Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

HADIN KAI Complete Hausa Novel Document by HADIN KAI


HADIN KAI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 85482



HADIN KAI

Reading Time: 7 Hours

Added On: 13, Aug 2024

Author: Asma Baffa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : +234 8061929616, 08033933642, 09032409668, +227 90795939

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 439.96 kb

File Type: txt

Views: 625+

Download: 1308+

Last download: 2 days ago

Description/Story: ๏ปฟ[9/4, 10:25 PM] Sis Asma: ๐Ÿ•HADIN KAI๐Ÿ•
COPY BY ZAINAB BUTALAWA








1







Official







By
AsmaBaffa












BISMILLAH









Alhmdllh fans Allah ya kawo mu sabon Novel,Allah yasa mu fara lfy mu Gama lfy,Kuma Allah ya bada ikon amfani da fadakarwarsa.

Pls Sharhi nake so da Haka zanfi Jin dadi typing,Kuma zanyi kokarin yiwa kowacce reply inshallah.



Son Kai zanyi wannan page Na ASMABAFFA FANS CLUB ne, ku zan fara bawa.๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹.












Gombe state Kauyen Dingawa Babban kauye ne kusan ma kamar Local Government ne Amma ba a bashi LGA ba, garine na fulanin asali kana Shiga ba sai an fada maka ba.
Fadila Tahir shine cikakken Suna na,Tahir Adam tukur shine Sunan mahaifina,Tahir Adam tukur Asalin fulani ne mu Amma yanzu ba shanu sun Kare,Tahir Su uku ne duk maza iyayensu suka Haifa Wanda har yanzu Suna Raye kakanni na na wajen uwa Dana uba duk ba Wanda ya rasu suna da ransu, Babana shine Babba wajen iyayensa daga shi sai kaninsa kawu Salisu da kawu Usman, gaba daya Allah ya wadatasu Alhmdllh a kauyen Nan Babu masu kudinsu,harkar noma da siyar da kayan masarufi ne sanaarsu,Babana Tahir har mota kurkura da Golf yake dasu duk Ana jigilar Kai Kaya kasuwanni daban daban,Kawu salisu ma Yana da kurkura,Haka Iyayensu Baffa da Yafendo suna Jin dadi ba yunwa ba rashin sutura,sai abinda suke so, daga kakannina har iyayenmu duk sun je aikin Hajji,mune kawai yaran bamu je ba.

Suna da matukar biyayya sai abinda kakanninmu suka tsara shi sukeyi,Tahir da kannensa duk auren zumunci akayi musu,Salisu da Usman matarsu daya Basu Kara aure ba,Salisu Yana da Yara Biyar manya samari guda biyu Mahmoud 28yrs da Umar 26yrs samarine kyawawa farare kasancewar Family dinmu kaf Babu Baki kowa fari ne tas sai dai wasu sunfi wasu fari.
Bayan Umar akwai mace wacce mate Dina ce Saratu18yrs,sai Zainab,da Kuma Abida Yar auta.

Kawu Usman kuwa yaransa biyu Rak Matarsa Bata haihuwa sosai Duk Mata ne Aisha da me Sunan Yafendo Fatima Ana ce Mata Mama.
Babana Wanda shine Babba Tahir Matansa biyu Babata itace ta farko da akayi Masu hadin zumunci Hajiya Hadiza muna kiranta da Hajiyarmu,Bayan Sunyi aure Ta haifi Salman shine 28yrs saurayi saan Mahmood ne Kuma abokai ne,sai kaninsa Musa saan Umar 26yrs, sai Ni Fadila Yar auta a wurin Hajiyarmu Wanda Kuma Ni kadai ce mace a gidanmu,Sai kishiyar Babar mu Haj Balki Amarya tana da Yara hudu Amma duk maza ne Kuma yarana ne kanana Babban 15yrs Abdullahi,Ramadan 12yrs ,Shahid 9yrs sai Ahmad autanta a yanzu 5yrs.

Duk da a kauye muke muna zuwa makarantar Gomnati da Islamiyya,Haka Salman da Musa tare da yaran su Kawu Salisu duk sun Gama HND a garin Gombe Sunyi service Kuma yanzu aiki ake nema musu sannan sai suyi aure Amma har yanzu aiki Bai samu ba sai da hanya Babba.

Ni Kuma na kusa candy muna Ss3 jarabawa zamu zana ta fita,sauran kannena suna secondary wasu primary,muna da kokari gaba daya danginmu Babu dakiki,Sabo da Kawu Usman Yana dauko mana Yan bautar kasa iri iri suna koya Mana turanci karatu da rubutu shi yasa muka iya turanci duk da cewar ba kamar masu yin makarantar kudi ba,ko mutanen birni,iyayenmu suna son juna suna da hadin Kai Amma duk da Haka mu yaransu ba a fiye Zama lfy ba,sabo da munafunce munafunce irin na dangi musamman iyaye Mata su ke haddasa fitina iri iri.

Hajiyarmu Allah yayota Masifaffiya ce number 1 a kaf kauyen Nan an San da zamanta sabo da masifarta,har mu yaranta Bata raga Mana,ita Bata fiye tsokana ba Amma idan aka tabo ta ba mutunci,shima Babanmu Tahir Abbu balainsa yayi yawa Babu Wanda ya kyale Amma Kuma Yana da Dan saukin Kai,ga addini,Kuma Yana da nutsuwa kamar Hajiyarmu matsalarsu rashin Kara da kau da Kai komai masifa.

Kishiyar Babarmu wacce muke Kira da Anty ita Kuma tana da hakuri gata Shuru Shuru sai kisan mummuke,a boye take shuka tsiyarta ga tsokana,shi yasa kullum fadansu baya karewa dare da Rana Amma kowa mutan gari laifin Hajiyarmu ake gani Ana tunanin ita take zalintar Anty sabo da ita Bata kyalewa idan anyi mata.
Babanmu kuwa shima yafi ganin laifin Hajiyarmu,shi yasa ya tsaneta ya tsanemu mu yaranta,Yaran Anty da Anty yake kauna.

Matan su Kawu Salisu kuwa magulmata ne su ke haddasa rashin zaman lfy a dangi,Kuma Kakanninmu sunfi kaunar Matan Kawu Salisu da Usman sai Anty da yaransu,basa kaunar Babarmu ko kadan,muma yaranta abin ya shafemu basa kaunarmu,Hajiyarmu Har danginta ba wani sonta suke ba sabo da halinta na Saurin fada da masifa,Bata da kawaici iyayenta kadai ke Dan sonta,muma kakannimu na wajen uwa basa wani sonmu Wai bamu da kunya Yan iska ne mu sabo da kawai muna karatun boko mun Dan waye muna Yar kwalliya mun banbanta da mutanen kauyen shine kawai suka ce mu Yan iska ne Haka mutanen gari ma Ware mu akeyi,kawayena kullum zagina da gulmata sukeyi akan nace zanyi University bazan yi aure ba sai naci da biro, Hajiyarmu tana daura min tallan Dafaffiyar gyada Ina kaiwa makarantar boko da ta yamma,sannan Ina sai da goro da Sassafe kafin na tafi schl sai nayi tallan goro,Sabo da Abbu baya son Hajiyarmu Bai Hana a daura min tallan ba,Amma yaran Anty hanawa yayi a Dora musu talla.
Takaitattun matsalar mu kenan Nan gaba za kuji Wanda baku San dasu bama.

Allah yayi min baiwar hakuri ban gaji iyayena wajen masifa ba,sanyin Hali gareni,ga tsoro,sannan Ina da matukar addini,sannan kaf danginmu Babu me kyauna da kokarina,nafi kowa kyau da fata me kyau kamar jinin balarabiya wasu sun Dan fini haske da kadan duk da cewa Nima farace Amma hancina Bai cika tsini ba Kuma ba gajere ba,sannan Dan bakina karami jajir,gashina Baki sidik ga tsayi ko kitso baya yi,har gadon baya,idona farare tas Dara Dara,tun daga gaban goshina zaka ga gashina yalala ya kwanto, Ni ba rammiya ba ba Kuma me kiba ba,ga shape dirina abin kallo ne duk Wanda yayi tozali Dani sai ya kara, sabo da tsananin kyau na, idan baka sanni ba zaka rantse balarabiya ce ni, Amma duk kyan Nan nawa bani da saurayi bani da mashinshini sabo da halin Hajiyarmu Babu Wanda ke son hada zuria da Tata an Gama yadawa da sharri iri iri ake yi Mana kowa yazo wajena sau daya bazai dawo ba,a cikin dangi za a samu wasu munafukai suje su fada cewar Yar iska ce Ni har cikin shege na taba yi an zubar,sannan suce idan ya aureni zan mallakeshi,ga Masifar uwata,duk kawayena anyi musu aure tuni, sai Ni kadai Wanda a rashin miji ne yasa nake Karasa secondary Amma da ace na Samu miji ko jss1 bazan je ba za ayi min aure,yaran su Kawu Mata du Sunyi aure suna da Yara biyu Kuma mate Dina ne.

Dangi an Kara tsanata Wai ni nake korar samari sai talla da iskanci a garin Ina kwalliya Ina iyayi,Hajiyarmu ma da Abbu laifina suke gani shi yasa suke Kara Jin haushi na,dangi ko biki ko suna bana iya zuwa kullum daga schl sai gida sabo da irin ci min mutunci da akeyi Akan Wai naki aure Nasa yaudara a gaba,dangin uwata ma Haka ga mutan gari,Haka nake Addua Ina kuka kusan kullum Allah ya bani Mijin aure ko wanne irine aura zanyi na huta da bakin cikin da nake kunsa.

Yaya Salman ne kadai da Mahmood suke lallashina sannan suna matukar ji Dani,Mahmood ya taba furtawa zai aureni babarsa Matar Kawu Salisu tace zata tsine Masa shine yasa ma ya hakura Dani.
Takaitaccen tarihina kenan.

Ci gaban labari.

Rataye nake da Yar Jakar makaranta ta wacce Ya Salman ne ya siyo min a garin Kaduna lokacin da suka je service, Uniform dina fes dasu Allah yayoni da Tsafta sosai kullum fes nake ko Ina kungu da sako na jikina,ga Mahmood Yana yawan bani kyautar turaruka masu kamshin gaske
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download HADIN KAI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album