ya ke ciki ba hankalinta ba zai kwanta ba. Ganin yanda kofar gidan ya kwarabe sai da gaban ta ya fadi,bare da ta shiga gidan,kamar ba nan ne Innar ta ke rayuwa ciki ba da,gidan ya lalace,ya kazance. Muryar Indo ta ji ta na musayan magana da matan su Mudi,Indo na fadin wlh sam ba ku kyau ta ma na ba,amma ba laifin ku ba ne,laifin mazajen ku ne,idan ku be haife ku ba ai su ya haife su. Tare su ka ce eh mun ji din,yo ba shi ya ce a bashi garwashin ba,sai mu hana shi?ace mun yiwa siriki rowa? Muna fama da yara muna fama da tsoho,ai idan ba a gode mana ba ba a zage mu ba. Baba kwance gaba daya hannun sa na dama ya kone,yatsun duk sun durkushe,sai nishi ya ke dan azaba,bakin sa karkace daga alama barin jikin sa ya shanye. Hajjo ta yi sallama jiki sanyaye. Indo ta amsa ta na yauwa Hajjo gwara da Allah ya kawo ki,ji yanda Baba ya sanya hannun shi cikin garwashi ya kone dan Allah! Sai ta sa kuka…Matan Su Mudi su ka rude ganin Hajjo,dake sun santa tin kafin ta auri Garbati,tare su ka yi wasa,amma zaman kauye sun tsufe sun tsomare kamar ba sa’annin Hajjo ba. Su ka fara laha’ila Hajjo,Hajjon ce kuwa! Ko ta kan su ba ta yi ba,ta karasa wajan Baba da tin randa ya ce ta zauna wajan Indo ba ta kara sa shi a ido ba,gaba daya ya tsufe ya tsomare saboda cuta da rashin gata. Gaban shi ta zauna ta na hawaye. Jin ana Hajjo Hajjo! Idanun sa runtse sai yayi sauri ya bude ya na ina Hajjo? Ina diya ta Hajjo,ku hada ni da Hajjo na nemi gafarar ta! Indo ta ce yi magana Hajjo,taba shi ya jiyo ki! Hajjo ta sanya hannun ta cikin na Baba,ta kasa magana sai kuku. Tana kuka Indo na kuka. Su kuwa matan su Ayuba sai abun ya zama mu su na kallo.
Sani Hajjo ta nema,su ka yi sa’a shigowar sa kumurya kenan,ya ce gashi nan tafe. kafin su iso Indo ke ba ta lbryn yanda aka yi Baba ya kone,wai cewa yayi a bashi garwashi zai yi turare,da ke Baban ba lfy gare shi ba,ya na cikin turaren ya yanki jiki ya fadi,sai hannu ya fada garwashi,gashi bangaran jikin sa ya shanye,ba daman ihu,baki ya karkace ko ya yi ihu ba mai ji bare a ka masa dauki,matan ‘ya’yan sa ba sa iya kula da shi,sai da babban dan Mudi ya gifta ta dakin ya ga Baban ya fasa ihu,shi ne fa aka zo aka cire hannun. Mudi da Ayuba sun dawo,sai mita su ke wai laifin Baba ne,shegen rigima na tsoho,ina shi ina turare! Abun mamaki da kudirar ubangiji a nan shine diyoyin matan na sa da ya guja ya ke kyama,ya ke kira da jidali su ke jin kan shi su ke tausayin shi,su kuma ‘ya’yan na sa maza da ya nunawa gata sam ba su damu da shi ba,shi ne ma ya zame mu su jidali su da matan su,sun ma daina kiran sa Baba sai rikitaccan tsoho. Jin yanda su ke wa Baban ran Hajjo ya baci,ta ce da Sani ya sa Baba a mota,su fara tsayawa a gida ta dan wanke konuwar in ya so sai wuce kano. Hakan ko aka yi,gidan Indo a tsakar gida aka yiwa Baba shimfida,Hajjo ta wanke konuwa ta ma sa dressing. Zaune gaban sa ta na ma sa fifita Sani ya ce bara ya samo mai ya kara a mota sai a tafi. Fitar shi ba da dadewa ba sai gashi ya dawo tare da Khalid.
