Join Our WhatsApp Group

Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

HAMSHAƘIYAR UWA Book 1 Complete Hausa Novel Document by HAMSHAƘIYAR UWA Book 1


HAMSHAƘIYAR UWA Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 28717



HAMSHAƘIYAR UWA Book 1

Reading Time: 2 Hours

Added On: 07, Jul 2024

Author: Halima K Mashi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08140004302

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 140.86 kb

File Type: txt

Views: 940+

Download: 714+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*


*NA*


*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*


_PAID BOOK_
_Kuɗin Karatu 600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_



_Godiya ta tabbata ga Allah maɗaukakin sarki mai kowa mai komai,tsira da amincin Allah su tabbata ga annabi Muhammad(S.A.W)._

_Kamar yadda na fara lafiya,Allah ka bani ikon gamawa lafiya,Allah ka bani ikon faɗakarwa gwargwadon iyawata,Ya Allah ka yafe min duk wani kuskure da hannuna zai rubuta,Allah ka bani ladar faɗakarwar._


*DOKA*
_Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_

*Free Page 1*

Kan shi a ƙasa bayan ya zube a gaban ta gwiwoyin sa suna ƙasa tamkar mai neman gafara. A hankali ya furta Hajiya Barka da dare.Ta ɗago kai daga kan TV da ke nanne a bango cikin wata ƙatuwar ma'ajiyar ta bango guda. Ta maida kanta gare shi ta na nazarin fuskar shi, sannan ta dubi yarinyar da ke zaune a ƙasa tana shafa mata man zafi a ƙwauri ta ce, "Azima ta shi ki je ki kwanta." Cikin sauri yarinyar ta miƙe ta re da faɗin sai da safe Hajiya. Allah ya tashe mu lafiya, Hajiya ta furta a hankali. Ta maido kallon ta ga gareshi sannan ta soma magana cikin isa "Shamaki zauna da kyau Allah ya yi maka albarka." Ya ce Ameen Hajiya. Ta ce "Bisa dukkan alamu ka ga wadda ta yi wa ranka, ko dai birgewa ko kuma ta baka shi'awa, faɗa min wani abu dangane da ita."

Ya sake gyara zama bai yi mamaki game da kalaman mahaifiyar ta sa ba,domin ita mace ce mai tsananin basira tare da karantar ɗan Adam, in har za ku yi zaman minti talatin da ita ba ko shakka zata iya zayyana maka abubuwa da dama daga cikin ɗabi'u ko halayyarka. Sannan babu abinda tafi saurin ganewa irin ka yi mata ƙarya. Ya ce Hajiya so ɗaya na ganta zata je Islamiyya na tsaya zan yi mata magana ta ja tsaki ta wuce, maimakon in fusata sai kawai na ci gaba da bin ta a baya bata sani ba har ta shiga makaranta.
Na san cewa kamar shidda sun ta so na koma sai ban ganta ba, yau na bi ta layin da na ganta cikin sa'a sai na hange ta a wani shago tana siyayya,na jira ta gama na bi bayan ta na ga gidansu yanzu ina neman iznin zuwa ne in Allah ya sa an bani izni.
Hajiya ta yi shiru kamar ba zata ce komai ba, zuwa can ta ce "Je ka kwanta amma kafin hakan ina son ka yi sallar istikhara da safe ka zo ka kuma bani wannan labarin da ka bani." Ya miƙe a hankali tare da faɗin na gode a tashi lafiya. "Allah ya maka albarka." Ta furta tare da ɗaukan goran ruwa a gefen ta ta buɗe da zumar sha.
Firgigit ya farka ya na kallon ɗayan sashen da take kwance, mafarkin yana dawowa a zuciyar sa, babu ko shakka sai ya yi wanka domin ya cimma hakan a mafarkin sa, bai taɓa samun hakan ba duk zaman gauran takar sa, kila gara lokacin da ya ke saurayi farkon balaga. Ya yi addu'a a sallar sa, domin bai samu zuwa Masallaci ba sakamakon makara,ba zai iya tuna lokacin da ya rasa jami'in sallar asbahi ba. Ya jima kwance jikin sa lankwas wanda yin hakan ba al adarsa ba ce. Sai ya ji kamar wani ɗan zazzaɓi ya na sarfatar sa. Cikin hakan ya ji ana kwankwaso ƙofarsa, ya tashi zaune sannan ya bada iznin a buɗe. Ta turo ƙofar ta na sanye da kayan makaranta, Azima ce. Ta ce"Yaya Shamaki Hajiya ta ce in duba ka." Ya ce ki sanar mata ina zuwa. Ya miƙe ya ɗauki jallaiya bulu mai gajeren hannu tasha aiki da sirfani mai ruwan zaiba ya saka.
Yana fitowa falonsa Meema ta na shigowa ta nufeshi da gudu tana faɗin "Dadi! Ya sa hannu ya ɗaga ta sama ya sata a jikin sa tare da faɗin Mamana Ina Mubina ina Anisa? Ta nuna mishi hanyar ɗakinsu tare da faɗin "Suna ciki Rahin tana shirya su." Ya lakaci kuma tun ta ke fa? Ta ce "Ni'ma yanzu za 'a shirya ni." Ya dire ta to maza kar ku yi latti ki tafi a shirya ki. Ta ruga da gudu. Shi kuma ya nufi sashen Hajiya.
Tana zaune a kan sallayar ta ƙafafun ta a miƙe sanɓal ta rufe kanta da hijabi na alfarma ƙamshin ta na tun fil"azal ya na tashi tana riƙe da carbi tana lazimi. Ya samu gefe ya zauna zama irin na girmama wanda ka ke gaban shi. Ya kalle ta cikin darajawa tare da faɗin Hajiya ina kwanan ku? Ta sauke numfashi cikin ƙasaita, sannan ta amsa da "Lafiya lau Shamaki, me ya same ka yau ba ka je sallar asbahi ba?" Ta yi tambayar cike da kulawa. Ya sunkuyar da kai, jikina yau na tashi babu daɗi sam, kuma sai na makara. "Me ya biyo bayan neman zaɓin da ka ba Allah ajiya! Ka ji wata damuwa game da yarinyar ko kuma Allah ya haska maka wani al'amuri a cikin baccin ka?"
Ta jeho masa tambayoyi. Shamaki ya ce eto har zuwa yanzu ina jin ƙaunar ta kuma na yi mafarkinta. Ya sunkuyar da kai domin ba zai iya bada labarin mafarkin ba. Hajiya ta ce "Ina sauraron ka." Ya sa hannu ya shafa fuskar sa sannan ya saci kallon ta ta tsira mashi ido,ba ko shakka so ta ke yi sai ta fahimci ko zai mata ƙarya. Ya ce cikin wani yanayi muka haɗu Hajiya Allah dai ya kyauta.
Ta yi ɗan murmushi da alamu ta fahimci ina ya dosa. Shike nan, ka sake bani labarin da ka bani jiya game da yarinyar. Ya gyara zama ya zayyana mata komai kamar jiyan. Ta numfasa tare da faɗin shike nan ka je ka fara bincike a kanta kafin ka je gurin ta. Sannan kar ka manta. da sharuɗɗa na akan duk wata mata da za ka aura. Bana son ka sake sakin mace daga guda ukun nan da ka yi, amma ka sa a ranka matan ka huɗu ne in Allah ya ƙaddara ina aɗdu"a. Kaje ka shirya yau kai zaka kai yaran ka makaranta domin tun jiya suka nemi alfarmar hakan.
Sannan in kaji zazzaɓin zai matsa sai ka sha magani, duk da nafi zargin zazzaɓin na soyayya ne. Ta kai ƙarahen maganar da 'yar dariya irin ta manya cikin ƙasaita.
Ya shafa kanshi tare da yin murmushi mai sauti,ba ko shakka zolayar sa Hajiya ke yi.
Ya ɗan rusuna. zan yi yadda ki ka ce insha Allahu Hajiya. Sanna ya miƙe ya nufi ciki. A mota tare da 'yan yaran sa mata su uku, Meema da ke zaune a gefen shi ta ce "Dadi za ka dawo ka ɗauke mu?" Ya dube ta sannan ya girgiza kai, Bazan dawo ba Mamana zan tafi kasuwa ne fa. "To zaka raka mu har ajin mu?" Ya kai hannu ya shafi kanta me zai hana zan raka ku in kuna so. Anisa ta sako hannuwan ta daga can baya ta shafo kumatun sa, Dadi muna so 'yan ajinmu suna cewa basu taɓa ganin Babana ba. Mubina ta ce Nima haka Dadi za ka raka mu kowa ajinta. Ya ce to shike nan sai mu fara kai Anisa ita ce Smaller ko sai mu kai Mubina, sai in kai Anty Babba ko Meema? Cikin jin daɗi ta ce e Dadi na.
Sun yi kamar yadda suka tsara da 'ya'yan na sa sannan ya ciro kuɗi ya raba wa malaman sannan ya tafi suna ta godiya sannan ya kama hanyar kasuwa.
Tun da ya zauna a ofishin sa da ke babban reshen manyan katunan sa wato Zeena Galary da ke ƙatuwar plazarsa mai suna Gidan Zeena a babbar kasuwar kwari da ke Kano. Dukan yaransa na katin sun fahimci ya na da 'yar damuwa, kasancewar ba haka ya saba zuwa ba. Shi kansa tunda ya ke bai taɓa samun kansa cikin wannan yanayin ba game da matansa da ya aura a baya. Ko matarsa ta fari bai ji irin abinda ya ke ji a wannan lokacin ba. Yana jin in bai fita ya nemo yarinyar nan...


Read / Download HAMSHAƘIYAR UWA Book 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album