Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

maza ta mike ta nufi kofa batare da ta kalle shi ba, da ma da hijabinta jikinta. Yareema bai mike ba, ya ci gaba da durkuso a inda ta barshi. Sai ta ja ta tsaya daga bakin kofa tana kallonsa questionably. Ya lumshe mata shanyayyun idanunsa ya ce,
Saadatuh, not even a good morning kiss?
Saade ta juya masa baya cikin jin haushi, zuciyarta na tafasa, ita wane kiss ta iya? Meyasa bai samo can a wajen tubabbiyar baturiyar sa da ya dauka suka tafi hotel suka bar ta ba? Tana mai tambayar kanta wai dama ashe haka Uncle Yareema yake tana masa kallon salihi duk da abinda matar sa ke fade a kansa mafi muni?
Daga sanda ya taso ya tako zuwa gaban ta, zuwa sanda ta ji saukar hannunsa ya zagaye bayan ta gabadaya ya rungume ta tsam-tsam, ba ta tantance ba.
Im sorry Saadah, very sorry. Ban yi da niyya ba, uzuri ne mai karfi ya rike ni. Amma ko ina nake, cikin kowanne hali kina rai na Saadahtuh.
Saade bata san yaya aka yi ba ta sunne kai cikin kirjin Yareema, zuciyar ta tayi wani irin sanyi da yadda Yareema ke lallashin ta, daga can kasan makoshin ta ta ce,
Ni ai ban ce komai ba Yaya Yareema, ko ka ji na yi complaining? Na riga na san mijin wata aka aura min, don haka I should expect things like this. Don Allah mu bar zancen nan mu je wajen su Fulani. Sai hawaye.
Wadanda tuntuni suke son samun damar zubowa, bata basu dama ba, sai yanzu da weakeness din ta na kishi ya nuna a cikin sautin furucin ta.
Ya ce, Don zuwa za mu je, amma kafin nan he began to kiss her passionately, wani irin zazzafan kiss wanda ya sa Saadatu gigicewa da ficewa a hayyacin ta. Har yanzu ta kasa sabawa da sumbar Yareema Sageer mai tsirgawa har cikin ruhin ta, she always feels it strange a tare da ita. Sai da ya yi mai isarsa amma ko taya shi bata yi ba, sannan ya kama hannunta suka fito. Ya rasa kuma ta hanyar da zai bi ya goge laifin sa.

A hotel din hilton sun samu Fulani da Maimartaba sun shirya, direban Yareema kuma ya debo su Fanna, don haka ba su bata lokaci ba kuma bata samu damar yin wata magana da Fulani ba sabida Askirama yana wajen, da ta yi mata korafin abinda Yareema yayi mata jiya; ya tafi ya bar ta ita kadai ranar ta ta farko a gidan sa (the first challenge), don haka basu bata lokaci ba suka wuce filin jirgin saman Nnamadi Azikwe. Ta hadiye bacin ran ta ita kadai.
Da kyar Saadatu ta saki Fulani lokacin da jirginsu zai tashi, tana kuka Fanna na yi. Sai da suka ga tashin su Yareema ya kama hannunta suka koma gida, jikinsa a sanyaye don har zuwa lokacin Maimartaba ya ki sakar masa fuska. Kuma bai yarda sun yi musayar kowacce kalma ba har jirgin su ya tashi. Sannan Saade ma ta ki sakar masa fuska har yanzu fushi take.
Suna shigowa gida ya janyo daya daga cikin jakunkunanta da ta dawo da su ya soma fidda mata kaya da kansa. Sai da ya fidda kala bakwai ya ce ta dauki duk abin da ta san za ta bukata na kwanaki bakwai, yana rike da kafadun ta bayan sun shiga dakin ya ce,
Za a yi refurbishing gidan nan kafin ki fara zama a cikin sa. Zaa fidda komai dake ciki a kawo wanda Maimartaba ya yi miki ki tsara shi yadda ki ke so.
Ita dai ba ta ce komai ba, ta gane so yake ya wanke laifinsa. Ko ina zai kai su kuma? Oho! Bai jira amsarta ba ya tafi nasa dakin don ya hada nasa kayan.
Har ya janyo madaidaiciyar trolley ya fito zuwa dakinta Saadatu ba ta motsa daga inda ta ke ba. Da alama wanka ya kara yi ya canza kaya zuwa wani danyen yadin boyel fari kal mai shara-shara har tana iya hango singlet dinsa. Ya tsaida trolley din a kan tayoyinta ya karaso cikin dakin, cikin sanyin murya ya ce,
Saadatuh mu je ko?
Ta sunkuyar da kai hawaye na son zubowa, kewar Fulani, Fanna da Zarah ke damun ta. Yanzu kuma Dr. Sageer na cewa zai kwashe ta su yi wani wurin har tsayin kwana bakwai.
Ni ba inda za ni, jibi za mu koma makaranta.
Dr. Sageer ya harare ta, ya ce, Ko yanzu za ku koma ke ba za ki koma ba, gara tun wuri ki sani, da da yanzu ba daya ba ne, lokacin da babu nauyin kowa a kanki. So ki bi ni a hankali in na ga dama sai in soke karatun gabadaya.
Hawayen da ta ke ta tattali kada su zubo suka zubo din. Ta mike cikin fushi ta dauki handbag dinta. Ba abin da ta dauka bayan ita, shi ya ja mata tata jakar suka fito.
A cikin motar Yareema 4Maticsuke tafe, babu mai magana daga shi har Saade, tuki kawai yake cikin nutsuwa da kwarewa. Tun tana tsammanin cikin Abuja ne inda za su je din har ta ga ya kama hanyar barin gari. Mikakkiyar tafiya sosai suke yi akan titin Jos, uffan ba ta ce masa ba. In ma sayar da ita zai yi ya sayar, Fulani da Maimartaba su suka jawo mata.
Sai wajejen azahar suka shiga garin Jos, ya nemi wajen sallar matafiya a gefen hanya wanda mata za su iya amfani da shi ya yi parking. Kwarai ta ke son shiga toilet don haka har ta riga shi fitowa.
Sai da suka yi sallar azhar (kasaru) sannan suka sake daukar hanya.

What do you want to eat? (Me ki ke so ki ci). Yareema ya tambayi Saade.
Shiru ta yi masa kamar ba da ita yake magana ba. Ya yi kwafa ya ci gaba da tuki. Ya rasa gane inda ta sa gaba, in laifin da ya yi mata jiya ne ai ya ba ta hakuri, ya kuma karbi laifin sa. Yayi duk irin lallashin da ya kamata. Wannan shirun da ta ke masa yana ci masa rai. Ya ci gaba da tukinsa yana tunanin ta inda zai billo mata.
A hanyar fita garin Jos ya tsaya ya saya musu gasasshen nama mai laushi, kuma mai yawa, ya hada musu da gorar ruwan swan mai sanyi, sannan suka sake daukar hanya.
Ya bude naman ya ajiye a gefenta, kamshinsa ne ya tado mata da tsohuwar yunwa kuma da ma dai akan abinci ba ta iya filako. Don haka ta yi fuska abinta ta hau cin nama cikin yanga.
Ta gefen ido Dr. Sageer ke kallonta yana murmushi, komai na Saade burge shi yake ba tun yau ba. Suna cikin tafiya wayarsa ta yi kara, da ya duba sunan Ya Gumsu ne. Sai da ya ji gabansa ya fadi, har fargaba yake magana ta sake hada su. In dai alkawarin da ya yi mata ne ai ya cika.
Saade ido kawai ya zuba mata sai dan abin da baa rasa ba, wanda dan Adam ba shi da iko a kansa. Tsoro yake kada ta yi masa maganar Hajjaju shi ya sa da ya je mata sallama bai gaya mata tare da Saade zai taho ba.
Amma ya san bai isa ya ki daga kiran mahaifiyarsa ba. Duk irin rigimar ta, wadda ta diga masa jinin haihuwa ta dauki cikin sa watanni tara ta haife shi cikin wani hali na kaka-ni-kayi ba tareda taimakon kowa ba.
Don haka ya rage gudun motar ya amsa kiran Ya Gumsu da sallama cikin tsantsar ladabi. Ko amsawa ba ta yi ba ta jefo masa tambaya.
Da gaske da yarinyar nan ka tafi Abuja?
Yareema Sageer ya yi shiru cikin rashin sanin abin cewa.
Ya Gumsu ta yi kwafa, cikin tsananin hushi ta ce,
Watanni uku na ba ka ka zo a yi maganar auren ka da yar Sarkin Bauchi (Hajjaju) kuma watanni uku na ba ka ka sako mata yarta, idan ba haka ba ALLAH YA ISA haihuwarka da na yi, na sallama ka ga Bilkisu da yarta.
Tana gama fadin hakan ta kashe wayarta.
Yarima ya ja wani irin birki a tsakiyar titi, ji ka ke kuuuu! Saura kadan ya buga wa motar gabansa. Daga shi har Saade suka jirkito sannan suka koma mazauninsu daidai kasancewar duk da belt a jikinsu.
Da sauri ya sa wa motocin bayansa signal, sannan a hankali ya sauka gefen titi, ya danna wani abu gilassai bakake (tinted) suka maye gurbin masu haske. Saadatu ba ta yi aune ba sai ji ta yi Yareema Sageer ya jawo ta jikinsa da karfi ya rungume ta, cikin kunnuwanta yake rada mata.
Cikin kowanne hali kada ki rabu da ni Saadatuh!
Shiru ta yi, bugun zuciyoyinsu na bugun kirjin juna. wani irin moment ne mai wuyar fassarawa ga Saade komai na Yareema ratsa ta yake har cikin kwakwalwa his gentle touches, his sexy voice, and everything da yake yi a yanzun. Kasa magana ta yi, domin gabadaya Yareema ya gama rikirkita duniyarta da zuciyarta cikin dan lokaci kalilan.
Ta ga ba shi da niyyar ci gaba da tukin motar ga yamma na yi musu, ga shi ba ta san iya inda za su je ba, don haka ta janye gefe tana regaining consciousness. Lokacin ne ya ja motar suka ci gaba da tafiya. Amma sabanin lokacin tahowarsu ta lura wannan karon akwai babban abin da ke damunsa tun wayar da ya amsa.
A hankali kuma barci ya dauke ta. Ba ta farka ba sai da suka shiga garin Bauchin Yakubu. Nan ma ta dauka masauki zai nema musu musamman tunda dare ya yi, amma sai ta ga ya kara nikar hanya.
Ba ta so Yareema ya ji muryarta balle ya yi tunanin ko ta huce daga fushinta (sunan littafin Takori mai zuwa, NAHUCHE), shi ya sa ta yi masa shiru. Ba su dade suna tafiya ba ya karya kan motar suka hau titin da ta ga sign board dinsa zai kai mutum ne YANKARI GAME RESERVE.
******

Yankari game Reserve and Resort na nan a Wikki Camp. Yankari na daya daga cikin Nigerias Foremost Tourist attractions, ana kuma kiransa (home of wild life) saboda wadatar manyan namun jejin da ke cikinsa.
A ciki akwai hotel domin maziyarta wato Marshall Suit a nan Yareema ya kama musu daki V.I.P Room.
Kwarai attraction na Yankari ya dauke hankalinta har ta manta fushi ta ke da Yareema, duk da cewa dare ya yi musu amma koina haske yake da fitilu kamar rana. Ba ta san lokacin da ta dora hannunta a kan na Yareema ba, wanda ke bisa birkin mota.
Uncle au? (ta toshe baki da ta tuna ya hana ta kiran sa Uncle) Prince, kwana za mu yi? Kwana nawa za mu yi a nan?The place is quite attractive and I like it.
Mutane da yawa na kiransa Prince, musamman abokai, amma bai taba jin wanda ya fada with correct accentdawankakken harshe da makogaroirin Saade ba. Bai san sanda ya yi murmushi ba don ya ji dadin sunan da ta canza masan. Ya dube ta da gajiyayyun idanunsa irin na wanda ya sha tukin mota ya gaji,
In kin yarda za ki yi min tausar tukin nan da na sha, kuma za ki ba ni baby in sa masa suna Dan Yankari, ko kwana nawa ki ke so mu yi sai mu yi abinmu, tunda babu mai jiran mu ko neman mu.
Da sauri Saade ta kai tafukanta ta rufe fuskarta, kunya kamar ta yi ya ya, da ta san abin da zai fada kenan da ko kusa ba ta nuna shaawar wajen ba har ya gane ya nemi reward.
Reward din da duka cikin biyun da ya ambata babu wanda ta ke jin za ta iya, don sosai ta ke ganin girman Yareema Sageer, ta kasa accepting reality na kasancewarsa miji a gare ta har zuwa yanzu. Har gobe kallon matsayinsa na baya ta ke masa (Uncle/Guardian) duk da he seldom kisses hera duk lokacin da ya bukaci hakan a kwanaki bakwan su tare, cikin siga mai nuna tsananin bukatuwar miji zuwa ga matarsa (physical urge).
Suna shiga dakin nasu ko zama ba su kai ga yi ba Saade na ajiye handbag dinta akan kujera wayar Sultana ta shigo wayarsa. Bai ki amsawa ba, amma da ya daga wayar bai ce komai ba, sauraron ta yake yi.
Sultana ta ce cikin fushi.
Sageer ina ka shiga ne har yanzu ban ganka ba? Na dawo aiki tun dazu ga Uche baya gidan
Ina inda ki ka aike ni tare da amaryata. Ke da ganina sai ranar da ki ka karbi addinin musuluci da gasken-gaske, sai kin tuba kin bar giya gabadaya, if not ki kama hanyar Korea ba ni da ranar dawowa.
Wani ihu Aisha-Sultana ta saki a cikin wayar, You are lying you cant do this to me Sageer remember Im your Rose, wadda ta bar kasarta da addininta ta shigo wani saboda kai.
Ya ce, sabida jiki na dai. Notbecauseofme, in sabida ni ne you can sacrifice everything for my sake, you will give me children. Abu daya nake dubawa da ya sa ban sake ki ba a jiya; mahaifi na baya barin saki.
You hurt my father ko gaisuwa ta ya daina amsawa. Sultana ina yi miki sallama, na gaya miki in bazaki iya barin giya ba zaman mu ba zai taba dorewa ba, kin cire mahaifa ba da sanina ba, kin dauke ni kawai a matsayinsex slave ban yarda da wannan soyayyar taki ba. Na ba ki zabi, ko barin GIYA ko komawa Korea ne ko Amsterdam ke ki ka sani....
Yana gama fadin haka ya kashe wayar gabadaya ya ajiye ta gefen bed side-lamp. Saadatu tuni ta shige toilet da ta fahimci sensitive magana yake yi da matarsa.

Ta yi wanka ta gasa jikinta sosai daga gajiyar zaman mota. Ba ta san me ya sa ya zabi su taho a mota ba tun daga Abuja har Bauchi. Daga baya ta lura cewa tukin mota is his hobby. Ko ba komai yana jinsa a privacy da Saade, ba tare da wani ya gifta a tsakaninsu ba, ko da kuwa ba za ta yi masa magana ba.
Kafin ta fito ya yi musu odar abinci na alfarma, kayan da ta shiga da su da su ta fito a jikinta, sai tawul da ta rufo a kansu. Yareema ya shiga wanka wannan ya ba ta damar shiryawa a nutse. Amma maimakon ta sanya kayan barci sai ta dauko wata kakkaurar laffaya ta nannada ta dora a kai. Kai ka ce unguwa za ta tafi, ba ta yi wa fuskarta kwalliyar komai ba banda wet-lips da ta shafa kadan, amma ba karamin kyau ta yi ba.
Ta daga ido ta dubi Yareema Sageer yana fitowa daga toilet ruwa yana yarari daga cikin gashin kansa. Bakin kyakkyawan Babarbare mai kama da Mai Askira. Tawul kawai ya daura zuwa gwiwoyinsa, ta hango wani ingarman physique chestna manyan maza wanda ya sanya ta ba shiri ta sunkuyar da kanta.
Lokaci guda jikinta ya dauki rawa da makyarkyata lokacin da Yareema ya tako zuwa gabanta.
Kamshin bathrobb din da ya yi amfani da shi na desire dunhill ya bakunci hancinta. Saadatu Hashim, tayi saurin sunkuyar da kan ta cikin neman taimakon Allah ganin irin kallon da Yarima ke mata. Kallo ne mai aika sakon kiran miji zuwa ga matar sa. Ya kira sunanta da wata siga da bai taba kiran ta da ita ba wanda hakan ya sa ta dago ido a hankali ta dube shi, idanun ta na ragaita, ya kama dukkan hannayenta ya mikar da ita tsaye, hannayensa sarke cikin nata.
Ya ce, Saadatu hakurina ya gaza, na yi alkawarin da ba zan iya saukewa ba, Im so sorry Saadatu. Na daga kafar iya yadda zan iya, kuma na tabbatar kin samu tsarki, ki yarda ba zan cutar da ke ba, kuma ba zan hana ki karatunki ba, sannan zan bi hanyar da ba za ki samu ciki yanzu ba.
Ki yi hakuri Saadatu, hakkina nake so na aure a daren yau ba sai gobe ba Saadatu, I promised you it will only be sweet, not hurting akwai barazanar da nake fuskanta wadda tasa dole zan tabbatar da aurena a yau.
Saadatu ta soma kuka, Yaya Yareema ni ban shirya ba, na karanta a biology (reproduction) yana faruwa ne sanadin haka in na zo haihuwa mutuwa zan yi. Im only 19 years.
Daga yadda jikin Yareema ke kyarma ta tabbatar yau ba ta da maceci sai Allah. Kalaman fatar bakin ta sun yi kadan su sa Yarima fasa abinda yayi niyya.
Cikin wata sassanyar murya ya ce, Saadatu hakuri za ki yi, ni ma ban shirya hakan a yau ba, amma ba zan bari a raba ni da ke ba, dole in tabbatar da ke matsayin matata a daren yau.
Iyayenmu har shekaru sha hudu ana musu aure, kuma suna haihuwa lafiya tambayi Fulani shekararta nawa sanda ta haife ki.. and he began from there... with very hot and irresistible kisses..Saadatu roko ta ke tana magiya, amma kamar tana kara zuga Yareema Sageer ne.
To ka bari in ci abinci?
Ta fada cikin ragaitacciyar murya jikin ta na kara karkarwa. Kafin kukan ya kwace mata gabadaya.
Ya soma warware mata laffayar idanunsa ko buduwa ba sa yi, Abinci? Abinci fa ki ka ce Saadatu? Im sorry ki ba ni only two hours in ba haka ba zan cutu Saadatu.
Da ta ga ba sarki sai Allah, sai ta mika lamarinta ga Allah. Hawaye na bilbila, in wuya ta yi wuya ta kira sunan Fulani, yau har Hanne da Raheema sun sha kira da neman taimako daga bakin Saade. So it was with every woman. Cikin awanni biyun da Yareema Sageer ya ambata, ya mayar da Saade cikakkiyar matarsa, wadda ko mutuwa ya yi sai ta yi masa idda.

Bayan samun nutsuwarsa bai juya mata baya ba, rungume ta ya yi with utmost devotion and affection wanda baki ba zai iya fassarawa ba. Tunda yake biye-biyen matansa, farare, jajaye da bakake, da aure da ya yi na shekara da shekaru bai taba zama sexually satisfied irin yau ba. Rayuwarsa daga ranar ya tabbatar ta juya zuwa anotherdirection, zuwa sabuwar rayuwa wadda babu sauran sabon Allah a cikinta.
Saade na kuka, Yareema na lallashi, ta rantse cikin daren nan sai ya maida ita Askira, bazata kuma zuwa gidan sa ba, ashe haka auren yake bata sani ba? Kuma ya rasa da wa zai yi sai ita kanwar sa da aka bashi amana don kawai ita ba Askirama ne ya haife ta ba? Kuma ta rantse sai ta gayawa Fulani komai. Wani abun in ta fada dariya Sageer yake amma a cikinsa, yadda ta ke a fusace din nan daren yau za ta iya kai duka, tunda cizo da yakushi ya sha su har ya gode Allah.
Na ji duk abinda kika ce Saadatu, na ji ni dan ne, amma na Saadatu da Aisha-Sultana kadai, na amshi laifina ki yi hakuri ki yafe min, rayuwar will not besmooth ba tare da wannan din ba, baki ji ba yanzu duk wani tension da ke kaina ya fita, duk wata damuwa ta gushe, babu komai a rai da zuciya ta sai SAADATOUH,and I want to use this mediumin gaya miki tun daga karkashin zuciya ta cewa;I love you very- very muchhh!.
Yadda ya furta kalaman na karshe har cikin ruhin Saade, ta ci gaba da kuka ba ta ce komai ba. Har ya je ya hada ruwa ya dawo ya dauke ta ya sanya a jacuzzi idanun Saade a rufe suke suna bulbular da hawaye.

Idan wannan ita ce rayuwar diya mace hakika ta jinjina wa mata. Duk wani taimako da ya kamata miji maabocin kulawa ya nuna wa matarsa, Yareema Sageer ya nuna wa Saade daren yau.
Abincin kuma da ya ce ta ci bayan sun kimtsa, cewa ta yi ba za ta ci ba, sanda ta ce zata ci ai bai saurare ta ba. Ya yi juyin duniya ta ki, sai kuka.
A haka suka kwana, washegari ko waya bai kunna ba, tunda ya yi wanka ya tafi falo ya barta a dakin, ya kunna talabijin domin ya gaji da lallashin. Ko yaron goye nan ya ga Saa ya barta wajen kukan banza.

SAADATU SAAR MATA!!!
Yareema Sageer ya fada a fili, yana tuno kalaman Mai Askira.
Za ta dauke kwadayinka a kan sauran mata tunda Bilkisu ce ta haife ta matan Baggara ne don manya aka halicce su.
Murmushi ya yi yana jin kaunar mahaifinsa na kara ratsa shi. Sai kawai ya dauki wayarsa a gefe ya kira Maimartaba.
Da kyar ya daga wayar tashi, sabida a ganinsa Sultana ta ci gaba da kafirci ne da sakacin Yareema. Ga shi an ce Da na kowa ne ba zai so ya sa shi sakinta ba. Amma Allah ya gani auren Aisha da Yareema ya fice masa a ka. Damuwarsa ita ce irin tarbiyyar da za a bai wa yaya idan Allah ya kawo.
Ciki-ciki Mai Askira ya amsa gaisuwar Yarima, shi kuma excitedly yake bayyana masa dalilin kiransa da ya yi
Godiya marar adadi da ba shi auren Saadatu, ya kuma yi alkawarin rike aurenta da daraja da amana har karshen rayuwarsa. A karshe ya dora da bada hakuri a kan Sultana, ya ce, ya dauki matakin kaurace mata har sai ta daina shan giya.
Idan ba za ta iya dainawa ba ya ce ta tafi garinsu. Wannan hukunci ya sanyaya ran Askirama har ya sanya musu albarka, ya kuma ce ya saya wa Saadatu waya mahaifiyarta na cikin kewarta, ga shi ta bar wayarta a nan dakinta na Unguwar Fulani Bilkisu.
Yareema ya ce, A nan inda muke ba za a samu waya ba, amma in mun koma Abujan zan saya mata.
Mai Askira ya ce cikin tsokana.
An bar kasar ke nan zuwa shahar asal (honeymoon)?
Yareema ya yi murmushi cikin jin kunya yana shafa kai, ya ce,

DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MASARAUTAR MU
avatar
zainabaliyu

8 months ago

Reply

I really appreciate masarautar mu, thank you

Please Login or Register in order to submit comment