Jin muryar Khalid cikin gidan gaban Hajjo ya fadi,ta tashi da sauri ta shige ciki ba tare da ta ko daga ido ta kalle shi ba bare ma ta ga yanda ya ke a birkice. Daga ciki ita da Hajjo su ke jiwo maganar su,ya na ta jajanta jikin Baba,gashi ganin Hajjon kan sa ya ji dadi kwarai. Sani ne ya kwallawa Indo kira,ta fito su ka gaisa da Khalid,ba dan ta na fama da ciwan Baba ba da babu abunda zai hana ta dariya ganin Khalid ba yanda ta saba ganin sa ba,yau takalmin ma hadin bauta aka sako,lalle kanwar ta ta ruda shi,dake ta ba ta lbryn abun da ya faru. Khalid ya ma ta ya mai jiki,tare da fatan samin lfyar sa. Sani ya ce da Indo ta kawowa Khalid dadduma bara ya je ya karo mai. Khalid ya ce ka bari mana a tafi a tawa motar? Sani ya ce da ke har da su Mudi za a tafi,wajan ba isar mu zai yi ba. Khalid ya ce eh haka ne,toh a dawo lfy.
DEDICATED to The Women Of Virtue💁👰🙋(group)
[7/25, 6:13 PM] Salmah Ateeku: [12:01pm, 6/14/2015] Khadija Sidi: 👭👭👭DIYA MACE👭👭👭
6⃣1⃣
Daga can gefe ya na fuskantar inda Baba ke kwance ya zauna bisa dadduma. Indo ta zauna ita ma daga gefe,su na dan tattaunawa,Khalid ya kawo maganar Hajjo,ya ce wato Yaya ta(sunan da ya ke kiran Indo tin da ya auri Hajjo)na ji dadi kwarai da na ga Hajjo na kula da Baba,da har ina zargin ta da kin kula da lamarin sa da ma lfyar sa,ki ga sanda ya kwanta dinnan ko duba shi kin zuwa ta yi. Indo ta murmusa tare da fadin ai ina ga duk cikin mu babu wanda ke kula da Baba kamar ita,ka ga kwanciyar ta shi da ka ke magana a kai,eh kwanciyar da yayi ba ta je ta duba shi din ba,amma ita ta biya duka kudin asibitin,ina sanda ka zo ka ke tambaya ta wa ya biya kudi ka je biya aka ce an biya? Ai ita din ce ta biya. Khalid ya ruke baki tare da fadin ikon Allah,wani abun sai Hajara,a haka sai ka yi zatan ba ta damu ba! Indo ta ce ai haka take,ba mai gane halayyar Hajjo,ita dai kam wuyar sha’ani gare ta yanda ka san hawainiya haka ta ke rikida. Toh amma duk cikin mu babu wanda Baba ya yiwa ba daidai ba kamar Hajjo. Ta ba shi lbryn Hajjo tsaf,ba ta boye ma sa komai ba,gaba daya jikewa yayi da zufa,idanun sa sun yi jajur kwalla fal ciki,wani irin abu ya ke ji game da Hajjo,tausayi ga kuma abun da ya ke ji na game da ita da shi kan sa ya kasa ganewa. Shiru ya yi,ya ka sa magana dan ya rasa me zai ce yanda ya ke jin kan sa.
Baba ne ya fara tari mai karfi,fitowar Hajjo da gudu da kuma tashin Indo da sauri lokaci guda ne,su ka yi kan sa,Hajjo ta tallafo kan sa hannun ta ruke da hannun sa mai konuwa,ita kuma Indo hannu bisa kirjin sa ta ke dan masa luf luf. Sha’awa su ka bawa Khalid,yanda su ka damu da mahaifin na su da yanda su ke ma sa sai dai diyoyin mata,ga mazan na shi can majalisa suna hirar su,wai suna jira Sani ya zo su tafi. Duk kiyayyar ta shi na diya mace gashi diyoyin na sa mata ne ke ji da shi,su ke ta hidama da shi,gaba daya soyayyar diya mace ta shiga zuciyar Khalid,gaskiya duk wanda be haihu ba abin tausayi ne,haka kuma duk wanda ya haihu din amma be sami diya mace ba toh be gama morewa. Idanun sa bisa Hajjo,sun samu tarin na Baba ya lafa,ta dauko ruwa ta na bashi da cokali saboda yanda bakin yayi. Hasken farin wata da na fitilar tsakar gidan ya haske fuskar ta,sai ta kara kyau da annuri,ji ya