Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)






8⃣





Hassan dake waya da Husaini yanajinsa yana kalmar shahada a waya,
gaba d'aya hankalinsa ya tashi ya fito da saurin shi baibi ta kan kowaba ya shiga motarshi yajata da k'arfi ya mik'i hanya,
ya nufi wurin da yaji Husaini yace masa ya kawo."

Cikin minti talatin ya isa wurin ya d'aga wayarsa ya shiga kiran wayar husaini, d'aya daga cikin wad'anda suka kawo masu taimakon gaggawa, ya d'aga wayar yashiga yiwa Hassan bayanin abunda ya faru, ya shaida mashi da cewa gasunan Asibity, Had'ida yimashi kwatancen asibity dasuke."

Cikin tashin hankali Hassan yanufi Asibity idonsa yana zubar da hawaye kamar macce."

A Gaban gawarsu yake dur'kushe yana kuka yana jijjiga Husaini yana fad'in "Husaini katashi don Allah karka mutu kabarni rayuwata idan babu kai bnga amfaninta ba,
kai kad'ai ne d'an uwana jinina Wanda nake shawara dashi husaini katashi."
Kuka yakeyi sosai kamar ya d'auke numfashi yana jijjigar gawar Husaini."

Mutanen wurin suka tallabeshi suka bar wurin dashi ana bashi hkr,
Snn dga k'arshe yakira mahaifan Bilkisu da sauri suka zo, snn ya kira Kaka da tsohuwa, a tare sukazo asibity aka d'auki gawarsu aka nufi Kano da su gidan Hassan akayi masu wanka da sutura aka kaisu gidansu na gskiya."

A nan gidan Hassan akayi amsar gaisuwa,
Inda Dijama tana rungume a hannun tsohuwa tana bata madara."
Hassan yayita lallashin tsohuwa akan ta amince tabari Hajara taci gaba da shayar dasu tareda fateema,
Amma tsohuwa ta kafe tace "sam bazai yiwoba, kuma da anyi sadakar bakwai zatayi tafiyarta gida, tare da dijama tazata tafi Dan bazata bartaba."

Hankalin Hassan ya kuma tashi, ya shiga rok'on tsohuwa akan ta amince ta bar masa dijama zai kula da ita ya had'ata da 'ya'yanshi yanda bazata tab'ayin maraiciba."

Tsohuwa tace "Sam bazai yiwoba, itama ita zata dinga gani a gabanta tana jin sanyi tana d'ebe mata kewar Husaini da tarasa."

Hakan akayi bayan sadakar bakwai ta harhad'a kayanta ta goya Dijama zata tafi, direba yana jiranta."

Hassan da iyanlansa suka yomata rakiya, ko wannensu idonshi cike da hawaye domin ji sukeyi mutuwar Husaini ta kuma dawo masu sabuwa."

Mahmud kuka yakeyi sosai yana birgima yarik'e tsohuwa yana fad'in bazataje masa da dijamarsaba."

Kuka yakeyi sosai kowa ya tausaya masa, tsohuwa tace a had'o masa kayanshi sutafi tare idan hutunsu na mkranta ya k'are sai aje a d'aukoshi, tun da daman hutun makaranta sukeyi."

Haka kuwa akayi, aka had'awa Mahmud kayansa yana murna yana dariya, sukayi masu rakiya zuwa mota direba yazasu suka d'auki hanyar Tofa."

Wnn shine dalilin zaman dijama a wurin tsohuwa a cikin k'auyen tofa."

Tsohuwa bata son jin kukan dijama bata son ganin b'acin ranta,
Haka mahmud da zarar akayi masu hutun mkranta zai tsira fita a kan dole sai ankawoshi wurin tsohuwa yaga dijamarsa."

Itama dijama tun tana k'arama da zarar Mahmud yazo hutu,
bata kuma yarda da kowa sai mahmud a tare sukecin abinci a tare suke kwana, idan tayi kashi shike wanke mata, shike mata wanka,
zarar hutunsu ya k'are Idan direba yazo d'aukarshi, da kuka da komai suke rabuwa,
Tsohuwa tana jijjinawa wannan shak'uwa tasu, haka shima Abbah wato Hassan kenan shima yana jijjinawa wann soyayyar tasu."

Wnn dalilin ne yasa mahmud duk lokacin da suka samu hutu baya iya zama garin kano sai dai yatahowarsa Tofa yayi zamansa saboda dijama, har zuwa yanzun da girma yazo masa ya mallaki hnkalin kansa yashiga jami'a a yanzun yana zangonshi na k'arshe a dgree d'insa."


Tun tashin dijama a rayuwa babu abunda ta nema ta rasa, domin tsohuwa da Kaka da muhmud basu da wani buri da yawuce a koda yaushe su farantawa marainiya, basa son ganin kukanta."

Abba shike d'auke da karatunda da duk wani Abu da yashafi rayuwata, tunda tsohuwa ta kafe a kan cewa baxata bashi itaba, amma shi har ga Allah yaso ya d'auki dijama ya had'ata da yaranshi yabata gata Wanda yin hkan shi zai sanyashi ako da yaushe zai dinga ganin kamar Hussainin shi yana nan bai mutuba."

Tun tashin Mahmud shi mutum ne mai son a girmama shi, baya d'aukar raini a gida ko a waje,
K'annansa su fateema da zarar yashigo a gida kowa yake kama Kansa, idan ba hakan ba da zarar sunyi abunda ba dai dai ba a nan take zai hukuntasu. Ya azzabtar dasu yayi tafiyarsa."

Wnn dalilin ne yasa yaji ya tsani dijama saboda rashin jinta, gata bata gane karatu,
Kuma bata ganin girmanshi kwata kwata ta rainashi raininda ba Wanda ya tab'a yi mashi irinshi."
Tsohuwa bata ganin laifinta duk rashin kunyar da zatayi jan maganar da zatayi a waje tsohuwa bata ganin laifinta,

Wann dalilin yasa a rayuwarshi yaji ya tsaneta basa shiri kwata kwata.wani lokaci Sai ya d'auki niyar cewa bazai k'ara zuwa Tofa hutuba saboda rashin kunyar dijama,
Amma da zarar anyi masu hutun ko na kwana biyu ne baya iyawa sai yazo Tofa yayi hutunsa snn ya koma."

Kamar ynzun da Hutu yazo yayi, bai iyar da kammala hutun nashiba, ta had'ashi dasu Buba, ya tattara kayansa ya koma warsa gida Wanda tsohuwa tacika da mmki."

*Wnn kenan mudawo labari*

***************

Mahmud na komawa gida, kowa ya cika da mmki dan ganin hutunsu bai k'areba ya dawo."

Abba ne yakirashi a falonsa yana tare da momy mahaifiyarsu yashiga tmbayar sa, lafiya me yadawo dashi bayan ba hakan ya sababa hutunsu bai k'areba?"

Murmushi yayi ya sunkuyar da kansa yace " Ba komai Abba hakan nan kawai nadawo babu abunda ya faru."

Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "ina fatan kowa yana lafiya?"

Ya 'yata Ummie ina fatan tana cikin k'oshin lfy?"

Murmushi mahmud ya k'ak'aro yace kowa lfy Abba. Kaka ne kawai yake fama da ciwon k'afa, amma kuma yaji sauk'i sosai."

Abba yace subahanallahi!!! Ai kuwa zanje cikin _weekend_ d'in nan nadiboshi,
Momy tace "Allah yabashi lafiya."
Suka amsa da "Amin gaba d'ayansu."

Snn Abba yayi kyaran murya yadubi mahmud da kyau yace "dama ko baka dawoba zankira ka, a waya nace kadawo, domin Alhaji Atiku commonden d'in sojoji wnn abokin nawa yayo mun waya a kan cewa anfitarda form na sojoji ya d'aukar maka d'aya,
Saika had'a takardunka katafi Abuja cikin satin nan zakuyi jarabawa Allah yabada sa'a yasa a dace."
Suka Amsa da Amin."
Sannan Mahmud yayi masu sallama ya fito yanufi d'akinshi yana kuma jin haushin dijama a ranshi."

**************

Dijama zaune a kusa da tsohuwa tana turo baki, tsohuwa nayi mata fad'a akan ta fara gajiya da halinta kullum saita janyo mata fad'a da fitina a mak'ota."

Ta mik'a mata kud'i tace "gashi kitafi gidan jummai ki kai mata kud'in zubi, dan Allah dijama karki tsaya kuma karki kula kowa a hnya kiyi tafiyarki."

Mik'ewa tsaye tayi had'ida turo baki tana gun guni, sannan ta karb'i kud'in ta fita."

Tana tafiyarta cikin natsuwa abunda bata tab'a yiba, k'awayenta su lantana tagani sunfito daga rafi, suka had'a baki suna mata magana suna cewa "dijama 'yar gidan tsohuwa sai ina?"

Bata tsaya ta kulasuba sai dai ta nuna masu da hannu tana tafiya tace "Tsohuwa ta aikeni gidan jummai nakai kud'in zubi, batajira taji amsarsu ba, tayi tafiyarta, sab'anin da, da sai ta tsaya sunyi jan magana snn kowa ya kama gabansa."

Mmki suka shiga yi ko meyasamu dijama?"
Lantana tace ko dai batada lafiya ne?"

Suka had'a baki sukace lafiyarta k'alau akwai dai abunda ke damunta."
Sukace "Allah ya kyauta gaba d'ayansu sannan sukayi tafiyarsu."

Dijama anfara jin mgnar tsohuwa kenan, hnmmm Bari dai mugani."

Tana gafda da zata shiga gidan jummai mai adashi, taci karo da Antyn lantana wadda tabata takarda ta kaiwa yaya Mahmud,
ta sha gabanta tana fad'in "yawwa dijama shine nabaki sak'o ki kaiwa yayanki d'an birni shine baki bashiba kika yaga."

Bata tanka mata ba, sai ma k'ok'ari takeyi tabi ta gefenta ta wuce, ta kuma tarar gabanta, tana d'auke da k'waryar da tayo nik'an dawa a kanta,

Tacewa dijama "wani sabon iskanci kika samo wadda idan ana yimaki mgna kidinga kyale mutane, taciyo kwalar rigar dijama."

A rayuwar dijama babu abunda ta tsana irin a rik'e mata kwalar riga, cike dajin haushi ta dubeta tace "lallai ma Antynnan harda wani rigemun riga, bakisan ina ragamaki bane a k'auyen nan saboda lantana amma yau zakisan kowacece dijama."

Ta duk'a kamar wadda wani abun nata ya fad'i a k'asa zata d'auka,
Tasanya hannunta ta yaye k'afar Antyn lantana, sai gata tafad'i k'asa dab'as kwaryar nik'an dawa ta rabe biyu, nik'an ya zube k'asa
Ta rik'e k'ungunta tana fad'in "wayyo Allah nashiga uku K'uguna dijama kin lahantani."

Me dijama zatayi idan ba dariya ba, tace "dankinga ina ragamaki, lallai ma Antyn nan to ba tsoronki nkejiba, ni bana tsoron kowa a garin nan ki kiyaye ehe."

Babu abunda antyn lantana takeyi sai kuka da murje2 sboda masifar rad'ad'in da k'ugunta yake mata."

Dijama nayi mata dariya, ta rab'ata zata wuce, saiga samarin Antyn lantana sunbiyo ta wurin, zasu wuce

Ganinta sukayi zaune a k'asa warwas dafe da k'ugu tana kuka tana fad'in wayyo dijama kin lahantani wayyo k'uguna."

Dijama na ganinsu taja da baya ta koma hanyar gida, ta arce da gudu, basu ankaraba sai ganinta sukayi tana gudu kamar filfilwa ta kusan shanye kwanar gidansu." Dijama ba dai guduba kamar mai Aljanun gudu."

Saurayin Antyn lantana yace "nayi Alk'awarin tunda dijama tashigo gonata saina saita mata hankali A garin nan."

Yashiga taimakon budurwanshi ya mik'ar da ita tsaye ya rakata yarakata har k'ofar gida sannan ya juya ya tafi."

Dijama na shanye kwana gidansu sai hango motar Abban kano tayi a jiye a k'ofar gidansu, murna tashigayi tun daga nesa ta dinga stalle Tana "Abba oyoyo."

Kai tsaye taje kan jikinshi ta fad'a tana dariya tana murna ganinshi domin Abban kano yana sonta sosai,
Murna yayi da ganinta yashiga shafar bayanta yana fad'in "Iye Ummie na ta girma, kina nan kina karatu kuwa?"

