Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA RETURN...*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



Rubutawa...
*JAMILA MUSA...*




*SAI NA AURI D ' K*



🅿 ------ 1


Da sunan Allah mai rahma mai jinƙai....



Dakel aka fiddoshi daga wurin , dan bashi da hankali akan ɓarar da kuɗi. Idan zai kwana a haka baya gajiya kuma ba zai daina ba , zaiyi ta zubawa ne baya gajiyawa , haka kuma idan zai bayar yake kyauta maisa ɗimuwa.


Wace ce ita...............???


Wata irin dariya yakeyi bayan an fito dashi yana tsaye gaban Momy data bishi da kallon takaici , hahahaha yaci gaba da dariya yana kallonta , nima binshi nayi da kallo ina murmushi saboda ba ƙaramin kyau yakeyi ba idan yana dariya....

Momy tace idan ka gama haukar ka ɗauki matarka ku tafi gida , daina dariyar yayi tare da taɓe fuska , a yatsine yace ai ba tare nazo da ita ba. Murmushi mai cin rai nayi , ba tare dana sake kallon inda yake ba. Kafin inyi magana akaja Momy wai anayin faɗa , binta Rabiya tayi da sauri ni kuma na kalli Dikko ƙasa da sama a yatsine nima nace , tir tittir nabi tsoho ya ɓatamin wanka , nine tsohon ? Ya tambayeni yana nuna kanshi.

Yadda ya ɓata ranshi yasa nayi shiru ina kallon ƙasa , jinjina kanshi yayi cikin ɓacin rai sannan yace Allah ya maida mu gida lafiya , banyi magana ba kuma banyi gigin sake ɗagowa na kalleshi ba , nine dai tsoho ko ? Ya sake tambayata da yanayin ranshi ya mishi babu daɗi , hmmm tsoho , ƙara jinjina kanshi yayi cikin ɓacin rai , mtswww , ya wuce daga wurin yana magana ƙasa².

Da sauri na ɗago ina kallonshi dan harya tafi ya sake dawowa , nine dai tsoho ko ? Dan ina tausayinki kenan yasa kika raina ni ? Har nine zaki kalli tsabar idona kicemin tsoho tsabar kin ɗaukeni sallau , duk shekarar nan ni banma samu wanda ya ɗaukeni sakarai ba kamar ki , ajiye kai yayi da ɓacin rai , zaki ci gidanku Allah ya maida mu gidan lafiya zaki faɗamin nine tsohon idan na riƙeki , yana faɗin haka ya wuce , a firgice na juya bayana da sauri , Rabiya ce ta dafoni ta baya , nayi tunanin shine ya sake² dawowa.

Ana fita da Dikko itama ta sulale ta fice daga cikin holl in da farin cikinta , ta wani ɓace abunta ba tare da anga fitarta ba , jikin motar ta , ta tsaya ta saka hijabi da niƙaf , bayan ta gama ta wani shige tayi layar ɓata abunta , wannan shine ɗabi'arta , hijabi da niƙaf , bata rabuwa dashi ita musulma , idan kuma zata tafi bariki bata fita da motarta dan gyaran tako.....

Wai ke me zakiyi mata ne kike neman ta ? Barni na ganta sai in ɗauki mataki a gabanku , tou wai yaushe suka saba haka har ya saki jiki yana mata ɓarin kuɗi a gaban bainan nasi....? Waye ma zai iya sani ? Tsoki ƙawarta tayi cewa wai kema Jiddah bazaki bar wannan banzan Dikkon ba ? Sai kace Dikkon diamond ? Murmushi Jiddah tayi tare da kallon Mardiyya cewa faɗa mata waye Yaya D ' K.

Cike da tsantsar soyayyar Dikko Mardiyya ta fara rattafo mata , hmmm ai ya wuce duk inda hankali baya tunani , saima kin ganshi , gashi mai kyau , ɗan gayun bala'e uwa uba ga kuɗi ga mulki , idan yana magana sai ya baki sha'awa , gashi sakatacce wani irin kallo yakeyi mai burgewa , Dikko matashi ne mai wayewar kai , buɗewar ido da gogewar rayuwa amma bashi da mutunci ko kaɗan , damen ɗan iska ne , kuma shiɗin ƙyalƙyal na lariya ne , tantirin kwallon ɗan iska ne yanzu mutum anjima bai sanki ba , yana da baƙon hali , haƙurin zama dashi sai ɗiyar ɗan caca , dan itama "yar tasha ce. Kinsan auren tasha baya ƙarewa saida aci uban juna yanzu , anjima kuma a zama masoya , duk da biyu Mardiyya tayi wannan maganar , sanin manufarta na faɗar haka sai ita da kanta.

