Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

suka san kan mazan su ta yi durkuso a gaban sarki, ta ce "Alanguburo (Allah ya kara yawan rai) Yarima na rokon alfarmar a bar shi ya zo gida, ko da na sati daya ne, shekaru goma kenan rabon sa da gida, yayi digiri yayi masta ya jima yana aiki har ya fara digiri na uku, yana cikin damuwar rashin sanin halin da 'yan uwan sa ke ciki, yayi alkawarin baza'a sake samun sa da laifi makamancin na baya ba".
Nan da nan wani kwantaccen bacin rai ya bayyana a fuskar sarki, ya dago idanun sa da suka kada ya dube ta, sai da hantar cikin ta ta kada. Ta yi azamar sunkuyar da kai amma a ranta zata jure komai in har zai bar dan ta ya zo gare ta, haka kawai ai ba shikadai ne fitinannen Da ba, fitinannun nawa ya haifa? Amma bai daukewa Ya Kirjinoma nata ba sai shi kadai bayan ba fin su fitinar yayi ba. Yana kusa da su ma suna masa fada ai zai fi gyarawa fiye da hannun aminin nasa.

Sarki Yusufu AbdulHakimu mai Askira, ya dubi uwargidan sa Ya Gumsu da idanun bacin rai kamar koyaushe ta sako zancen YARIMA SAGEER a gaban sa, idan da abunda ya ke bata masa rai a rayuwar sa to al'amarin Yarima Sageer ne, babban Da, kuma zakka a cikin 'ya'ya mazan da Allah ya bashi, yet mafi madaukakiyar soyayya a zuciyar sa.
Dama an ce wai fitinannun 'ya'ya sun fi shiga zuciyar iyaye. Kusan wannan magana haka take. Duk cikin 'ya'yan sa maza da mata ba wanda yake so irin Muhammad Sageer, sai kuma ya zamo mafi munin jarraba da Allah ya taba yi masa. Ubangiji yayi gaskiya da ya ce "ya'ya da dukiya fitina ne......".
"A takaice dai kina rokawa dan ki alfarmar ya dawo cikin gidan nan ya cigaba da turmushe 'ya'yan mutane, ya cigaba da wulakantani tare da tozartani a idanun Bayi na da hadimai na dake tsananin ganin girma na, ta hanyar turmushe musu 'ya'ya dake hidimta masa?".
Fulani ta runtse ido cikin jin zafin kalaman sa, "Alanguburo, wannan abu ne na kuruciya, kai kan ka da ka ga Yarima ka ga nutsuwa da hankali a tattare da shi, abinda yayi yana yaro ba zai taba maimaitashi cikin hankalin sa ba, balle da 'ya'yan bayi makaskanta a gare shi. Wallahi don an ki yarda da nine, amma Yarima makiya ne suke jifan sa a baya, ba yin kansa bane.
Kai shaida ne akan tsantsani da tsafta irin na Yarima, amma a ce ya rasa matan da zai bi sai 'ya'yan bayi, ai daga nan zaka gane akwai lauje cikin nadi a al'amarin sa.
Bayan haka kuma na dukufa da yi masa addu'a tun tafiyar sa, Allah kuma baya juya addu'ar Uwa, inada kyakkyawan yaqinin cewa ya daina, mu taru mu kyautata masa zato, mu bashi dama ya rayu cikin gidan su kamar kowanne Da cikin gidannan, idan aka sake samun sa da wani laifi makamancin wannan, na amince ayi masa duk hukuncin da ya kamata da shi".
Maganganunta ga dukkan alamu sun dan shigi Askirama. Ya dade cikin halin shiru, ya kasa cigaba da cin abincin sa. A karshe yace da Ya Gumsu wadda ke jiran amsar sa kamar ta shiga zuciyarsa taga abinda yake yankewa.
"Zan yi shawara da Waziri".
"Alanguburo (Allah ya kara maka yawan rai nagode matuka, kuma insha Allahu Waziri zai amince da abinda na zo da shi, don shima na tabbata yana son ganin Awaisu)".
"Ina bukatar kadaicewa". Ya ce da ita.
Ta mike cikin azama ta soma tattare akusan abincin dake gaban sa. "In ma kwana zaka yi kai kadai ka yi, ni dai a bar Da na ya dawo gida". Ya Gumsu ta fada cikin ranta, a fili kuwa dukawa ta yi a gaban sa tana fadin.
"Na bar ku lafiya gatan Askira".

Fitar ta ke da wuya ya kishingida ya lula cikin tunani. Tunani mai zurfi na shekarun da suka gabata.
****










SHEKARUN CAN BAYA
(A Masarautar Askira)
Lokacin da Ya Gumsu ta samu cikin babbar 'yar sa 'Yaa Maira' duk burin sa da dokin sa shine a haife masa Da namiji domin ya samu magaji, kamar yadda kowanne sarki ke burin samu. Amma sai aka haifi Ya Maira, ciki na biyu ma yayi ta fata da addu'ar samun da namiji, amma sai ta kara haihuwar diya mace. Dalilin sa kenan na kara auren Ya Kirjinoma a daidai lokacin domin yana ganin 'ya'ya mata kawai Ya Gumsu zata yi ta haifar masa.
Kamar Allah ya san cewa bai yi farin ciki da haihuwar Mairam Lubabatu ba, bata fi shekaru uku ba Allah ya karbi abinsa.
Ya Kirjinoman ma da ta tashi haihuwar ta ta fari, sai ta haifo masa Mairam Murjanatu. Wannan ya kara mayar da shi desperate ga son haihuwar da namiji. Ba ruwan sa da 'ya'yan sa mata, duk kulawar su da hidimar su da tarbiyyar su tana wuyan iyayen su mata. A kullum ya tuna wancan lokacin ya kan ce "wannan shine deadly mistake da ya taba yi a rayuwar sa". Ba shikadai ba, masu sarauta da yawa hakane tunanin su akan haihuwar fari, idanunsu rufewa yake ga son haihuwar da namiji ba tare da baiwa Allah zabi ba.

Ciki na uku da Ya Gumsu ta samu kusan a tare suka sameshi itada Ya Kirjinoma. Ita ta haifi MUHAMMAD SAGHEER, Ya Kirjinoma ta haifi MUHAMMAD ASHGAR tsiran watanni biyu kacal ne a tsakanin su.
Ashgar sai ya zo da rashin lafiya ta Autism wadda aka fi sani da (autism spectrum disorder). Baya magana (in a meaningful way) tun yana karami saidai ya maimaita abinda aka fada masa sannan kamar kwakwalwarsa ba daidai take ba.
Wannan yasa sarki Yusufu ya dauki soyayyar duniya da tattali da kulawa ta duniya bakidaya ya dora akan lafiyayye Yarima Sageer, wanda hakan ya ruruta wutar mummunan kishi tsakanin Ya Kirjinoma da Ya Gumsu, ya kuma sa Ya Gumsu daukar girman kan duniya ta dorawa kanta, da jin tafi kowa, tunda kuwa ita ta haifarwa sarki Yarima. Koma waye zai biyo baya saidai ya zo a matsayin kanin sa ba Yayansa ba.
Soyayyar data sa tun yana yaro daga uwar har uban suka sangarta shi, basa iya kwabar sa, gata na duniya babu irin wanda basa gwada masa. Hakan bai hana shi yiwa Sageer addu'a ba a duk sallahr farillar sa kan Allah ya kare masa shi a duk inda ya shiga. Musamman da ya bayyana ga kowa cewa yaron fitinanne ne na kin karawa.
Ya addabi 'ya'yan jama'ar gari da mugunta da tsokana, baya zama cikin masarauta saidai cikin 'ya'yan talakawan gari, sune abokan sa abokan mu'amalar sa, don Sageer ya tare yaro a lungu ya targadashi ya fasa masa hanci babu gaira babu dalili ba wani abu bane sabo a wajen jama'ar gari, suna dauke ido ne sabida mutuncin mahaifin sa da farin jinin yaron. Yaro ne mai shiga rai matuka, sabida kwarjini da kyawun suffar da Allah ya bashi.
Yana girma fitinar sa na karuwa a ciki da wajen masarauta.
Kullum Sageer ya fita makaranta da yaron da zai targada ko ya fasawa hanci ba'a kuma isa a kawo kara ba sabida tsoron Ya Gumsu, saidai Awaisu ya gani ya zo ya fada a gida. Waziri ya aika a bada hakuri. Don ba'a bari ma Sarki ya ji. (Awaisu dan Waziri ne kuma sa'an Sageer don haka tare aka raine su), har ta kai ga Awaisu ya kwaso kayan sa duka ya dawo dakin Sageer kwatakwata, sai dai hali kowa nasa daban. Don kuwa Awaisu babu ruwan shi yaron kirki ne, amma duk inda Sageer yasa kafa nan zai mayar da tasa.
Darajar Sarki yasa jama'ar gari suka yi ta hakuri da Sageer tun yana yaro har ya shiga sakandire anan Askira. Kafin ya gama sakandire ne kuma yayi dan hankali ya daina taba 'ya'yan kowa, sabida yawan addua'ar Alanguburo akan sa. Har yake dan shigowa fada a zauna zaman fada tare da shi kamar yadda Sarki ke so ya dinga yi kullum amma ya ki. Lokacin da Sageer ya soma balaga, sai abubuwan gabadaya suka canza, 'yar nutsuwar da yake da ita tabi ruwa. Ya koma neman bayin sa mata.
Lokacin da wannan mummunan labari ya kai kunnnen sarki Yusufu mai Askira sai ya kira Wazirin sa cikin sirri.


"Na yanke shawarar in aura masa mata hudu a rana daya, ina ganin hakan ne kawai mafita ga al'amarin sa".
Waziri Ibrahim ya girgiza kai yana kallon maimartaba sarkin Askira cikin tausayi, ganin yadda ya zabge ya birkice a kwanaki uku kacal da samun wannan labari da yayi. Lallai 'ya'ya da dukiya fitina ne. Kamar yadda mulkin kansa fitina ne da rashin kwanciyar hankali ga bawa. Yace.
"Baza'a yi haka ba Askirama. Baza'a yi haka ba gatan Askira, aure ba laifi bane a shekaru goma sha tara amma karatu za'a kai shi, zamani ya canza, auren mata hudu a rana daya ba zai zamo solution ba, don kuwa zai hanashi maida kai ya yi karatu musamman idan ya soma tara iyali. Ka manta da komai ka kwantar da hankalin ka ka barshi yayi karatun da zai amfane shi muma watarana ya amfane mu. Zan hada shi da Awaisu zuwa duk inda zaka kai shi zan kuma san yadda zan yi Awaisu ya zame masa jagora a komai nasa. Mafi a'ala shine mu bisu da addua".
Ya sani duk duniya babu mai kaunarsa cikin 'yan uwan sa na jini irin Waziri Ibrahim, wanda ya kasance Da ga wan mahaifin sa marigayi sarki AbdulHakimu mai Askira. Bai taba bashi shawarar da in ya bi ta baya ganin mafita da yaqini a cikin ta.
Don haka yayi na'am da shawarar Waziri ba tareda shawara da Ya Gumsu ba.

Kafin ya zama sarki shi Ambasada ne na kasar Egypt, saida mahaifinsa Sarki Abdulhakim ya rasu ne aka dawo dashi gida aka bashi sarauta, don haka yana da kyakkyawar alaqa da ambasadan Egypt mai ci a lokacin kamar amini yake a gare shi, sannan yana da connections mai yawa da kasar ta Misra domin yayi sama da shekaru goma yana aikin jakada a cikin ta.
Don haka ya yanke shawarar kai shi kasar muslunci bai kai shi kasar turai ba don ya kara hankali, a Egypt din ma hannun Aminin sa Amb. Hassan Labaran ya damka shi bai yarda ya zauna a hostel ba. Amb. Hasan bai taba haihuwa ba shida matarsa Hajiya Laila, suka karbi amanar Sageer da Awaisu a gidan su wadanda aka samarwa gurbi a jami'ar Al. Azhar. Saidai ba fanni daya suke karanta ba.
Daga wannan lokacin ne kuma haihuwar 'ya'ya maza ta budewa Sarki Yusufu daga duka matan nashi biyu, a lokacin ne ya hadu da Hibbani ya aure ta, daga baya ya auri Bilkisu, haihuwar ta biyar suna mutuwa.
Amb. Hassan zazzafan da boko ne mai zafi da sanya ido akan iyalin sa, tashin farko ya gano dabi'ar da Sageer ya zo masa gida da ita ta shan sigari, kuma ba jimawa yayi fata-fata da ita, ya cigaba da dora shi a hanya ta hanyar tsawatarwa da jan sa a jiki, yana nuna masa illar smoking ga lafiyar sa ta dan adam. Wani abu da bai samu daga iyayen sa ba sabida kawaici na masu sarauta ga 'ya'yan su. Gara ma Maimartaba akan Ya Gumsu wadda babu wani kusanci ko kankani tsakanin ta da dan nata, bata san me yake ciki ba, bata taba bincikar halayyar sa ba, ita dai burin ta ya kasance cikin gata ya samu duk abinda yake so, ya girma ya gaje sarauta.
Cikin dan lokaci kankani Amb. Hassan ya canza da yawa daga baragurbin halayen Sageer sai abinda ba'a rasa ba. Shima Awaisu a nasa bangaren yana iya nasa kokarin wurin ganin Sageer ya canza munanan dabi'un sa zuwa na cikakken dalibin da ya san ciwon kansa.
A karshe Awaisu ya fahimci wani abu, zai iya nasarar raba Sageer da komai, amma ba zai iya raba shi da 'yammata ba.
Mahaukatan kudin da sarki ke turo masa don yayi hidimar karatu, da wadanda Amb. Ke basu lokaci-lokaci duk a hidimar 'yammatan sa yake karar dasu. Yana kuma da masaniyar cewa yana branching da 'yammata a hotel ba da sanin Amb. Hassan ba.
Al'amarin ya kara kazanta ne lokacin da aka yiwa Amb. Hassan sauyin kasa, daga Egypt zuwa Amsterdam akan aikin jakadancin sa. Suka tattara suka bar Egypt suka koma can. Inda suka fara karatun doctorate degree dinsu a fannin da kowanne yake a babbar jami'ar Amsterdam. Awaisu na karantar (Social Work) yayinda Sageer ke karantar (Pure and Applied Chemistry).
A duka wadannan shekarun bai kara ganin kowa nasa ba, wadanda aka haifa baya nan bai san su ba. Haka wadda aka aura a bayan sa wato Fulani Bilkisu. Bayan su akwai kwarkwarori da yawa. Sannan elder sisters dinsa biyu duk sunyi aure sun hayayyafa: Ya Maira da Mairam Murjanatu. Bayan su an haifi maza biyar, biyu Ya Gumsu, uku Ya Kirjinoma, sannan Hibbani na da Humaira da Najaatu. Bayan kammala M. Sc din su dukkan su sun samu aiki a kasar Amsterdam, Awaisu aikin asibiti yake yi yayin da Yarima Sageer ke aiki da wani mashahurin kamfanin sarrafa kayan abincin gongoni na kasar.
Tuni sun manta daga gidan sarauta suka fito, sun karbi rayuwar gidan Amb. Hassan wanda bazaka taba sanin ba shi ya haife su ba. Rayuwar kasar Amstedam ta karbe su sosai, sun tara arziki nasu na kansu, ga aiki ga muhalli ga ababen hawa. Amma duk da haka a gidan Amb. Suke zaune.
Tun barin sa gida sai a shekarar baya ne maimartaba da Ya Gumsu suka kai masa ziyara, bisa tsananin rokon Amb. Hassan don maimartaba yace shi har abada Sageer bazai dawo masa gida ba, ya barwa Amb. Hassan shi duniya da lahira sabida gamsuwa da irin rikon da yake musu shi da Awaisu, shi kansa Waziri bai taba bada shawarar su dawo gida ba.
Sai kuma ga abinda Ya Gumsu ta zo da shi yau, na nema masa alfarmar zuwa gida yayi ko sati daya ne.
Ya sake lumshe idon sa ya bude a hankali. A fili ya furta "nima ina kewar ka Muhammad Sageer, tsoron abinda zai je ya zo nake. Ina tattalin mutuncin ka a idon al'ummarka. Duk da Baban ka ya tabbatar min baka da matsala yanzu".
****
A shawarar da suka yi da Waziri ya karfafe shi akan ya bar Yarima ya zo gida, koda sati dayan ne, tunda dai bazai dawwama a kasar da ba tasa ba, dole watarana zai zo gida, sannan Amb. Hassan ya tabbatar musu komai lafiya a tareda Yarima. Awaisu ne dai da yafi kowa kusanci da shi ya ce da Babansa Waziri da saura. Wazirin kuma bai gayawa sarki hakan ba don ya samu nutsuwar barin dan sa ya shiga cikin 'yan uwan sa ko yaya ne. A gefe ya saka limamin Askira da sauran malaman fada yin addu'a ta musamman akan zuwan Yarima Sageer, Allah ya kintsawa mahafin sa shi a matsayin sa na magajin sa.
Da wannan sarki ya yiwa Yarima umarnin zuwa gida don yayi sati daya. A wannan lokacin Amb. Hassan ya gama tenure dinsa na aikin jakadanci yana shirin dawowa gida gabadaya, don haka tare suka soma shirin tahowa shi da 'ya'yan nasa Sageer da Awaisu, inda Amb. Hassan zai sauka a kasar shi ta haihuwa Kanon Dabo, kafun ya koma Birnin Tarayya da zama.
*****
"Na ga sai wani zumudi kake zaka je gida, kamar wani special abu ne zamu je mu taras banda zafin Maiduguri, ni banda Ya Gumsu ta dage sai naje ai har abada na bar Askira kenan, tunda Alanguburo baya son gani na".
Awaisu yayi murmushi yana ninke kayan Yarima yana jera masa cikin tsadaddiyar trolley din sa. Bai yi niyyar bashi amsa ba sai da ya ji Yarima ya sake yin kwafa, "ni ko satin ma bazan cika ba zan dawo, ka san nextweek akwai birthday din da na hadawa (Rose), kawai sai jin zancen tafiyar nan na yi, da na san da ita da tun satin da ya wuce mun yi mun gama, she will be 26 by next week". (Rose, yarinyar Yarima ce da yake ji da ita, 'yar asalin kasar Korea ta kudu), Awaisu ya tamke fuska kamar bai ji shi ba, ya cigaba da jera masa kaya. Daga baya kuma ya ce "ayya! Ai kawai ka tafi da ita Askira ka hada mata birthday din acan zai fi bada ma'ana" Yarima yayi miskilin murmushin sa, ya ce "me kake ci na baka na zuba? Ka zuba ido zuwa shekaru biyu zan kaita Askiran ne, amma a matsayin matata ba budurwa ta ba".
Awaisu ya dauka ya fada ne kawai don ya ji dadin bakin sa, ya manta da wani hali na Yarima Sageer Yusuf Askira, duk abinda ya furta yana nufin sa ne har zuciyar sa. Amma akan zancen Rose bayahudiya bai taba kawowa Yarima da gaske aurenta yake da niyyar yi ba.

A halayen Yarima in ka dauke son matan sa, sauran duka ababen sha'awa ne, Awaisu ba zai daina kiran sa (his role model) ba. Mutum ne mai muhimmanta sallah da kiyaye lokutanta, mai kirki mai kyauta, abun hannun sa bai taba rufe mai ido ba. Ga jin kan na kasa da shi, ga girmama iyaye, sannan ga kokari wajen neman na kai kamar ba dan sarki ba.
Bayan kamfanin da yake yiwa aiki yana kasuwancin automobile daga Amurka zuwa Amsterdam. Duk da haka maimartaba bai taba fasa turo masa kudi duk karshen wata ba, shi Awaisun shine akan komai na kasuwancin nasa kuma kyautatawar da Yarima yake masa a ciki sai ka rantse su biyu suka mallaki jarin kasuwancin.
Babban abunda ke burge Awaisu a halayen Yarima Sageer shine submissiveness, ya san shi mai laifi ne a gurin Ubangiji, amma yana yawan ce da Awaisu ya kasa dainawa, kuma yana so ya daina din, mata sun zame masa barin rayuwa da baya iya rayuwa daidai sai tare da su, don haka kullum cikin istigfari yake yana fadin yana rokon Allah yasa kada ya mutu yana aikata laifin da yake aikatawa.
Ko Awaisu ya soma wa'azi, baya arguing da shi, cewa ya ke ya sani babu kyau ya taya shi addu'a. Sai Awaisu ya koma yi masa yakin karkashin kasa, don kuwa yarima tausayi yake bashi, kana sabo ka san kana yi amma ka ce ba zaka iya dainawa ba, duk yarinyar da ya gani tare da shi zai bi ta bayan idon sa ya ci mutuncin ta ya razanata akan tarayya da Sageer, wani zubin har ya ce Sageer nada cuta, ga turawa da shegen tsoro, saidai Sageer ya nemi yarinyar sa sama ko kasa ya rasa, a karshe saidai ya nemo wata, shi kuma Awaisu baya gajiya da lalatawa, kamar yadda shima baya gajiya da sake nemowa.
Wannan itace rayuwar Yarima Sageer da dan uwan sa Awaisu a kasar Amsterdam. Tamkar ciki daya suka fito, sha'awar su akan komai daya ce ra'ayin su daya, sannan zuciyar su tsayayya ce akan junan su, saidai hali kowa nasa daban.
Jirgin su ya sauka a filin jirgin saman Maiduguri da asubahin safiyar Litinin, zaratan matasan suka soma saukowa daga matattakalar jirgin 'AZMAN' cikin shiga ta barebarin usli, wadanda fatar jikin su ta jiku da boko da kasar sanyi, kai da ganin su ka san sun fito ne daga sarauta ta ainahi ko daga irin takun su da kasaitar su.
Suna sauka motar 'Askira Emirate' na jiran su. Tun a Abuja suka rabu da Amb. Hassan da Mama Laila wadanda suka hau jirgin Kano, su kuma suka hawo na Maiduguri.
Dogarawa bila- adadin duk daga motocin masarautar Askira, suka bude musu kofar motar BMW wadda maimartaba kadai ke hawan ta a gidan. Daga nan basu bata lokaci ba suka kama hanyar Askira da motar civilian mai dauke da wasu fadawan cike fal a cikin ta.

Yau tun safe masarautar Askira ta tashi da bushe-bushen algaita da kalankuwa da goge irin na masarautar, baka jin komai sai tashin kirarin gidan sarautar Askira, maroka da makada daga kowane bangare na garin sun barko sun cika kofar fada, haka tun jiya 'ya'yan sarki maza da mata na nesa dana kusa sun hallara a gida dakunan iyayen su mata ba don komai ba sai don marabtar Yarima Sageer wanda ya kwashe shekaru goma baya cikin masarautar gabadaya. Mairam Murjanatu ce kawai bata samu halarta ba saboda ta yi nisa tana kasar Turkiya.
Naja'atu da Humaira kusan sun fi kowa zaquwa da murnar ganin Yariman domin sune basu san shi ba, suna kanana sosai ya tafi, sai kuma jikokin gidan wato 'ya'yan Ya Maira su wajen takwas. Lokacin da motocin su suka iso fada, sai kade'kaden da bushe-bushen ya karu. Wani abu ne da Sa'ade bata saba ji a cikin masarautar ba in ba wani muhimmin abu ake ba, kamar nadin sarauta ko bikin aure. Duka-duka ma dai tun zuwan ta Askira bai fi sau biyu ta ji irin wannan ba, don haka ta gane akwai muhimmin abin da ke faruwa yau a masarautar.
Tana so ta san me ake yi, amma ta rasa wanda zata tambaya, don Fulani ma tun safe tasa aka shirya Zarah suka wuce babban falon ganawar sarki da iyalin sa, inda sauran iyalin gidan suka hallara, ko ta kanta bata bi ba. Fanna ma dai ta lura yau dukkan su busy suke a cikin gida da girke-girken da iyalin gidan zasu ci da wanda za'a tarbi Yarima Sageer da shi.
Don haka itama tun safe bata sa ta a idanun ta ba.
Sa'ade duk ta zama curious ga son sanin me ake yi haka cikin gidan, a ranta tace yau dai zata yiwa Fulani laifi sau daya, dole taje ta baiwa idon ta abinci, iyakaci Fulani in ta kamata ta murde mata kunne ko ta mare ta.
Da wannan tunanin ta dau mayafin ta, sadaf-sadaf ta fita daga sassansu, a falon daya raba sassan Fulani da inda sauran bayinta ke shige da fice ta ci karo da wasu duk suka zubo mata ido, bata ko kallesu ba ta daga kafa ta fice daga unguwar Fulani Bilkisu.
Mayafin ta ta janyo ta rufe rabin fuskarta, idanun ta kawai ake gani. Ta rasa ina zata dosa? Dan ba sanin kan gidan tayi ba, daga bisani ta lura da inda bayi ke karakaina da manyan farantai, kanta tsaye ta doshi wajen.
Wani babban falo ne ta ga bayin suna shiga da sundukan abinci da katon katon na lemukan gongoni, ta bi bayan su a hankali har zuwa kofar falon, sai ta zagaya ta bayan tangamemeiyar tagar gilashi ta falon ta leka a hankali. Ba zata iya shaida fuskokin data gani ba don tagar ta baya ce duk sun juya bayan su, ta dai hango Alanguburo akan kujerar mulkin sa, zagaye da shi kananan yara maza da mata har da matasan 'yammata kamar ta, a gefensa daura da shi bisa kujerar da bata kai tasa ado ba wani zankadeden matashi ne, duk da bata yi nasarar ganin fuskar sa gabadaya ba ta ga gefen fuskarsa, da dogon karan hancin sa, kalar bakar fatar sa kamar ta mutanen kasar Morocco, hular sa ta nitse a cikin tarin sumar kansa sannan fararen kayan dake jikin sa babu ado irin na sarauta a jikin su. Normal tsadadden yadi ne (filtex London) mai taushi a idon mai kallon sa, sauran mata da mazan dake zagaye dasu duk bata ganin fuskar su, amma ta shaida bayan uwarta Fulani da kalar tufafin dake jikin ta kasancewar ta san ta da kayan. Wata zuciyar ta ce "yi ta kanki Sa'ade, idan Fulani ta kama ki a gaban kowa sai ta yi miki dan banzan duka. Tunda dai kin gani taro ne suke yi nasu su-ya-su (family get together)".
Wata kyakkyawar mata ta juyo tana magana da wata dattijuwa, sai ta gane fuskar ta, tana daga cikin wadanda suka je wa Humaira visiting har suka kira ta (Ya Maira). Salin-alin ta soma ja da baya, sawun ta a likkafa, sannan ta juya da sassarfa akan kafafun ta ta koma inda ta fito. Ko ba komai ta ba idon ta hakkin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MASARAUTAR MU
avatar
zainabaliyu

8 months ago

Reply

I really appreciate masarautar mu, thank you

Please Login or Register in order to submit comment