ke kamar ya tashi ya je yayi hugn din ta,kamar ya ruke ta gam ta shige har tsokar sa,kamar ya yi kissing din ta fiye da wanda yayi rannan…kamar kamar kamar…God i love dis woman! Abunda ya fada cikin ransa kenan ba tare da ya san ya fada ba a lokaci guda kuma ya ankare,ya fara tunanin so yace? Yes so ne,ya na san Hajara,ya kuma dade da fara san ta,soyayya da sabon da yayi da Hauwa ya sa ya kasa ganewa! Shi kadai ya ke murmushi idanun sa kan Hajjo,ta kwantar da Baba za ta koma ciki Indo ta ce kin ko gaisa da mijin ki? Wani irin kallo a marairaice na nuna rashin jin dadin maganar Indon ta yi ma ta. Shi kuwa Khalid cewa ya yi bar ta ta huta Yaya ta,ma gaisa anjima. Da amsar ta sa ta yi shigewar ta ta ciki. Sani ya dawo aka shirya tsaf aka sa Baba cikin motar Sani,Mudi ya zauna da shi a baya kan Baba bisa cinyar sa,Hajjo ta yi saurin shiga gaba. Khalid ya ce ta sauko a tashi za su tafi,ta ce wlh ba za ta shiga ta sa ba,aka yi aka yi ta fito ta bawa Indo wuri ta ki,da dai suka ga su ka biye ta Hajjo bata ma su lokaci za ta yi,sai aka hakura,Indon ta shiga bayan motar Khalid,Ayuba a gaba,Khalid sai kwafa ya ke bini bini. Su ka dau hanyar kano.
Sai wajan goman dare su ka isa kano. Asibitin nasarawa su ka kai Baba da ke AKTH suna yajin aikin,ita ko Hajjo haka daidai ya ma ta,ga ta ga Baba ta fi kula da shi. Aka ba su daki V.I.P.,da ke baban Doc Hajara ne har riga rigan duba shi da kula da shi doctors din su ke,hakan ya burge Indo,cewa ta ke hmmmm ilimi dadi,kai ilimi yayi. Su kuwa Mudi da Ayuba sai kallo,wai Hajjo ce ke da matsayi haka har mutane ke dawainiya da Baba dan darajar ta? Shi ko gogan na Hajjo wato Khalid cikin takama ya ke jin kan sa,yes shine fa mijin Doc Hajarar nan,gwara kowa ya sani,kamar cingum ya like ma ta,ko ina ta yi biye da ita ya ke. .
DEDICATED to The Women Of Virtue💁👰🙋(group)
[12
[16/10 21:48] .: 13pm, 6/14/2015] Khadija Sidi: 👭👭👭DIYA MACE👭👭👭
6⃣2⃣
Kan kace mai har an duba Baba an daura shi kan medication. Sai fa rigimar kwana ta tashi tsakanin Indo da Hajjo,Indo ta ce Hajjo ta bi mijin ta ta tafi gida ita za ta kwana da Baba,Hajjo ta ce ba inda za ta sai dai Indo ta tafi,Mudi da Sani su ka sa baki,a dole su ka ce Hajjo ta tafi ta bar Indo tinda ita ce babba. Shi dai Khalid ya na gefe be tanka ba,amma har ga Allah ba zai so Hajjon ta kwana ba,zai fi so ya tafi da matar sa. Shi kuwa Ayuba cewa yayi toh kai Mudi kai za ka kwana ko? Dan ni ina da abun yi. Mudi ya ce sai na kwana din.
Hajjo ta yiwa Indo da Mudi sallama rai bace baki zunbure Khalid ya tisa ta su ka tafi. Sai da su ka dau hanya ya ruko hannun ta,Hajjo ta yi saurin kokarin fizgewa,ya ruke gam,ya ce am sorry,am realy sorry Suger! Ta ma sa banza,ta ma ki kallan sa. Da ya ga haka sai ya yi shiru. Sai da su ka isa gida,bayan yayi parkin za ta fita ya ce diya mace kenan,duk abunda Baba ya mi ki,ki ka iya cire komai a ran ki,ki ka manta, ji yanda ki ka damu da shi Hajara,diya mace daban ta ke,Allah ya kara azurta ni da wata bayan Neena. Sai da ta bude motar ta sa kafar ta daya waje ta,sai ta juyo ta kalle shi ta ce na iya cire wanda ka min daga rai na,na manta bare na mahaifina da na ke tsatson shi? Shiru yayi har ta fice bai sake tankawa ba dan ta rufe bakin sa.
Ta na shiga babban falo ta ga Hauwa na zaune,ta kafa ta tsare,sai cika ta ke ta na batsewa,yau girkin ta Khalid ya fice tare da amaryar sa har shadayan dare ba su dawo ba,ta kira ta kira wayar Khalid din be daga ba,ba ta san cikin aljihu ya aje wayar ba,ga shi a silent ta ke be sani ba. Sallama irin na dan Musulmi kawai Hajjo ta ma ta,ta shige na ta bangaran. Khalid na shigowa ta tare shi da masifa,inda ta ke shiga ba nan take fita ba,maimakon ya ba ta amsa,gudun kar rai ya baci kawai sai shi ma ya haye na shi bangaran,haka kusan sa Hauwa hauka yayi,gani ta ke Hajjo ta gama asirce Khalid,ya mutumin da ya gama lallaba ta dazu dazun nan,zai kuma shigo yanzu ya ma ta haka? Ba shakka akwai sa hannun malami! Sai kuwa ta shige na ta bangaran ita ma ta na rusa kuka.
Washagari da duku duku gari ko haske be gama yi ba Hajjo ta shirya,ta fito za ta asibiti. Da ke Khalid ya san halin matar ta sa da wutar ciki tin da ya dawo daga sallar asuba ya zauna a babban falo ya na jiran tsammani. Ganin ta fito sai ya tashi,ya na Suger an fito? Ta kalle shi cikin girmamawa amma ba sakin fuska ta ce ina kwana? Ya ce lfy lau Suger,wuce mu tafi ko? Hauwa za ta yi brkfast zuwa anjima sai na kawo mu ku. Ita dai ba ta tambaye shi ba dan haka shiru ta ma sa,shi kuwa ko a jikin sa,shi mai laifi ne burin sa ya shawo kan Suger ya farantawa Suger ko ta huce. Sai da ya duba Baba sannan ya juya zai koma,ganin Hajjo ba ta da niyyar raka shi,ya ce Suger dan taka min mana. Gudun surutu da mitar Indo sai kuwa ta biyo sa din,su na fita ta ce ni fa yau ina da call,so kar ka yi expectn zan kwana a gida. Yayi jim ya ce toh yanzu ki na nufin tin 8 idan ki ka fara aiki ba za ki dawo gida ba ko kin ta shi? Ta ce ai kasan 4 na ke tashi,so daga 4 zan fara call din,sai kuma 8 na safe zan gama shi. Ya ce sannan ki dawo gida? Ta daga kafada ta sauke tare da fadin ya danganta. Kai ya gyada kawai tare da fadin Allah ya kyauta,sai na dawo. Ta ce a dawo lfy. Ya na tafe ya na tunanin Hajjo,shi fa a aikin Hajjo babu abunda ya tsana kamar wannan cal din na ta,dadin ta ma a wata be fi ta yi sau biyu ba,amma dai ya na tsaya ma sa a rai.
Ko da gari ya waye sosai,wajan 10 sai gashi da Hauwa sun zo asibitin,wato sun aje Neena a makaranta. Ba su sami Hajjo ba ta tafi ta fara aiki,sai ya bar Hauwa wajan Indo,ya tafi office din Hajjo. Ga patience zauna akan layin ganin ta,ganin Khalid ba wanda bai bi shi da kallo ba,gaskiya ya hadu kwarai.kai tsaye ya kutsa,ya shige office din. Ta na duba wata tsohuwa Allah ma ya so ta gama da ita sai gashi tsakar office din. Ganin shi sai da gaban Hajjo ya fadi,dan duba tsohuwa ta ke amma ya na ranta,missing din shi ta ke sosai. Idanun sa kan Hajjo da ta wani basar kamar ba ta gan shi ba ya gaishe da tsohuwar tare da fadin Baba mata ta ta duba ki da kyau ko? Tsohuwa ta ce eh,ai akwai aiki,kai ne mijin ta? Cikin jin dadi an yabi Hajjo ya ce eh,tsohuwa ta ce kai amma ka yi sa’ar mata,Allah ya sa mu ku albarka. Ya na dariya ya ce ameen,amma dai Baba ai ita ta yi sa’a,dubanni fa kyakkyawa da ni? Tsohuwa ta ce eh wlh ga kyau ga ado,eh ta wannan dai ta yi sa’a,ya kashewa Hajjo ido,Hajjo ta yi rolling idanun ta,irin kai ka sani,ta ce iya za ki iya tafiya,sai a je a siyi magani Tsohuwa ta ce toh madallah. Ta tashi,tare da yiwa Khalid sallama ta fice. Tana fita ya zaga gaban Hajjo ya yi kissin kumatun ta tare da fadin u see Suger,har tsofaffi yabawa su ke da Khalid,you should b glad am urs….ta na ji wata za ta shigo tsohuwar na fadin ku dan dakata ya fito,mijin ta ne. Ajiyar zuciya Hajjo ta yi gami da fadin dan Allah Khalid ka tafi am too busy wlh,marasa lfy ke jira na fa. Ya ce ni ma mara lafiya ne,wani abu ya fito min a baki,da sauri Hajjo ta tashi ta na menene? Mu gani?daga zaune ya dan daga kai ya bude baki kamar mai nuna ma ta abu din. Hajjo ta dan matsa kusa da shi kamar ta na tsoran matsawa kusa sosai,ta ce ka ma kasa tsayawa na gani,ya ce matso kusa sosai za ki gani,ta na matsowa yayi saurin janyo ta,cikin zafin nama ya fara kissing din ta,ta na kokarin kwacewa ta kasa,dan kan sa ya sake ta,ta yi baya za ta fadi ya yi saurin ruko ta…..
DEDICATED to The Women Of Virtue💁👰🙋(group)
[7/25, 6:14 PM] Salmah Ateeku: [12:20pm, 6/14/2015] Khadija Sidi: 👭👭👭DIYA MACE👭👭👭
6⃣3⃣
Ta fizge hannun ta tana mayar da numfashi,ta ce nan office dina ne,ba gidan ka ba ne,ba dakin ka ba ne,pls kar ka jawo min mutane su shigo su raina ni mana!dan Allah tashi ka tafi. Ya daga kafada ya sauke tare da fadin ke fa mata ta ce,na fi bukatar ki fiye da kowa. Hajjo ta ce plss ka fita. Ya tashi ya na murmushi ya ce akwai abunci wajan Indo,ki daure idan kin sami dama ki ci. Tare na ke da Hauwa,ta na mi ki ya mai jiki. Ya juya ya fice. Sai da ta dau kusan minti goma zaune sannan nutsuwa ta dawo ma ta,ta cigaba da duba jama’a.
Lokaci lokaci ta na zuwa ta na duba Baba,ranar har Hajiya sai da ta zo duba Baba,su Jabir,Nabila ne,Ayush hatta su Doc Hussaina sai da su ka shigo wajan sa,masinjoji da nurses ma ba a bar su a baya ba,kowa na zuwa duba baban Doc Hajara,sai dai ba a ji ba. Hajiya ce ta kai mu su abuncin rana,da za su tafi Nabeela ta ce ita za ta kawo na dare. Jikin Baba kuma ba laifi jikin na sa da sauki,ya na gane jama’a,ya ga yanda jama’a ke tururuwan zuwa duba shi,duk dan darajar diyar sa mace,diyar sa mace ce yau ta zama abun alfahiri ga jama’a,ta zama kamar tauraruwa kuma ya ke cin darajar ta,diyar da be san darajar ta ba,diyar sa Hajjo,ina ma matar sa Ameenutu na raye ta ga baiwa da daraja da yayiwa diyar su mace. Kai kawo na Khalid kuwa ba adadi,bini bini sai Hajjo ta ga ya zo ya duba su,har sai da ta ce ya huta haka da ta raka shi har mota bayan magrib. Ya ce toh gobe da sassafe zai dawo,ta ce Allah ya nuna mana. Su ka yi sallama suna missing juna gaba dayan su.
Washagari da asuba bangaran Baba da ya shanye ya fara motsi,Hajjo ta tadda Mudi ya dan jinginar da shi ya sallaci asuba. Kujera ta ja gaban sa,ganin ta farin ciki ya bayyana fuskar Baba,ya ce Hajjo,Allah ya mi ku albarka ke da yar uwar ki,Allah ya sa diyar ki ta mi ki yanda ki ka min,Hajjo kin cika diya,da na san haka dadin diya mace ya ke da ban kyamace ku ba,da na yi addua’a Allah ya bani diya mace ba adadi,ki yafe min diya ta,na zalince ki yafe min diya ta. Hajjo na murmushi,idanun ta cike da kwalla ta ce ba komai Baba,ni ya kamata na nemi yafiyar ka,na kaurace ma tsawan shekaru,dan Allah Baba ka yafe ni. Ya na murmushi ya ce haba ai tsakani na da ku sai albarka,diyoyi na kun min komai,hakan zan yi kashi na yi fitsari a sitira yar uwar ki Indo ta sa hannu ta wanke,da kuwa matan yayyan ku sai dai su kyamace ni,su ka ma hana yaran su jikokin na zuwa waje na,na fada ma mazajen su sai suce na fiya korafi…..sai ya fashe da kuka,kunya ta kama Mudi,Indo da Hajjo su ka shiga rarrashin Baba,har su ka samu yayi shiru. Haka suna dan hira sama sama,Hajjo ta ce bara ta karasa aikin ta ta zo,ta tafi ta na murna Baba sauki ya samu.