Ƙawar Jiddah tace tou ni me yasa baku kirani na ganshi ba lokacin daya shigo ? Murmushi Jiddah ta sakeyi tare da cewa har hanzu baki makara ba , Mardiyya bata hotonshi ta gani , a duniyance Mardiyya tace waye yaba Mardiyya hatimin nasara ita ba jikar matsafi ba , ai hoton Dikko sai wurin matarshi , gaba ɗaya suka ɗingumo suka yo wurina !

Sultana Momy tace muje in ajiyeki gida , tou na faɗa tare da kallon agogon wayata 11:22am gaba nayi ba tare dana sake magana ba , ta baya Jiddah ta riƙomin riga , da sauri na juyo dukana dan ganin waye ya rainamin wayau haka ? Cikina ta kalla sannan kuma ta kalleni amma yanayin fuskarta ya nuna taji babu daɗi , amma dake "yar duniya ce , saita wayance da murmushi cewa ina ta magana shiru nace ai nasan bakiji ba , banyi mata magana ba na tsareta da ido , dafe kafaɗa ta tayi kamar ƙawarta tana cewa Aunty Rabiya ai muma a gidan Yayan zamu kwana.

Rabiya bata kalleta ba tace ai kina da numbershi ki kirashi ki faɗa mishi , ai basai na kirashi ba kuje gidan muma muna zuwa bayanku , Rabiya bata sake magana ba ta wuce , sauke hannun Jiddah nayi daga jikina nima na wuce muka tafi , har muka zo gida Rabiya batayi magana ba nima banyi ba , a waje ta ajiyeni ta wuce. Ni bansan abinda ya haɗasu ita da ɗan uwanta ba , ni na shiga da kaina ciki raina a jagule , a get na biyu na haɗu da Ashiru , yana gani na ya tsaya yana cewa ranki ya daɗe mai gida yace naje na taho dake , ko inda yake ban kalla ba kuma banyi masa magana ba na wuce , shi kuma ɗayan marar kunyar a get na ukku na haɗu dashi shima fita zaiyi , wato bai gaji da iskancin ba zai sake komawa , kenan dawowa yayi gida ya sake sabon wanka , yanzu garin nashi ya waye , ko wane bawan Allah idan dare yayi yana gidanshi yana bacci , koba a gida ba duk inda kake idan dare yayi zaka samu natsuwa , idan bakayi bacci ba , tou kana kusa da ubangiji kana bauta masa a dai² irin wannan lokacin , amma banda Dikko daya maida dare lokacin huɗɗoɗinshi.

Shima magana yayi min wai daga ina nake ? Kuji fa ? Wai ma daga ina nake ? Kamar ma baisan ina ya baroni ba , shima ko inda yake ban kalla ba na wuce , An mata bakyaji ina miki magana ne ? Ban dawo ba kuma ban tsaya ba na wuce , da ribos ya biyoni saida yazo inda nake yace ke Yarinya bakiji ina magana ne ? Canja hanya nayi naci gaba da tafiya , An mata dake nake fa ? Ganin Sultana tabi hanyar da zata shigar da ita ciki batayi mishi magana ba , yasa yayi parking ya fice da sauri yabi bayanta.

A palo na zauna ina cire takalmi na , idona cike da hawaye , ai dama Inna ta faɗamin Dikko ƙyalƙyal na lariya ne , bana iyawa da duniyancin shi , tace Dikko ba mijin aure bane ba , amma na kafe kai nace ni ina sansa a haka , yau naga kaɗan daga iskancin shi. Goge hawayen da suka gangaromin a fuska nayi tare dayin shashshekar kuka , shine saida aka tara taron dubu da dubu ya fito yana ma wata liƙi dan ya nuna ma duniya ni ban kai mace ba , ni ban kai sahun irin matan da yake aura ba , ya nuna ma duniya ni ba'a bakin komai nake ba a wurinshi , Momy tace masa ya taho dani gida yace shi bashi ne yazo dani ba , ashe kuma gidan zai taho dan ya sake nunamin ban kai macen dashi zai saka a gaban mota ba ko wayewa yasa ya taho ya baroni , hakan bai mishi ba zai tura Ashiru ya ɗaukoni dan ita budurwar tashi taga shi bashi ne ya taho dani ba , ta gani saida shi ya koma gida sannan ya turo driver ya ɗaukoni , dole Ashiru ya ɗaukoni mana tunda dare yayi yanzu ne yasan amfani na , maganar Inna ta sake duwomin da tace , haka zaiyi ta ɗura miki ciki kina haifar mishi "ya "ya nan ne kaɗai matsayinki.

Da sallama ya shigo palon , takalmana na ɗauka nayi gaba , ban ansa sallamar ba haka kuma ban kalleshi ba , An mata baki lafiya ne ? Yayi maganar yana biyo bayana , ban mishi magana ba har ɗakina , ina shiga na fara tattara kayana , miye haka kikeyi ne ? Haba An mata wai duk miye na fushi ? Kiyi haƙuri akan abinda ya faru dan Allah , goge hawaye na sakeyi naci gaba da tattara komai nawa , kusa dani ya matso yace An mata Dikko zaki ma yaji ? Haba jarumar mata ban sanki da irin wannan halin ba , kiyi haƙuri ya ƙarasa maganar yana riƙeni jikinshi , kalleni , saida na sake goge hawaye na kalli Dikko , nine ? Yayi maganar kamar zaiyi kuka , banyi magana ba ina kallonshi shima ni yake kallo , a kasalance yace kinyi haƙuri ko ? Ya ƙarasa maganar yana warware fuskarshi da yanayin burgewa , har yayi surutunshi ya gama bance masa kaci kanka ba , saida ya gama rattofo yaudararrin kalamanshi yai tafiyarshi ya barni.

Tun daga ranar Dikko ya sake ɗaukewa , ma'ana ban sake ganinshi ba , nima ban sake komawa gidansu ba , Jiddah kuma a ranar waje ya ganta masu gadi sun hanata shiga , saida yayi mata rashin mutunci mara ɗaura zani ya ƙara da cewa dama yana cike da ita akan abinda tayi ma Papi , akwai lokacin daya iba mata zai sameta har gaban uwarta anan zai nuna mata tsabar rashin mutuncin shi , duk su basu san halinshi ba labarin iskancin shi sukeji. Tou zaizo har Kadunar , shiru yayi yana kallon wayarshi , bayan wani lokaci yaci gaba da cewa tou a ranar zataji shi yadda yake , kuma idan take sake shiga sabgar iyalinshi kota kuskura ya sake ganinta a goruba koba gidanshi tazo ba , ya jinjina kanshi tare da cin taya ya barɓaɗeta da ƙura , ta gane abinda yake nufi , kawai zaibi ta kanta ne kamar yadda yaci ƙasa ya wuce abunshi....

Ko a makaranta , haka nake kasancewa suku². Banayin wata walwalla , ina ɗauke da damuwar da tafi ƙarfin shekaru na , cikin kwanakin da basu wuce biyu zuwa ukku ba nayi duhu na rame , kuma ba rashin ci ba nasha , babu abinda na nema na rasa , ina tunanin Dikko ne kawai dakemin wahalar gani , dan yanzu ankai gafen dako text na tura mishi baida lokacin bani ansa , idan na dameshi sai yacemin wai bansan yadda abubuwa suka sha mishi kai ba , saiya rufeni da faɗa ta waya , idan kuma nace na taga barinshi Inna bama zata anshe ni ba , haka nan kawai na fashe da kuka a class , kuma gaba ɗaya ajin yayi shiru saboda malamin dake ciki , duk wanda ke cikin kilas in maza da mata kowa ya juyo yana kallona , miƙewa nayi na fara tafiya ina ƙara yawan kuka na , har nayi nisa. Na dawo na ɗauki sch bg ina da makullin mota naci gaba da kuka ina fita daga cikin ajin ko malamin baimin magana ba.

Daga makaranta kai tsaye gida na nufa har naje kuka nakeyi , dakel nayi parking na fita ko gabana bana gani na shiga ciki , a palo na sameshi zaune , hankalinshi kwance yana cin abinci baida wata damuwa , kenan idan ina makaranta yake dawowa gidan yayi duk abinda zaiyi ya tafi kafin in dawo tunda yasan lokacin dawowana , sannu da zuwa ya faɗa tare da bina da kallo , cike da ɓacin rai na nufi kicin na ɗauko wuƙa ina cewa saina kashe ka , da sauri ya tashi yana innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , An mata kinyi hauka ne ? Yake tambayata yana nuna saman ƙoƙon kanshi , ey hauka nakeyi , na faɗa ina matsawa kusa dashi , da sauri ya koma can saman inda ake jingina na kujera idan an zauna ya zauna ƙafafuwanshi a saman wurin zaman , yace waye yace miki ana wasa da wuƙa ? Ba wasa nake ba kashe ka zanyi kowa ya huta na gaji da baƙin halinka ko kuma ka sakeni in kama gabana , ta baya ya sauka yana dariya. Lallai An mata amma ban taɓa sanin mahaukaciya bace ke sai yau. Ai dole zakacemin mahaukaciya tunda ka samu mai hankali , riƙe wuƙar nayi dai² yadda zatamin sauƙi wurin burma mishi nace ka sakeni kafin in tuno maka asiri , dafa kujera yayi yana kallona ,

Zagayawa nayi inda yake har yanzu ban daina kuka ba , dariya yakeyi sosai , cikin dariya yake cewa ni idan wasa kikeyi nawa na gaske ne , ina nan yadda kika sanni ban canja ba. Dan kinga kwana biyu na ƙyaleki kike duk iskancin da kikaga dama , cike da tsantsar ɓacin rai yazo kusa dani yace cakamin wuƙar , cikin hayaniya yace caka׳ , shiru nayi nasa wuƙar ta kalli ƙasa , ƙaryar rashin kunya dakin sake nunamin ita dasai na burma miki ita kin mutu kuma na kashe banza , bari jin Mama tace ke taurin kai gareki , ke kuma kina iƙirari idan kika sa kanki abu babu wanda ya isa yasa ki bari ni nafiki taurin kai da rashin kunya , zanje in zauna ko motsi mai ƙarfi kika sakemin sai kinga yadda zanyi dake , yayi maganar yana komawa inda yake yaci gaba da cin abincinshi.

Kuma koba yau ba saina kashe ka , ke idan wasa kike ni zan kasheki da gaske ne , a tsorace na wuce ban sake magana ba , shi kuma yace zoki ki zauna muyi magana , ƙara fashewa nayi da kuka nace bazan zo ban , ki daina ganin ina lallashin ki , duk ranar da kika cika ni idan kika bari na riƙeki jikinki zai baki labari yayi maganar yana nunamin belt in dake ɗaure ƙugunshi , a wurin da nake wucewa na yadar da wuƙar na wuce ciki ina gunguni , kuma saina ɗauki number duk wata mace a wayarshi , anan zan gano wace ce zai aura saina cicci ubanta.....

Satina ɗaya rabona da zuwa makaranta , kuma Nabeela da kanta ta tabbatar min cewa Yaya zaiyi aure , zai auri ɗiyar ƙanwar Dady da suke Baba ɗaya , { idan baku manta ba shi Dady a ɗakinsu shi ɗaya ya rage , "yan uwanshi kaf sun rasu sakamakon gobara data cinyesu , su kuma sauran matan bayan an basu kuɗi ko wace ta kama gabanta ita da "ya "yanta , dalilin auren ne yasa yake aikin gidanshi na G R A , kuma itace yarinyar da yayi ma liƙi , Dady ne yakejin farin ciki Dikko zai auri ɗiyar "yar uwarshi kuma shine yayi mishi tayin auren dan ƙara ƙarfafa zumincinsu a matsayin shi na babba , wanda shima Dadyn Mamar yarinyar ce ta nuna masa alfanun hakan , tunda tayi tayin Dady ya karɓa dan cika farin cikin mahaifinsu da yace yasan ko baya raye Umar zai zama jigo ga "yan uwanshi , wanda shima Dadyn yake fatan Dikko a zama bango ga "yan uwanshi mata idan baya nan , shi yasa ya miƙe tsaye saida ya tabbatar Dikko ya daskaru hankalinshi ya kwanta tare da binshi da addu'a , Momy ce bata san auren dan ta raina ahalin Dady yadda mai tunani baya zato , wannan dalilin ne yasa duk suke fushi da Dikko , da Momy ta fara wani tirje² Dady yace ta bari kar rabo ya kashe ta , ai itama an auri nata "yan uwan amma ba'a dace ba , dan haka a bari a taga gaba ko a dace dan auren zuminci abu ne mai kyau , wannan kenan. }

A makaranta kuwa an kira Dikko cewa na daina zuwa makaranta , su kuma ƙawayena har gida suka zo , suka tambayeni abinda yasa nayi kuka a waccan rana , da abinda yasa na daina zuwa makaranta , na faɗa musu mijina ne zaiyi aure , kuma auren ma na zuminci dan dai kawai su haɗemin kai da "yar uwarshi ni a juyamin baya , na kuma basu labarin liƙin da yayi mata , wanda ni bansan dalilin da yasa yayi shi ba , juyamin baya da rashin san kasancewa dani a inuwa ɗaya , rashin dawowa gida da wuri sai nayi bacci , fita tun safe kafin in tashi , da dai wasu halayya dani bansan yana dasu ba sai yanzu da zai ƙara aure , shine Farisa tacemin ai mazan yanzu idan ana raga musu iskanci suke na wuce shari'a , kar in wani damu kuma na daina ajiye damuwa idan ba haka ba hawan jini zai kamani na mutu a banza in bar yarana , shi kuma zaiyi jimamin rashina na kwana 3 daga nan yayi aurenshi ya buɗe sabuwar rayuwa ya manta da labarina , "ya "yana kuma ayi ta gana musu azaba , su tashi babu wani galihu ko "yanci kamar almajirai , itace ta bani shawara ƙauracewa ɗakin miji , daina bashi abinci , rashin kunya kuma saina cire shakkun Dikko dan matsoraci baya zama gwani ko waye , ta ƙara da cewa na fita sabgar kaf ahalin miji dan dasu ake haɗa duk munafurcin , wannan duk ɗabi'ar mahaifiyarta ne , idan suka samu matsala da Dadynsu bata zuwa ɗakinshi kuma batayin yaji saida tanayin gayu mai ɗaga hankalin namiji , tace idan anyi yaji babu ta inda za'aga miji bare a samu damar gasa masa aya a hannu , a gida za'ayi duk masifar ayi a gama , tou kundai ji matan aure , shine fa tun daga wannan rana na birkice na zama fitsararriya , abun bai tsaya a iya Dikko ba ya shafi kowa da kowa.

Wani irin gigitaccen mari na yankawa Papi tare da ce masa dan ubanka waye yace ka zubarmin lemu a kafet......? Tashi Papi yayi ya tafi wurin Dikko.......! Da fatan mai karatu ya gane...........???

Ci gaba nayi da cewa ni banajin tsoron wani zare²n idon banzar mutum , idan taƙamar mutum yace zai dakeni saina bari ya kwanta bacci in mishi wanka da ruwan zafi ko in dafa mai in toye mishi fuska , ko inda nake Dikko bai kalla ba yaci gaba da rirriga Papi da yaƙi ya daina kuka , ni har an nunamin iya zare ido ? Ko rashin kunyar kafi ni iyawa ne ? Nima nan na iya ai shiru² ba tsoro bane ba , kace tuf ka gani , saboda nasan nayi masa nisa , dan tunda na mari Papi na koma matakal bene na zauna daga wurin nake yanko magana , { idan kun tuna benen g r a ya sauke lokacin dana faɗo , na goruba kuma na hau nace zan faɗo ? Yace shine zai jefani na faɗa na mutu , wanda bayan na gudu da yake bani labari yace shi ya ɗaure kanshi da wayar wuta ya faɗo daga sama , wanda ya tafi doguwar jinya.... } fita yayi yaje ya bada Papi ya dawo , har lokacin ban daina zage² ba , shine yajani yakaini ɗakinshi ya rufe bakin rashin kunya.

An mata wai meke damunki ne ? Gaba ɗaya kin zama mahaukaciya , cike da ɓacin rai nace kaine mahaukaci........ , duk girman kwanakin da kake saukewa ai ba'a kaina kakeyi ba , wannan matsalarki ce , tunani da neman mafita ya rage naki ƙaramar yarinya......! Riƙe yatsana yayi a bakinshi....... ` saida ya gama duk abinda zaiyi ya shirya ya fice abunshi.....

Wasu irin zafafan mata ne zagaye dashi ,,,,,,,,,,,,, duk girman daren nan batajin shi bata kuma ganin shi.````, tsaye take a jikin madubi , fitowarta daga wanka kenan , da wayarta ta saita kanta bayan ta danna video
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On KWARATA RETURN
avatar
fatima-kasim

3 months ago

Reply

Naji dadi sosai sosai Allah y kara basira

avatar
daiy

3 months ago

Reply

Replying to fatima-kasim

Ameen muma munji dadin kasancewarki anan.

Please Login or Register in order to submit comment