Taji gabanta ya fad'i domin Abba baya wasa idan akazo fagen karatu."

Tayi saurin kauda maganar da cewa "Abba ina su fateemah?"

Yayi dariya yace sunanan lfyrsu glau, suna gaisheku."

Anan suka shiga shirya Kaka domin a d'aukeshi a tafi dashi asibity dake cikin garin domin a kuma diba mashi lfyar k'afarshi."

Alhmdulillah anyi mashi aune aune angano ciwon k'afar da sauk'i, aka rubuta mashi magani Abba yasawo mashi sann suka dawo gida."

Anan Abba yace zai kwana sai gobe idan yaga ynda jikin Kaka ya kwana snn sai yatafi gida ko da marecene yatashi safiyar _Monday_ a garin kano."

Tun zuwansa garin bai hutaba, mutane ne cingim a k'ofar gidan tsofaffi da samari,

Abba sai rarraba masu kud'i yakeyi suna godiya tare da sanya mashi Albarka."

Abba mutum ne mai taimako da tausayi, wannan dalilin ne yasa mutanen cikin garin tofa suke mutuntashi da darajashi."

Washe garin ranar lahadi da safe, misalin k'arfe goma na safe,
Abba yana stakar gida zaune, tsohuwa na gefensa d'aya gefensa Kaka ne zaune da sandarsa gefensa a jiye, Abba yana b'are mashi ayaba yana bashi yanaci had'ida sanya mashi Albarka."

Dijama na cikin d'aki zaune ta fito daga wanka tana tsara kwanliya." Fuskarta tasha kwalli da jambaki da hoda."

Tsohuwa tashiga kiran sunanta tana fad'in "dijama kiyi Sauri Ki shirya kizo na aikeki gidan kuluwa ki kaimata tsarabarda bbnki yazo da ita."

To dijama tace had'ida mik'ewa tsaye ta d'auki kayanta tasanya
Snn ta fito."

Tsohuwa ta mik'a mata Leda cike da ayaba da lemu tace "ungo ki kai mata kuma Dan Allah karki tsaya a kan hanya."

Tace "to." Ta karb'a had'ida fita, Abba ya dubita yayi murmushi yace "Ummie ba dai wayoba."

Tsohuwa tayi dariya,
Kaka kuma yace "hmmm yaja bakinshi yayi shuru."

Bayan ta dawo aiken datsohuwa tsohuwa tayi mata tana tafiyarta a hanya tana wak'a tana rawa, tana d'an karkad'a k'ugunta."

Wazata gani Buba tagani a gabanta yana wasar Baki yana fad'in dijamata kinyi kyau wnn kwanliya hkan."

Bakin buba ta kalla inda har ynzun bai iyar da warkewa ba daga kumburin da yayi."

Batasan lokacin da dariya ta sub'uce mata ba,
Ta dubeshi tana dariya tace "Wai amma dai Yaya mahmud ya iya duka."

Wai kai Buba kana aikin me harya kumbura baka Baki, ta kuma shek'ewa da dariya, ta dubeshi
Tace a hkan kake cewa zaka aureni. Allah ya tsaran da auren ragon mutum kamarka,
Ni nafison na aure jarumin namiji mai firgita 'yan maxa, amma kai ai macce ne."

Ta rab'ashi ta wuce tana dariya,

Buba yaji haushi ya k'ulu iya k'uluwa, idonsa ya canza launi zuwa ja, ya zunduma ashar, Wanda yasa dijama saurin juyowa da sauri tana kallonsa."

Yace "duk son da nake maki dijama yau bazai hana naci ...... Ya zunduba wani kalar shar ya dafawa dijama da saurinshi cikin hushi."

Dijama na ganin hakan ta zuba da gudu ai kuwa buba ya dafa mata, da yaranshi."

Gudu takeyi tana kuwa tana fad'in "wayyo Allah jama'a kutaimakeni 'yan fashi wayyo Allah 'yan fashi.da makami"
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅





Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)





*10*




Gafda da sallar magariba suka isa gida,
Horn Abba yakeyi baba maigadi yafito da saurinshi ya bud'e mashi get yashigar da motar sa."

Dijama sai waige waige takeyi tana kallon yanayin tsarin ginin gida."

Abba da kansa ya bud'e mata murfin mota tafito, ya zagaya but ya d'auko jakar kayanta ya rik'e mata suka jera a tare suka shiga ciki."

Gaba d'aya family gidan suna kan dinner table suna cin abinci cike da burgewa, Abba yayi sallama da gudu Fatima ta rugo ta rungumeshi tana oyoyo Abba."

Ba Wanda ya lura da dijama a gefensa, yaya muhmud daya kai lomar tuwon shinkafa miyar a gushi a bakinsa ya d'aga kansa sama yana murmushi zaiyiwa Abba sannu da zuwa karaf yayi da dijama a tsaye a gefen Abba."

Kasa iyar da had'iye tuwon yayi, ya rik'e baki yana nuna dijama batare da yayi maganaba."

Sai a lokacin hankalin kowa ya tafi wurin dijama dake tsaye sai zarar ido takeyi,
Khalil na ganin hakan yatashi yaje wurin Abba yayi mashi sannu da zuwa, had'ida kallon dijama ya mere baki☹
Ya ranb'a ta gefensu yayi tafiyar shi."

Khalil dama hakan yake ko oho gareshi, a rayuwarshi bbu abunda ya tsana sama da mutumin k'auye bagidaje, ko kuma yayi ido biyu da mummunar mace,

Wnn dalili. Yasa baya zuwa Tofa gurin Tsohuwa,

Ya kuma yiwa kansa Alk'awarin bazai tab'a auren macce mummunaba, ko bagidajiya, sai Wanda ta amsa sunanta macce ta ko ina."

Fateema tayi saurin sakin Abba taje ta rungume dijama tana fad'in oyoyo dijamar tsohuwa kai amma. Naji dad'in zuwanki."

Hakan itama momy tazo ta kama hannun dijama gaba d'aya suka zauna a kan kujera har da Abba."

Mahmud dake zaune a kan dinner table ya kasa motsawa kamar wani mattance saboda ankawo masu fita a gida."

Muryar Abba ta ankarar dashi dayaji yana cewa "mahmud lfy kake kuwa ka k'ame wuri d'aya kamar Wanda baya motsi,
Bakaga 'yar gidan taka bace Ummie?"

Bayan nan tukuna tashi mutafi masallaci mu farayin sallah sann mudawo muyi magana."

Mik'ewa sukayi suka nufi masallaci domin gabatar da sallar magariba."

Da fitarsu momy ta kama hannun dijama cike da kulawa tace "ummie ya hanya?" Ya kuka baro Kaka da tsohuwa?"

Dijama tace "lafiya glau sunce a gaisheku."

Murmushi momy tayi, ta kai dibonta ga fateema tace "fateema d'auki kayan 'yar uwarki ki kaimata d'akinki, kibata ruwa tayi Arwala kuyi sallah ki kuma taimaka mata ta cire kayan jikinta kibata d'aya daga cikin kayanki ta sanya sannan kufito taci abinci."

Cikin ladabi da biyayya fateema ta "amsa da to mmy, sann ta d'auki jakar kayan dijama had'ida rik'a hannunta suka nufi d'akin fateema. Ita dai dijama biye take sai zarar ido takeyi tana kale kale."

Suna tafiya momy itama ta tashi tayi Arwala tayi sallah, tana kammalawa yayi dai dai da shigowar Abba da mahmud."

Abba ya dubi Mahmud yace "kaje kafad'awa khalil da zarar munyi sallar isha'i kuzo gaba d'ayanku inaso zanyi mgna daku."

Mahmud ya d'an runsuna yace "to Abba."
Yana so ya tambayeshi dalilin da yasa yazo da dijama masifa amma baiga fuskaba a wurin Abba hakan yanufi d'akinshi da yana sak'awa yana kwancewa a ransa."

Bayan Abba yayi wanka yaci abinci yayi sallah isha'i yana gincire a tsakar falonshi momy na gefenshi tana yanka mashi kankana tana bashi yana sha suna firarsu cike da kulawa da sha'awa."

Mahmud da khalil sukayi sallama saka shigo, sannan fateema tareda dijama suma suka shigo, suka zauna a gefen momy."

Babu abunda khalili yakeyi da yayi ido biyu da dijama sai ya mutsa fuska kamar Wanda yaga kashi."

Dijama na lura dashi, ta wurga mashi harara had'ida murgud'a mashi baki,

Karaf sai a kan idonshi, zaro ido yayi yana kallonta cike da mmki."

Abba ya katse masa tunani da yafara magana
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅





Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)





*11*





"Abunda yasa na taraku a nan sai Dan in gabatar maku da 'yar uwarku, Ummie ya nuna dijama dake zaune a gefen mmy."

Yanuna khalil "Musamman kai khalil da bakowa kasani ba a cikin dangi, saboda baud'and'en ra'ayinka,
Amma kasan ko wacece dijama, kasan matsayinta a gidan nan,
Baka buk'atar na kuma yi maka wani dogon bayani a kanta."

Ya kuma maida hankalinshi a kan Mahmoud, yace "Mahmoud ga k'anwarka nan nasan kafi kowa farin cikin dawowarta gidan nan baki d'aya."

"Abunda nakeso daku Ku d'auketa kamar yanda kuka d'auki fateema a wurinku, kubata kulawa kamar yanda kuke bawa fateema,
kai inma son samune Kubata kulawa fiye da ynda kuke bawa fateema saboda Ummie marainiyace."

Sai a lokacin mahmoud yayi mgna yace "Abba meyasa ka d'auko mana dijama?"
Abba dijamar da kasani a da ayanxun ta canza hali,
Na rantse da Allah dijama tana iya tayarda gidan nan da unguwar nan gaba d'aya saboda hatsabiban cinta."

Nidai Abba dazakaji sha'warata da anmayar da dijama can Tofa Dan tafi ganewa can, kowa ma sai yahuta."

Dijama tayi saurin d'ago kai ta dubi yaya Mahmoud ta murgud'e mashi maki cike da tsiwa, ta karkace kai tace "lallai ma yaya nan wai a mayardani tofa to sannu."

Khalil yayi saurin nufarta ya sanya hannu ya buge mata baki, dama yana ganin take takenta saitayi rashin kunya."

Dijama tayi saurin rik'e baki, tana fad'in wayyo Allah na ya fasa mun baki"

"Yace k'azama 'yar k'auye, yaya muhmoud d'in kike yiwa rashin kunya?"

Abba ya doka masu tsawa cike da b'acin rai yace "kar in kuma ganin d'aya daga cikinku ya kuma dukanta, bana son hkan,
Na rantse akan Ummie zan iya sab'awa da kowa a cikinku,
domin ganin farin cikinta, na kuma rik'e Amanar d'an uwana."

Ya maida kallonsa zuwa wurin mahmuod yace "Kai Mahmoud yaushe kuka fara 'yar hakan da kaida Ummien taka?"
"To koma dai me takeyi a can k'auye ba ruwanku,
Domin yanxun ta baro k'auye ta shigo birni."
Rayuwarta zata canza, kuma banason tsangwama da hantara a tsakaninku."

"Idan Allah ya kaimu gobe kaje makarantar su fateema, Kasan yanda za'ayi ayo mata takardun shedan ta kammala primary sannan, sai a sanyata a jss1 sai suci gaba da karatunsu tare da fateema."

Kai kuma khalil kaje islamiyarsu fateema ka yanko mata form a d'unka mata uniform sai ta tafara zuwa."

Batare da sun musaba suka amsa da "to Abba."

Ya dubesu yace "Allah yayi maku Albarka."

Suka amsa da Amin."

Sannan ya dawo wurin fateema yace "fateema ga 'yar uwarki nan Ku had'a kanku, kiko ya mata wasu abubuwa wad'anda batasaniba,
Kuma ina so ki d'auketa tamkar 'yar uwarki Asma'u da kika rasa,
Allah ya jikan Asma'u da rahama suka amsa da amin gaba d'ayansu."

Sannan ya basu umurnin kowa ya tashi,
Bayan sunfita ne ya kuma kiran Mahmoud ya dawo ya tsuguna,
Yace "ya kukayi da baban naka Alhaji Atiku?"

Mahmoud ya sunkuyar da kai, yace "zuwan danayi Abuja wurinsa ya karramani sosai, sannan ya turani mukayi jaraba."

Yace kuma "nafad'a maka musanya ido daga nan zuwa wata biyu za'a lik'a sunayen mutanen da sukaci, sannan zai kirani mutafi wurin trening

Abba yayi murnushi yace "karka damu indai Alhaji Atiku ne kasanyawa rayuwarka har kazama soja."

Momy tace "Allah ya taimaka ya tayaka rik'o da gaskya."

Suka "Amsa da Amin."

Sannan yayi masu sallama yatashi ya fita."

Abba ya dubi momy da sai murmushi takeyi d'auke a kan fuskarta,
Yace momyn yara babu abunda zance maki a rayuwa sai dai Addu'a domin kinsamarmun farin ciki a cikin zuri'ata Allah ya barmu tare dake, babban burina shine na faranta maki har k'arshen rayuwarta."

Ya Matso daf da ita, yarik'a hannunta ya shiga murzawa yana kallonta had'ida kashe mata ido d'aya."

Yace "kinsan wani Abu kuwa?"
A kasalance ta dubeshi ta girgiza kai alamar A'a."

"A kullum idan ina tare dake jinakeyi tamkar ina tare da yarinya yar shekara 17,
saboda komai naki na dabanne a koda yaushe yarinya kike komawa."

Ya kuma shege mata a jiki yana shishinar daddad'an k'amshin jikinta,

had'ida sab'ule mata d'ankwalin kanta yana shafa gashin kanta dayasha gyara da mayunka masu Sanya laushin gashi da santsi uwa uba kuma k'amshi."

_Ina ganin hakan nayi saurin fitowa cike da mmkin su Abba da momy ba'a tsofa🤔_


Mahmoud yaje makarantarsu fateema yayi duk abunda Abba ya umurceshi,
ya k'arb'o mata uniform d'inta da littafanta yataho mata dasu,
Ranar Monday zata fara zuwa makaranta."

Da sallamarshi ya shigo cikin babban falon gidan,
ba kowa a cikinsa, sai tausin k'arar TV kawai yakeji yana tashi, gefe d'aya yaji sai dariya akeyi harda buga k'afa.'

Koba'a fad'a masaba yasan dijama ce."

Mmki yashigayi yanufi wurin TV yayi saurin kashewa,
Ya juya ya kalleta, sukayi ido biyu da ita,
ta turo baki tana hararsa k'asa k'asa."

Cikin fushi yace "lallai d'an k'auye yashigo birni yafara wayewa,
Tomu a nan gidan ba'a mana kallo a k'urema volume, anan gidan karatu akeyi a koda yaushe ba zaman shashnciba da rashin kunya, takwala kawai Wanda bata gane karatu."

Ya jefa mata ledar kayan makarantarta yace "gasu nan ki kwana da shiri gobe Monday zaki fara zuwa makaranta, kuma nizan kaiki da kaina, zan shaida masu cewa baki gane komai kwakwalwar kifi ce dake, kuma da zarar kinyi masu irin rashin kunyar da kikeyi a k'auye, zance suyi fata fata da naman jikinki su jefar dake a bula."
Dama tsohuwa ke tare maki yanxunfa?"

Kallonshi tayi idonta cike da hawaye domin a rayuwarta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmoud ya kirata da takkwala mai kwanyar kifi."

Shima yayi mmkin ganin zubar hawaye a idon dijama anan take lokaci d'aya."

Zata bud'a Baki tayi magana kenan ya matso daf da ita, yace "muddun kika bud'a baki kikayimun rashin kunya saina tattakaki."

Ta fasayin maganar ta sunkuyar da kanta k'asa tana aika mashi da Allah ya isa a zuciyarta.'

Mik'ewa tayi tsaye ta d'auki ledar uniform d'inta, saida ta kwatanci saiti wurin k'afarshi ta
sakar mashi remote d'in TV a babban d'an yatsan k'afa, sai da yayi sarin runtse idonshi yace "washh."
Saboda zafin dayaji wurin namasa."

Ta zuba da gudu ta haiye sama tanufi d'akinsu, taja tayi tsaya a bakin k'ofar d'aki, tana kallonshi tana burgud'a baki tace "kuma bani bace takwala sai dai inkaine."

Kuma tunda kakeyimun gorin karatu saina baka mamaki mugu kawai, dan kana ganin nazo gidanku, to kasani duk abunda kakeyimun a rubuce yake a
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment