Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ganta se kun rantse da Allah ba ita bace ba duk ta rame sbd ciwo amma har yau babu wanda ta sanarwa abunda ke damunta)
Tace..
Nikam da abba da ya sanar min mgnr aurena da sarkin daura..
Da farko a gsky ban amince ba dan ina da manema sosai a lkcn..
har sai da jalal yaje har kasar mu muka hadu dashi..
Sannan ne na amince dashi..
Juwairiya tayi murmushi....
Khadija zatayi mgn..
Zainaba da juwairiya suka kwashe da dariya..
   Ta watsa musu harara wato dan kunsan sirrina ko?
Juwairiya tace,mun san komai kuwa masoyiyar ya jalal..
Gaba daya suka saka dariya..

****************

Yau juwairiya da kan ta taje har sashen jalal ta same shi ya fito daga wanka kenan..
   Kyallen da yake goge jikinsa ta amsa..

Ya sakar mata murmushi yana fadin..
Kamar kin san tunanin ki nakeyi wlh..
Juwairiya na goge masa jikinsa tace..
Ni kaina tunanin ka nakeyi amale amma kasan abunda ya kawo ni yanzu?
Jalal ya girgiza kai yana kura mata ido..
Taja hannunsa suka zauna a gefen gado..

Tace amale ni kuwa ko surayya ta samu fada maka meke damun ta?
Jalal ya girgiza kai,nayi nayi ta fada min amma taki..
har fa kwana a sashena ma ta daina yi se de tazo ta gaishe ni ta tafi abunda ni kaina al'amarin nata yana daure min kai...
ko umma zan sanarwa ta tambayeta oho..mutum sai karewa yakeyi babu wani dalili..

Juwairiya tadan jinjina kai..
Tace...
ni kaina ramar da takeyi ta fara bani tsoro har fa baiwarta na kira na tambaye ta ko surayya bata cin abinci ne sosai amma se ta tabbatar da cewa tanacin abinci...

Na kasa gane daga ina damuwar take har yanzu?
Jalal ya jawo ta jikinsa yana zame dankwalin dake kanta..
Tabbas kin cika me kyakkyawar zuciya juwairiya..
duk abubuwan da surayya tayi miki a baya amma kin damu da ita haka?
Juwairiya ta kwantar da kanta a kirjinsa..

     Ni ban rike ta da komai ba amale sbd nasan kishi babu abunda baya haddasawa mutum bare mu mata..
Jalal ya sumbaci goshinta,shiyasa nake son ki sosai...
juwairiya ta dago itama ta sumbaci goshinsa kafin tace..
nima haka Amalena...

Yace kada ki damu dolene mu tuntubi surayya dan ceto rayuwar ta...
duk da dai zan iya cewa abunda ta shukane take girbewa yanzu..

Juwairiya tayi saurin rufe masa baki tana girgiza masa kai..
Yayi dariya yana fadin..
to uwar hakuri..
Nidai ba kamar ki bane dole na fadi gsky abuna...

******
"Magaji ne ya kalli juwairiya da tsabar mamaki..
Ta gyada masa kai tana fadin kaji fa abunda daya faru kenan..
ashe wai har yayi aurensa wannan Mustaphan gashi yanzu ni kaina na kasa lallashin zainaba dan ta saka damuwa sosai a cikin ranta kasan yaudara babu dadi ko kadan..

Magaji ya gyada kai cikin jimami..
ni ma a jiya nayi aike can kasar kanon don a gano min meke faruwa dashi ashe shi gayen har yayi auren sa Allah sarki haka kaddarar su take..

Juwairiya ta gyara zamanta..tace
Shine nake so dan Allah magaji ka taimaka min wajen saka zainaba ta rage wannan damuwar da ta jefa kan ta a ciki..kaga kaima yayanta baza so ta kamu da wata cutar ba ai ko?

