Join Our WhatsApp Group

Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

TARAR ARADU Book 3 Complete Hausa Novel Document by TARAR ARADU Book 3


TARAR ARADU Book 3

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 14068



TARAR ARADU Book 3

Reading Time: 1 Hours

Added On: 04, Jul 2024

Author: Umar Lawan ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Action Novels

File Size: 74.52 kb

File Type: txt

Views: 346+

Download: 123+

Last download: 1 day ago

Description/Story: TARAR ARADU
Littafi na Uku 3
Umar lawan Abdul
Typing Shuraih Usman
Page 1
.
.
Na kara kiran sunanta tun iya karfi "farida" Amma shiru farida batako motsaba
.
Na rikice na kuma dimauce hankalina ya nemi gushewa tuni alamomin tambaya suka runtumo kaina shin me haka yake nufi? Farida suma tayi ko mutuwa? In har mutuwa tayi baga abunda zai hana na bita ba, na mike tsaye tsayuwar taki yiwuwa, sai na sake komawa na tsugunna
Bakina na kara a kunnenta na kara kiran sunan da karfi , shiru haryanzu bata canja zani ba, sai na fashe da kuka kukan da bazai taba zama magani ba, ban san adadin mintunan da na karar ba a wannan hali nidai na kiyasta awa ko fiye
.
Ana haka na jiyo takun kafafu ban iya tashi domin dubo ko wayeba bada jimawa ba sai gata a ciki, Mummy ta dawo tayi sallama bata yi ba nidai ban sani ba , ta dubeni a rikice "umar me ya faru?"
.
Rudun dana shiga gami da rikici mai kama dana tsufa suka sanya ne furta a zancen da ba shi ya kamata ba, dubanta nayi kai tsaye "ta mutu"
.
Ta dora hannu aka "ta mutu"
Eh! Nace mata ba a'a ba
Akwai tashin hankali ganin yanda matar ta fashe da kuka gaba daya "inna lillahi wa inna ilaihi raji'un, shikenan farin ciki yayi nisa dani 'yata daya jal dana kwallafa raina akanta ta tafi, Ya lillah"
Itama sai ta zube anan muka ci gaba da kukan tare , cikin rashin samun wanda zaiyi karfin halin lallashin wani, kimanin minti goma muna wannan hali, a sannan ne wani sauti ya fito kamar minshari, farida ce taja dogon numfashi, mummy ce tafara mikewa "umar suma tayi ba mutuwa ba"
.
Na tashi nima gami da matsowa kusa da ita numfashinta ya fara fita ahankali
Na dubi mommy "yaya za a yi?"
"Asibiti zamu tafi , titi da nisa kafin a dauko mota an bata lokaci gashi tana bukatar agajin gaggawa, da ina da cikakkiyar lafiya dana goyata"
"Ni zan goyata mummy sai mu tafi"
.
Ina maganar ne cikin halin zubar da hawaye.
Ta girgiza kai "farida tayi maka nauyi"
"Babu komai, lokaci yana kara kurewa"
Ta kimtsa ta sosai sannan ta taimakamin na goyata, muka fito daga gidan a gaggauce ga duk wanda ya ganmu dole ne ya tausaya mana.
Mu dai gamu muna tafiya cikin halin rudu, da sauri, ga kuma mara lafiya goye a bayana, Bakunan jama'a suka juri fadin Allah yabada sauki
.
Tafiyace mai nisa Amma banji alamun gajiya ba a haka har muka riski asibiti, muka sami motar da muka sakata
****
Na cigaba da kai kawo a dogon zauren asibitin zuciyata fal damuwa, sakamkon rashin sanin halin da farida zata wanye, daga lokaci zuwa lokaci nakan dubi mummy wacce ke zaune cikin tagumi, tun data zauna hawaye bai daina zarya ba a fuskarta,
Tsawon lokaci likitocin suna kanta, bayan abun daya tunkari awa biyu wata Nurse ta fito na ga sanda ta kira mummy take shaida mata wani abu
Na nufi wajen bayan da suka kammala
.
"Yaya akayi"
Ta share kwalla da gefen mayafi "cewa sukayi tana kan hadari, zai yi wuya ta iya numfashi da kanta yanzu, sai dai da taimakon na'ura"
Kaina ya sara da karfi hakika wannan wata hanyace ta nisa da rayuwa da yawa sun zarce a irin haka nan, me yiwuwa farida ma haka ce zata faru, kuma duk ni naja, da ban bata labari ba dayanzu tana nan kalu, kaito na!"
.
Mummy ta cigaba "umar inaga kakoma gida , awa ashirin da hudu suka ce zatayi"
Nayi karfin halin kai idona ga kallonta "to mummy izan na tafi wa zai rinka taimakawa"
Ta zurawa kasa ido kuri "ida wata ya wannan yanzu ma badon kai ba jigata zata yi sosai, umar biyanka sai dai mahalicci"
Na daga mata hannu " kar ki damu, na cancanci yin komai don farida na matukar lallabani"
.
Aka sami shiru na dan lokaci a cikin sane ma na sami damar yin tunani, sai yanzu alkawarin dana daukarwa mahaifina na komawa ayau ya fado raina, hakika babu makawa na cikashi, to amma ya kamata na tsallake na bar farida a wannan hali? Alhali idan nayi nazari zan ga cewa dukda ran da bani da lafiya bata nisa dani,
Na tuno yanda da kanta taje bakin bariki ta daukeni zuwa asibiti (karken littafi na daya 1,) na tuna yadda take kwana ta kuma yini a wajena ,batare da tunani ko tsoron afkuwar wani abu ba, kudadenta da lokutanta duk ta kashe a kaina, saini yanzu bata da lafiya sai na tsallake na barta da mahaifyarta saboda itace dolenta? Kai dasake akwai butulci zalla a cikin aikata hakanan, sai kawai na fashe da kuka,
.
Mummy ta dafa kafadata "umar sai hakuri na sani kana kaunar farida sosai mai yiwuwa ma fiye da ni, sai sauki idan Allah yayi hukuncinsa ya za'ayi?"
Na share hawaye "mummy bari wannan zance farida ba mutuwa zatayi ba, tana da sauran kwanaki"
Ta kwantar da kai "to Allah yasa hakanan dan idan farida ta mutu ban san inda zan saka kaina ba, na sani ko wace uwa tana kaunar danta, amma ni nasan kaunata da farida na musammance ba kowacce uwa zatayi ma danta kaunar da na ke yiwa farida ba, saboda ita naki aure shekaru sha shida kenan, domin ni bazan barta a wani waje ba, kuma ni bazan je da ita agolanci ba, karta rasa walwala da jindadi,
Me yiwuwa wata rana agoranta mata wanda da haka ya faru duk kimar mijin na rabu da shi"
.
Tausayin mummy ya kamani ni sai yanzu na san dalilinta na kin yin aure na dade ina ta yan kame-kame , kyakkyawar mace kamar ta da bata haura shekara talatin da biyar ba ace bata da aure shakka babu abin a duba ne
.
Na kara yin kasake ina tunanin wacce za a yi, hakika abubuwan da gazawata zata fito fil yawa ne da su, bazan auna a wajen farida ba kuma bazan dauki nauyinta kamar yadda take daukar nauyina ba, abun danake magani naira dubu shida suma daga kudin data yimin kyauta ne a baya, na fara kashe su a asibiti sai taci gaba da daukar dawainiyata,
Wani abun kuma ita kanta dubu shidan tana dakina anan na boye don gudun kada ta hadu da tsautsayi, in har ta halaka banga inda zan samu sisin kwabo ba
.
Na dubi agogon hannuna karfe biyar da minti hudu, hakika ya kamata nasan wacce za'ayi idan zaman zaman idan kuma komawa kauyen komawar
Na yanke shawarar tuntubar mommy sai na dubeta sa'ar data ke cikin tagumi
"Mummy ina mai bada hakuri nayi bakin ci da zan matsa daga nan sai dai babu yanda zanyi mahaifina nayiwa alkawari cewa lallai zanje yau kuma ga abinda ya faru"
.
Ta cira kai "kar ka damu kaje wajen mahaifinka umar yanzu ma abun da kayi ya isa Allah ya rabaka lafiya da su"
Na amsa "amin" sannan na ci gaba
"Mummy idan farida ta tashi ki shaida mata cea ta kwanatar da hankalinta ba zamu rasa juna ba, na tafi fafutukar sama mana mafita gobe-gobe zan dawo"
Ta kalleni cikin bkuatar karin haske" menene ya ke faruwa?"
Na sunkuyar da kai "babu komai"
"A'a Umar kar ka boye min , ka dauka cewa agare ka ina matsayin uwa"
Hawaye ya biyo kumatuna nasa hannu na share sannan na fara da cewa wani rikici ne ya bullo tsakani na da iyayena an kai masu labarin na zama dan iska shine suke so na koma can da zama kuma an nema min aure, wai jibi ma za'a daura shi, labarin naba farida ta shiga wannan hali
.....
Kai MALAM UMAR
Haryanzu fa akwai.......
.
Nidinne dai Shuraih Usman
Inkiya 99%
.
Yi maza ku like na page namu www.facebook.com/hausaebooksTARAR ARADU
Littafi na Uku 3
Umar lawan Abdul
Typing Shuraih Usman
Page 2
.
.
Tayi shiru tsawon lokaci , daga bisani tayi karfin hali "umar zama bai same ni ba, dole ne muje dakai na roki arziki,in har aka daura maka aure,to farida kuwa shikenan"
Na girgiza kai "mummy ba zakije ba , zuwanki ba zai fa'idantar ba, nasan iyayena in sukace baki ba zasu canja da fari ba, ki bari ni zan samo mafita"
"A wadannan 'yan awoyi Umar?"
"Asu din kuwa , ina jin radadin raba ni da farida bazan jure ba zanyi duk abinda zan iya don ganin bata faru ba"
"To don Allah ka taimaka ga Allah nake dogara amma na san farin cikin 'yata na tattare da kai"
Na mike "kar ki damu zanyi fafutaka iya yina har komai ya faru yanda ake nema"
Itama ta mike muka kama hanyar fita daga asibitin a haka har gamu a titi, ta dafa kafadata "Umar haka ceci rai , ka tallafawa rayuwar marainiya"
Na gyada kai "Mummy zan yi"
***
Nayi shiru a shagona, cikin tunanin hanyar da zanbi na tarwatsa maganar aurena, shakka babu jan aiki ne wanda fasa goron dutse da cokalin roba zai fishi sauki, na sani a irin dattaku na mahaifanmu maganar fatar baki bata isa ta rusa auren ba, babu wata kalma da...


Read / Download TARAR ARADU Book 3

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album