Join Our WhatsApp Group

YAN ARABIC Complete Hausa Novel Document by YAN ARABIC


YAN ARABIC

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 127223



YAN ARABIC

Reading Time: 10 Hours

Added On: 05, Sep 2023

Author: Layuza Kabir Adam ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 720.76 kb

File Type: txt

Views: 764+

Download: 1067+

Last download: 1 hour ago

Description/Story: 🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 YAN ARABIC🌸
🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑
An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__

*DEDICATE*
_to_ _All_ _Arabic_ / _Islamic_ _students_
󨐽ρ† ½ρ† ½ρ† ½ρ† ½ρ† ½ρ† ½ρ† Š
Ina k'ara godiya ga Allah subhanahu wataa'la daya k'ara bani damar fara rubuta wannan littafi nawa na ya'n Arabic ina fatan dikkan Abinda yake dai-dai Allah ya bani ikon rubutawa aminπŸ‘.

πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š
Ina d'aliban Islamic / Arabic midium wannan littafi sadaukarwa ne gareku kuyi yanda kuke so dashi Allah yasa ku kasance cikin farin ciki aduk inda kuke a fad'in duniya.
πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š


ZAMANI WRITERS ASSOCIATION
(we are here to educate,motivite and entertain our reader's)
🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸



0⃣0⃣1⃣




Cin cirundan d'alibai ne nake hanga a can nesa dani wanda suka hau layi- layi amma yawansu baya bada damar a gane a layi suke,dik girma irin na filin dake bayan I.C .T na wannan makaranta d'aliban k'ok'arin cikeshi sukeyi, kasance war d'alibai ne mabanbanta courses wasu hira suke wasu kuwa gajiya tasa ko hiranma basayi gasu dai tsaye suna jiran layi yazo Kansu ko wanne hannunsa rik'e da credentials d'insa kana ganunsu dai kasan masu neman Admission ne.
Yawancin matan a zazzaune suke wasu a tsugunne .

Can gefan titi motar tai parking ya juyo ya kalleta da D'an mirmishi a kan fuskansa yace" To Nahnah Khadeejah ga skul d'inku kuma wad'an nan tarin jamaa'r da kike gani dikka masu neman Admission ne kamar ki don haka yanzu cikinsu zaki shiga saiki Tambayi ya'n Department d'inku kema kibi layi"

Dafe baki tai cike da tsoro tace "yanzu yaya dik wannan tarin muta nan kar b'ar Admission letter zasuyi to ta yaya zan samu karb'a ayau"?

Mir mishi ya k'ara yi yace" To ai dik ba course d'aya kuke ba kowa department d'insa daban don haka in kin je zaki ga kowa data windows d'in da zaki ga masu basu"

"Tom yaya saina dawo" ta bud'e murfin motar tana fita,
Kud'i ya d'auko 2k ya mik'o mata"ungo wannan ki rik'e a hannunki don neman wani kud'in ko in kin fara jin yunwa don zaku iya kai yamma"

Karb'a tai tana fad'in "Tom yaya na gode"

A hankali ta k'ara so wajan k'irjinta nata dukan uku uku don ita jama ar yawansu yana bata tsoro ,gefan dataga matan suna zaune ta k'arasa da sallama abakinta " Ψ§Ω„Ψ³Ω„Ψ§Ω… ΨΉΩ„ΩŠΩƒΩ…" wasu daga cikinsu sun amsa mata yayin da wasu suke bidirin gabansu wasu kuma binta sukai da kallo irin kallon nan da mata kewa y'ar uwarsu mace musamman idan tai babban wanka,😜

Gyaran murya tai cikin sanyin miryanta tace"Don Allah ina Tambaya ne"
"OK Allah yasa mun sani"
"Don Allah *YA'N* *ARABIC* nake nema"
"To gaskiya sai dai ki matsa can gaba kad'an kiyi Tambaya nan dik babu su"
Gaba ta k'ara kad'an ta k'ara Tambaya nan wata dake zaune agefe tace "gamu nan "
K'ara sawa tai kusa da ita ta zauna tare da mik'a mata hannu sukai musabaha tace" nima *YA'R* *ARABIC*ce zan amshi Admission letter ne"
Kallonta tai sosai tace"Ok kice y'ar uwace kinga duk way'an nan ma department d'inmu d'aya" ta fad'a tana nuna sauran y'an Matan dake gefe,dik mik'a musu hannu tai sukai musabaha"
Nan suka ci gaba da zama suna jiran a fara raba musu letter n.


Khadeeja Alk'adi yusuf haifaffiyar garin sakkoto ce y'a ta goma sha bakwai acikin gidansu kuma ita ce autarsu,
Mahaifinsu Alk'adi Yusuf tsohon Alkali ne a babbar kotun Shari ar musulunci ta garin sakkoto Dattijo ne me cikar kamala da addini yana da mata biyu da ya'ya' goma sha bakwai maza goma sha biyu mata biyar,
Babban D'ansa Namiji ne Yaya babba kenan sai na biyunma na miji ne yaya Sani sai ta uku mace Aunty sai ta hudun Aunty Amina ta biyar ma mace ce Aunty jamila bayan Aunty jamila saida aka haifi maza hud'u sannan aka k'ara haifar mace agidan wato juwairiyya daga nan aka k'ara maza shida sannan aka haifi auta Wato Nahnah khadeejah, y'ar gata ce sosai agidansu don dikkan yayyanta mata an musu aure mazanma duk sunyi aure mutum hud'u ne kawai basuyi ba wato yaya nura , yaya usman ,yaya kabir da yaya sadiq , duk suna karatu basu kammala ba gidansu Nahnah khadijah gida ne na y'an boko kuma suna da ilmin addini sosai mahaifinsu ya yabar aiki tun bayan haihuwar Nahnah khadeejah ba dad'ewa kasan cewar ya tsufa sosai yanzu yana zaune ne agida cikin kulawar y'ayansa da jikoki,
Zuri arsu suna da yawa sosai don mahaifinsu ma agidansu su ashirin ne don haka su d'un y'an dangi ne sosai in suna taro su kad'ai ma suna cika gida ko busuyi gayya ba.

Yaya Haroon d'a na tara agidansu mutum ne me barkwanci da yawan wasa yana da tsana nin son y'an uwansa me zimunci ne matuk'a bai iya siwa kansa abu ba tare daya saiwa wani daga cikin y'an uwansa ba, yana son Nahnah matuk'a dikkan hidimarta akansa yake ya dauke komai haka Nahnah kulum bakinta yana kiran Yaya haroon sun shak'u sun saba dikda kowa na gidan sonta yake kasancewarta k'arama kuma mace acikinsu, wata shahararriyar makaranta tahfeez/ Arabic primary and secondary skl dake garin sakkoto ita Yaya Haroon yasa Nahnah ai kuwa kafin ta kammala primary ta iya larabci sosai ta yi hadda da yawa ,bayan ta kammala primary ta zarce jenior acikin makarantar, a lokacin yaya Haroon ya sami canjin aiki k'ark'ashin federal a kano nan da nan ya had'a kayansa yai shirin tahowa kano kuka gun Nahnah kamar ranta zai fita shi kansa sai da yai kwallar rabuwa da Nahnah ya d'au hanyar kano.

Haka rayuwa taci gaba da tafiya koda yaushe in Yaya Haroon yazo Hutu in zai koma sai yayi fama da kukan Nahnah, yaya Haroon yai dacan zuwa kano don ya sami matar aure har sun dai daita Kansu iyayensa sunzo daga sakkoto ansa ranar aure anyi komai.



Taku ce
Layuza kabir AdamπŸ™‹β€β™€
🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸YA'N ARABIC🌸
🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑🍑


NA
LAYUZA KABIR ADAM


DEDICATED
TO ALL ARABIC/ISLAMIC STUDENTS
πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š


*πŸ’»ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

πŸ“ .
​​WΙ› Ι‘Κ€Ι› Ι¦Ι›Κ€Ι› tΡ³ Ι›Ι—ucΙ‘tΙ›, MΡ³tiΡ΅Ι‘tΙ› Ι‘Ι³Ι— Ι›Ι³tΙ›Κ€tΙ‘iΙ³ Ρ³uΚ€ ʀɛɑɗɛʀร​​

β€‹πŸ“š ​​Zaku iya samun littafan mu a Facebook​​ πŸ‘‡πŸ½
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

πŸ“© ​​Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu​​ πŸ‘‡πŸ½
Zamaniwriterassociation@gmail.com


0⃣0⃣2⃣




Tunda NahNah taji yaya Haroon zaiyi aure ta shiga murna tana fad'in"shike nan zan koma kano gidan Yaya tunda aure zaiyi" kowa ta fad'awa sai dai yayi dariya don sun San Baffa da son y'ay'a bazai iya bada Khadeejahnsa ba yanda kullum zansan sa na kanta kullum nasihar sa ga y'ay'ansa su rik'e mai Nahnah koda bayan ransa kada su bari tai kukan rashin uba,

Bayan wata hud'u akai bikin Haroon ya
Tare da amaryarsa a garin Kano cikin unguwar hotoro agidansa daya siya k'aton gaske,

Bayan bikinsu da wata guda ya kawo amaryarsa sakkoto donta gaisa da danginsa suga juna,
Murna wajan Nahnah ba'a magana taga yaya da matarsa aikuwa Hafsa ma tanata murna yau taga Nahnah kullum bakin Haroon naga Nahnah, kwanansu Biyar sukai shirin tafiya ai kuwa Nahnah tace ina ai k'afarta k'afar yayanta tun suna zaton abin wasa ne har abin ya fara basu mamaki,k'am ta rik'eshi tana kuka harda shishshik'a yaya Usman uban y'an masifa ya fuzgota yana fad'in " Dalla malama rufe mana baki hauka mukeyi za a barki ki tafi kano"

K'ara take cikin tsananin kuka tace" wayyo Allah na yaya Haroon don Allah karka tafi ka barni inka barni mutuwa zanyi wayyo yaya nah"

Baffa ne ya dogaro sandarsa ya fito daga sashinsha yana fad'in "wai auta wane irin kuka ne kikeyi haka sai kace wanda aka cirewa ido ko kukan Harunanne"?
Yana k'arasa fitowa yaga yanda Nahnah ke turje turje tana ihu, rik'o hannunta yai cikin sigar rarrashi yace"yi shiru auta ta kinji rabu dasu anayin Hutu zansa Bashir ya kaiki"
"Ni banso Banson makarantar ni yaya nah zanbi kano"
Jim Baffa yai ya kalli Haroon yaga yanda shima duk idonsa yai jawur harga Allah badan yasan Baffa bazai tab'a iya bashi Nahnah ba daya rok'i alfarmar tafiya da ita,
Muryar Baffa ce ta katse mai tunaninsa"Haruna zo ina son magana dakai kaida matarka"
Ciki suka koma bangaran Baffan yayin da yaya usman ya ciccib'i Nahnah zuwa cikin d'aki ya rufeta tanata dukan k'ofar tana ihu,
Bayan sun zauna Baffa yai gyaran murya ya fara magana"Haruna ka sani ni bana bada aran d'ana bare inyi kyautarsa tun tuni y'an uwanka maza da mata na nesa da kusa sukemin nacin d'aukar khadeejah amma bantab'a amsawa wani ba akan idonka ko kwana uku Khadeejah bata tab'ayi gidan wani ba cikinku amma yau na d'auki amanar Khadeejah na dank'a muku kaida matarka koda bayan raina Khadeejah ta kuce Ku rik'emin ita amana Ku zama iyayenta Ku share hawayenta kunji"
Tsananin farin ciki ne yasa Haroon kasa magana illa zuwa da yai ya rik'e k'afafun Mahaifinnasa yana d'ora kansa a cinyoyinsa,
Hafsa cikin jin kunya tace"Mun gode Baffa Allah ya bamu ikon rik'e amanar daka bamu"
"Ameen Hafsa Allah yai muku albarka" nan ya taro dikkan jama'ar gidan ya shaida musu kyautar da yaiwa yaya Haroon aikuwa kowa ya cika da mamaki yanda akasan k'aunar dake tsakaninsa da Nahnah, nan dai kowa yai musu fatan alkairi, Nahnah ko daketa kuka a d'aki harta gaji tai bacci bata San meke faruwa ba,dole Yaya Haroon ya d'aga tafiyansu sai nan da kwana biyu.

Makarantar su Yaje ya nema mata transfer don lokacin j.s.s two take,
Bayan ta farka a bacci ake shaida mata Tare zasu tafi da Yaya Haroon Baffa ya bar mai ita ai kuwa kamar tayi me don murna, nan da nan ta shiga shirya kayanta.

Kwana d'aya Transfer d'in ta fito don haka washe gari suka d'au hanyar kano, shike nan Nahnah khadeejah ta zama ya'r kano,

Tunda suka dawo yaya Haroon ya shiga nema mata makarantar da zata ci gaba wadda tai dai-dai da irin karatunta, Tambaya yake akan wace makaranta ce ta Arabic wadda take da karatu da tsari nan wani ya bashi shawara akan ya kaita "TAHIR GIRL'S ISLAMIC/ARABIC SENIOR SECONDARY SCHOOL GYAD'I-GYAD'I KANO"

Ai kuwa nan da nan ya nema mata gurbin karatu a Tahir kasancewar lokacin za'a fara jarabawar shiga babbar secondary wato senior nan yai mata registration itama ta zana.

Zaman Nahnah a
gidan Yaya Haroon ba k'aramin dad'i yake w Hafsa ba don Nahnah yarinyar kirki ce ga son aiki bata da ganda ko kad'an,kullum tana waya da y'an gidansu a wayan yayanta don haka bata da kewansu.

Ahaka Nahnah Khadeejah ta gama secondary skul d'inta cike da tarin nasarori kasancewarta yarinya zak'akura ita ta rik'e head students har tai Candy duk wani quiz da za'a fita a skul d'in ita ke jagoranta.

Satin Nahnah biyu da candy akayo musu waya jikin Baffansu yai tsanani an bashi gado a asibiti ba shiri suka d'au hanyan sokoto,
Tunda suka sauka garin suka ga yanayin jikin nasa hankalinsu ya tashi matuk'a don baima San Wanda ke kansa ba ko kad'an, kwanansu biyu agarin Allah ya karb'i ran Baffah Sunyi kuka matuk'a na rashin gwarzon uba musammam Nahnah da take jin tafi dikkan y'an uwan nata k'aunarsa, to koma dai yaya ne ya tafi ya barsu sai fatan dacewa.

Saida sukai sati biyu a sokoto suka dawo bayan an raba musu gadonsu kamar yanda yabar wasiyya kar suja lokaci wajan raba...


Read / Download YAN ARABIC

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album