  Magaji ya jinjinar da kai dan kuwa shima ya tausayawa zainaba sosai..
Yace babu damuwa zan gwada na gani..
Juwairiya tace nagode sosai magaji..
Ya mike yana fadin..
Ai GIWAR AMALE  duk abunda kika ce nayi miki ya zama dole nayi miki shi ai.
Juwairiya tayi dariya..
Ai kuwa godiya nake sosai..

*******
Tunda ga wannan lkcn magaji ya zage sosai wajen farantawa zainaba har mamakinsa takeyi..

  kullum Shine duk safiya kafin ya shiga fada sai yayi (branching) a sashen ta sun gaisa..
Da yamma ma haka kafin ya tafi gida sai ya leka wajenta sun yi sallama..
  Zainaba tun abun yana isar ta har dai ya zamo itama ta fara jiran zuwan nasa a kullum..

Kamar yau jiya har alkawari yayi mata akan zai zo su fita wajen masarauta tare suyi yawo amma taji shi shiru wannan lkcn abunda bai saba ba..

  Ta kalli zabba'u tace..
Kije ki duba min a fada ko magaji yana can..
cike da damuwa tayi mgnr..
Zabba'u tace toh ranki ya dade..sannan ta fita da sauri..
Tana fitane sukaci karo da rabi da khadija su kuma zasu shiga sashen.
Zabba'u ta gaishe su tayi gaba abunta..
Su kuwa suka karasa cikin sashen..
Suna shiga zainaba ta mike a tunanin ta ko magajin ne yazo..

Tana Ganin khadija ce sai taja tsaki..
Khadija da cikinta har ya fito sosai tace..
Ai dole ne kiyi min tsaki tunda naji lbrn kin fara mallake min yayana..

Zainaba ta waro ido..
Ni ? yaushe?
Khadija ta kalli rabi sukayi dariya..
Ai duk masarautar nan bayi sun gama dauka soyayya kukeyi da yaya magaji wai kullum ashe se yazo sashen ki...hakane?khadija ta kashe mata ido..

Zainaba taja tsaki,ai dama gulma bata yiwa yan masarautar nan kadan..
Khadija ta kalleta da gefen ido kafin tace..

Ai shikenan dama tunda babu abunda ke tsakanin ku dama wani sako ne ya aiko min na fada miki amma....
Ai zainaba bata san lkcn data riko khadija gaba daya ba tace..
Me ya fada miki dan Allah?
Dama wlh neman sa nakeyi..
Duk yau bai zo ba..

Khadija ta kwashe da dariya..tace
Toh taya kike so marar lafiya yazo nan din ?bacin yana can a kwance..

Zainaba hankalin ta duk ya tashi..
Ta mike babu shiri tace..
Dan Allah khadija kizo muje gidanku mu duba sa..
Khadija tace,lallai ni da wannan cikin? bazan iya wata tafiya ba gsky..kije ke kadai ai masoyinki ne ko?

Zainaba taja tsaki ai dama ke ba mutumci bane ya ishe ki,bari naje samira tayi min rakiyar.
Khadija tace,yarinya wlh gwara ni..
samirar da laulayin cikin zata miki rakiyar?bari ya turaki ya kamaki..
Zainaba taja tsaki tayi gaba abunta da sauri...

"hansai ce ta kalli laure sun saka juwairiya a gaba wai su ala dole dubata sukeyi..
Ace anyi aure har ya kai wata uku kenan amma shiru babu wani lbr?
  Juwairiya ta shagwabe fuska tace..
Umma na fada muku ni bani da komai wlh..

Laure tace baki da komai shine duk kika canza cikin yan kwanakin nan..
kece shan mangoro kullum fa sai Amale ya aiko jakadiya da rabin buhu kuma baifi kisha biyar ba..
sai dai mu dau sauran mu kai rumfar cab bayi a shanye shi.

Hansai tace, gashi yanzu bakya cin abincin kirki se kin amayar dashi..
Laure tace,ranar ma du'bu cemin tayi kin aika hanne wai danwake kike son ci..
Juwairiya tayi wiki wiki da ido..
Toh umma dan kawai inason danwake shine inada wani ciki?
   Sallamar gimbiya kilishi ce sukaji..
Duk suka mike dan gaishe ta..
Ta kallesu tace..
Me naji kuna fadane?
Kun tsare min diyata da wasu tambayoyin ku..
Ina ruwanku idan ma cikin ne da ita?

(Dan taji komai kafin ta shigo dama jakadiya ce takai mata lbrn kuma tabbas ta gano juwairiya ciki ne da ita,ba karamin murna tayi ba )..
juwairiya ta rufe fuskarta cike da kunyar kilishi..

Hansai da laure sukayi murmushin murna..
Kilishi tace,yanzu dai ina so kulawar ku a gareta ta linku dan yanzu muke bukatar kulawar ko? Ta kalli juwairiya..dake ta sunne kai..

Hansai tace,ai gimbiya kada ma ki damu da wannan dan ya zama dolen mune mu kula da diyarmu.
Kilishi tayi murmushi tace toh mun gode sosai..


***********
Labari ne yaje wa SARKI JALAL har fa'da..
Dan dama kowa burinsa yaje yayi masa wannan albishir din ko zai samu wani abu daga wajen sa na tukwici...

Wayyo zo kuga murna kamar yayi mai..!dadi sosai ya mamaye zuciyarsa..
Ya kasa ma yarda wai juwairiyar sa ce keda cikin sa a jikinta?..
Ya mike babu shiri yayi waje..

Ko Kafin ya karasa sashenta sai da yayi kyauta har babu adadi duk wanda ya hadu dashi se ya bashi wani daga jikinsa...

Yana shiga sashen nata ya tarar da hanne a falon..
Tace masa ai uwar dakin nata na cikin uwar daki..

Ciki ya shige cike da murnarsa..
A lkcn juwairiya na tsaye ne tana daura zaninta..
Sai ji tayi kawai anyi sama da ita..

Jalal na dariya cike da farin ciki marar misaltuwa ya shiga juyawa da ita yana ta shi mata albarka..
Sosai take dariya itama tana rokon sa daya sauke ta kasa..

Jalal ya sauke ta kan gado yana kamo hannayenta duka biyun ya rike gam..
Yace..
Giwata na gode kwarai da gaske..
Juwairiya ta lumshe masa ido tace..
Amale ai Allah ne abun godiya bani ba ..

Jalal yaja lumfashi ya daga kansa sama yace..
Ya Allah na gode maka da wannan babbar kyautar da kayi mana,Allah kayi wa dan mu albarka ka kuma sauki matata lafiya..
Juwairiya na murmushi ta amsa da amin..

Jalal yace,wlh bakiji irin farin ciki da nake ciki bane yanzu..
Khadija zata haihu haka ma kema a cikin wannan shekarar zan zama baban yara biyu....

Juwairiya ta dan kamo hannunsa..tace
Amale ka kuwa samu lkcn tambayar surayya meke damunta?

Jalal ya girgiza mata kai abubuwa ne dayawa a kaina juwairiya..
Amma zan saka hamza ya dauko min me magani zuwa gobe se a duba ta..

Juwairiya taja lumfashi tace hakan ma yayi..
Jalal ya rungume ta yana fadin..
Na kagara naga dan'mu/yarmu ni dake Giwata..
Yadan rike habar sa🤔Ko dawa zayyi kama a cikin mu?
juwairiya tayi dariya..
Da ni mana tunda a cikina yake..
Jalal ya dago fuskarta yace..
Ke yarinya SARAKI da babansa zayyi kamanni..
Juwairiya tace amma ai a cikin mamansa yake ko?😛

Jalal yadan turo baki...
Wato ma zolaya ta kike ko?
juwairiya ta make kafada ni na isa nayi wa baban SARAKI zolaya?
Jalal ya mike yana fadin..
Toh bari naje wajen khadija tunda ita har addu'a takeyi danta/yarta yayi kama da ni..

Juwairiya tayi saurin mikewa tana fadin..
Nima ai na yarda..
Jalal ya kwashe da dariya yana sake rungume ta ciki da tsantsar farin ciki da nishadi...




Team RUMFAR BAYI
             *RUMFAR BAYI*
          (A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 43

*KARSHE.........*

ONELOVE😘

********************

      "Washe gari...
Sai ga mai magani ta dira a cikin sashen sarki jalal..
Jalal ya saka jakadiya taje tayi masa kiran surayya da kuma juwairiya..

   Ai kuwa sai gasu sun shigo..
Surayya gaba daya jikinta babu wani karfi duk tayi laushi..
Jalal ya kalleta yace,surayya tunda kin ki sanar dani meke damunki yanzu dole ne ki tsaya me magani ta duba mana ke dan mu san halin da kike ciki..bakya ganin duk yarda kika koma ne?

Surayya ta shiga girgirza masa kai tana zubar da hawaye...tace
Sarkina nasha fada maka babu abunda ya ke damuna kada ka damu dani duk laifin da nayi muku....am...kuka yaci karfin ta..
Juwairiya ta dafa ta..a sanyaye tace..
Ah ah surayya ki bari kawai a duba ki dan hankalin mu bazai taba kwanciya ba idan har bamu san meke damun ki ba...

  Da kyal su juwairiya suka samu surayya ta yarda me magani ta duba ta..
   A firgice me magani ta kalli jalal tana fadin..
Mai martaba ai guba ce a jinin ta....

GU'BA!!!!!!
Jalal da juwairiya suka hada baki wajen fada cike da tsananin fargaba..
Ita kanta surayya sai da lumfashin ta ya dauke na wasu yan dakikai..

    Mai magani ta saka surayya ta kwanta flat a kasa,sannan ta saka wasu allulori ta tsaka su a saman ciki ta  sake fitowa dasu..
Sai ga wani bakin jini ya fito bakikkirin dashi..
Ta sake kallon jalal tace, Guba ce me tattare da bakin asiri,kuma tabbas da baku kawo ni nan yau din nan ba ina tabbatar muku da cewa a cikin watan nan zata iya rasa rayuwar dan bakin asirin dake jikinta ya gama gurbata jinin dake jikinta..

Jalal tashin hankali sosai ya shiga..
Juwairiya ma duk ta rude ta kama hannun surayya dake kuka sosai tace..
Dan Allah surayya ki sanar damu meya same ki?waye yake son kashe ki?
A ina kika ci wannan bakar Gubar?

Surayya duk a rikice take jin abunda me maganin nan ta fada..
Ta rirrike  juwairiya tana wani irin matsanan cin kuka...
Sannan ta sanar dasu duk abunda ya faru..
maganin neman haihuwa  ne da sukaje amsa a wajen wani malam can Sandamu,tunda tasha maganin ta rasa sukuni...

  Jalal  kam takaici duk ya ishe shi..
sbd neman haihuwa gashi nan  taje zata kashe kanta a banza..
Mai maganin tace..
Ni abunda ban gane ba a nan shine..
Shi me yasa malamin zai nemi ya kashe ki da bakar guda?
Bacin da kudin ki kika je wajen sa neman taimako..
Juwairiya tace nima shine na gani ai..
Ta kalli jalal tace..
Amale dan Allah ka saka aje a dauko mana wannan malamin ya fadi dalilinsa na son kashe surayya da bakar guba..
Jalal ya kalli jakadiya yace..
Kije ki sanar dasu shamaki aje can sandamun a dauko min wannan bokan malamin!!!..

"Malam sandamu a gaban sarki Jalal da sauran(royal family)...

Jalal ya kalli sarkin dorina dake tsaye yana ta bude hanci..
Yace..
idan har bai fada mana gsky ba akan dalilinsa na son kashe gimbiyar daura surayya.. toh na baka izinin lugwigwita shi a nan wajen..
   Malam na Sandamu ya hau wiki wiki da ido tsoro ya shige sa sosai..
Hamza yace..
Kayi mgn malam!!!!ko kaga tsararrakin ka a nan ne?

Malam ya zube kasa yana neman gafara yace..
Wlh tallahi babu ruwana a ciki..
Sarkin dorina ya kai masa duka mai shiga jiki..
Malam ya hau ihun azaba sannan yace..
Wallahi BAIWARTA ce,baiwarta ce wlh babu ruwana a ciki !!!!..

Jalal yace baiwarta ce?
Gaba daya wajen suka cika da al'ajabi da kuma tsananin mamaki!..

Surayya da kyal take iya bude ido ta kalleshi..
UMAYMA ta gama cutar  da ita..
har abada ba zata taba yafe mata ba..
Yanzu dama kashe ta dake da niyyar yi?
Lallai mutum abun yarda bane..

    Turaki yace,me baiwar tayi?
Malam yace,watarana ne tazo har wajena da makodan kudi sosai..
tace min..
zasu zo tare da uwar dakin ta akan tana neman haihuwa...
Shine ta biyani akan tana so na taimaka mata mu cuce ta mu bata wannan Gubar a matsayin maganin daukar cikin..
   Shine na ni kuma na hada ta da wanj bakin aljani shiyasa take ta fama da wannan ciwon ciki duk dare,aljanin ne yake zuwa yana lalata jinin ta da wannan gubar..

      Gaba daya wajen aka hau sallalami...
Nan suka tsare shi sai ya karya wannan asirin da yayi mata..
  Malam yasha bugu kamar ba gobe sannan ya karya asirin dake jikin surayya..duk ya gama tsorata..
  A Take surayya ta sume a wajen kilishi ta saka bayi suka dauke ta zuwa sashen ta..

""""""A cikin kankanin lkc labarin duk bazu a cikin masarautar...
juwairiya kam ta tausayawa surayya sosai...
Mutum ba abun yarda bane ashe dai cutar ta kawai umayma takeyi..
oh rayuwa kenan se ka rantse da Allah umayma tafi kowa san surayya...
ALLAH dai ya tsare gaba..
Amin

****************
""""A haka rayuwa taci gaba da tafiya a cikin masarautar ta daure...

Dan A yanzu kam surayya ta murmure sosai jikinta ya dawo..
dan kuwa tana samun kulawa sosai daga wajen yan gidan..
Duk da dai da farko sun ji haushin ta sosai na bin malamai da takeyi..
Sai kuma daga baya suka gane dai cewa abunda ta shuka ne ta garbe yanzu duniya tayi mata hankali..

"Wasa wasa cikin juwairiya ya fara girma gashi yanzu har yayi wata shidda...
Jalal kam na mugun son cikin nan dan kullum sai shiga sashen ta ya duba ta..
Duk kuma abunda da take so sai ya saka ayi mata shi..
khadija kam a watan nan ake saka ran haihuwar ta..

"Yau dai shirye shirye kawai akeyi a cikin masarautar dan yau ne daurin auren MAGAJI DA ZAINABA..

    Juwairiya ce uwar biki dan kuwa duk ita aka bar wa duk wani shirye shirye na bikin..
hakan kuwa ba karamin bata wa jalal rai yayi ba dan shi kam yafi so a bar masa giwar sa ta huta...

"An daura auren ne da karfe biyu na ranar asabar..

Dun'bim jama'ar kasar daura suka halarci daurin auren MAGAJI dan gidan WAZIRI da kuma gimbiya ZAINABA diyar mai martaba tsohon sarki Abdul-Jabbar..

"Amarya zainaba ba karamin  gyara tasha ba..
Dan tun sati daya kafin bikin me gyaran jiki tazo daga kasar borno ta shiga gyara ta a can sashen juwairiya.. dan nan ta dawo da zama ko su samira sai dai su leko su..

"Yau kuwa fulani ce ta aiko mata da kaya na alfarma data  saka ayi mata na musamman..
Gimbiya kilishi ma dai ba'a bar ta a baya ba dan kuwa sai data aikowa zainaba zinari me kyan gaske..

  Samira itama da tsohon cikin ta,nafisa kuwa cikin ta karamine shiyasa duk  tafi su karfi a wajen hidimar da akeyi da ita da surayya..

Dan itama Surayya dai har a wannan lkcn shiru bata samu cikin ba,sai dai a yanzu ta bar wa Allah komai ta rungumi kaddarar ta..

  Magaji ango ansha babbar riga sai washe baki akeyi...
jalal ne babban abokinsa kuma babban yayar amarya,hidima kam a ranar ba a magana..

"Karfe shidda na yamma aka fara shirin kai amarya..
Khadija dama ita tana can gidansu tunda sune dangin ango da katoton cikin ta haihuwa yau ko gobe..

An kai amarya dakin ta lafiya a can kusa da gidan Waziri magaji yayi ginin gidansa babban gaske..
taro ya watse lafiya aka bar amarya da halinta..

  Magaji kam yayi farin ciki sosai da kasancewa da zainabar sa dan kuwa a daren farkon su ba karamin faranta masa tayi ba..

Kwana biyu da auren su da zainaba..
Khadija ta sullubo yarta mai kama da ita sosai..
Jalal yayi murna sosai hakama sauran yan uwa..
Yarinya taci sunan kakar su jalal wato SHAFA'ATU

******************
Bayan wata uku..

"A yau juwairiya ta tashi da nakuda sosai..
Hansai da laure sukayi kiran jakadiya aka sanarwa sarki da kuma su gimbiya kilishi..

    Addu'a sosai aka shiga yi mata dan ta haihu lafiya dan ba karamar wahala take sha ba.

Surayya kam na gefen ta tana rike da hannunta tana tayi mata sannu..
Jalal kam ya kasa zaune ya kasa tsaye..
Turaki da hamza ne ke ta basa baki dan ya kwantar da hankalin sa..

Bayan wucewar awanni uku sai ga kukan jarirai ya cika sashen..
Nan aka hau murna bayi nata wakokinsu na nuna murna da farin ciki..
  Hansai ta kalli laure duk sunyi zufa tace..
Allahu akbar....
Yan biyu ne kuma duka maza.....!!!!!!!
Gu'da du'bu ta hau yi jakadiya kuwa tayi waje da gudun ta...

Sai sashen Sarki jalal..
Yana ganinta ya mike tsaye da saurinsa... ya taro ta hankalinsa a tashe..
Ta shiga rangwada guda tana rangwado wa jalal kirari cike da tsantsar farin cikin ta..
"Ga toya matsafa,babban Bajimi Babban Bako,Ga magajin Rumfa!
Ga........
Jalal yayi sauri tsayar da ita cike da kagara yaji da mai ta zo....dan kuwa hankalinsa ya kasa kwanciya ko kadan.....bai san halin da juwairiyar sa take ciki ba...
Jakadiya taja lumfashi kafin tace
Allah ya sauki GIWAR AMALE lafiya sumul..
ta haifa mana samari har biyu kyakkyawa kamar ka Sarkin mu..,Allah ya kawo mana TAGWAYEN SARAKAI..jinin JALALLUDEEN sarkin da ba kamar sa...!

Murna sosai Jalal yayi...
Ya rasa me zai ce sai godiya da yake ta zuba wa Allah...
turaki da hamza ne suka zo suka rungume sa suna taya sa murna sosai suma..

Sati na zagayo wa akasha bikin sunar yan tagwaye..
ba karamin kudi jalal ya kashe ba..
Mai martaba tsohon sarki ne ya radawa yaran suna..
Hassan shi yaci sunan ABDULSAMAD na biyu...
Shi hussaini kuwa yaci sunan kakansa ABDUL-JABBAR na biyu..

Sai dai gimbiya kilishi ta samo musu sunan banza kamar haka..
Hasssan wato abdulsamad zasu ringa kiran sa da YARIMA SARAKI..
Shi kuma hussaini Abdul-Jabbar SADAUKI zasu ringa kiransa dashi..

Bayan sati biyu itama samira santalo nata dan shima namiji ne,ranar suna yaci sunan JALALLUDEEN na biyu wato kawun sa sarki Amale kenan..

  Nafisa kuwa sai da yan biyu sukayi kusan wata uku sannan ta haifo yarta mace wacce taci sunan kilishi wato MAIMUNA kenan..
  Surayya baiwar Allah se dai ta zama uwar ya'ya dan kullum hanne sai ta kai mata yan biyu dan su dan debe mata kewa..
Hakan kuwa ba karamin dadi yakeyi mata ba,kullum sai tasha kukan bakin cikin yarda ta mayar da rayuwar ta a baya gashi yanzu ta cuci kanta...

Jalal kuwa har tausayin ta ya fara ji dan kullum bata da mgn sai ta Sadauki da saraki..

************
Bayan shekaru sha tara 19yrs..

"A cikin wadan nan shekarun  da suka gaba ta...
juwairiya ta sake haihuwar yan matan ta har biyu..
akwai me sunan mahaifiyar ta wato ZARAH'U fatima kenan suna kiranta da BATOOL sai kuma JAHAWIR itace karama kuma autar su a ciki..
Zainaba da magaji nada yaran su biyu suma mace da namiji..
Akwai IBRAHIM KHALEEL da RASHIDA..
Samira ma ta sake haihuwar ZEENATU...
nafisa kuwa yaranta uku yanzu itama maimuna,Ramla da halimatu..
Khadija ta sake haihuwar ABUBAKAR  da FADILA..

Masarautar daura kam ta cika da yara masu albarka da shiga rai..

"Juwairiya ce na hango ta kara girmanta tayi jiki ta kara haske ga wani irin kwarjini da ta kara....

Zaune take a sashenta..ta hakimce akan kilisar..
  ta kalli hanne tace wai ina yarima saraki ya shiga ne?
  Hanne ta buga uban tagumi tace..
Ai ranki ya dade ni na rasa me yarima saraki yake nema a cikin *RUMFAR BAYI*.... nan kullum fa sai ya matsa min akan wai shi sai ya shiga har ciki yaga irin tsarin wajen....
Nasha fada mishi Kanskanci ne ace dan Sarki kamar sa ya shiga RUMFAR BAYI  amma gaba daya ya kasa fahimta..

Juwairiya tayi murmushi tace,Saraki kenan yanzu...
Yanzu dai jeki ki kira min shi sannan ki biya sashen khadija ki kira min su BATOOL da JAWAHIR suma tunda shi sarkin yawo Sadauki yabi babansa ziyara gidan magaji..
Hanne ta mike ta fice tana fadin toh ranki ya dade ....

"Tana shiga sashen khadija ta iske yaran gaba daya yan matan sai wasa sukeyi amma banda JAWAHIR ta na can a zaune abunta tana kallonsu..
Hanne da rabi sukayi murmushi dan ba karamin burge su halayen jawahir yake ba kullum a natse zaka same ta..ga fara'a da son mutane sam bata da wata damuwa ba kamar Batool ba..
 
"YARIMA SARAKI  kuwa yana can kogin mai martaba a zaune tare da bawan sa Cigari suna shan iska abunsu..

Ya hakimce yana kallon yarda ruwa ke gudana a wajen ga iska me sanyi yana kadasa sai lumshe ido yakeyi..

  Hanne ce ta shigo wajen da sallama..
Ta jinjina kai tana mamakin irin kasaita da girman kai na yarima saraki...
Sam shi ko mgn ma wahala take masa in ba da babansa sarki  JALAL suke mgn ba toh da kyal ne kaji muryasa a wani waje..

Shiyasa take tausayawa cigari kullum sai dai suyi zaune babu uhm bare uhm uhm..
   Kirari kawai ta shiga yi masa...

Lafiya jinjirin wata sha kallo..
Lafiya sukukun bakaka..
Lafiya kwankwason jimina mai wuyar shafawa.
Lafiya Gar'kami wandon karfe
Lafiya Toron Giwa SARKIN GOBE..

Kai kawai ya jinjina mata kafin a kasalance yace..
Meke tafe dake inna hanne?
Ta kalli Cigari daya tsare ta da ido..
Tace,dama GIMBIYA GIWAR AMALE  ce take son ganinka..
  Ya mike cike da nutsuwa ya kalli Cigari yace muje..
Sukayi gaba aka bar hanne tana ta sakin murmushi..

"A falon ta ya iske ta saman kilisarta..
Ya zauna yana yankwashe kafafunsa..
juwairiya ta kurawa dan nata ido tabbas dolene ta gode wa Allah daya bata ya'ya nagari masu so da kaunarta..

   "SARAKI inaso ka fada min miye dalilin ka na son shiga cikin RUMFAR BAYI?
Ya dago suka hada ido da ita..
Yace umma.....
Kawai so nake naga a inda mahaifiyata tayi Rayuwa a baya...
Juwairiya tayi murmushi..tace
Saraki kenan...
Ya dan dukar da kai yace,ki bani izinin ki gobe na shiga cikin RUMFAR BAYI..
MUMA haka UMMA...!
Sukaji muryar JAWAHIR da BATOOL  a bayansu..
Juwairiya tayi murmushi kawai kafin tace dasu...
kada ku damu yarana gobe nayi muku alkawarin zamu shiga  cikin RUMFAR BAYI..daku
Zamu canza DOKAR wannan masarautar..
Dan babu wani Kanskanci aciki..
dan kawai Jinin sarauta ya shiga muhallin Bayinsa.....
Nayi rayuwa a cikin RUMFAR BAYI kuma tabbas yana da babban tahiri a kaina..

********
"A Lkcn da jalal ya dawo tare da SADAUKI a sashen juwairiya suka sauka nan suka hade da yaran duka aka hau fira cike da kaunar juna..
Kafin saga bisani jalal ya janye matarsa sukayi sashen sa..

"Suna shiga ya jawo ta jikinsa ya Rungume ta yana fadin..
Maman yara nayi kewar ki dayawa..
Juwairiya tayi murmushi tace..
nima haka Amalena..
Ya shafa gefen fuskarta yace...
a kullum bazan bar shi miki albarka ba dan kuwa nasha fada miki KE Din TA DABAN CE a cikin zuciyar JALALLUDEEN...
Juwairiya tayi murmushin farin ciki tace..
Nagode sosai da soyayyarka ALLAH YA KUMA BARMU TARE har abada..
Jalal ya janyo ta jikinsa kafin ya amsa da..
AMEEEEN....GIWATA...

                            Karshe...

Tammat...
A yau na kawo muku karshen littafin RUMFAR BAYI...
"Idan nayi laifi ko wani sa'bo a rashin sani ina neman gafarar ka Allah...

Godiya ta musamman ga...
"Duk Fans din RUMFAR BAYI nagode sosai da Kaunar ku,na kuma gode da duk addu’o'in ku Allah yabar zumunci..

"Godiya ga dukkan RUMFAR BAYI whatsapp Groups..
"Godiya ga PHERTY NOVELS group.
"Godiya ga FATIMERH XARAH didi i love you😘
"Godiya ga WATTPADIANS u guys r just d best..
"Godiya ga TASKAR MARUBUTA group.
" godiya ga RASH KARDAM HAUSA NOVELS.
"Godiya ga QUEEN MEEMI Fans..


AFRAH BHAI LOVE YOU ALL...😘😘

Watch out for my new novel inshaAllah...
                        Coming Sooon....

And👇

Dnt forget to follow me on instagram @khadi_nana

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu

Please Login or Register in order to submit comment