Wajan 7 ta koma wajan Baba,ya na ganin ta ya ce Hajjo kishi na ke ji,taimake ni da ruwa,ta dauko ruwan ta dan bashi ya sha,ya koma ya kwanta,Indo na murmushi ta ce din dazu yace ya na jin kishi fa,da na dauko zan bashi sai ya ce shi sai Hajjo ta zo. Hajjo ta ce Allah sarki ina ruwan Baba. Hannu ya daga kamar mai magana,Hajjo ta matsa kusa da shi sosai,sai cewa yayi Hajjo numfashi na neman ya gagare ni,numfashi na daukewa ya ke…ai kuwa sai ya fara gasping,gaba daya su ka rude,Indo ta ce Mudi kira likita kar mu rasa Baba,ta ma manta Hajjo likitan ce. Ita kuwa Hajjo jikin ta ne ya dau rawa,ta na san halin da Baba ya ke ciki,ba kan shi ta fara gani ba,ta sha gani marasa lfy na yi,ta kuma san karshen,dan haka sai ta juya ta fice da sauri sauri gudu gudu,a kofar da zai sada ta da waje ta yi karo da mutum har ta fadar ma sa da flask din hannun sa. Ya ruko ta,daga idan da za ta yi ashe Khalid ne,ya na menene Hajara? Me ya faru? Baba,Baba kawai ke fita daga bakin ta,ganin Mudi ya wuce su a guje,ga doctora har su hudu biye da shi sai sassarfa su ke dan karasawa ceton ran Baban Doc Hajara,Khalid ya gane me ke faruwa,ya janyo Hajjo jikin sa yayi hugn dinta ya na shafa bayan ta ya na fadin is owk,it is owk Hajara,yi masa addua!!!!
DEDICATED to The Women Of Virtue💁👰🙋(group)
[16/10 21:52] .: 2:33pm, 6/14/2015] Khadija Sidi: 👭👭👭DIYA MACE👭👭👭
6⃣4⃣
A kumurya aka yi zaman makokin Baba,can Hajjo ta tare. Ta ga jama’a an mata kara,ba wanda be je mata gaisuwa ba,hatta Hauwa sai da ta kai mahaifiyar ta da yan uwan ta,bare su Nabeela da Ayush. Ayush ke fada ma Hajjo Suraj na ma ta gaisuwa,ta ce a ma sa godiya,Allah ya bada lada. Amma fa duk abunda ake Hajjo ta ki tayi kuka kamar dai rasuwar Inna,abun na matukar bawa Indo da Khalid tsoro dan sun na zuci ta ke. Sai da aka yi bakwai Hajjo ta koma gidan ta.
Da daddare zaune bisa gadon ta,ta hada kai da gwiwa,gaba daya ji take duniyar ma ta ishe ta. Khalid ya shigo ya zauna kusa da ita,ya ce Suger ya dai? Ta ce ba komai. Ya ce toh ki daure ki cire damuwa daga ranki,duk kan mai rai mamaci ne,mu ma ta mu ke jira. Har ran sa so ya ke ya kwana tare da ita dan ya debe ma ta kyewa dan ya san tin rasuwar Baba cikin mutane ta ke kwana,toh amma ba dama saboda he is man of his words,ya ce ba zai kwana dakin ta ba sai idan ita ta gayyace shi da kanta. Ya tashi tare da fadin bari na bar ki ki kwanta Suger,sai da safe. Ta ce toh. Sai da ya kai kofa ya ji ta kira sunan shi,ya juyo tare da fadin yes Suger? Ta yi kasa da ido ta ce dan Allah ka kwanta….ina nufin ka kwana dakin nan in ba damuwa…..ya san ba karamin abu zai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment