Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled by Umar Dalha.

. BIBIYATA AKEYI

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
_Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)_

Page 1

Zaune take acikin wajan amma hankalinta baya jikinta domin kana kallanta kasan tana cikin matsananciyar damuwa wanda hakan yagaza boyuwa sanda yanuna akyakyawar fuskarta,

Tunani take acikin zuciyarta shin ko tajene tasamesu taji dalilin wannan *bibiya* da takura dasuke mata ne, atake wata zuciyar tayi saurin gargadarta domin batasan mugaye bane,

Amma aida mugaye ne dasun dade da cutar dake, wata zuciyar tace da ita. Mtswww taja wani dan siririn tsaki, ni wallahi tsoronsuma nakeji tafada cikin muryar kuka tareda kifa kanta ajikn table dinda yake gabanta.

Tosu wayannan mutanen suwaye?? mesuke nema awajanta??? Wani laifin tamusu dasuke *bibiyar*rayuwarta?? dataga dai bata dayadda datasamu amsar tambayoyinta kawai tamike tare da zarar jakarta tayi hanyan fita daga restuarant din dake cikin school din zuwa hall na lectures dinsu tana kallo daya yayiwa daya mZ33yyb3rw3ramu nuna masa ita yayi akan tatashi subita koda taga haka wuff tafice daga cikin wajan batareda datsaya biyan kudiba dan damuwa bata barta tayi ordering komaiba

Koda tafita tayi noticing ana binta amma hakan be daga mata hankalinta dan abunyafara binjiknta direct hall dinda zasuyi lectures tawuce tasamu har malamin sunshiga sa'arta daya bame tsanani bane yasa tayi saurin shiga tasamu gefen kawarta amira tazauna

Amira rada tamata akunne ke inata kiran phone dinki ina kika shiga kikabari phone anata kira banza ainaso kiyi missing attendance,

Gabaki daya wannan surutun da amira takeyi batasan atakure dakeba kawae tatashi tacanja wajen zama tace kici kanki

Ana tashi kuwa ko takan amira batayi ba tafice dama shine last lecture dinsu na ranan, kodatafita batayi mamakin ganinsu ba don tasan za'a rina (wae miji ya saki mata ubansa yaje zauranci)
Fita tayi tawuce gida koda tana keke napep ma haka taga suna binta sanda tazo dab shiga gida kafin suka juya,

Tana shiga gida tasauke wata nauyayyan ajiyan zuciyarta,
Da sallama tashiga tasamu babansu harya dawo tatsuguna aladabce tamasa sannu da hutawa ya amsa cikin sakin fuska sannan tatashi zata tafi harta fara tafiya naji yace, *hanna*

*Hanna*ni unknown nakara maimata sunan araina nace amma sunan yayi saurin juyowa tayi cikin ladabi da nitsuwa tace na'am baba yace idankin shiga ciki kyakiramin mamanki toh tace tareda juyawa

Tacigaba da tafiya cikin nutsuwa giftawa tajeyi taji wani zancen daya hargitsa mata Tunani yakara gigitata tare da tsundumata cikin damuwa kunnenta takara kawowa kofar dakin taji hajiyah lami wacce suke kira da Amma tanacewa,

Ai aikin malam nakarangi yanakyau kiduba tun yarinyannan naarama danasa yatura mata aljani wadda ze hanata aure aizancen danake miki haryau bbu wanda yataba sallama da sunan yazo wajanta ga yan uwanta komai ya kankama biki kawae muke jira itakuwa shiru kikeji kamar an aiki bawa garinsu tana gama fadin haka suka tafa tareda shekewa da wata shedaniyar dariya aibata jira sunkara wata maganar dazata daga mata hankaliba tawuce jiri na ebar ta harshirin yasadda ita yakeyi

Tana shiga dakin mamansu kawae tafada kangado tasaki wani marayan kuka me tsuma ran me sauraro

Temakonta daya mama bata dakin yasa tayi kukanta mai isarta daganan tatashi tawanke idonta daganan taadauro alola tayi la'asar tayita addu'o in neman tsari daga sharrin mutum da aljani

Mamane itada inna kaltu mai aikinsu Zaune akicin tana dafawa baba ruwan shayi ni inna kaltu kuwa kinga diyarki tadawo daga makaranta

Najita shiru haryanxu batazo tacemin tadawoba inna kaltu take aikwa bangantaba inaga bata dawoba, to halan cewar mama dauke da gajeruwar damuwa aranta

Yarone dan kimanin shekaru 12 yayi sallama mama waekije inji baba yana falo yana jiranki toh kace masa ganinan zuwa

Fita tayi daukeda farantin ruwan shayi ahannunta tanufi falo anan tatarar da baba yana karanta jarida sallamarta ce tasashi ajiyewa tareda zare gilashin dake idonsa amsa sallamar yayi sannan takaraso ciki tazauna tazuba ruwan shayin tamika masa yakarba yadan kurba sannan yayi gyaran murya mama tajuya ta fuskanceshi dan da'alama maganar dayakesonyi mai mahimmanci ne

Shin waini halima meyake damun diyarkine gabaki daya ina lura da ita kwanannan batasakewa batada walwala shin meke damunta?? Hmm wani gauron numfashi taja wallahi alhaji nima kwanakinannan haka nake kallonta narasa meke damunta nifa alhaji inaji yarinyar nan dagaske fadan mutanenne halan aljanine ya aureta

Kul karnasake jin wannan zance abakinki baba yayi saurin gargadarta ni inaji aji kina wani alkhairi ne yake BIBIYAR RAYUWARTA kace mahaifiyarta keyakamata kije kiji damuwarta

Bayan ta idarda sallah ne taki shingida tafara gyangyadi tagakamar inuwar mutum akanta agigice tafarka ta............

Shin wae wayake BIBIYAR rayuwar *hanna*??????????

Shin wae Su wayannnan mutane dasuke BIBIYAR yaruwarta ta suwayene???????

Shin dagaske Aljanin da aka turo mata ya sameta kuwa ko akwae wani boyayyen al'amari ne

Domin samun amsar wannan tambayoyi kubiyoni musamosu tare

Ur's
Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
_Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)_


Page 2
*
Gani tayi kamarda inuwar mutum akanta agigice tafarka lokaci daya kuma tasauke ajiyar zuciya ganin mama dake tsaye akanta,

Sunkuyar da kanta tayi sannan tace sannu dashigowa Mama batareda ta amsa taba tasamu waje tazauna sannan tace *hanna* ta dago takalleta cikin sanyin murya tace na'am mama,

Meyake damunki kifadamin dan banasan kallonki cikin damuwa murmushin yake ta kirkiro sannan tace bbu komaifa mama mekika Gani shiru mama tayi tazuba mata ido tana nazarin yanayinta ta kunsan uwa da danta koyaya dah yakai da boye damuwarsa takan gane yana cikin damuwa

*hanna* sunanta da mama takira ne yasata dago kanta daga sunkuyen da take sannan tace na'am mama tadaura da cewa nimahaifiyar kice kina tunani idan baki fadamun damuwarkiba akwae wanda yacancanta kifadawa bayanni

Murmushin yake takara kwakulowa sannan tace Allah mama bbu komai kainane yakemin ciwo kuma gashi samester yazo tsakiya karatu yafara zafi

To Allah yasauwake kisha magani saikihuta mama tafadi hakane bawae danta yarda cewa yartata bata da wata damuwa ba, kuma bawae dan tanada tabbacin datasha maganinba

Mama nafita tasauke ajiyan zuciya tareda jawo alqur'ani taci gaba da karantawa nantake taji kashi tamanin daga cikin dari na damuwarta ya gushe damuwarta ta batafi saura kalilanba

Rufe qur'anin tayi sannan tanade pray mate din cikin natsuwa tanufi kofar Fita daga dakin

================

katafaran masarautace mai girman gaske
Wanda ko bantsaya muku bayaniba kunsan yanayin girman masarautar kano dan tana daya daga cikin masarautu masu girman gaske
A wannan kasa tamu masarautace mai yawon jama'a

Da dumbin alkhaire atattare acikinta wanda kuma tasamu adali jajirtaccen sarki dattijon arziki mai farar aniya

*Sarki*Abdulaziz lamido

Wata mata nahango zaune akatafaren falon sarki wanda yasha kayan alatu dana more rayuwa matar dake zaune afalon kana kallonta koba'afada ba kasan itace matar sarki domin ko daga yanayin kayan dayake jikintama zainuna hakan balle azo zuwa yanayin fatar jikinta

Dukda dai bawata walwala atare da ita amma hakan baihana kyawun fatarta futowa kallo daya daka mata kagane damuwar dake tattare afuskarta

Ahankali tasa gefen gyalenta tamatso kwalla sannan tace mai martaba badai kanaso kagwadamin bani na haifeshiba shiyasa kaki amincewa da kudurina amma kasan yanda nake sansa araina koh yayan dana haifa bana sonsu haka

Kasan yadda nake jinsa araina kuwa tafada cikin muryar kuka inajin ciwo acewae shekara 35 amma haryanxu yagagara yin aure kuma munzuba masa idoh muna kallonsa

Nifa wannan yarinyar daya damu da ita atunanina aljanace ba mutum ba, mai martaba yakura mata ido kawae domin bayaso yatsaida ita saita dasa aya

Sannan taci gabada cewa tayaya xa'ace shekara tara kenan kullum zancensa mutum daya bamusanta bamutaba kallontaba

Mai martaba baza'aduba wannan zance ba idan da'abi shawarata atara malamai kawae suyita masa rokon Allah har adace wannan aljana tarabu dashi

Gyaran murya mai martaba yayi sannan yace bawae naki tatakiba amma yakamata mujira harsai shekatunda ya eba mana suncika kafin muyanke masa hukunci

Ainida ba se anjira ba dan wannan ba mutum bace ga yar uwarsa intisar aisai ahadasu

Kilishi Kilishi Kilishi mai martaba yakira sunanta tareda hadaerai sannan yace

Nafada miki alkawari na dauka zanbarshi yacika wannan lokacinda ya eba donhaka banasan sake jin tashin maganar nan

Toh tace amma bawae dan ranta yasoba sannan tatashi tawuce zuwa shashinta

Tana Fita fadawa sukafara kwasan gaisuwa amma ko kollonsu batayiba tawuce dayake Kilishi Allah yayita mace mai girman kai dakuma nuna isah

================

Zaman cikin gidanne yasoma gagararta domin sai habaice habaice kawae akeyi

Koda Mama taji abinda Su Amma sukeyi hakan baisa tatanka musu ba dan inda sabo tasaba kuma Allah yayita mace mai hakuri wanda gane fushinta abune mai wuya

Juyarda kanta tayi wajan inna kaltu sukacigaba da aikinsu domin yau itace mai girki domin bata taba bari mai aiki tayi ma mijinta abinci itata keyin kayanta

*Hanna* tashi tayi tayi da niyar shiga daki Hafsat da rabi'ah wanda suke yayu a wajanta ne suka tafa tareda shekewa da dariya Hafsat tace dama wasukam Ai saidai Zaman daki domin ba mashin shini suka kara tafawa yoh saima kunbata bakinkune kewar amma aixaman daki yanxu akaafarashi

Zuruf *hanna* tashige daki domin itama kanta abunyana damunta wani irin bakin jinine dani tafada tareda fashewa da matsanancin kuka

Amma yau tasamowa kanta amsar tambaya tada dade tana addabarta aranta, aljanine dagaske ya aureta tunda da kunnan ta taji bawani bane yajimata

Toh sukuma wayannnan masu *bibiyarata* suwaye shin ko suma aljanune??? ta tambayi kanta

Wannan tambayarne haryanxu takasa samun amsar ta kuma batasan wazata nema ya amsa mataba

Saidai takudirta aranta bawanda zaiji wannan zancen
Ai idan aljani yafi karfinta Toh itama akwae wanda zata kai karansu wajan sa

Tadauki alkawarin yin tsayiwar dare tahana idanta barci harsai Allah yamata sakayya da wayannan azzalumai masu BIBIYAR rayuwar ta.

Shin wae waye itah wannan hanna?????

Shikuma wannan wanda iyayansa suke tunanin aljana ta aureshi wayeshi????

To be continue

Ur's
Z33iiyyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)

Page 3
*
DUBAI

Wani tangameman gida nahango, wanda fadin girmansama tsayawa bata bakine, kyawunsa kuwa kokadan baya misaltuwa domin bansan dawani yare zanmuku bayanin da har zakugane kyau tsaruwar wannan gida ba, hatta tsaron gidan ma, sojojine masu tsaran gidan sunza gayeshi , tako wani sako da lungu gaba da baya,
Azatona tunda kasar larabawa ne nadauka sojajin larabawa zangani amma inah zancen yasha bam bam,

Sojojine kala kala wanda kowace kasa sanda suka bada gudumawa wajen kare lafiyar wannan bawa nasa, kowani soja yana sanyene da kakin kasarsu sojojine bila adadin wanda irga yawansuma bamai yiwuwa bane,

Mamaki da alja'abi suncikani waishin waye wannan dan adam dinda ake gadin rayuwarsa haka. ko sucurities dasuke gidan shugaban kasa basukai natsaron wannan bawan Allah yawaba,

MAJOR GENERAL (MG) Abudullahi kukeji daya tamkarda dubu, gwarzon namiji wanda kallonsa kadae ke razana makiyah, ba country dinsa ba kadai
hatta da sauran kasashen sunaji dashi shiyasa suke bada gudumawa wajen kare lafiyarsa, domin shi mai sadaukarwa al'ummah rai da lafiyarsa ne,

Zaune yake kankujerar tangameman falonsa kafanshi daya akan daya ya jingina da kujera karkada kafansa yakeyi ahankali cikin nutsuwah da solon birgewa,

Farineh tass kyakkyawan gaske wanda kana kollonsa dakaga kamanninsa da larabawa dogo neh sambal mai faffadan kirji, gwarzon namiji, subhanallah kyawun wannan bawan Allah, abin ba'acewa komai, saidaai hamdala. idanuwansa farare tass kwayar cikin kuwa bakikirin shape dinsu oval ne masu kyawun gaske, gashin kansa bakine sidik, with his cute pink lips, OMG he's damn cute, i don't even knw how to describe him, he's so muah👄

Rurinda wayarsa tadaukane yasashi bude idoh ahankali cikin nutsuwa daukan wayar yayi tareda karata akunnensa.

Amsa sallama yayi sannan yayi hade dayin murmushi subhanallah kyawunsa baisake bayyana ba saida both side na face dinsa suka lotsa (beauty point)
Abin al'jabin baizoba sanda yafara magana da hausa wadda hakan ba karamin abin mamaki bane
Amsawa yayi da toh abba ammafa akwae abinda nakeyi wadda haryanxu bankarasaba yana maganane cikin natsuwa abba ba halin tafowane cewarsa dadahali danazo cikin week dinnan saboda nima nayi kewarka ina bukatar ganinka to
Call u later baejira mai za'aceba kit yakashe wayan

Wata nauyayyar ajiyar zuciya yasauke kokadan bayason abinda zaisa yaje gida yanxu

Danbaxai iya jira lokaci yacika kafin ya cika kudurinsaba yafi masa sauki yajira lokacin kafin yashiga kasarsa tahaihuwa

Karar saukowar takalmintane yakatse masa tunanin dayakeyi
Wata farar matace wacce bazatafi shekaru hamsin da biyar ba kana kallonta ko tantama bbu dakasan itace mahaifiyar MG Abudullahi balarabiyace
Kyakkyawar gaske
Ko banfada ba kunsan yanayin yanda kyawun larabawan Dubai yake
Karasowa tayi dauke da murmushin dake kara fitoda kamanninsu da MG Abudullahi zama tayi kusa dashi tadafa shi sannan tafara magana cikin harshen larabci

Meyake dmunka haka naga gabaki daya yanayinka yachanja lokuta da dama nakan fada maka kacire wata fargaba bbu wata wacce xatasamu miji kamarka tace bataso kanada kyau da mulki da kuma dukiya bbu wata mahalukiayar da zata kika

Shiru yayi nayan wasu dakika sannan yace ummee bana so asoni dankyawu na ko kudi kowani mulki danake tattare dashi

Mutane dayawa bawae sunasona bane wasu tsoro nane yakesawa sununamin so wasu kuma dan dukiya da mulki yasa suke sona bawai har zuciyah ba wani zafaffen huci yafitar yakara damke hannun ummi dayake rike dashi ummee tajawoshi jikinta ahankali tafara shafa kansa batareda tace komaiba

Aranta kuma tanace Allah kasaukakawa wannan bawa naka wannan jarabawar da ya tsinci kanshi aciki tana tausayin danta ace yakamu dasan wanda basumasan ko tana existing ba

================

Yauma kamar kullum shiri tayi tsab nazuwa makaranta doguwar rigane ajikinta ta yane kanta da gyalen rigar wadda hakan yafito da sihirtaccen kyawunta wanda ba lokaci daya kake kollonta kagano wannan kyawunba

Jakarta ta zara direct dakin babansu tanufa dasallama tashiga sanda ya amsa sannan tashiga tagaisheshi ya amsa da fara'arsa kinfuto kenen eh baba yanxu zanwuce dari biyar yaciro yabata godiya tayi masa sannan tatashi yafibata dakyakkyawar addu'a wadda yakamata duk wani mahaifi yayiwa diyarsa lokacin da zataje wani waje nadaban

Fitowa tayi zuwa bakin titi domin samun abun dazatahau tawuce makaranta duk da chanja mata dasukayi hakan baihanata fahimtar suwaye acikin motar ba adaidata tayi saurin tsara tahau batayi mamakin binta da motar takeyiba har zuwa makaranta sannan ta sallami mai adaidata tayi cikin school din

Sanda suka shiga lectures 80:30 tayi basu suka fitaba basai 11:30 dayake 3hour lectures ne sunafita taji wani irin........

To be continue

Ur's
Z33iiyyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r )



Page 4
*
Suna Fita daga lecture taji wani irin yunwa takamata, wanda bazata iya jira bah harsai tanemi wani abu tasa acikinta,
bawani kudin kirki bane a hannunta yasa kawae tashiga wani dan shop a skull din tasaya malt da biscuit

Juyowar dazatayi gam tayi karo da mutum,
baya tayi zata fadi
Cikin tsafinnama dakuma jarumta,yayi
saurin tarota ,yadaidaita mata tsayuwa, dagowa tayi da niyyar kollon ko waye wannan fuskarta cike damasifa,
lokacin daya kuma ida nuwansu yasauka cikinna juna, wani irin faduwar gabane taziyarci zuwa tanufa,
Zubawa junansu ido sukayi na yan dakiku,
Wani irin shock ne yafara bin tundaga kafarsu zuwa kokon kansu gabaki daya wani yanayi suka tsinci kansu mai wuyar fassarawa,

Saurin dauke kwayar idonta tayi daga cikinnasa, dakyar ya tattaro nutsuwarsa waje daya, sannan kwakwalwarsa ta iya tattaro masa kalma daya yace SORRY, yayinda yakafeta da ido, awani irin salon murya irin na mayaudaran mazannan yayi wannan magana,
Wanda idan sunyi sukan sace zuciyar mace, koya takai dajin kanta,
Amma anashi wajan bawae yayi dan yaudaraba saidan besan lokacin yayi wannan salon ba ,
Aikuwa hakanne tafaru da ita domin wannan murya tagama tafiya da imaninta gabaki daya gabanta ne yahau bugawa dasauri da sauri, cikin dakewa tace is ok tawuce batareda ta kara waiwayowa ta kalleshiba,
bawae kuma dan batasan sake kallonsa ba,
Saidan bataso yamata wannan kallo mai kashe mata jiki.

Matsallaci tawuce Kaitsaye,
dan tasamu tasa wani abu acikinta donko karywa batayiba amma takasa,
abu kamar wasa yanason zama gaske, tunanin wannan bawan Allah yahanata sake,
Zuruf tamike, bata wuce ko inaba sai bakin titi tanemi abin hawa,
Domin yafi mata tawuce gida, bazata iya jure irin wannann sabon yanayi datacinci kanta, acikinta.

================

Wacece ita abinda yake tambayan kansa kenan dukda dai yayi soyayya da mata daban daban amma wannan yanayi daban yake, komade Wacece ita saina samota yafada afili,
wannan itace tadace dani dama inason nace maikyau da tarbiya wannan ko yanayinta yanuna daga gidan tarbiya take,
Numfashi mai zafi ya furzar sannan ya cigaba da driving cikin kwanciyar hankali da nishadi waka yasa yana mamin sayya shafa gashin kansa cikin kwaciyar hankali, yadan daki sitiyari yana kada kai, kana kallonsa kasan akwai nishadi atattare dashi.

================

Mai adaidaita dan Allah juya kamaidani GRA
federal lowcost mukayi zankaiikifa eh nafasa kajuya nace
Kaitsaye GRA suka nufa yasauketa tabiyashi yajuya abinsa,
wani dan madaidaicin gida nagani mai kyan gaske nan tanufa cikin nutsuwa takwankwasa gate din gidan wani dan dattijoneh ya budeh washe baki yayi cikin fara'a yar baba dama kinanan inanan baba ina wuni lpy klau yar baba yakaratu Alhmdllhy tace atakaice tareda wucewa cikin Kaitsaye wata kofa tanufa
Bude kofan kenan amal tajuyo Ai aguje tazo ayoyo ummah(yawanci akan kira kanwar uwa da umma ) anty anty anty aibashiri anty tafuto Lafiya amal irin wannan kira
Tsayawa tayi turuss sakamakon ganin *hanna* anty yayar hannace uwa daya uba daya tanada aure da yara biyu amal da bashir, *hanna* takanyi wata uku bata leka gidan sister dinta ba saboda Allah yayita mai maqon uwa nan dacan taje sai tafara cewar mamanta shiyasa batacika futaba yanxu haka, halinda ake ciki yau *hanna* watanta biyu rabonta da gidan antynta kunga kuwa hanna mai laipy ceh sosai.

Saurin sauke amal tayi
Kama kunnunwanta tayi da hanna yenta biyu alamunna tuba nake,
Folding hanneyanta tayi irin banhakuraba rausayarda kanta tayi tace pleassssssse ok amma da sharadi ehem inaji karkira yin sati baki zoba nayadda tace cikin sauri karasowa tayi suka rungume junansu jin amal sukayi tanacewa nibanda ni jawota *hanna* tayi suka hada suka rungume

Yawwa ainaji dadin zuwanki dama aiki yamin yawa narasa yadda zanyi yanxu saiki canja kaya mushiga kicin,
Gaskiya anty ninagaji kiyi kayanki kawae, yawwa waeni meya hana baby amal zuwa makaranta,
Kedai bari wae uncle dinsune yadawo daga karatu shine wae yau saidai abatta daizo ganinsu, aikuwa yanxu kusan 12:00 harmafa dataje tadawo

Wallahi abbansu amal dinnanma
Agaisheshi dan kaninsa zaizo sai ahanata zuwa maaranta yajira ran weekend mana kafinya gansu mtsww taja guntun tsaki,
Aibaki saniba duk abinda yarannan yafada yazaune
Nibari wannan bamai karewa bane tashi kidauramin abinci.

Tashi tayi cikin azama tafara girkawa dama ita ba bayaba wajen iya girki bawani abinci mai yawa tayiba dan ita aganinta yin abinci kala kala masuci kalilan almubazzarancine.

Fried rice tayii mai raida lpy wadda tasha kayan lambu kala da iri dakuma hanta wanda akayankata kananu sannan tahada coslow wadda yasha dafaffen koyi bama kamar zeyi magana., zobo tahada wadda yasha kayan kamshi sannan tayi kunun aya tahada ayan da dabino da kwakwa ta markada,
daidai cikinsu tayi wadda babu barna aciki, jan nama tasoya tazuba akan abincin tarufe zuwa 1:30 tagama komai tajereshi adaining ta kimtsa ko ina ta wanke kwanukan da akayi amfani dasu,

Fitowa tayi tagyra ko ina nagidan sannan ta jona burner tazuba turare mai dadin kamshi kamkace meh gidan gabaki daya yadauki kamshi mai sanyin dadi.

Wanka tashiga adakin amal daganan tadauro alwola tayi sallah ta idar lokacin anty harta gama shiryasu amal da bashir itama tayi wanka tashirya,

Fita tayi zuwa dakin anty kibani kaya nasa bude wadrop kidauka mana to Ai naga duk kintaba sawane kajimin yarinya wanda bantaba sawaba kikeso nabaki hava anty yanxu ya mahmood yaga kaya ajikinki nima kuma yagani ajikina haba Ai abunda kunya uhm kyaji dashi bude akwati kidauka to anty tank u

Simple makeup tayi dama ita bama'abociya san kwalliya barkatai bane,
Jan swiss less tadauko dinkin riga da siket tasa,
Ya matukar amsar kalan fatarta, dayake farace amma batacika haske sosae ba saidai kuma baza'a kirata da baka ko chacolate ba,
Tayi mamakin yanda kayan yazauna mata chif chif kaman angwada,
Anty kuma tadan Fita kiba kadan.

Fotowa tayi daga dakin tanacewa anty amma kayannan bama kanki kika dinkawa bako????
Fitowa tayi daga dakinsu amal tana rikeda rigar bashir ahannu, wanda tacire masa ranan kewa,
Au dama wannan kika dauka Toh kinyiwa kanki dama dinkin sallah namiki kuma bazan sakeba, hava anty nidin kinefa,
Eh kedin tawa😏, kantarufe baki sukaji karan door bell, jeki duba barin futoda Su amal, juyawa anty tayi ciki itakuma danufi kofa bude kofan tayi tajuya tanayiwa anty magana, alamu taji kaman Ana kallonta, Juyowar dazatayi daga mutum abakin kofa yakafeta da idoh yajingina ajikin kofa tareda harde hanneyanta,

Baki tabude tana kollonsa jitayi yace......

To be continue

Ur's
Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment