Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sabon salo da yaji sunayi mashi kasa d'auka yayi sai nishi yakeyi yana wani irin sabbatu."

Gaba d'ayansu suna kanshi kowa ce da irin nata salon Jan hankali."

Duk yanda khalil yake buk'ace da macce sai ya fara sanya hannunshi a gabanta da zarar yajita a bud'e to ba zai kusance taba."

Hakan yaci gaba da wasa da 'yan matan nan yana kashesu da zazzafar soyayyarshi, sannu a hankali cikin wani salo,
yafara sanya hannu a gaban d'ayan mai suna billy,
Jinshi yayi kamar yajefa hannunshi a rame, saboda zurfi da fad'i,da take dashi."
cikin wani salo yashiga wasa da hannunshi cikin HQ d'inta snn daga k'arshe ya fitar dashi ynda bzata fahimci komai ba."

Wurin d'ayan ya nufa mai sona sa'ade, hakan itama yasanya hannunshi ya shiga wasa dashi a gabanta, amma har k'ara Billy a kan sa'ade."😊

Cikin dubara ya kai kwance suka haye kanshi suna faranta mashi har sai da yabiya buk'atarshi batare da ya kusancesuba."

Safiyar Monday dijama shiri akeyi domin zuwa karanta, murna kawai takeyi za'a kaita makarantar kwana,
Duk wata siyayyar kayan makaranta Mahmud yayi mata."

Momy da Abba nasiha suke mata akan ta tsaya tayi karatu,
Abba yyi mta Alk'awarin cewa da zarar ta d'auko na d'aya zai saya mata handset wanda take mutuwar so ta ganta tana dannawa."

Ihu ta kurma tana tsalle tana fad'in "nagode Abba indai zaka sayamun waya to ni kuma nayi mka Alk'awarin nice xanyi ta d'aya."

Mahmud ya fito cikin dakakkiyar shadda mai kyau mai tsada fara fesπŸ‘ŒπŸ» wanda ta amshi shi yyi kyau sosai, da key d'in mota a hannunshi."

Ya tsugunna ya gaida momy da Abba, snn ya juya ya kalli dijama Wanda ta tsura mashi ido tana kallonshi, ganin tayi yayi mata kyau."

Tsawa ya daka mata had'ida zare mata ido yace "baki iya gaisuwa bane, kika kafeni da ido kamar baki sanniba."

Turo maki tayi tace "dan kasamu na kalleka,
gani nayi kayi kyau shiyasa nke kallonka."

Kuma zaro ido yayi waje ya yunkura zai kaimata duka, tayi saurin zuwa wurin momy ta b'uya.

"Rashin kunya zakimun, to k'ulelanki karki cinyemun kyau da wnn bakin naki na rashin kunya."

Ya mik'e tsaye yace idan kingadama kifito mutafi kayanki na mota."

Momy ta rik'a hannunta tareda Abba suka yimata rakiya har mota, zata shiga gidan baya mahmud ya Daka mata tsawa yace "keni direbanki ne."

Ta marairaice fuska tace momy Abba Dan Allah kuyi mashi magana karya dakeni."

Abba yace "Mahmud karka kuskura ka dakarmun ummie kaji na fad'a mka."

Murmushi mahmud yyi yace "to Abba."

Snn tadawo gidan gaba ta zauna, ya tayar da mota suka tafi. Tana d'agawa Abba da momy hannu."
Sai da sukaga fitarsu gidan snn Abba yyi murmushi yace ummie na case ce, narasa a inda tagado rashin jin nan."

Momy itama dariya tayi tace "ai mahmud yafita zama case
meye a ciki Dan mata ta kalli mijinta tace yyi kyau."

Abba ya kuma yin dariya yace "ai basu San da wnn mgnarba."

Tafiya sukeyi ba Wanda ya kula d'an uwansa sautin karatun qur'ani kawai yake tashi a mota k'ira'ar sudes,

Tafiya mai nisa sukayi snn suka kawo makarantar mahmud yayi parking a harabar mkrantar yafito dijama na biye dashi a bayanshi."

ofishin shugaban makaranta ya nufa ya gabatar da komai."

Shugaban makaranta ya kira wata prefet ya had'ata da dijama, ta kaita class snn idan aka tashi ta nuna mata d'akin barcinsu."

Mahmud yace "kayanta na mota, suka d'unguma har prefet d'in suka nufi motar mahmud ya shiga fitowa da dijama kayanta harda 'yar katifarta ta kwana."

Bayan ya gama fito mata da kayan ne ya dubeta yace "to dijama nakawoki inda dole ki tsaya kiyi karatu
arabic da boko ko jikinki ya fad'a maki. Bakida wnda zai ceceki ba tsohuwa ba Abba ba momy dagake sai halinki."

Ya juya zai shiga mota tayi saurin binshi da gudu ta rik'e mashi riga, idonta ya cika da hawaye tace "tafiya zakayi kabarni yaya?"
Dan Allah kayi hak'uri karka tafi kabarni bnsan kowaba a nan, nayi maka Alk'awarin duk halina Wanda bakaso zan daina."

Tabashi tausayi sosai domin dijama jininshi ce k'anwarshice Wanda yakeji da ita a cikin k'annanshi rashin jin maganarta ne yake had'ashi da ita."

Yyi k'ok'arin saita kanshi, ya ciro hankacif a Aljihunshi mai cike da k'amshin turare ya mik'a mata yace "goge hawayenki, ta amsa ta goge."

Yace "idan kika tsaya kikayi karatu da zarar nazo yimaki visting k'arshen watan nan zancire ki natafi dake gida,
Idan kuma baki tsaya kikayi karatuba kikaci gaba da rashin kunyar da kika saba, to anan zaki tabbata har sai ranar da kika fara ganewa."

Yaciro kud'i ya mik'a mata bai kuma bi ta kantaba domin tana iya karya mashi zuciya."
Yayi shigewarshi motarshi yayi tafiyarshi yana kallonta a madubi tana kuka tana share hawaye da hankacif d'inda ya bata."

Prefet d'in ta taimaka mata ta kaimata kayanta d'akinsu snn ta nuna mata class d'insu jss1A dijama tashiga jikinta duk a mace sai sharar hawaye kawai takeyi."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )πŸ˜…





Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)





*19*






"Inason yusra tare danida mahaifiyarta saboda batada k'ane ko k'anna, burin a kullum shine muga Yusra cikin farin ciki da walwala."

Babba burinmu a rayuwa shine muga ranar auren yusra."

Manyan mutane shuwa gabanni da Alhazai,
samari da magidanta, sunta fitowa Neman auren yusra amma sai dai tanuna gaba d'ayansu bbu wnda takeso."

Munshiga damuwa mai tsanani da nida mahaifiyarta,
Amma ba yarda zamuyi sai dai muka tashi tsaye da yimata addu'a, Allah ya fito mata da Wanda takeso ya aureta,
Abun mmki sai gashi abun yazo gidan sauk'i kaine Wanda yusra tagani taji tana so.

Alhaji Atiku ya taso daga Inda yake zaune yaxo daf da mahmud ya zauna,
Wanda yayi mutuwar tsaye, saboda mmki, da Al'ajabi,
ko a shirin film bai tab'a ganin rayuwa irin ta wnn gidan ba mai shinfid"e da rashin tarbiya.

Ya dafa kafad'arshi yce "mahmud bazan yi maka doleba, amma nasan bazakak'i 'yataba domin nasan 'yata Yusra ta tara duk wani Abu da d'a namiji yakeso ya samu a jikin macce,
Yusra cikakkiyar macce lafiyayya Wanda bata illah ko ta ina."

Kaje kayi shawara kuma Ku fahimci junanku Allah yayi maka Albarka, tashi kaje ka huta ka kwana da shirin gobe fitar asuba zakuyi."

Mahmud bai samu bakin yin maganaba saboda gaskiyar tayi mashi yawa, hakan ya tashi jiki ba kwari ya fito, ya nufi masaukinshi."

Jiki ba kwari ya shiga d'akinsa Wanda aka ware mashi,
shi kad'ai Wanda yake d'auke da katafaren gado da duk wani abun more rayuwa."

Ajiyar zuciya yasaki ya'ajiye akwatin kayanshi gefe d'aya, ya fad'i zaune a kan gadon yana tunanin, "Alhaji Atiku dake fad'a mashi wai 'yarshi a duniya babu abunda ta rasa."
Kuma ta cika macce ta ko ina, to ya akayi yasan da hakan?"

Babu abunda ta nema ta rasa Wato harda shi kenan yana nufin harta sameshi,
Hmmm lallai kuwa zai nunawa Alhaji Atiku ba komai ake nema a gidan duniyar nan a sameshi ba."

Zai nunawa yusra cewa ba komai take iya samuba a duniya, musamman ni kaina da kwatata bata cikin tsarin matan da nakeso, Asalima koda nayi ido biyu da ita bntab'ajin na tsani wani mutum ba kamar yanda naji na tsaneta."

Mik'ewa yayi jiki ba kwari ya cire kayan jikinshi yafad'a toilet domin yayi wanka yayi sallah la'asar ko zaiji dad'in jikinshi."

Fitowa yayi sanye da jallabiya ya shinfid'a abar sallah ya yatayar sallah."

Bayan ya kammala sallar ne yaji yana da buk'atar Hutu, yatashi daga kan abar sallar ya haye kan gado ya kwanta.

Yashiga tunani Dijama ta fad'o mashi a rai, murmushi yayi ya kuma mirginawa da ya tuna da rashin jin da takeyi a gida."

Koya zata kasance a boarding school?
yasan dai muddun tayi ba dai dai ba a can dukan tsiya zata sha domin bakarantar kwana ba uwa ba uba dole kayi biyayya ga senior dinka."

Yana kwance ruf da ciki. Sai mutum yaji a gefenshi a kwance yana shafa kyawawan k'afafuwanshi da suka lullub'e da gashin jikinshi,
a kan farar fatarshi mai cike da santsi da laushi."

A razane ya mik'e zaune cike da fargaba da b'acin rai ya kai dubonshi wurin wazai gani *Yusra* ce cikin shiga ta wasu k'ana nun kaya riga da siket Wanda iya kacinsu a kan cinyarta rigar kuma mai kamar best duk gaba d'aya Rabin k'irjinta a waje yake." Kanta ba d'an kwali ta zubo gashinta a kafad'a

Kallo d'aya yayi mata ya runtse idonshi had'ida kauda kanshi gefe d'aya,
yayi saurin durowa daga kan gadon cike da b'acin rai."

Ya doka mata tsawa yanuna mata hanyar waje yace "xoki fita d'akin nan shed'aniya kawai."

Zaro ido tayi waje tana mmkin kalamanshi gashi kyakkyawa ajin farko
tana tunanin ya waye Ashe kansa a cikin kwali yake." To meye a ciki Dan tazo d'akinshi ta tab'a jikinshi?"

Cikin rausaya da jan hankali ta nufeshi da nufin kai mashi runguma, yayi saurin zaro ido waje had'ida ja da baya, da sauri
Ya d'aga hannu ya kai mata mata mari a fuska har sau biyu,

Yana huci yana fad'in karki kuskura kice zaki had'a jiki na da naki
Domin ni ko a mafarki bana Fatan Allah ya nuna mun wnn nakasanshin jikin naki mai d'auke da najasa."
Kifita a d'akin nan nace karna tattakaki."

Murmushi tasaki mai cike da takaici tana shafar gefen fuskarta a inda ya mareta duk ga shatin ya tsun hannunshi Nan ya kwanta a gefen fuskarta

Tunda Allah yasa a ka haifeta har ta girma babu wnda ya tab'a yimata fad'a bare tsawa bare har a xo ga dukanta,

Amma gashi abun mmki yau itace wani d'a namiji ke d'aga hannu ya mareta har sau biyu."

A maimakon taji zafin Marin, saima jitayi sonshi da k'aunarshi ya kuma lumkuwa a cikin zuciyarta."

Still idonta a kanshi tana mashi kallon sha'awa.
Tana shafar kunci, murmushi tasaki tace "ina sonka Mahmud,
kuma kasani zan iya jure komai akanka."

Ya kuma kallonta a hasale yace " ni kuma banasonki, ke barima kiji bantab'a jin na tsane wani Abu a rayuwata ba kamar yanda nakiji natsaneki."

Kalamanshi sunyi mata zafi sosai, tasaki dariya mai Sauti tace "kasanyawa zuciyarka sai na aureka domin bantab'a Neman Abu na rasaba a rayuwata, dan haka dole ka soni kuma ka aureni tunda kana k'ark'ashin mahaifina,
Kama d'auka daga yau na zama matarka."

Tana kaiwa nan ta fito idonta yana xubar da hawaye."

Kai tsaye palon daddynta ta nufa, tana zuwa kai tsaye ta fad'a kan jikinshi ta fashe da kuka mai sauti,

Abunda daddy bai tab'a ganiba a idon 'yatshi,

tace daddy ina sonshi, katai makamun ka aura munshi."
Wlh Mundun narasa Mahmud xan iya rasa rayuwata."

Cikin razana ya janyota ya rungumeta yace daina kuka shalele bazaki mutuba a kan wani,
"indai INA da rai da lafiya INA numfinshi a doron k'asa baxaki tab'a Neman wani abun kirasaba, shalele daina kuka ki d'auka har kin aure mahmud,
Har Mahmud ya zama mallakinki."

Dariya tasaki tace "Ngd daddy nah."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )πŸ˜…





Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)





*18*





Mahmud yana komawa gida dama ya shirya kayanshi yau zai wuce Abuja zasu fara trening."

A kwati kayanshi ya d'auka tare da duk wani Abun da yake buk'ata yafito,
Abba yayi mashi rakiya tareda Sanya mashi Albarka yana kuma jaddamashi akan yayiwa Alhaji Atiku biyayya ya d'aukeshi tambakar mahaifinshi."

Mahmud yayi murmushi yace "insha Allah Abba bazaka samu wata Matsala daga gareniba."

Suka had'a baki tare da momy sukace Allah yayi maka Albarka yabaka sa'a aduk abunda kasanyawa gaba."

Yaji dad'in Addu'ar tasu,
ya runsuna k'asa yace "Amin Abba da Momy ngd, Allah ya barmun ku, naci gaba da kyautata maku har k'arshen rayuwata,
idan
khalil ya dawo mmy kice masa na wuce."

Yana fad'in haka yabud'e mota yashiga yatayar suna d'aga mashi hannu har ya yafita get d'in gidan ya d'auki hanyar Abuja."


****************
Bayan antashi break fast Kowa ya fito daga aji yanufi wurin cin abinci dijama kuma taja wuri d'aya gefe d'aya ta rakub'e babu abunda takeyi sai ruwan hawaye."

Tana tunanin tsohuwa, tana nan zaune tana tunani tana hawaye batasan kowa ya watseba ya ba kowa a wajen duk ankoma class."

Bata ankaraba sai saukar bulala taji a bayanta a firgice ta zabura ta mik'e tsaye cike da tashin hankali da tsoro tana kallon wanda ya daketa."

prefet ce tsaye a gabanta tana fad'in ubanme kikeyi a nan kowa ya koma aji ya barki, sai magana ake maki kin kyale mutane."

Zuciyar dijama takawo mata a wuya, dame zataji da kad'aici ko da mugunta,
Prefet taga dijama bata da niyar motsawa daga inda take ta kuma d'aga bulala cike da jin haushi ta kuma doka mata a tsakiyar baya." Sai da dijama ta gantsare saboda axabar zafi, tunda Allah yasa aka haifeta ba'a tab'a yimata irin wnn dukanba."

Tana zaune a inda take bata da alamar motsawa bare ta tashi daga wurin."

Prefet d'in ta kuma harzuk'a cike da takaici ta d'aga balala zata kuma kai mata a karo na uku, tana wani huci."

Dijama tayi saurin mik'ewa tsaye cikin zafin nama ta rik'e bulalar,
ta duk'a ta d'auki prefet d'in saida ta d'agata sama snn tabugata a k'asa, ta karb'e bulalar hannunta tashiga zuga mata ita."

Ganin duka da bulala b'ata lokacine tayi jifa da bulalar ta haye ruwan cikinta tashiga nusarta."

Ihunda prefet d'in keyi shi yaja hankalin sauran d'alibai da malamai suka firfito. Cikin hanzari suna kallon ikon Allah,
D'alibai sun zagayesu suna kallo,
Duk a tunaninsu Aljanun dijama ne suka tashi, dibo da yanda suka dijama ta haye kanta, nesa ba kusaba prefet tafi dijama girma tsawo da k'iba da komai, duk cikin makarantar bbu wanda d'alibai ke tsoro sai ita saboda girman jikinta gashi kuma muguwa ce bata ragawa nak'asa da ita, malamai su kansu sunsan da hakan,

Amma yanzun abun mmki
gata a k'asa k'aramar yarinya 'yar shekara 14
'yar jss1 ta d'agata Sama ta kayar k'asa ta danne tana duka sai ihu takeyi."

Wnn yarinyar Aljanune suka hau kanta bayin kanta bane, inji malaman dake tsaitsaye sunkasa isa wurin su taimaki prefet. D'in."

Dijama tanajin malamai na fad'in Aljanune ai kuwa ta kuma birkicewa taci gaba da jifgarta, ta mak'e murya kamar ba muryar taba tana fad'in "Dan kinga mun kyaleki, kina dukanta,
bakisan ko mu suwaye bane?"

Can wata malama tayi k'arfin halin tunkararsu da kyar tasamu ta fincike dijama a kan prefet d'in."

Dijama na huci tana harararta tana fad'in "idan kika kuskura kika kuma kulamu sai munyi maki illah a makarantar nan."

Ai kuwa malamai sukayo kan dijama aka shiga bata hak'uri had'ida yi mata Addu'oi."

Shugaban makaranta yana office yana aiki labari ya sameshi, cikin hanzari a ka had'a Assambully kowa ya hallara, A ka d'ora dijama a kan Assambully, sai zarar ido takeyi tana turo bki."

shugaban makaranta yashiga bayani a kanta, yashiga nunata yana fad'in "kuyi taka tsantsan da ita kadda Wanda ya kuma kulata a cikinku, idan tayiwa wani daga cikinku wani abun ya hanzarta zuwa wurina ya kawo mun k'ararta ninasan yanda zanyi mata."

Idan kuka lura da abunda tayiwa 'yar uwarku, ya nuna prefet d'in dake rakub'e wuri d'aya sai zare ido takeyi tana sauke numfashi da sauri, alamar ta daku."

Ya isa kubawa kanku amsar cewa Nana khadija Hassan ba ita kad'ai takeba tana tare da Aljanu,
ko Aljanun manyan Aljanu."

Dan haka abunda nkeso daku shine ku kiyaye abunda na fad'a maku a kanta,

Suka amsa da "to malam."

Snn ya umurci kowa ya watse ya koma aji,
Dijama na shiga aji kowa ya kama kanshi da ita,
Hakan malamin English yashigo suka fara karatu gadan gadan."

Bayan antashi daga makaranta kowa yanufi d'akin barci domin cin abinci suyi wanka ayi sallah, snn akoma karatun marece wasu kuma sutafi islamiya."
Dijama taja tayi tsaye a wuri d'aya domin batasan inda zatajeba."
Anan idonta ya fara cika da hawaye."

Prefet d'in da tafara gani farkon zuwanta Senior Rukayyah ita tagani a gabanta tana mata murmushi ta rik'a hannunta suka nufi d'akinsu inda ta ajiye mata kayanta."

Senior Rukayyah tun lokacinda taga dijama taji tashiga ranta,
Hakan kuma a nan take taji ta kamu da son Mahmud lokaci d'aya, wnn dalilin yasa tad'auki d'amarar taimakawa dijama. A kan karatunta domin ta fahimci burin yayanta kenan tayi karatu."

*****************

Mahmud ya sauka Abuja lfy, Inda yaga karramawa wurin Alhaji Atiku.

Yana zaune cikin katafaren palon gidan Alhaji Atiku commondent anzagayeshi da kayan ciye ciye da abinci kala kala."

Alhaji Atiku a gefenshi nesa dashi yana mashi bayanin yanda zasu fara trening d'in gobe."

Sai jiyaniya sukeji tana tashi a harabar gidan, mahmud baiyi mmkiba dibon da yayi tundaga farkon layin gidan har zuwa cikin gidan
sojojine birjik aka Zuba a wurin."

Yashiga tunanin wata k'ila bak'ine Alhaji Atiku, yayi

Bai gama tunaninsaba aka bud'o k'ofa aka shigo batareda anyi sallama ba."

Ganin murmushi yayi d'auke a kan fuskar Alhaji Atiku, waigawa yayi domin ganin mai yake kallo yake yiwa murmushi."

Wata tsaleliyar budurwa yagani fara fes da ita wanda bazata wuce shekara 23 ba a duniya.

tana da kyaunta ba laifi, ta sanya riga da wando wad'anda suka bayyanar mata da duk ilahirin surar jikinta, ta d'ora wani figigin gyale a kanta Wanda dashi da babu duk d'aya. Fuksarta sanye da bak'in glass hannunta d'aya d'auke da katuwar waya. D'ayan kuma d'auke da jaka.
Gefen hannunta dama da hagu, sojojine ke take mata baya."

Hannu ta d'aga masu tare da ya tsine fuska a kan suyi tafiyarsu,
Saida suka Sare mata snn suka juya suka tafi."

ganinta yayi taje cikin shagwab'a ta haye a kan cinyar Alhaji Atiku."

Mutuwar tsaye Mahmud yayi ya tsura masu ido yana kallon ikon Allah."

Cikin shagwab'a take cewa daddy na gaji dayawa."

Hannu ya sa yana shafa bayanta yana "fad'in Ayyah sannu shalele kitashi kitafi kiyi wanka ki huta momynki na ciki, tayi maki tausa."

Turo bki tayi tace "ni kai nakeso kayimun."

Dariya yasaki mai sauti yace "nida kaina shalele?" To tashi kitafi gani nan zuwa yanzun nan

Yace baki gaida yayankiba gashi nan zaune, ya Nuna mata Mahmud da yasaki baki yana kallonsu."

Taya tsine fuska ta kai dubanta ga mahmud, dan bata lura da akwai wata halitta a wurinba,

Ido biyu sukayi da Mahmud ta tsayar da idonta gareshi ta kasa d'auke idonta a kanshi gaba d'aya kyanshi da haibarshi ya tafi da imaninta."

Mahmud kuma lokaci d'aya yaji ya tsaneta, saboda daga ganinta bata da tarbiya da kamun kai a tare da ita."

Wow ta furta had'ida mik'ewa tsaye tanufi wurin mahmud tasanya hannu zata shafi gefen fuskarshi yayi saurin rik'e mata hannu had'ida had'e fuska yayi jifa da hannunta gefe d'aya saura kad'an ta fad'i k'asa"

Bata damu da abunda yyi mataba, illah tazo gabanshi daf da shi ta zauna yanda suna iya jin saukar numfashin junansu tace "kana da kyau wanda baya misaltuwa, ina sonka."

Ta juya ta dubi Alhaji Atiku tace "daddy wnn yana da kyau ina son shi zan aureshi."

Alhaji Atiku yasaki dariya, yace shalele ai yayankine Abu yazo gida kenan, ki sanyawa rayuwarki kinsameshi, harma kin aureshi."

Mahmud yayi saurin d'aga kai sama ya dube Alhaji Atiku cike da mmki."

Shalele tasaki dariyar jin dad'i, tace "nagode daddy na dan haka nake sonka fiye da momy, tana kaiwa nan tafita cike da jin ddi

Tana fita Alhaji Atiku ya maida kallonshi a kan mahmud da murmushi a kan fuskarshi yakira sunanshi.

