Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[8/6, 5:59 PM] mrs bilkisu: ________________________________
BAN SAKETA BA!!!
________________________________
NA
BILKEESA IBRAHEEM
{Bilyn Abdul}
________________________________
https://mrsbilkisa.blogspot.com






ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN.
ya ALLAH kabani ikon faďin abinda zai amfani al'ummarka ka tsare harshrna daga faďar abinda zai cutar da al'ummarka.AMeen.
😂ina farincikin sake haďuwa daku a sabon littafina, mai suna BAN SAKETA BA😂👌🏻.

Duk wanda ya canja mini wani abu aciki ban yafe masaba😎.


Ina mi'ko ďunbin godiya da gaisuwa tareda fatan alkairi ga dukkan masoyana, ina godiya da ďubin gaisuwarku gareni, dason fara rubutun BAN SAKETABA,, da nabari sai bayan biki amma 'kaguwarku tasa bazan iya share bu'katunkuba,, dan haka zan fara, saidai zakumin uzuri dan zan gaza baku posting akowace rana, sakamakon nayi busy dayawa, ALLAH yasa mudace,, muje zuwa LABARI😁👌🏻.

Sadaukarwa~ ya Abdul {city phone's}



Page......1⃣

.......Yauma kamar kullum tana 'kasan dalbejiyar data zame mata tamkar ďakinta aduk lokacin da bata da lecture's.
Kallo ďaya zaka mata kagane tana cikin duniyar tunani, da sauri taďago kai tana dube2, taja numfashi mai 'karfi, cikin sanyin murya ta ce, "hancina kadaina faďa min 'karya, ka daina sha'ko min abinda ba gsky ba, tunda nake awajen mutum ďaya nata6a jin wannan 'kamshin, kuma tunda yanisan ceni ban sake jiba, ban bashi damar dazan sake jiďinba, domin shi ya kasance mugu azzalumi, macuci!!!....ta faďa tana mai zubar da hawaye.
Wlhy na tsaneka Isma'il!!! mayaudari kawai ta fashe da kuka mai ban tausayi.
Haba iman kina ganin haka rayuwa zata kasance kullum cikin kuka da tunani??, maganar miss xoxo takatsema iman surutan datakeyi, iman mu masoyankine masu 'kaunarki 'kauna irinta 'yan uwan juna, tundaga randa muka fara ganinki a school ďin nan mukaji muna 'kaunarki, dan ALLAH badan muba ki sanar mana damuwarki kozaki samu sau'ki, idan kuma munada taimakon dazamu yimiki saimu taimaka miki koda da addu'ane.
Gsky ne Miss xoxo yakamata iman tasanar mana damuwarta inhar ta yarda damu kamar yanda muka yarda da'ita, yau kusan shekararmu biyu da watanni tare bamu ta6a 6oye miki sirrinmuba, duk abinda yadamemu muna sanar da junanmu, ke kaďaice acikinmu kike 6oye mana sirrinki, bamusan dalilin hakanba kokuwa bamu cancanci sanin taki damuwar bane oho??, amma kinsan damuwarki itace tamu, farincikinki shine namu, wlhy inaji ajikina tamkar uwa ďaya uba ďaya suka haifemu.
Gskyarki ne Reefat xoxo tafaďa tana gyara zama, takamo hannun iman ta rumtse anata, iman inhar kin ďaukemu a matsayin 'yan uwa ko 'kawaye na kwarai to ki sanar damu damuwarki, koda addu'ane mutayaki, mungaji da ganinki haka iman, shekara biyu ba kwana biyu bace, inkuma bazaki faďa manaba bazamu takurakiba, saidai zamu taimaka miki da addu'a insha ALLAHU.
tami'ke Reefat tashi mutafi xoxo tafaďa tana kama hannun Reefat.
Iman ta fashe da kuka dan ALLAH xoxo karku tafi, kuyi ha'kuri ku saurareni.
Ya za'ayimu saurareki iman kullum haka kike faďa mana amma kin kasa faďa mana komai, kina ganin zamu cigaba da takuraki harsai kin sanar damune??, dammi zamu takura miki akan abinda bakida ra'ayin faďa mana???.
Naji na amsa laifina amma dan ALLAH kudawo karkuyi fushi dani, wlhy nima ina 'kaunarku inajinku tamkar 'yan uwana najini.
ALLAH sarki xoxo akwai tausayi dan haka saita jawo hannun Reefat suka dawo suka zauna, tsakiya suka saka iman, Reefat ta ce, "iman muna jiranki dan ALLAH ki sanar damu damuwarki kinji, 'kila mu iya taimaka miki da wani abu.
Iman tasa hannu ta share hawayenta tareda ďanjan hancinta, tabi aminan nata da kallo, miss xoxo Reefat kuyi ha'kuri ban ta6a 6oye muku wani abu daya danganci rayuwata saboda rashin yarda daku ba, a'a ina ganin abinda yafaru dani tamkar sirrinane tunda yafaru dani a shekarun bayane kafin na haďu daku, sannan ina ganin abinda yafaru dani yariga ya faru ya wuce, amma ina neman afuwarku gareni, insha ALLAHU a wanan karon zan faďa muku wacece SAUDAT!?" saidai kuyi ha'kurin zuwa weekend sanan muna free saimuyi maganar atsanake.
Zan faďa muku tushen rugujewar rayuwata da tushen tubalin ginin damuwata......ta fashe da kuka mai tsuma zuciya da ruhi, ganin haka Reefat da xoxo suka shiga tayata suma, saida sukayi kuka mai isarsu babu mai lallashin wani, saida suka gaji dan kansu sanan sukayi shiru.
Mi'kewa sukayi suka nufi class kowa zuciyarsa babu daďi, iman sai waige2 takeyi danjin tamkar 'kamshin turaren yana bibiyarsu, Xoxo ta ce, "iman wai mikike nemane??, lokaci da dama nakan ganki kina waige2 miyasa??.
Murmushi Iman tayi na takaici, wanan duk yana cinkin tarihin rayuwata xoxo karki damu asannu zaki gano abinda yakesani waige2 a wasu lokuta da dama.
Daga nan suka shiga aji, babu daďewama malami yashigo suka fara ďaukar darasi...............✍🏻



Tofa masu karati komi wanan littafi ya kusa??, shin miye damuwar kawarsu Miss xoxo ne??, dani daku duk akan tambaya ďaya muke, domin nima bansan komai gameda hakaba, sai munbi wanan labari sannu ahankali sannan zamu samu amsar tambayoyin dake fal a zuciyarmu.

Takuce dai Bilyn Abdul.
Saikunjinei!!!!!!👌🏻
















Luv u oll my fan's
©2017
Battery low🔋😜👌🏻
[8/6, 5:59 PM] mrs bilkisu: ________________________________
BAN SAKETA BA
________________________________
NA
BILKEESA IBRAHEEM
{Bilyn Abdul}
________________________________
https://mrsbilkisa.blogspot.com





Sadaukarwa~ ya Abdul {city phone's}



MIYAKAMATA NAYI???.
amatsayina na uwa miya kamata nayi??, alokacin dana fara mallakar 'ya'yana 'kyautar ALLAH, 'kyakykyawan lafazi, yawan addu'a, nasiha alokacin dasukayi ba dai2ba, cusamusu tsoron ALLAH azuciyarsu tun suna 'kanana, domin icce tun yana ďanye ake lam'kwasashi,
ALLAH yasa mu gyara.



Page~2⃣

...........miss xoxo & Reefat matasan 'yammata 'kyawawa, ga nutsuwa da ilimi, tundaga randa aka kawo iman school ďinsu suka haďu suka 'kulla abota mai 'karfi da zuminci, suna 'kaunar junansu, wanda bai saniba idan yagansu saiya ďauka 'yan uwan junane dama can, amma abin ba haka bane..
Miss Xoxo 'yar Kano ce karatune yakawota garin na ZARIA...Reefat kuma 'yar Yola ce ADAMAWA itama sanadin karatu tazo garin na ZARIA, itakam iman 'yar katsinace & kano .
Bayan sun kammala luctures ďinsu suka nufi ďaki agajiye, Reefat tazube a tsakar ďaki tana faďin wash ALLAH na, nagaji wlhy, malamin nana yayi mugun wahalar damu gsky.
Miss xoxo ta ce, kibar ďan iska Reefat saikace daga kansa aka fara ilimin boko, ALLAH na tsanesa tamkar mutuwata, shege gashi mummuna sai girman kan tsiya kamar ďan wani da wata.
Kudai ALLAH ya shiryeku iman tafaďa tana fitowa daga bayi, kuzauna kuyita zagin malamanku saikace wasu 'kawayenku.
Reefat ta harareta ai dama ke bazaki ganewaba, wannan ďan iskan malamin bashida kirki, kidubafa yanda yadaka miki tsawa ďazu ALLAH yabani haushi.
To kuyi ha'kuri malamin mune, kunga yanada ikon nuna mini kuskurena kenan..
Xoxo ta ta6e baki kinga Reefat barta indai iman ce babu abinda zaki faďa akan malamai ta amince.
Iman ta ce, "kudai kuka sani nikutaso muci abinci ALLAH yunwa nakeji.

Yau juma'a 'yammatan suna free basuda lectures ko ďaya, suna gida, dawuri suka gama komai na al'adar rayuwarsu dan sonjin labari, suduka suna cikin ďakinsu sun saka tiren indomi a tsakkiya kowa da kofin shayi agabanta.
Iman ta mi'ke domin ďakko wayarta dake ajikin caji, kamar jira ake ta kunna kira yashigo, tayi murmushi sanan ta ďaga, hello my bro's ya gida??.
Daga can 6angaren aka amsa mata, ta ce, "yasu gwaggo??,
Kowa 'kalao aunty, ya karatunki??.
Muna nan muna bugawa.
To ALLAH ya taimaka.
Amin autan gwaggo.
Dama Musayyeef ne ya ce, "nakira ki ku gaisa, okey yana ina??, gashi.
Hello aunty Maa! kina lafiya??, lafiya lau musayyeef ykk ya makaranta??.
Aunty maa! lafiya lau.
To kana dai 'kokari ko??, eh mana, harma anty tace nafi kowa 'kokari a class ďinmu.
Da 'kyau ďan albarka, to mikake bu'kata??, babu komai aunty maa! dama inaso na sanar miki jiya da dare uncle ďi na yazo.
To naji sai anjima na kiraka muyi hira yanzu ina karatu.
To aunty maa! sai anjima....yaron ya faďa cikin tsallen murna.
Bayan ta kashe wayar tadawo ta zauna saidai fuskarta babu walwala.
Xoxo ta ce, "lafiya naga kin canja fuska dawa kikayi waya??, tayi murmushin ya'ke lafiya lau mikika gani??, da Musayyeef nayi waya fa.
Reefat ta ce, "miyasa baki bani shiba mun gaisa, autan gwaggo sarkin wayo, inason yaronnan wlhy kamar gwaggo tabani, iman tayi dariya mizai hana tabaki indai kinaso??.
Xoxo ta ce, "aii koni ina 'kaunar yaronnan, duk yafi 'yan gidanku 'kyau, kamar ba ďan gidanba.
Iman tayi dariya hakadai kukace, amma yama za'ayi yafimu 'kyau, aii banma yardaba, hakadai sukaita hirar Musayyeef har suka gama cin abincinsu.
Bayan sun gaba duk suka nutsu suna sauraren iman, iman ta gyara zama sanan taja ajiyar zuciya mai 'karfi.

SAUDAT SULAIMAN UMAR, shine cikakken sunana kamar yanda kuka sani, amma ana kirana da iman kasan cewar naci sunan kakata ta wajen uba, mu uku iyayenmu suka haifa, Aunty Salma itace babba saini saikuma auta Shamsuddeen muna kiransa da deeni.
Asalinmu mu 'yan jihar katsina ne a 'karamar hukumar musawa, aikine ya kawo Abbah kano.
Aunty salma ta girmeni sosai gsky dan tsakanin mu akwai mutum biyu amma sun rasu, ni 'yar gatace agidanmu saboda kasancewar naci sunan kakata dan haka Abbah yake jidani sosai, to itama gwaggo haka, inada muskilanci dan bakowa nake kulawaba shiyyasa natashi banida 'kawaye, lokacin dana gama primary ne muka dawo kano, ita kuma aunty Salam ta kammala secondary ďinta.
A nana kano taci gaba da karatunta a FCE kano, nikuma secondary, deeni kuma yacigaba da primary kasancewar mahaifinmu ďan bokone, balaifi munada hali iya gwargwado dankuwa ba'a kiramu talakawa ti6isba, komai muka bu'kata mahaifanmu suna mana iya bakin gwargwado.
Ina js 2 akayi bikin aunty salma da ya Abdu'majeed wani ďan uwanmune dake can katsina, shekarar su biyu a Kt aka dawo da ya majeed kano a wajen aiki, zuwa sannan sun haifi ďansu Bello suna kiransa Affan saboda sunan baban ya majeed ne.
Agidanmu suka fara sauka, bayan kwana biyu suka shirya komawa gidansu sanan an kammala gyarawa.
Ya Majeed ya bu'kaci su tafi dani nayi musu kwana biyu tunda muna cikin hutu, da Abbah ya'ki amma dasuka dage saiya yarda akan sharaďin danayi sati ďaya zan dawo gida, ba musu suka amince..
Ranar adaren muka tafi, gidan ya haďu dan ya Majeed ya gyarashi da 'kyau.
Kwananmu uku da zuwa gidan ya majeed natashi da matsanancin ciwon ciki, haka na rin'ka kuka ina kiran gwaggo da Abbah, dan tunda nake ban ta6a ciwo mai kama da wannanba.
Aunty Salma tashiga ruďu gashi ya majeed baya nan yafita aiki, tayi 'kokarin kiransa a waya ta shaida masa halin danake ciki, ya ce, "gashi nan zuwa dama baiyi nisaba.
Cikin minti 15 ya Majeed ya iso, bai jira komaiba ya ďaukeni muka nufi mota, aunty Salma ta biyomu abaya, a bayan motar yasakani aunty Salma tashiga ta ri'keni ya amajeed yaja motar muka tafi asibiti.
Waya yaďauka yakira wani abokinsa dake aiki a asibitin kansa, muna zuwa akayi mana tarbar gaggawa, aka kuma bamu taimako na musamman.

Sai wajen 'karfe uku na yamma na farka, aunty Salma ce zaune akusadani sai kuma ya majeed zaune akujerar dake gefen gadon.
Ahankali na buďe ido ina kallon silin, aunty Salma ta ce, "iman kin farka?, kai na ďaga mata alamar eh, ya majeed ya ce, "sannu iman ya jikin naki?, na ce, "da sau'ki yaya, ya kuma faďin yanzu ina yake miki ciwo?, ahankali na ce, "yaya babu ko ina saidai inajina akan laima.
Aunty salma ta ce, "laima kuma?.
Na ce, "eh.
Aunty salma tasaka hannu a 'kasana saiga jini, ta ce, "jini kuma iman? miya sameki haka?, da sauri ya majeed ya ce, "jini kuma?, aunty salma ta ce, "wlhy kuwa yaya jini, ya mi'ke kinga bari nakira Isma'il yagani.
Babu daďewa yaya yadawo tareda Dr Isma'il, yaďanyi dube2nsa sanan ya kalli ya majeed abokina karku damu, bawata damuwa bace yanzu ta tashi ta gyara jikinta bari na turo Nurse ta taimaka mata.
Kai kuma mije na ganka a office.
Suna fita saiga Nurse tashigo, itada aunty salam suka taimaka min na gyara jikina, Nurse ďin ta gyara gadon kamar komai bai faruba, nadawo na sake kwanciya dan jikina babu kwari ................✍🏻








Luv u oll my fun's
©2017
Battery low🔋😜👌🏻.
[8/6, 5:59 PM] mrs bilkisu: ____________________________
BAN SAKETA BA
_______________________________
NA
BILKEESA IBRAHEEM
{Bilyn Abdul}
________________________________
https://mrsbilkisa.blogspot.com




Sadaukarwa ga~ ya Abdul (City phone's)




MIYAKAMATA NAYI???.
Kasancewata uwa yakamata nayi 'kyakykyawan lafazi ga ďan daba nawaba alokacin danaga yayi ba dai2ba, karna la'anci ďan wani kona kirashi lalatacce, shiriyar ALLAH yakamata na ro'ka masa, domin ďa na kowane, bansan mi gaba zata haifarba akan nawa 'ya'yan.
ALLAH yasa mu gane.



Page...3⃣

Ya majeed kam yana office ďin Dr Isma'il, bayan sun zauna Dr Isma'il ya kalli ya majeed abokina ba wata matsala bace take damun 'kanwarmu ba, ciwonsu ne na mata, dan tafara period ne, saidai yazo mata da matsalar ciwon mara, amma karku damu dama hakan yana faruwa, zamu bata magani insha ALLAHU komai zaiyi dai2, inagama zuwa anjima zan sallameku inasha ALLAH.
to abokina mungodefa sosai ALLAH yabar zuminci.
Daga nan sukaďanyi hira ya majeed ya fito dan Dr Isma'il yanada masu jiransa.

Aranar aka sallamemu muka dawo gida, washe gari da yamma saiga Dr Isma'il yazo gidan ya majeed.
An masa tarba ta mutunci, bayan an gama gaishe2 ya ce, "ni banga patient ďinaba kumani ita nazo dubawa.
Aunty salma ta ce, "tana ďaki tanakuma jinmu inaga miskilancinne ya motsa mata, bari nakirata, bayan aunty Salma ta kirani na saka hijjab nazo, suna zaune a falo Affan yana cinyar Dr Isma'il, na zauna a'kasa cikin jin kunya na gaidashi, duk miskilancina da shagwa6a inada tsananin kunya.
Cikin fara'a ya amsa, ya ce, "my patient ya jikinki??,
"Na ce, "da sau'ki.
''Ya ce, "ALLAH yakara sauki.
Na ce, "amin.
Nami'ke da nufin komawa ďaki, Dr Isma'il ya ce, "a'a my patient sai ina kuma??, Na ce, "zanje cikine, ya ce, "da wuri haka?, kofa gaisawa bamuyiba kuma zuwannan nakine.
Nayi murmushi wanda mutane dayawa suke faďamin yana 'kara min 'kyau, kasancewar ban cika yiba saboda miskilancina, idan nayi kumatuna sukan lotsa.
A zuciyarsa ya ce, "ya salam yarinya 'karama zata haukatani.
Ganin kallon dayake mini yasani tashi da gudu na shige ciki, yabini da kallo yana murmushi harna 6acema ganinsa sannan yaja ajiyar zuciya.
Ya majeed ya ta6ashi abokina miye damuwarka??, Dr Isma'il yasaki sassanyar ajiyar zuciya sanan ya ce, "brother 'kanwarka ce damuwata, saidai tayi 'kan'kanta dan na lura bata wuce sha biyarba.
Ya majeed ya tuntsure da dariya kai Isma'il wlhy kaidai baka rabo da wasa, kai yanzu idan ance ka tsaya jiran iman saika tsaya??.
Dr Isma'il ya ce, "kajika da wata magana, aini koba ace najirabama zan jira kuma zaka sha mamakina..
To ALLAH ya taimaka amma saidai ta biyu ko??, harararsa Dr Isma'il yayi, ta biyu kota ďaya, aini kasan babu mata biyu a tsarina saidai kaddarar ALLAH, dan babu inda bata kai mutum.
Ya majeed ya jinjina kai yana murmushi, amma abokina kana ganin ya Mansur da mama zasu yarda, yakamata fa ace kayi aure tuni, kosaika zama tunzurun zurun ne?.
Dr Isma'il yay dariya, kana min wula'kanci wlhy majeed kaima naga duka shekararka nawa da auren?, su yaya kuwa banida matsala dasu, abinda nakeso suma shi suke so, kaidai katayani da addu'ar neman za6in ALLAH kawai.
Shikenan ALLAH yaza6a mana abinda yafi alkairi.
Amin Dr Isma'il yafaďa.

Da dai ya majeed ya fahimci Dr Isma'il da gsk yakeyi, saiya shige masa gaba awajen Abbah.
Abbah yayima Dr Isma'il tambayoyi kamar yanda shari'a ta tsara, yako amsa masa yanda yadace.
Saiya bashi izinin neman SO a wajena, nikam bammasan abinda ake cikiba, dan lokacin da nadawo gida mun koma makaranta.
Kai kutashi muyi sallah ďaya ta wuce, kuma ALLAH yunwa nakeji, Xoxo ta harareta ALLAH iman kin iya wula 'kanci saida labarin yafara ďaukar daďi zaki 'kir'kiroma mutane wani jin yunwa, inama laifin muyi sallar??.
Iman tayi dariya sorry dear karki damu aii idan tunbi ya ďauka labarin saiyafi daďi ko??.
Reefat ta ce, "ALLAH ni ko yunwarma banaji, burina kawai naji 'karshen labarinnan, karku damu aii muna gamawa zan cigaba.
To gsky saidai asiyo abincin ko asake cin indomi dan in ba hakaba girki zai 6ata mana lokaci, gsky ne Xoxo kunga kuyi sallar tunda ni an hutar dani, kafin ku idar naje na samo mana abinda zamuci ko bai yiba??.
Sukace yayi.
Bayan sun gama cin abinci iman ta ce, "saitayi wanka sanan, saida tagama ja musu rai sanan taci gaba.

Dr Isma'il yakasa sanar dani sirrin zuciyarsa saboda yana min kallon 'karamar yarinya, dan gsky asanan ban wuce sha biyar ba.
Ahaka wata yazagayo al'adata tazo nasha wahala sosai, su gwaggo suka rasa yanda zasuyi dani, na daure na ce, "sukira aunty Salma.
Babu 6ata lokaci aunty Salma tazo muka tafi asibiti wajen Dr Isma'il, shiyya dubani yamin allura yaďan kwantar dani na yini ďaya.
Daga nanfa ciwon mara yazamemin jiki, har fargaba nake wata yazo, hakama gwaggo tana tausaya mini sosai.
Ana haka Dr Isma'il yazo ma Abbah da zancen zai shiga soja, dan dama burinsa kenan tun yana yaro, amma saboda yayansa yanason yazama likita ya ha'kura yayi karatun likita, to yanzu damace tazo masa, shine yakeson yayi amfani da ita.
Abbah ya ce, "ALLAH sarki, ai haka akeso Isma'il mutum duk inda yake yazama mai biyayya ga nagaba dashi, saiyaga yazama abinda baiyi zatoba arayuwa, dan masu iya magana nacewa dana gaba ake gane zurfin ruwa, to inamaka fatan Al'kairi arayuwar ka, domin kai yaron kirkine, ALLAH yabada abinda akaje nema, kuma ayo nasara.
Amin Abbah nagode da addu'arka gareni ALLAH yasaka da al'kairi, babu damuwa abba yafaďa, kaga bari naturo maka iman ďin kuyi sallama ko??.
Cikin jin kunya Dr Isma'il ya ce, "Abbah dama ka 'kyaleta.
Abbah ya ce, "sabodami Isma'il?, ba sallama zakuyiba?, Dr Isma'l yaďan sosa gefen wuyansa saboda jin kunya ya ce, "Abbah karka damu, iman tayi 'karamane yanzu, inason saita gama koda secondary ne, saina fahimtar da ita nufina akanta, amma yanzu za'a raba mata hankali gida biyu.
Abbah yay dariya to shikenan Isma'il ALLAH yay maka albarka, yakuma bada sa'a akan abinda akaje nema.
Dr Isma'il ya ce, "Amin Abbah ngd da 'kaunarka gareni.
Abbah ya ce, "karka damu aii kai yaron arzi'kine wanda ya cancanci a 'kaunacesa fiyema da haka..
Daga nandai sukayi sallama, Dr Isma'il yatafi training ďin soja na wata shidda..
Nikam ban saniba, nagadai bana ganin yana zuwa wajen Abbah yanzu kamar yanda yakeyi da, ban ta6a yun kurin tambayar waniba, dan babu wata ala'ka tsakanina dashi banda ta mara lafiya da likita, haka nacigaba da shan wahala duk 'karshen wata, dukda wani likita yana dubani a asibitin su Dr Isma'il, amma bai iya shawo matsalata kamar Dr Isma'il.

Awata Asabar datayi dai2 da dawowar Dr Isma'il kano, dan ayanzu yazama soja, ALLAH yacika masa burinsa, yazama likitan sojoji, gashi likita gashi babban Soja.
Aranar natashi da matsanancin ciwon mara wanda zan iya cemuku tamkar yafi na kullum ma dan har suma nake, gaba ďaya hankalin iyayena yatashi, ankira
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment