Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yana kallon kumburarriyar fuskar Saade da ta hade ta cakude ta yi jajir.
Wa ya kawo ta? Ina Yareeman? Dukanta ya yi?
Muryarsa ta karye gabadaya cikin debe tsammanin abin da Hibbani ta gaya masa.
Fulani Bilkisu ta yarfar da hannu, ta ce, Wallahi Allah ban san komai ba. Yadda ka ganta ni ma haka na ganta. Na kuma yi tambayar duniya ta ki ce min komai.
Jikinsa har rawa yake ya ce, Bari in kira shi a waya, amma in ya tabbata abin da aka gaya min ne zan sa kafar wando daya da Yareema.
Yana kokarin kiransa ne sai ga kiran Yareeman ya shigo. Ya amsa wayar ba tare da ya ce uffan ba.
Daga can bangaren Yareema ya ce cikin wata irin murya da Askirama ya kasa gaskatawa ta Sagirunsa ce.
Alanguburo, Allah Kawun jo (Allah ya kara maka yawan rai) a taimake ni a gaya min ko Saadatu ta zo Askira???
Kamar ba zai yi magana ba, amma tabbas yana son amsa guda daya kwakkwara daga bakin Yareema.
Ka fara gaya min abin da nake son sani, sakinta ka yi?
Yareema ya wani irin girgiza kai, tamkar Askirama na ganinsa, gumi ya wanke masa fuska, muryarsa na hardewa ya ce, Babu saki tsakani na da Saadatu har abada! Babu wulakanci tsakanina da amanarka har abada. Sai kauna da soyayya mara yankewa domin na samu fiye da abin da ka kwadaita min samu cikin aurena da Saadatu
Na je in kai resignation letter ga V.C in cike takardu in dawo mu taho tare sabida wata yar matsala da na samu wajen aikin nawa, kafin in dawo sai sai sai.
Ya kasa karasawa. Ambatar sunan mahaifiyarsa a wannan gabar ya san daidai yake da raurawar igiyar aurenta kamar yadda ya tabbata nasa auren yana rawa a halin yanzu, in har komawar Saade gida ya tabbata kuma ya je kunnen Askirama.
Wata tsawa da Maimartaba ya daka masa sai da ta hautsina gabadaya kayan cikinsa, Ba za ka gaya min abin da nake son sani ba? Sakinta ka yi ko aah?
Yareema ya kifa kai jikin kujera ya saka kuka kamar Mai Askira na gabansa.
Ban sake ta ba wallahi ban sake ta ba Ya Gumsu ce ta kore ta, kuma Uche ya gaya min har dukanta sun yi. Im on my way nowto Askiratunda alhamdulillahi ta iso gida.
Waye ya gaya maka ta iso gidan? Ka fada wa Babarka ta share dakin Saadatu ta zauna, don nata dakin na rufe shi daga yau.
Kai kuma bana bukatar ganinka gabana ka je ta aura maka duk yar uban da ta ke so.
Yareema kadan ya rage ya zauce, bai iya sauraron bakaken maganganun Askirama ba ya ji sallamar Ya Gumsu da Aunty Daja.
Ya Gumsu ta dube shi ta kyabe baki, ta ce, Yanzu sabida na raba ka da wannan jarabar shi ne ka ke yanka wannan uban gumin? Sannu tattabara sarkin soyayya. Ai da ma waadin watanni uku muka yi da kai za ka mayar wa uwarta yarta yadda ka karbe ta. To na ji shiru, shi ne na zo ni da kaina na sake ta, ka gaya min hadisin da ya ce ba ta saku ba.
Aunty Daja ta karbe, Ban da abinka Yareema, uwarka gata ta ke maka, yanzu aure na neman ci gaba ake yi ba na komawa baya ba. Kamar ka Yareeman Askira mai jiran gado ka rasa matar aure sai agolar gidanku? Ban da uwarka tsayayya ce ai da yanzu labari ya sha bambam.
Bai san sanda ya kai mata kutufo ba, ta yi maza ta kauce ya naushi iska. Ya daga ragaitattun idanunsa ya dube ta.
Aunty Daja ki ke ko wa? In uwata za ta shiga hurumina in kyale ta ban da ke wallahi. Na auri agolar tunda ke kin auri Minista ina ruwanki? Agolar na ga ta fi dacewa da rayuwata, sai ki zuba ruwa a kasa ki sha kun kore ta kamar yadda Askirama ya kori uwata.
Bai ankara ba ya ji hawaye na son zubo masa, don haka ya tashi ya bar wajen. Ko a jikin Ya Gumsu, ta ce, Ya dade bai kore ni ba, tunda ya auri uwarta na kara gane kansa? Sau dubu gara min tubabbiyar nan a kan diyar Bilkisu. Dadin abun ina da inda zan zauna ko ba gidanka ba. Kuma ba zan bar gidan nan ba sai ka rubuta takardarta ka ba ni
Yareema bai tsaya ba ya nufi motarsa. Yana ji Aunty Daja na lallashin Ya Gumsu, ta yi hakuri tunda dai sun kore ta ba sai ya yi saki ba, ko ba komai sun kunsawa Bilkisu bakin ciki, kuma in tana son yarta ba za ta barta ta dawo ba a yadda suka ci zarafinta.
Yanzu abin da ya kamata ki maida hankali a kai shi ne, nema masa auren Hajjaju.
Ya Gumsu ta balla mata harara tana zama cikin royal chairs din Saade, ta ce, Ke ma kina wasa ne, wa zai karba masa auren a halin yanzu na taba yar mowa? Da na sani ma ban kore ta ba, dagewa na fara yi aka auri Hajjajun, bayan ta shigo sannan mu san yadda zamu yi da ta gidan, amma yanzu na tabbata na bata goma ne daya ba ta gyaru ba. Tunda ki ka ji ya ce ubansa ya kore ni.
Ya Gumsu ta fada cikin damuwa, wadda ba ta karasa har kasan ranta ba.
Aunty Daja ta yi tsaki, ta ce, Haba Gumsun Askira, ke ce fa uwar Yareema, uwar Ya Maira, masarautar Askira taki ce ke da yayanki, kin taba jin an saki Gumsun gari uwar iyali?
Ai sai dai ya yi fushinsa ya gama ya sauka, amma ba sa saki, shi ya sa na tabbatar miki yaron nan ba zai saki yar Bilkisu ba, mu dai yi kokari ya yi aure na shiga tsara ki manta da wata yar Bilkisu. Kishiya kadai ta ishe ta.
Hum! In ji Ya Gumsu. Ba ta san irin bayanin da za ta yi wa yar uwarta ba, ta gane cewa, kishi da BAGGARA ba abu ne mai sauki ba, sai dai ita kishiyar ta yi ta jin jiki tana kunsar bakin ciki har karshen rayuwar ta.
Ta yadda Mai Askira zai yarda ya karba wa Yarima auren yar sarkin Bauchi yanzu shi ne ba ta sani ba. Babu ubansa Sarkin Askira kuma wa zai bashi auren? Ko ita za ta je ta nemo masa waliccin auren yar sarkin Bauchin da kan ta?
Ta fahimci ta lalata chance dinta ne kawai na kara auren Yarima da korar Saade da dukan ta. Da ta sani ma kafewa ta yi the other way kan cewa, tunda ta bada dama ya auri zabin ransa da zabin ran mahaifinsa, to ita ma ya auri zabinta. Amma yanzu ta tabbata kwabarta ta gama yin ruwa.
Don haka ta kasa zama gidan Yarima kamar yadda ta yi niyya, ta bi Aunty Daja gidanta tunda shi ma ya fice ya bar musu gidan, ta kuma tabbata Askira ya nufa.
Uche dake shigowa a lokacin yana ganin fitar su ya je ya kulle koina na gidan.
Tana kallon kiran Maimartaba yana ta shigowa wayar ta, amma ta yi funfurus ta ki dagawa sabida tsoro. Ta san ba zai taba sakinta ba, amma in ka tabo shi hukuncinsa ba shi da dadi.
Suna tafe a hanyarsu ta komawa gidan Daja, ta gaya mata Maimartaba yana ta kiranta, Daja ta ce,
Ki dauka a yi ta ta kare.
Ta kuwa daga ta hanyar cewa,
Allah Kawun jo (Allah ya kara maka yawan rai). Ina kan layi.
Muryar Askirama mai zurfi da kauri (husky) ta bakunci kunnuwanta.
Bana zaton Yareema ya gaya miki sakona. Cewa na yi ki share dakin Saadatu ki zauna, don ba ki da daki yanzu a gidana.
Cikin gatsali ta ce, Allah ya kara yawan rai wani abu aka ce na yi? Ziyara fa kawai na kawo musu. Ta fashe da kuka, kukan da daga ji za ka san bana gaskiya ba ne. Don takaici Mai Askira sai ya kashe wayarsa, kada ya yi abin da zai zo daga baya yana nadama.
Ya Gumsu ta shiga bandaki a washegarin ranar za ta yi wanka. Ta sa kafa a cikin bahon wanka ba ta lura da jikakken sabulun da ke ciki ba, kafarta ta sauka a kan sabulun ta zame ta tafi gabadaya ta yi wata irin mummunar faduwa. Faduwar da sai daukanta aka yi ranga-ranga zuwa asibiti baki ya karkace yana ta fidda kumfa.
Idan Ubangiji ya nufi alamari, bawa ya nuna ja da hukuncin Ubangiji, sai Ubangiji ya barshi da dabararsa, amma idan Ya ga dama talalar da zai maka ta dare daya ce. Wani rabon sai ya kawar da kai dagadoron duniya gabadaya. A ci gaba da rayuwar babu kai, babu mai tuna ka da kyakkyawar zuciya balle ya yi maka addua.
Don haka Gumsun Askirais lucky that shes alive a daidai lokacin da Saade ke jikin mahaifiyarta tana ta kelaya amai kamar da bakin kwarya.
Tunda ta iso ta ke zazzabi da ciwon kai, kafin wayewar gari kuma sai haraswa, ta kasa cin komai, gabadaya ta fige ta yi zuru-zuru. Fulani da Fanna suna tsaye a kanta tun jiya. Shi ma Maimartaba ba ya rufa awa guda bai kira Fulani ya ji me Saade ta ke ciki ba.
A karshe ya turo likitar matan gidan don ta zo ta duba ta a san takamaimai me ke damunta.
Ita dai Fulani tuni ta sha jinin jikinta. Tun daga sanda Saade ta ce ba ta son warin turarenta. Amma kuwa Yarima bai kyauta ba, ya saba alkawarin da ya yi mata. Saade is too young da haihuwa wani matsanancin tausayi ya kama ta.
Amma da ta tuna ba haramci suka aikata ba sai ta rage wa kanta damuwa. Wannan rabo na kurkusa da kofar daki ina Ya Gumsu za ta kai shi?
Ko kusa abin da Ya Gumsu ta yi wa Saade bai sa ta ji tana so a raba auren ba, ko don ganin halin bacin ran da Askirama ke ciki, wanda ko ita da ta haifi Saaden abin bai tabata har haka ba. Ta sa a ranta Ya Gumsu za ta yi fiye da wannan in dai a kanta ne.
Kuma a washegarin ranar bayan fitar Dr. Zainab da ta duba Saade ta tabbatar wa Fulani akwai ciki na sati Shidda, ta shiga don ta yi wa Askirama wannan albishir ta ji yana amsa waya. Sai kuma ta ji ya ce, Stroke? Cikin tsananin mamaki.
Gumsun da ko jiya na yi magana da ita a waya lafiya lau?
Aka yi magana daga daya bangaren wanda ita ba ta ji ba, sai ta ji ya ce, Ai shi ke nan, Allah ya ba ta lafiya. Yayanta sai su je Abujar su yi jinyarta, amma Allah ya gani ni ba zan zo ba Daja, yar uwarki ta girma ba ta san ta girma ba.
Na dade ina hakuri da halayenta ta kasa gane gata na yi wa rayuwar Yareema da shi bakidaya da na aura masa Saadatu. Babu yadda ban yi da ita ba ta karbi hukuncin Ubangiji, ta nuna min ta hakura har za ta kai musu ziyara, shi ne ta yi tattaki har dakin yarinya, ta ci zarafin marainiyar Allah ta koro ta tun daga Abuja har Maiduguri da Askira ita kadai a wannan marrar ta satar dan mutum kamar satar takalmi.
Don haka ina nan a kan bakana, Gumsu ta ci gaba da maye gurbin Saadatu wajen Yareema Sageer. Babu Saadatu babu danta, sai ranar da ta yo tattaki har dakin Bilkisu ta ba ta hakuri a kan cin zarafin da ta yi wa yarta. Ta kuma furta da bakinta cewa ta amince su ci gaba da zaman aure da bakinta. In ba haka ba shi ma Yariman kada ya sake ya tako min gida.
Yana gama fadin haka ya kashe wayarsa yana maida numfashi cikin bacin rai. Fulani Bilkisu ta karasa ta gurfana a gabansa, tafukan hannunta bisa tafin kafarsa. Cikin muryar lallashi da son kwantar masa da hankali ta yi masa albishir din da ke bakinta.
Da gaske?
In ji Askirama. Cikin excitement din da ba zai misaltu ba.
Ta kashe shi da lallausar murmushi, ta ce, Da gaske Dr. Zainab ta tabbatar da ciki na sati shidda a jikin Saade. Sabida haka Askirama ka yi hakuri da duk wani bacin rai, tunda Ubangiji ya nuna mana ayarsa. Idan ta warware kwana biyu a manta da komai a mayar wa da Yarima matarsa.
Mai Askira ya girgiza kai ya ce, Ayoyi kam ai muna ta ganinsu. Yanzu kanwarta ta kira ni ta shaida min cewa, suna asibiti da Gumsun Gari, ta fadi a bayan gida ta samu stroke.
Innalillahi wainna ilaihi rajiun. In ji Fulani.
An gaya wa Yarima da su Yaa Maira?
Cikin damuwa ya ce, Yarima ya taho tun jiya ta mota, babu jirgi, amma Awaisu ya gayaminya samu minor accidentahanya, bai ji ciwo ba amma ya bugu, kuma motar sa ta jikkata, ya iso Askira tun jiya, ni na ce da Awaisu ya gaya masa kada ya sake in ganshi gabana ko bangarenki. Ya Maira kuma sun kama hanyar Abujan.
Cikin dimbin alhini Fulani ta ce, innalillahi wainna ilaihi rajioun. Zama bai ganmu ba, ya kamata a shirya mana tafiya mu uku, ni da Yakirjinoma da Hibbani. Yareema na tabbata Awaisu zai bashi duk kulawar data dace, amma don Allah Askirama ka bar shi ya dawo gidan nan.
Ya yi ajiyar zuciya, wannan karon cikin muryar sa akwai sassauci, ya ce,
Su za su je, amma ban da ke. In kin tafi wa zai kula min da Saadatu da Chiroman Gari?
Ta yi murmushi kadan, jin har ya bai wa dan cikin Saade Sarauta tun kan ya iso duniya.
Ta ce, Fanna za ta kula da su sosai. Bai kamata a ce su sun tafi ni na zauna ba, sai ta dauka sabida abin da ta yi wa Saade ne wanda ni sam bai shafe ni ba. Ta kare zancen ta da cewa.
Ai Saade yarta ce! Koda bata auren Yarima.

Askirama ya kura wa matarsa Bilkisu ido, yana mamakin kyawawan halayenta. Matansa sun kasa fahimtarta ne, amma duk ta fi su kyan hali, ba ta taba dauko zancen wata cikinsu ta kawo masa. Su kuwa basu da aiki sai fadin aibunta. Sun dauki kishin duniya su duka sun dora a kanta. Sun kasa gane ba kyawun halitta kadai ke rudarsa a kan Fulani Bilkisu ba, har da kyawawan halayenta.
Amma duk yadda ta so Askirama ya barta zuwa Abuja duba Ya Gumsu ya ki amincewa da hakan.
Yaa Maira ce ta zo ta hada kan sauran kannenta mata da maza aka ba su motoci da dogarai suka kama hanyar Abuja. Cikin tashin hankali. Hibbani da Yakirjinoma jirgi daya suka bi tare da Ahmad da Suhail wadanda za su kula da su.
Fulani ta kira Yareema a waya bayan ta koma dakinta. Muryar Yareema har ba ta fita sosai, kamar ta wanda ke fama da mura, shi kadai ya san halin da yake ciki. Ciwon da jikin sa ke masa sakamakon buguwar mota bai dame shi ba kamar hukuncin da Askirama ya yanke akan sa na nesanta shi da Saade.
Yana gidansa tun isowarsa ko falo bai leko ba tunda Askirama ya aiko Awaisu ya gaya masa sakon kada ya sake ya ganshi a fada ko shigifar sa, kuma kada ya sake ya je inda Saade ta ke. Har sai mahaifiyarsa ta bada hakurin cin zarafin da ta yi mata har dakin auren ta.
Ta kuma yi alkawarin karbar Saadatu matsayin suruka sannan ne shima zai janye nasa takunkumin.
Shi ya san wannan decision ba mai sauki ba ne ga Ya Gumsu, a yadda ya san kafaffiyar zuciya irin tata in tana kin abu. Kuma bai fita daga wannan zullumi da tashin hankalin ba a daren jiya Aunty Daja ta kira shi tana kuka, wai Ya Gumsun ta fadi a toilet ta samu stroke.
Ya kwana cikin wani hali na kaka-ni-ka-yi, and he is speachless.Wordless. Moodless. Ko magana ba ya iya yi. Awaisu ya so ya taya shi hira a daren ranar bayan ya bashi magani ya kira likita ya duba shi ya tabbatar babu mummunan rauni a jikin sa, ya ce ya tafi kawai ba ya bukata, sai kuma yanzu da wayewar garin yau ya samu wayar Fulani Bilkisu.
Yareemah, kana lafiya?
Ta fada cikin tausayawa. Ji ya yi idanunsa sun cicciko da kwalla, bai zaci wannan rahmar daga gare ta ba. Abin da bai sani ba shi ne, ita halinta ya bambanta da na sauran mata. Mace ce mai hangen nesa da tsananin kawaici da maida dan kowa nata.
Im sorry Fulani, Im sorry. Ya furta in a subdued voice.
Ta yi murmushi, ta ce, Ba zancen Saade ya sa na kira ka ba. Na kira ka ne in jajanta abin da ya faru da Ya Gumsu. Da accident da aka samu, Allah ya tsayar haka, Ya sa kaffara, Allah ya ba ta lafiya.
Na so in bi su Yaa Kirjinoma Abujan, Askirama ya hana ni, sabida ita ma Saade kwance ta ke babu lafiya tun isowarta.
Tamkar zuciyarsa za ta fito ta bakinsa sabida zullumi, ya ce cikin wata marainiyar murya,
Me ke damunta?
Fulani ta yi dan jimm! Kafin ta ce,
Na dauka ka sani ai.
Gabansa ya yi mugun faduwa, kada dai Saade ta gaya musu maganar Dr. Ziyad ne? Yau da ya shiga uku in Askirama ya ji zancen nan ya san aurensa da Saade ya kare.
Hawaye suka fito daga idanun Yareema Sageer ba tare da ya shirya ba. Amma sai Fulani ta fadi abin da ya gigita shi, ya wanke zuciyarsa daga duk wani rudani da dimauta da ta ke ciki.
Ciki ne tare da ita na kusan watanni biyu.
Yareema sai da ya cire wayar daga kunnensa, don ya tabbatar da wanda yake magana, My inlaw ba gizo kunnuwansa ke masa ba. Ya wani irin lumshe idanunsa yana karbar wani irin excitement a cikin kirjinsa.
Don haka ka kwantar da hankalinka ka koma Abuja ka kula da lafiyar mahaifiyarka. Saade tana karkashin kulawarmu insha Allah. Kafin sannan zuciyar Askirama ta huce sai a ba shi hakuri.
Abin da nake so yanzu shi ne ka koma Abuja ka yi jinyar mahaifiyarka.
Insha Allah, I will. Ya fada cikin girmamawa.
Har sun yi sallama ya kasa jurewa. Cikin jin nauyi ya ce,
Fulanin Sarki zan iya magana da Saadatu?
Fulani ta ce, Ta samu barci, in ka koma Abuja ka samu nutsuwa ka kira ni, zan ba ta wayar insha Allahu.
Da wannan suka yi sallama.
A washegarin ranar ya tattara ya koma Abuja.
*****

Yau asibitin national hospital Abuja ya ga iyalin masarautar Askira, ko ina ka wulga motoci ne cike da dogarai masu rubutun Askira Emirate. Tabbacin mara lafiyar na da alaka da hamshakiyar masarautar Askira. Lokacin da Yareema ya iso an kai Ya Gumsu daki na musamman (V.I.P room) an ba ta kwanciya.
Sanda suka shiga shi da Awaisu Ya Gumsu barci ta ke yi. Amma jin muryar Yareema na magana da likita sai ta hau kokarin bude idonta.
Duk da barcin da ya ci karfinta kokarin magana ta ke yi da bakinta da ya karkace, amma ta kasa. Yareema ya matsa daidai kanta yana hawaye yana fadin,
Ki yafe ni ya Gumsu, na kasa cika alkawarin da na yi miki, amma na alakanta hakan da rabon gaggawar da ya rantse a tsakaninmu.
Ya Gumsu Saadatu ciki gare ta, na kasa cika alkawarin ki Ya Gumsu na kasa. Ya saka kuka tare da kifa kansa a kan cikinta.
Da hannunta mai lafiyar ta mika tana shafa sumar kansa, tana ci gaba da kokarin furta magana abu ya gagara, sai hawaye ke bi ta gefen idonta. Amma daga yadda ta kama shi da hannu daya ta kankame tana hawaye ya san alheri ta ke son fada.
“Is ok Ya Gumsu, ki yi barci. Ni dai fatana ki fahimci cewa Saadatu alkhairi ce a gare mu kamar yadda Alanguburo ya hango. Ya Gumsu ki kwantar da hankalinki a kan Fulani Bilkisu da ahalinta, wallahi ba ta nufinki da sharri. Idan Askirama ya fi sonta ba ya nufin ke uwar yayansa ba ya sonki. Yana son ta ne saboda kyautatawar ta gareshi tafi taku. Amma kowa da gurbinta, kuma kowa da matsayinta.
Sai ki duba ki tace ki ga shin me take yi wanda Askirama ke so? Kema sai ki kwaikwaya.
Shaidan ne ya ke kambama miki soyayyar Askirama ga Fulani Bilkisu, amma ita in ya sa ta tana yi, in ya hana ta tana hanuwa. Ke kuwa fa Ya Gumsu? Abin da ki ka ga dama shi ki ke masa, yana hakuri saboda mu, Ya Gumsu lokaci bai yi ba da girma zai bayyana a halayenki?
Hawayenta ya dadu, sai gyada masa kai ta ke akai-akai kamar kadangaruwa. Yarima ya ci gaba da cewa.
Ya Gumsu ki yafe mini ban cika alkawarin da na yi miki ba, musamman da na ji kin ce bayan watanni uku za ki raba mu. Na kasa Ya Gumsu, na kasa Saadatu ciki ne da ita, zan yi azumin kaffara ki yafe mini.
Tana so ta ce masa babu kaffara a kanka, tunda ba fadar Ubangiji ba ce, sannan baka sabi Allah ba, amma ta kasa. Yarima ya rungume ta yana ci gaba da rokonta rangwame da afuwa a kan aurensa da Saadatu wanda ya kara karya zuciyar Ya Gumsu, ta amince soyayyar danta ga yar Fulanin Askirama wani hadi ne daga Allah, domin ya dinke barakar da ke tsakaninsu. Ya kawo maslaha da fahimtar juna ga iyalan Maimartaba Sarkin Askira.

Kwanan Ya Gumsu da iyalanta uku a National Hospital, sauki na samuwa a hankali. Ya Maira
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MASARAUTAR MU
avatar
zainabaliyu

8 months ago

Reply

I really appreciate masarautar mu, thank you

Please Login or Register in order to submit comment