"Mahmud wnn itace 'yata kwaya d'aya tilo a duniya sunanta *YUSRA*
A duniya babu abunda yusra ta nema ta rasa."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_)πŸ˜…






Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)



*20*






Tafe take d'auke da robar abnci, a hannunta,
tuwon masara da miyar karkashi, tafito daga danie tafe take tana 'yar wak'arta wadda taji d'alibai nayi."
.
A gefen wasu manyan 'yan mata ta wuce da alama prefet ne
Taji suna fad'in "sai munyi mgnin wann shigiyar yarinyar badai ance Aljanu garetaba,

Idan dare yayi musameta a. D'akin da take,
ai a d'akin senior Rukayyah take, musameta a can idan tayi barci muci ubnta."
Suka sanya dariya harda tab'awa."

Dijama na gefensu basu lura da itaba, amma ta fahimci da ita suke,
Ta girgiza kai, ta kuma shan jinin jikinta saida taga wuce warsu tabisu a baya
Sai da taga inda suka shiga snn ta juya ta nufi d'akinsu."

Duk d'alibai kowa yanacin abincinsa amma bnda dijama, senior rukayya ta tambayeta meyasa batacin abinci?"

Murmushi ta kakaro tace batajin yunwa ba ynzun zataciba."

Misalin k'arfe 9pm kowanne d'alibi ya kwanta indai Junior ne."

Itama dijama ta kwanta barci yak'i d'aukarta gudun kartayi barci prefet d'in d'azun sushigo suyi mata illah duk a tsorace take."

Ai kuwa a can bayan d'akinsu taji tahowarsu suna fad'in ga d'akinsu nan mushiga muci uwarta."

Ai kuwa tanajinsu tayi saurin durowa daga kan gadon ta d'auki robar miyar tuwonta tanufi bakin k'ofar d'akin,
Kasan cewa k'ofar d'akin shafe yake da siminti,

Robar miyar ta d'aga gaba d'aya ta wanke k'ofar d'akin da miyar karkashi, ta juya takoma kan gadonta ta kwanta."

Su biyar ne ko wannesu da zangareriyar bulalarshi, a hannunshi suka tunkaro d'akin gadan gad'an suna zage zage,

Suna kawo wa kan dangaramar bakin k'ofar d'akin,
dukansu suka darje k'afa suka fad'i,
had'a baki sukayi gaba d'ayansu suka saki ihu suna fad'in "wayyo Allah jama'a kukawo mana d'auki,
Wnn tace k'afarta wnn tace wyyo hannunta wata kuma tace k'ugunta."

Dijama na kan gado ta lafe kamar barci, takeyi
Dariya ce kunshe a cikinta."

Anan d'alibai suka kawo masu taimako aka tallabesu aka d'aukesu daga wurin zuwa d'akinsu."

Kowa sai mmki yakeyi meyasa suka fad'i kuma a lokaci d'aya?"

Washe gari ko waccensu tayi targad'e a hannu wasu kuma a k'afa, suka jera suna tafiya zasu nufi class d'insu."

Dijama itama cikin shirinta na makaranta, sanye take da uniform, ta gabansu ta gifta ta wuce suka bita da kallo basuyi mata maganaba, d'aya daga ciknsu ta wurga mata harara,"

Suna ganin hakan suka had'a baki sukace daina harararta karki kuma janyo mana wani sabon bala'i,

Ina ganin Aljanun wancan yarinyar manyan Aljanune ko furtawa kayi zaka daketa, sunajinka zasu rama mata."

D'aya daga cikinsu tace nidai daga yau ko kallon inda take bazan kuma yiba wlh ba yarda za'ayi akasheni a banza ni kad'ai ce iyaye na suka Haifa."

Dukansu suka had'a baki sukace muma ai mun kyaleta, ,wurin da takema baxamu kuma bi ta wurinba."

Duk abunda suke fad'i shugaban makaranta yana bayansu basu saniba, ya kuma fahimci ko a kan waye suke magana."

Mmki ya shigayi da tunanin kalaman yayanta Mahmud a lokacin da ya kawota, saida yayi ta bashi hak'uri akan duk abunda dijama zata aikata na rashin jin magana yayi hak'uri dan Allah karya kureta, amma kuma ya hukuntata,
Daga k'arshe Yayi mashi kyautar kud'i mai tsoka yatafi."

Dama yasan batajin magana kenan."

Kai tsaye class d'insu dijama ya nufa, tana zaune a kan kujera ta d'auko
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment