Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

gefen wajen shine wajen zaman sa tare da mahukunta (king-makers) in ana wani muhimmin sha'ani kamar hawan sallah, nadin sarauta, bikin aure da sauran su. Akwai wata doguwar baranda a kasa wadda anan ya kan zauna a kowanne yammaci ya gana da jama'ar gari yayi musu maganin kukan su, alkalanci da zaman fada.
Daga hannun dama na tsakiyar ginin akwai wata babbar kofar katako wadda in ka bi ta zai kai ka barga (ma'ajiyar Dawakai). A kowanne yammaci kyakwawan Dawisu (Peacock) ne a gaban gidan bila-adadin masu ado da ban sha'awa suna baza dogon bindin su cikin nuna baiwar ado da kyau da Allah yayi musu wanda bai yi wa wani tsuntsu ko wata dabba a duniya ba. Akwai fili fetal daga get din farko zuwa ginin farko na shiga ainihin zauren farko na masarautar. Akalla zaka wuce zauruka shida kafin ka tarar da wajen zaman sarki na farko da jama'ar sa na nesa, kafin ka isa wajen zamansa da mahukuntan sa, sannan ka yi tafiya mai tsayi kafin ka shigo ainihin cikin gidan mazaunin iyalin sa.
Tsakanin inda sarki ke zama da 'barga' dakunan samarin gidan ne da yara maza da ake riko a gidan, sannan kayi tafiya mai tsayi wadda zata kawo ka get din cikin gida.

Bangaren sarki zaka fara taddawa wanda ya hadu da get din cikin gida, kuma akwai kofofi da ke hade da bangaren kowacce matar sa ta aure. Daga gaban ginin akwai baranda mai kama da balcony a gaban kayatacciyar shigifar sarki inda anan ne ya ke ganawa da 'ya'yan sa, matan sa da 'yan uwan sa mata. An fi yin wannan ganawa da yamma ko da daddare. A wannan shiyyar babu mutane da yawa, kowa yana bangaren sa, sai bayi mata wadanda suma suke shige da fice babu yawan surutu, kowacce tana bangaren data ke hidima suna kuma shige da fice daga wannan sassa zuwa wancan na matan Sarki.
Sarki kan zauna a kofar shigifar sa da yamma, don gabatar da sallahr la'asar, maza in na jiki ne suna iya shigowa nan, idan 'ya'ya ko jikoki suka shigo a daidai wannan lokacin saidai su rike takalman su a hannu su sunkuyar da kai su wuce in har ba shine ya ce a kira su ba. Amma in a barandar data raba shigifar sa data matan sa yake zaune, da 'ya'yan ko jikokin sun karaso zasu zube gaban shi su kwashi gaisuwa.....
"Alanguburo" (Allah ya kara maka yawan rai) shine abinda ake cewa. Ba'a gaida sarkin Askira da "ina wuni? Ko ina kwana?" Shi kuma ya amsa da "Allah Kawun jo" wato kamar ace (Allah yayi albarka).
Akasari a wannan shiyyyar babu dogarai babu bayi, in ya ga dama ya kan ja 'ya'yansa da jikokin sa da wasa, yayi musu tambayoyi akan rayuwar su a irin wadannan lokutan.
In ka wuce wannan shiyyar ne zaka hadu da bangaren matan gidan. Wato matan Sarki na aure.
Kowacce da bangaren ta wadatacce ginin zamani mai manyan shigifu, wanda aka yiwa ado da royal furnishing, babu abinda babu a ciki na jin dadin rayuwa, domin masarautar a zamanance take sannan ilmi ya wadaci al'ummar masarautar, ba abinda zai hada kowacce da 'yar uwar ta in har ba ita ta neme ta ba. Daga bayan nasu bangaren ne na kwarkwarorin sarki ya ke.

Ana kiran bangaren kowacce matar sarki da sunanta.....Unguwar Ya Gumsu (Fulani Babba), Unguwar Ya Kirjinoma (Fulani Halima), Unguwar Fulani Hibbani (matar sarki ta uku) sai unguwar Fulani BILKISU (amaryar sarki).
'Ya'yan gidan duk sun girma, mazan na wajen ayyukan su da masu karatu a garuruwa daban daban, matan duk an yi musu aure a masarautu daban daban na jihar Borno, 'ya'yan Hibbani ne kawai 'yan kasa da shekaru sha takwas. 'Yammata ne guda biyu: Naja'atu, da Humaira. Sune kuma kadai ba'a yiwa aure ba a 'ya'ya mata.
Kowacce cikin matan sarki tana da manyan 'ya'ya maza da mata, in ka dauke amarya Fulani Bilkisu, wadda har yau take haihuwa suna mutuwa tun suna jarirai wato (wabi).
Wannan a takaice shine description na gidan sarkin Askira mai ci a yanzu, da bayanin tsarin masarautar gabadaya. Masarauta ce mai farin jini da tarin arziki wadda aka yiwa shaidar adalci da kyautayi ga talakawanta. Daidai gwargwado 'ya'yan sarki maza da mata sun wadatu da ingantacciyar tarbiyya da ilmin addini da na zamani, duk da ba'a rasa masu fitina ba musamman samarin maza. Kishin da ke tsakanin iyayensu mata bai hana su hadin kai a junan su ba, suna matukar kaunar junan su. Sarki na da 'ya 'ya goma sha biyar, maza da mata da jikoki sama da goma.
****
Baba Saleh ya koma gefe ya daga kai yana kallon wannan babbar masarauta da bai taba mafarkin gani a zahiri ba, tun suna yara ya ke jin labarin masarautar Askira, irin tarin arzikin ta da karfin mulkin ta, hannun sa cikin na Sa'ade, sun yi zuru-zuru sabida yunwa da gajiya. Tunanin sa shine wa zai dosa ya ce yana son ganin BILKISU? Wadda marigayi Malam Hashimu ya ce tana daga cikin matan gidan???
Bar ta wadannan dogayen dogaran dake shige da fice suna muzurai kamar sa ci babu, wasu a tsaye kyam kamar an kafe su. Kai sai ka dauka babu bargo a cikin jikin su. Babban abinda ya fi razana shi shine shirgegiyar kofar masarautar, irin kofar nan ce ta jan karfe da ake kira mahdi-ka-ture.
Ya ajiye kunshin kayan Sa'ade dake hannun sa a kasa yace da Sa'ade ta hau kai ta zauna, shikuma ya zare sidadden silifan sa ya zauna akai ya kurawa kofar shiga masarautar ido yana tunanin ta inda zai bullo.
Kafin ya farga sai ya ga Sa'ade na gyangyadi akan kunshin kayan ta sabida wahala da gajiya.
Sai ji yayi wani Dogari ya buga musu gigitacciyar tsawa, "Kai tsoho! Me kuke nema anan?"
****

Baba Sale ya mike yana kakkabe kurar jikin sa Sa'ade ma ta yi firgigit ta farka daga gyangyadinta, sai rarraba ido take gabadaya ta firgice. Cikin raunin murya Baba Saleh ya dubi dogarin ya ce.
"Mu baki ne tun daga Tsanyawa ta jihar Kano, bawan Allah na zo garin nan ne takanas don in ga Sarkin Askira, don Allah don Annabi ka taimaka mana".
Wani wulakantaccen kallo dogarin yayi musu sannan ya ce "ka san wa ka ke nufi kuwa? Tsoho anya lafiya kalau kake?"
Baba Sale yayi murmushi mai ciwo irin wanda dan adam ke yi in yana son boye bacin ran sa, ya ce "bani da alaqa da shi, kuma ban zo neman komai wajen sa ba, sakon dana ke dauke da shi na matar sa ne, kaga kuwa bai yi daidai ba in nemi ganin matar sa ba tare da na fara neman alfarmar sa da yardar sa ba. Ka taimaka mana ko don yarinyar nan da ke jin yunwa, marainiya ce".
Dai-dai lokacin wani gajeren dogarin ya taso don ganin abinda ya tsayar da dan uwansa wajen wadannan mutanen masu kama da korarrun jeji, "Buba me suke nema ne?" A raine ya dube su sannan ya nuna su da bakin sa "wai maimartaba suke son gani" "amma shine zaka bar su a tsaye ko wurin zama bazaka basu ba?"
Ga dukkan alamu shi wannan din mai kirki ne, ya ce da dan uwan sa "maimartaba ya bada damar duk mai son ganin sa ya ganshi cikin kasar sa, cikin aminci da girmamawa, don haka barkan ku da zuwa Masarautar Askira, amma baza ku samu ganin maimartaba ba sai washegarin gobe in Allah ya kaimu idan an fito fada".
Baba Saleh yayi godiya sannan ya ce "don Allah ko zan samawa yarinyar nan wajen kwana? Ba mu san kowa a garin nan ba, ni bani da matsala ko a nan wajen zan iya kwana".
Wanda aka kira da Adamu wato mai kirkin dogarin, ya ce "ta zo muje in kaita wajen matata ta kwana, kai kuma ka biyo ni".
Matar Adamu itama baiwa ce a gidan, bangaren su yana daga can karshen masarautar, unguwa ce guda duk bayi ne da iyalan su, amma yawanci basa wuni anan kowacce tana sassan data ke aiki cikin masarauta, sai dare can suke komawa gidajen su.
Ta zubawa Sa'ade tuwo da miyar yauki ta kawo mata ruwa a kofin silba, Sa'ade ta tasar ma tuwon nan kamar Allah ya aiko ta. Sai da ta ci ta koshi matar ta zuba mata ruwa a buta ta nuna mata bayi, taje ta kama ruwa ta fito tayi alwallah ta shimfida mata tabarma anan dan tsakar gidan ta, ta shiga rama sallolin da ke kanta. Ana idar da sallahr isha kuwa barci ya dauke ta akan tabarmar data yi sallar, matar tayi mata shimfida a dakin ta ta tashe ta ta koma daki, ita kuma ta cigaba da ayyukan ta.
Washegari ta bata koko da kosai ta karya kumallo, ta sa ta tayi wanka ta canza kaya cikin nata dake kulle, Adamu bai shigo ba sai karfe goma na safe ya ce ta biyo shi. Tayi wa matar da ta ji ya kira Kubra godiya sosai, tabi bayansa, anan waje suka hadu da Baba Saleh ya ji dadin ganin ta cikin kyakkyawar kama, ya karbi kullin kayan ta suka bi bayan Dogari Adamu zuwa fadar sarki.
Wuce wannan shigifa, tsallake wannan soro, wuce wannan falo har suka dangana da inda Sarki ke ganawa da jama'ar gari a kowacce rana.
Dogarin ya ce su tsaya daga waje, ya shiga ya fadi yayi gaisuwa, sannan ya fadi sakon Baba Saleh, Wazirin sarkin Askira yayi masa tambayoyi a kan su kafin aka amince masa kan ya shigo da su.
Baba Sale ya shigo rike da hannun Sa'ade, ya fadi yayi gaisuwa yadda ya ga ana yi, dogarawa suka ce "Sarki ya gaishe ka, ka yi gaggawar fadin abinda ke tafe da kai".
Baba Sale ya muskuta sannan ya soma koro bayanin sa cikin nutsuwa, wasiyyar da abokin sa marigayi Malam Hashimu ya bashi a lokacin da yake cikin tsananin ciwo akan gargarar mutuwa, na cewa ya kawo yarinya Sa'ade hannun BILKISU a masarautar Askira idan ta Allah ta kasance da shi. Ya gaya mata cewa diyar ta ce da ta haifa tare da shi a garin Tsanyawa.
Sarki Yusufu Bin AbdulHakimu (mai Askira), ya dan zamo daga cikin kujerar mulkin sa ya tsurawa yarinyar ido, wadda ke sanye cikin ragga, 'yar kauye futuk, ya shiga tunanin ta inda ta fito daga jikin matar sa mafi soyuwa a gare shi, ya san ta taba aure kafin ya aureta, amma bai taba sanin tana da 'ya ba, bata taba gaya masa ba.... Sai dai ido, hanci da baki kadai sun nuna zahirin kamannin Fulani Bilkisu a tare da yarinyar. Jini baya taba buya. Har lange-langen jikin. Musamman data dago manyan idanunta tana kallon sarkin, sai ya ga kamar Bilkisun ce ke duban sa da manyan fararen idanun ta.
Magana yayi kadan da Wazirinsa, shi kuma ya yiwa bafaden dake gefensa magana, sai bafaden yace da Baba Saleh su biyo shi.
Wani hamshakin falo ya kai su can hanyar shiga cikin gidan, falon bai cika girma ba, amma ya sha adon kayan fata na sarauta dasu tum-tum, dogarin ya ce su zauna anan, su jira rabin awa.
Daga Sa'ade har Baba Sale ba mai magana, sai kalle - kalle suke mai nuna kauyancin su tifikal, zuwa can Baba Sale ya nisa ya ce.
"Sa'ade! Ko me kika ga ya faru da bawa haka Allah ya ga damar ya kasance a gare shi, idan mahaifiyar ki ta karbe ki shikenan, idan bata karbe ki ba, ni zan rike ki tare da Hanne a cikin iyali na har iyakar nawa numfashin".
Daga yadda yake magana zaka gane ya karaya, bai san girman masarautar da kasaitar ta ya kai haka ba! Bai san sarautar babba ce irin wannan ba! Ya dauka normal sarkin kauye ne irin wanda ya sani. Masarautar Askira kuwa tana cikin manyan masarutun jihar Borno masu tsohon tarihi da yalwar arziki wadanda ke sahu na biyu a jihar ta Borno bakidaya.
Sa'ade cikin rawar murya ta ce "Baba Sale ni dai mu koma Tsanyawa.... ko ta karbe ni bazan iya zama a gidan nan ba tsoro nake ji....wallahi bazan zauna ba". Baba Sale cikin lallashi ya ce "ki kwantar da hankalin ki Sa'ade, idan ta karbe kin shine babban gatan ki, kin ga ni na tsufa, ko zan rike ki na dan lokaci ne nima wa'adina zai cika, baki da kowa a Tsanyawa bayan ni da Innar Hanne, aure zai yi miki wuya don kuwa babu wanda ya san asalin iyayen ki".
Yana rufe baki suka ji ana "gyara kimtsi mai Askira......taka lafiya Giwan Askira.....". Sarki ya shigo falon shi kadai, dogarawan suka tsaya daga waje. Kujerar sa wadda ita kadai ce kujera a falon ya je ya zauna. Baba Sale ya fadi kamar zai yi sujjadah yadda ya ga ana yi ya kara gaida sarki, sarki yai masa murmushi ya amsa da wata irin hamshakiyar kamilalliyar murya. Ya mika hannu ya yafito Sa'ade,
"zo nan kusa gare ni diya ta".
Sa'ade ta rarrafa ta isa gaban shi, ya dora hannu a kanta ya ce "yaya sunanki?" Murya na rawa ta ce "Sa'ade!" Yayi murmushi ya ce "Sa'adatu dai ko? Sannu da zuwa Askira kin ji Sa'adatu?".
Sannan ya maida hankalin sa ga Baba Saleh yace ya bashi labarin rayuwar Sa'ade a hannun mahaifin ta tun daga sanda mahaifiyarta ta bar ta. Baba Sale ya gaya masa duk irin abinda ya sani cikin nutsuwa akan Sa'ade da Baban ta, da irin yadda yadda ya raine ta cikin tsananin kulawa, ya gaya masa malam Hashimu ya gaya masa ba don rayuwa da yake zaton ta kare masa ba bazai taba baiwa Bilkisu 'yar sa ba, sabida bai taba jin dadin zama da ita ba har auren shekara biyu ya shiga tsakanin su ya kare a shekaru biyu kacal.
Ya gaya masa wahalar da yarinyar ta sha a hannun matar uban ta, da yadda ta kare rayuwar ta a talle. Sarki Yusufu ya kara jan Sa'ade jikin sa yana tunani cikin ransa "anya Bilkisu ce da ya sani? Zata haifi Da ta tafi ba waiwaye shekaru goma sha biyu? Kuma bata taba gaya masa ba daidai da kuskure, ya san dai a bazawara ya aureta amma bai san komai ba bayan wannan akan auren nata na baya. Bata son zancen ko kadan. Shi kuma nan duniya sai ya samu zuciyar sa da matsananciyar kaunar Sa'ade, wadda tausayi da soyayyar uwar ta shine sila.
Ya tambayi Baba Sale asalin malam Hashimu, Baba Sale yace "kowa ya san Malam Hashimu bakon haure ne a Tsanyawa babu wanda ya san asalin sa, amma a sanda yake bashi wasiyyar kawo Sa'ade wajen Innar ta ya gaya masa shi dan asalin garin Damaturu ne.
Daidai lokacin da aka daga labulen falon, ta shigo cikin taku na kasaita, sanye cikin farar alkyabba da hular alkyabbar a kan ta. A kasan alkyabbar wani kasurgumin bakin leshi ne mai matukar nauyi. Doguwa sambaleliya, fara sol, kamar da ka taba ta jini zai yi tsartuwa. Fatar jikin ta a murje, ga tsayi ga zati, sannan ga kira ta matan Shuwa-Arab tattare da ita. Akwai barima ta danyen gold makale a gefen hancin ta. Manyan fararen idanun ta sun sha 'kohl' sai walainiya suke suna fidda wani sheki na musamman.
A hankali take taku har ta isa gefen mijin ta ta zauna. Kuyangin ta suka tsaya daga waje. Ta bi mutanen dake sunkuye a gabansa da kallon mamaki, don sun fi kama da normal talakawan gari, amma a falon ganawar sarki da iyalin sa? Kuma saboda su ne aka kirawo ta?
Idanunta suka kai ga birkitacciyar bakauyiyar yarinyar dake zaune gefen sarki, ya rike ta cikin jikin sa. Ta tsurawa yarinyar manyan idanun ta tana kallon ta, idanunta a hankali suke kara girma suna fidda mamaki da al'ajabi. Da gaske ne da aka ce duk inda uwa ta ga dan da ta haifa cikin kowanne hali sai jikin ta ya bata.
Babu wanda ya ce mata uffan tsakanin sarki da Baba Saleh, har saida ta dauke idon ta daga kan yarinyar ta sunkuyar. Wani abu yammmm! Na bin jikin ta. Tsigar jikin ta na tashi. Ta kifa fuskar ta cikin tafukanta, cikin zuciyar ta take fadin......
"dama na san ko bajima ko ba dade zata zo ne da kafafun ta, muddin ni na haife ta. Amma ban zaci a wadannan kananan shekarun ba, na dauka dai sai ta mallaki hankalin kanta zata kawo kanta".

Sarki Yusufu ya kama hannun Sa'ade ya sanya cikin nata. Expression na fuskarta kadai ya gaya masa duk abinda Baba Saleh ya fada gaskiya ne.
"Jeki ga mahaifiyar ki Sa'adatu, ki ji dumin jikin ta, kamar yadda kowanne da yake jin dumin jikin uwar sa".
Sa'ade ta kasa yin hakan, ganin yadda matar ta cire hannu daga fuskar ta ta bubbude mata ido, kamr tana gargadin ta da yin hakan. Ta dubi Baba Saleh da kakkausar murya tace.
"Kai dan aiken Hashimu! Ka koma ka gaya masa yadda Bilkisu bata taba son sa ba, haka bata son abinda ya fito daga jikin sa, bana bukatar 'yar sa ya cigaba da rikon abar sa shi kadai".
Sa'ade ta fashe da kuka, Baba Saleh kuma ya sunkuyar da kai. Sarki Yusufu ya daga ido cikin firgici ya dube ta, anya Bilkisun sa ce wannan? Wadda ko barorin ta bata dagawa murya tsakanin ta da kowa kyautayi ne da mutuntawa? Balle dan da ta haifa? Dan da kullum take adduar Allah ya bar mata ko guda daya?
"Ko da Hashimun ya mutu bazaki rike 'yar da kika haifa ba?"
Muryar sarki akwai fushi da fusata mai tsanani a cikin ta a lokacin da ya jefe ta da wannan kalami, mikewa tayi tana shirin barin falon ko kadan zuciyar ta bata russuna ba, "idan ya mutu yana da dan uwa a garin Damaturu, a kai ta can ya rike masa". Har ta kai bakin kofa sarki ya kira ta da kakkausar murya...
"FULANI BILKISU!"
Ta dakata, amma ba tare da ta juyo ba.
"Zo ki kama hannun 'yar ki ki tafi da ita sassan ki, ki bata duk kulawar da uwa zata baiwa danta, tana karkashin amana ta, zamana zata yi a gidannan daga nan har karshen rayuwar ta, a bisa kulawa da kiyayewa ta".
Yana fadin hakan ya mike tsaye, ya dubi Sa'ade da ke kuka wurjanjan, "daina kuka Sa'adatu, mahaifiyar ki ce bazata cutar da ke ba, dauki kayan ki ki bi bayan ta". Sa'ade ta share hawayen ta da bayan hannun ta, ita in aka ce wannan galleliyar matar mahaifiyar ta ce ma wani iri take ji, tsigar jikin ta har tashi take, tsoron ta take ji sosai, gata da manyan ido da wani irin kwarjini, ita gara ta bi Baba Sale su koma Tsanyawa, abinda ta fada cikin kuka kenan, amma Baba Saleh ya girgiza mata kai ya ce.
"Bi ta Sa'ade, kiyi mata biyayya a bisa dukkan umarnin ta, aljannar ki na tare da ita".

Ta dauki tsummokaranta tana waiwayen Baba Saleh, shikuma yana yi mata murmushi, tuni Fulani Bilkisu ta fice, kuyangin ta sun mara mata baya, sai da ta hada da gudu-gudu ta cimmasu, Sarki Yusufu yace da Baba Saleh za'azo a kai shi masauki ya huta har zuwa iya kwanakin da ya ke so, sannan zai sa a maida shi har Tsanyawa a motar gida, zai bada sallama a bashi, Allah ya kai shi gida lafiya, yana yi masa fatan hutu mai dadi cikin masarautar sa.
Baba Saleh ya zube yayi ta godiya, a take dogarawa suka kai shi masaukin bakin sarki, aka wadata shi da abinciccika da ababen sha na alfarma, sittiru da duk abinda zai bukata. Amma duk wannan bai dame shi ba, tunanin sa na ga halin da Sa'ade zata kasance a hannun mahaifiyar ta.
Wadda ta nuna a fili bata bukatar ta cikin rayuwar ta.
Bai san laifin da Malam Hashimu yayi mata ba, amma ya lura kiyayyarsa ce ta shafi 'yar sa.
Abu daya yake da yakini yake kuma dan kwantar masa da hankali idan ya tuna ita ta haifeta da gaske, duk kin ta da ita bazata cutar da ita ba, sai dai ta kasa nuna mata soyayya.
Yana tausayin Sa'ade sabida bata taba dandana kaunar UWA ba, bata taba jin dumin uwa ba, ga wahalar data sha hannun Laure, sannan yanzu ga ta ga uwar amma bata kaunar ta.
Zuciyar sa tayi maza ta ce masa "ba ita ce bata so ba uban ta ne bata so, da sannu in sun zauna tare Allah zai musanya zuciyar ta zuwa alkhairi akan 'yar ta"..
Da kyar ya samu ya runtsa a wannan dare sabida tunanin Sa'ade, hutun da aka ce ya zauna yayi ya ga bazai iya ba, washegari ya gayawa mai kula da shi ya gayawa maimartaba yau zai koma garin su. Sarki yasa aka yi masa goma ta arziki, aka cika masa bayan mota hilux, sannan ya damka mishi kyautar kudi da sittiru masu yawa.
Suka kama hanyar zuwa Tsanyawa a mota hilux zuciyar Baba Saleh cike da alhini na tausayin Sa'ade.
****






Sa'ade na bin kuyangin Fulani a baya, fada nan fada can har suka dangana da wani babban gini, kamar gida guda bangare guda haka, aka bude kofar Fulani ta sanya kafar ta kamar wata Dawisu sabida yadda take taku su kuma suna biye da ita, kyawu da kayatuwar ginin yasa Sa'ade sakin baki da hanci tana kallo, har tana tuntube saura kadan ta fadi.
Manyan faluka suka rika wucewa har suka tadda wanda daga shi kuyangin suke da shamaki, sai guda daya daga cikin su ce ta bi bayan Fulani, bata jima ba ta fito tace da Sa'ade wadda ta tsaya a inda ta ga kowa ya tsaya itama, ta biyo ta ta kai ta dakin da zata zauna.
Inda Fulanin ta shiga nan ta ga sun shiga, wani (english parlour) ne komai fari sol har labulaye da kujeru, kilishin falon ne kawai launin makuba shima da adon fari da baki a jiki, kofofi ne wajen guda hudu a falon bata san a wanne Fulani ke ciki ba, kuyangar ta bude daki daya suka shiga. Sa'ade ji tayi numfashin ta ya tsaya a wuyanta sabida kyawun dakin da tsaruwar sa, komai dake cikin dakin kalar blue and light pink ne, ga wani shimfidadden gado na sarauta (royal bed) da ya ji shimfidu na alfarma.
Kuyangar ta shiga bandaki ta hada mata ruwan wanka, tazo ta kama hannnun ta ta kaita har gaban kwamin wankan, ta nuna mata yadda ake amfani da komai don ba sai da bayani ba kallo daya za'ayi wa Sa'ade a fahimci bata taba alaqa da irin wannan muhallin ba a rayuwar ta. Ta kasa boye firgici da razanar data ke ciki.
Kuyangar tace zata cuda mata baya. Sa'ade ta zaro ido tace "bana so". Ta fita ta barta bayan ta tattare tsummokaran data tube ta hada da kullin kayan ta ta fita dasu ta zubar kamar yadda Fulani ta bata umarni.
Kafin Sa'ade ta fito ta ajiye mata dogayen riguna daidai tsayin ta guda biyu a gefen gado, sannan ta shigo mata da abinci lafiyayye kala kala akan tray. Ta zauna har ta fito daga wankan daure da tawul din data nuna mata sannan ta gaya mata nan ne dakin ta, ba koyaushe zata ga Fulani ba, in tana son ganin ta zata nemeta da kanta, ba'a yarda taje ko'ina bayan dakin nan ba, duk abinda take so ita kuyangar zata dinga shigowa tana yi mata, ta gaya mata cewa itace amintacciyar Fulani, kuma ita kadai ke shigowa wannan sashen, sunan ta "Fanna".
Sa'ade ta gyada mata kai alamar ta gane, sannan ta ce da ita "ga hijab nan da darduma kiyi sallah".
Bayan fitar Fanna Sa'ade zama tayi a bakin gadon a dofane tana ta kallon dakin, sai ta ji duk alatun dake cikin sa bai burgeta ba, ta ji duniya tayi mata kunci, kewar Baban ta mai son ta, ta zo ta lullube ta. Soyayyarsa ta fi mata duka wannan alatun da babu soyayya a cikin sa sai kiyayya zallah.
Amma duk da wannan damuwar dake cin ranta, ba abinda zuciyar ta ke hango mata sai fuskar Fulani Bilkisu ma'abociyar zati da kamala, da wani irin feelings mai fizgar zuciya tamkar maganadisu (maternal love). Wata irin soyayya da bata taba ji akan kowa a duniya ba bayan Babanta, wannan soyayyar har ta zarta wadda take ji akan Baban ta. Shine abinda ta ke ji akan Fulani Bilkisu!
Ta lumshe ido tana hasaso yadda ta zazzaro mata ido kada ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MASARAUTAR MU
avatar
zainabaliyu

8 months ago

Reply

I really appreciate masarautar mu, thank you

Please Login or Register in order to submit comment