Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[8/25, 2:59 PM] Real Mai Dambu: 🌹🌹🍀
            *MATAR SO*
                            🌷🌷🌻

*MAI_DAMBU*
            *Wattpad:Mai_Dambu.*
*HAZAKA WRITER'S ASSO*
(HWA)

    Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai....

Dedicater To Hafsat Abubakar💋


      _Fatan alkhairi ga sakonku Masu sharhin Da Ciwo A Rayuwata Allah yasaka da Alkhairi ga tukwaicinku nan😹_
      
   *Special Class*
*Na musamman*

dankalin hausa
dabino
kwakwa
kanunfari kad'an
peak

ki gyara dankali ki gurzashi saiki markada idan kika tace saiki saka markadadden dabinonki kisa peak da kanunfari gari kad'an
Free page....01👈
            Part One
         
A gajiye na shigo gida ɗauke da jakar makarantana sai haki knake tsabar na gaji, tun a falon Malam nake jin Muryan Umma tana faɗawa wasu, mikewa nayi na shige ɗakin Umma Amrya na zauna a kujeran dake kusa da ita, lazumi take tana ganina ta sallame tare da sakar min murmushi tace.
"Uwar Masu gida!, har kin dawo"
     Gyaɗa kai nayi na kwanta cikin nutsuwa ina kallon tv falonta, can na dubeta nace.
"Mama Amarya! Wai mike faru naji muryan umma tana faɗa haka? Ko wani abu ya farune?"

     Murmushi tayi cike da takaici sannan ta maida hankalinta kan tv, kafin tace.
"Ita da Gausiya ce! Wai yaji tayi shine takira mijin yake faɗar irin abinda take mishi."

    Tashi zaune nayi haba gaskiya mana da zan shigo naga motar Baban Yasmen, ashe dai haka ce.

    Cikin rashin sanin makomar mi zance, na koma na kwanta ina jinjina abinda Aunty Gausiya takewa Mijinta na rashin adalci, yana bani haushi. Tsaki nayi a fili nace.
"Albasa batayi halin ruwa ba, ta cigaba da wulakanta aurenta ita zatayi kuka da kanta."

         Cikin wani irin muryan kuka Mama Amarya ta kalleni sannan tace.
"Maryam Sajida! Yazanyi da Gausiya kinga yaron nan hidimar da yake mata kuwa duk cikin Yaran gidan nan itace tafita zakka, dan koda nakira Malam cewa yayi babu ruwanshi Sajida ya zanyi da Gausiya, rashin ɗa'arta har yakai tana bin miji waje tana cin kwalarshi."

     Cike da tashin hankali na sauko daga gadon nazo gabanta na zauna, nace.
"Mama Amarya, gani ga Rahima da Rahila bazamu taɓa barinki ki zubda kwalla ba kinji Mama kiyi hakuri kuma Nasan matukar Aunty Shema'u da Aunty Asma'u suka ji baxasu kyaleta ba."

            "Maryam Sajida kece kika zauna kina bawa Mama Hakuri, wannan na tsani Aunty Gausiya, sai kace ba jinin Malam ba kuma ai duk laifin Mama ne da take saka damuwarta a ranta, wallahi Mama duk mutumin da Malam ya zaɓa mana zamu zauna dashi, har sai in shine yace bazai zauna damu ba, ko sisters." ko kallonsu bamu yi ba, sabida sun karya doka babu wacce tayi sallama a cikinsu ganin haka Rahima ta ɗauki bag ɗinta fa shigo da sallama, dariya nayi na amsa, sannan Rahila itama tayi nata, duk zuɓewa mukayi a cinyar Mama muna rarrashinta.

     Muna cikin haka Umma ta ɗaga labule tare da sallama, amsawa mukayi, sannan tashigo tare da Aunty Gausiya  tsaki Rahila tayi tabar falon, haka ma Rahima, sai nice na iya kallon Umma da Gausiya na gaisheta, ina gamawa nabar falon.

        Cike da jin haushinmu ta kalle Umma tace.
"Umma miye na musu."

     Murmushi Umma tayi sannan tace.
"Kaɗan daga cikin saɓawa, Iyaye da miji knn wanda bai kai ya renaka ba zai renaka."

   Sunkuyar da kanta tayi cike da bakin ciki, bata kuma cewa kome ba.
       Cigaba Umma tayi da magana tace.
"Amarya kiyi hakuri ɗane ka haifeshi baka haifi halinshi ba, duk yanda kaso ba haka kake samu ba, kuma nayi mata faɗa zata bari."

      "Toh Umman Yara mi zan mata, babu abin bakin cikin kamar raine mijinta da tayi wai ɗiyar malam ce haka, kinsan jiya da naje ta'aziyar gidan Malam Mudi, akan idona ake cewa Yar malam taki halin malam, kamar ba'a bata tarbiya ba, Na aurar da Shukra da Hamdiya, ban sami matsala dasu ba sai itace zan ɗaurawa kaina matsalarta toh mi zan mata Allah ya shiryeta."

               Jikin Umma ne yayi matuƙar sanyi sannan tace.
"Toh munji amma ayi mana afuwa."

         "Hmm Allah yayi mana baki ɗaya, kamar yanda ta kwaso kafa haka zata koma, dan Malam yace kar wata ta rakata zaki iya tafiya"
   Mikewa tayi jikinta a sanyayye kamar da gaske nan kuwa, amma  huɗubar Maman Yaro makociyarta yafi nasihar Umma da Mama akanta.

                  ****
    Tsurawa computer ɗinshi ido yayi a nutse, bashi kaɗai ba dukkansu Uku, can ya sauke a jiyar zuciya sannan yace.
"Yunus hakuri zan baka kuma iya kar abinda zan iya baka knn, kai ka godewa Allah ukune da kai amma duk basu da lokacinka, Nifa ɗaya ce dani amma ji nake kamar na saketa na huta, idan na duba girman mutuncin Iyayenta da nawa sai naji kome ya kunce min."

      Gyara zama ɗaya daga cikinsu yayi, kafin Yace.
"Aman kana nufin har yanzun Hindu bata bar kazanta ba,, ni ina mamakin matanmu nan wallahi duk kokarinka sai sun kwareka,  bansan Ya zamuyi dasu ba wallahi."

         Dafe goshi wanda aka kira Aman yayi ya gyara zama kafin yace.
"Idan ina son nasami nutsuwa da ita, sai na biyata kuɗi sannan wankan jikinta sai nabiya kuɗin, kaii karewa abinci daga waje nake kaiwa gida macen da bata san ciwon kanta ba mi zai dameta, nidai gefe ɗaya Ina jan Allah ya isa da fitar da Apps ɗin Whatsp Hindu tasan kan whatsp amma bata san yanda zatayi da rayuwar gidanmu ba."

           "Hmmm. Aman knn gwara kai kana iya samunta a gida ni fa Hafsa bazaka taɓa samunta a gida ba, asalima, tafi bawa yawo degreen degirii akan zaman gida, itane yau bikin danginsu gobe sunan kanwar kawarta, kaii Uwa uba, ɗan uwana bai isa ya taka gidan ba, tashin hankali ya samu har sai ya bar gidan, ga ɗan banzan kishi ko muryata mi aikinta taji magana ya kare dole tabar gidan, da zaran na nimeta tace min ita bayanta na ciwo ko kirjinta, kaiii nikan miye mukayi haka Allah ya bamu mata marasa adalcine."
  

   Tunda suka fara magana yake rike da wayarshi kiran Iphone+8, va kome yake ba sai temper runinning, ya nutsu abinshi kamar baya gurin, dafashi Aman yayi zaiyi magana, Ya ɗagawa Aman hannu cikin murmushi kaman bazai ce kome ba, suma sun san halin Yunus Mai Nasara, sam bai damu da hayaniya ba ko surutu barshi idan abun ya motsa mishi zai iya kwana ya wuni bai cewa kowa cikanka ba,

       Ba iya jinin sarauta keda miskilanci ba, akwai mutanen da Allah yayo su a haka kuma basu damu ba, yafi mintina arba'in kafin yace.
"Ahmad,Aman! ai duk matsalarku kaɗan ne ni dukkansu Balkisu ce na aureta ina sonta sauran matan kuwa Fareeda Yar abokin Alhaji ce, Sai Aneesa yar Kawuna ce, so nikan bansan mi ake kira dadin aure ba asalima idan kaga na shiga al'amarin mace toh babu yanda na iyane shi yasa na rufuwa kaina asiri nake azumin, amma sha'anin matanmu sai Allah."

         Tsura mishi ido sukayi can Ahmad yace.
"Kasan Allah aure zan kara nima na hutu."

     "Kayi fatar ta gari ko dan matukar baka dace da ta gari ba, kasake faɗawa wata gararin rayuwa." Inji Aman.

            Shiru suka yi basu kara cewa kome ba, har biyar yayi na yamma a gogon Dubai mikewa sukayi kowa ya ɗauki kayanshi cike da bakin ciki, suka fito gashi dai Allah ya dafa musu ta ko ina, suna samun albarka sai dai Allah bai basu mata na gari ba.

        Airport suka nufo, inda zasu bi jirgin da zai kawosu kano daga nan subi jirgin kaduna.

              ***
  "Ranki shi daɗe mi za'a girka naji kince Alhaji yana hanya." Inji Kukun gidan kenan yake tambayar hamshakiyar mace wacce, kana ganinta kasanta haɗa abubuwa dayawa a tare da ita na rayuwa.

    A nutse ta kalleshi cikin isa da kasaita tace.
"Kayi whiter rice da veg soup,sai farfensun kan saniya."

    Tana gama faɗar haka ta cigaba da duba, jaridar Weekly Trust ɗinta, hankalinta kwance,

       Shigowar Yar budurwan Yarta wacce bata fi sha uku ba. A nutse ta zauna kusada mamarta tace.
"Mommy!!!"
      Bata ɗago kanta ba kuma bata amsa mata ba, tacigaba da karanta jaridarta cikin nutsuwa, sai da yarinyar ta sake kiran sunanta ta amsa mata da.
"Hmmm"
          Takaicine yasa yarinyar haɗiye abinda ya kawota ta mike tabar mata falon, ɗago kai tayi ta hango bayan yarinyar, taɓe baki tayi sannan ta cigaba da karanta jaridarta.

                   
                  Karfe goma na dare Jirginsu ya iso garin kano ba tare da ɓata lokaci ba, suks nufi jirgin kaduna, wnda ya kawosu sha ɗaya saura, drvn Ahmad ya ɗaukesu inda ya kaiii. Mai Nasara Unguwar sarki ya ajiyeshi sannan ya wucce da Aman kinkinau, sannan ya kai, Ya wucce da Ahmad G.r.a.

           A gajiye ya shiga gidan ba kowa sai Yarshi da sauri tazo ta faɗa jikin Uban tana sauke ajiyar zuciya tace.
"Daddy barka da dawowa, ya hanya."

     Shafa kanta yayi cikin nutsuwa yace.
"Huda Alhamdulillah nasameku lafiya, Yasu Mufida da, Sameer suke da fatan kuna lfy."

          Cike da farin ciki take gyaɗa mishi kai karɓan kayanshi tayi ta kai mishi har, ɗakinshi ta ajiye tafito, zama yayi sannan ya kalleta cikin nutsuwa yace.
"Jeki ki kira min Mommynku."

   Da sauri ta fito zuwa ɗakin Mamarta a falo tasamesu ana shafe mata jiki da dulke, cikin nutsuwa tace.
"Mommy Daddy yana kiranki."

          "Jeki kice mishi ana min gyaran jikine, sai gobe zan shigo "

    Shiru yarinyar tayi haka bai mata daɗi ba, ta buɗe baki zatayi magana uwar tace.
"Bace min da gani."

   Jikinta na rawa tabar side ɗin Maman zuwa ɗakin Uban kanta a sunkuye, murmushi yayi yace.
"Kira min Fareeda maman Sameer."

   Jikinta ba kwari ta fita, zuwa ɗakin Fareed, tana zaune ta baje takardu da na'uran lisafi, ga wayarta na tsiwa bata ɗauka ba sai buga lissafi take, da sallama ta shiga, dakyar Fareeda ta amsa mata tace.
"What??"
    
      Kamar zata fasa kuka tace.
"Daddy Is..."

       "Ok shine kika zo faɗa min ko ance miki bansani bane zaki fita, ko sai nazo kije kice ina aikine."

      Jikinta babu kwari tabar ɗakin  a falo ta zauna ta fashe da kuka, dukda kankantarta amma tasan daga Mamarsu har sauran matan basu ɗauki ubansu da kima ba, Asalima sunfi kambama rayuwar da suka tsarawa kansu, na duniya.

   "Heyyyy Daddy girl, keda waye baku da school ne gobe."
         Inji Aneesah, wacce tafito shan ruwa ne taga Huda na kuka, juyawa Huda tayi cikin nutsuwa  tana kallonta a tsorace tace.
"Daddy is back, nd"

    "Ok yana cikine, toh kice mishi ina gaisheshi gobe ina da meeting a bank, da na shigo."
     
   Da gudu Huda tabar falon ta shige sider ɗinsu ta rufe kofar tana me fashewa da kuka.

  Allah sarki bawan Allah tunda bai ga huda ba ya tabbatar babu wacce zata zo, dan haka ya shiga ɗakin ya gyara ko ina, sannan yayi wnka ya fito gurin abinci yaje yasamu yayi sanyi, haka ya tsakura yaci sannan ya koma ɗakinshi ya cigaba da aiki, kamar baya jin kome Allah yasa gobe asabar ne a zaria zaiyi wkend ɗinshi.

   ****
      Shiga Aman gida, ya samu wutar falo a kune zaro ido yayi cike da al'ajabi idan idanunshi basu mishi kary ba, da kayan jiknta ya tafi ya barta ya dawo ya sameta dasu cike da takaici yace.
"Hindu!! Kardai da bakiyi wanka ba."

   D'ago kai tayi a tsiwa ce dan ta nutsu tana chart a grp ɗin, Zubar gado fans murguda bakinta tayi, snnan tace.
"Kabiya kuɗin wankar kwnaki biyar ɗin da zakayi ne, nifa bana son reni."

               Kamar ya rufeta da duka haka yake ji jan kafarshi yayi ya bar falon,

  Hankalinta ta maida kan chart tana ihu tace.
"Sai ni matar so na juya miji kamar yanda ake juya underwear ɗina kuma haka zaiyi hakuri dani."

     Aikuwa take aka shiga turo mata stickers tare da Emoji irinsu, Tumbeleke na dariya, da wnd yake gudu😹, Marubuciyar Zubar gado tace.
"Matar So kina wuta ina binki ds gas, Ai maza yan kuttt, ni gwara ki gara min shi yasa idan ya faɗa hannunki ba sauki."

    Reply ta mika mata da cewa.
"Thank you My luvly roler model,  kinsan yanda yake son kuwa dole naja zamanina."

        
         Murmushi Rahila ta tura mata sannan tace.
"Allah sarki Matar so ammabaki ci sunar ba, ya zaki biyewa wasu suna ɗauraki a hanyar da bazata ɓule miki ba,..."

      Aikuwa sake sakon kamar an sake bom take masu laɓe sukaww Rahila caaa har da masu tambayarta kina da aure.

     Murmushi ta ɗaura musu tace.
"Wannan Year ɗin zan gama scndry schl.."

Tana turawa akayi removen ɗinta😹

        .....
   Ahmad ya isa gida sai dai Abin bakin cikin shine  Hafsat ta tafi dinner kanin kawarta........

              👌👌👌👌
      ```Shin Ya kuka ji labarin, Abin dariya ko ga tarin shirme da shiririta, amma kubi a hankali zaku tsinci wani abun ɗauka ku bar na bari```
[8/25, 2:59 PM] Real Mai Dambu: 🌹🌹🍀
          *MATAR SO*
                       🌷🌷🌻

*MAI_DAMBU*
*Wattpad:Mai_Dambu.*
*HAZAKA WRITER'S ASSO*
(HWA)

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai....

    Dedicater 2 Hafsat Abubaka

   *Fatan Alkhairi ga Mommyn Fadyl nagode*

*Special Class*
*Sirri*

nonon raqumi
dabino
abarba
kwakwa
hulba
zuma
ayaba
zaki jika dabino saiki markada sannan ki markada ayaba da abarba, saiki juye a mazubi sannan ki saka garin hulba kisa zuma a ciki kisha a tsawon wuni.


_Masu tambaya ta ina zasu biya suyi hakuri ranar monday Insha Allah xan ɗaura musu Phone number na da Acc ɗina Nagode_🥰


          Free Page..
*BOOK ONE...Page...02*

   Hannunshi rik'e da k'ugunshi sai sinturi yake yana duba agogonshi, tare da kallon kofar get ɗinshi zuciyarshi na kona komawa yayi ya jingina da motar idanunshi nakan get ɗin, karan mota yaji ajiyar zuciya ya sauke sannan yakara kallon, agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi jingina kanshi yayi da jikin motar. Ya lumshe idanunshi zuciyarshi kamar ta ɗirko, me gadin gidan ya buɗe mata kofa a hankali ta zuro kafarta cikin nutsuwa take taku, karan takalminta yake ji kamar ana kwala mishi guduma,

         Bata lura dashi ba sai da ta iso tsakiyar gidan a tsorace tace.
"My Toys luv."
             
      K'in buɗe runannun idanunshi yayi dan sunyi wani irin ja, wanda har maikon kwalla suke takowa tayi gabanshi tare da niman taɓa shi, cikin sanyi murya yaja da baya. Sannan yace.
"Ko zaki iya buɗe min..."
    Da sauri ta nufi kofar shiga gidan, tunda ta buɗe yazo ya shige ciki, rufa mishi baya tayi har ɗakinshi tana zuwa ta fara wurgi da takalminta, sannan ta rigashi shigewa ban ɗaki dan akwai inner wear ɗinshi da yabar ta wanke mishi , amma bata samu damar wankewa ba. Yana saka kafa yabar garin itama ta zari gyalenta tabar gidan.

           Gajiya yayi da zama ya juya yakalle bedsheet ɗin gadon take zuciyarshi tafara tafasa, mikewa yayi ya wucce ɗaya ɗakin acan yayi wanka, sannan ya kwanta a ɗakin.

                      ****
  Kallonmu Rahila tayi cike da takaici, sannan ta mike tazo tsakiyar mu da Rahima, tace.
"Kinsan anyi waje dani, a grp ɗin zubar gadi."

      Dariya muka saka mata sannan Rahima tace.
     "Wai ke! Miye matsalar ki da shiga abinda bai dameki bane?"

      Mikewa tayi ta shiga ɓalle rigarta, duk muna kallonta juya mana baya tayi bayan ta rike kugunta, a nutse tace.
"Wai shin bankaci mace bane? Ko ban isa ɗaukar wasu abubuwan bane?"
   Juyowa tayi tana kare kirjinta, da sauri muka juyar da kanmu dariya tayi ta ɗauki rigarta tasaka.
      
          " Kansacewarki cikakkiya ba zai hana ki iya samun matsala da mijinki ba koda abokiyar, zamanki ba kawai fatarmu mazaje na gari sai Rahila yaushe kika koma haka ne? Ni har tsoronki nake dan naga Idanunki sun buɗe."

   "Hmm! Maryam Sajida tambayeta dai yarinyar nan so take a kone tun bata tafasa ba" Inji Rahima.
              
  Dariya tasaka mana har da tafa hannunta tace.
"Woww! Kenifa ban ɓaci ba."
Haɗe baki mukayi dukkamu muka ce.
"Ai bamu ce kin ɓaci ba."

           Gyara rike wayarta tayi cikin nutsuwa tace.
"Ina karance karance kuma kunsan da haka, amma duk buk ɗin da nakaranta ina ɗaukar abun ɗauka na ajiye na banza, ina karanta buk na soyayya sosai amma kusan mi?"

         Girgiza kai muka tare da ce mata.
"Sai kin faɗa."

     "Ban taɓa yunkurin karanta buk ɗin da zai tada min feelings ba, asalima idan akwai romance a cikin page tsallakawa nake, kusan sabida me nake haka."

    Kamar wasu dolaye muka sake kad'a mata kanmu.
       
   Dariya muka bata tayi sosai sannan tace.
"Sabida bana son na rage karfin feelings ɗina tun a waje...."

  Bata karasa bayaninta ba muka ja bargonmu, muka rufe kanmu dariya tasaka mana tace.
"Hegu munahuka, daga jin ina magana kunja kun rufe kanku wai ma kunsan ma'anar ayaba a yaren noɓel."

   Janye bargonmu muka, cike da son jin kwaf amma girman abinda zata ce yasa muna tsoron fitowar shi daga bakinta.

     Haurowa katifarmu tayi, ta zauna a tsakiyarmu tace.
"Ma'anarshi, abin fitsarin Baby Khalif..."

    Dira nayi daga dagon na wahe gadonta nace.
"Kiwa darajan Allah ki barmu muyi barci,"

     "Eh nifa wayar muku dakai nake."
"Ina wayar dakai anan, zaki lalata mana rayuwa don Allah Rahila jeki kwanta ubangiji ya kawo miki shiriya a cikin barcinki."
   Rahima na gama faɗar haka ta juya mata baya, ita kuwa mi zatayi mana banda dariya har da rike cikinta.

              Dukka dukka shekarunmu basu wucce sha bakwai ba, da watannin amma rahila tasan iya karance karance, gyara kwanciyana, ina nazartan maganarta baki ɗaya bansan iya lokacin da na ɗauka ba, har barci yayi gaba dani.

               ........ Buga mana kofa Mama Amarya tayi dakyar na buɗe idanuna, wanda suke cike da barci mika nayi tare da salati nace.
"Yau fa asabar ne! Ai sai abarmu mu huta."

       Kallona Rahima tayi bayan tashigo ɗakin nace.
"A ina kika kwana.?"
    
      "Hmmm! Ai Allah ya takaita mana ne, jiya Asthmar Mama Amarya ya tashi ina kwance bayan kunyi baci sai ga, bakona yazo shine na tashi nashiga banɗakinmu naga baruwa, sai na ɗauki Pad da kuma pant ɗina na shige gurinta nasamu tana ta fama, gashi inhelarta ya kare, sai danaje na bugawa Malam kofa dan yana ajiye dasu, muna zuwa har idanunta sun fara hawa sama, kaii Allah ya isa mana tsakaninmu da Aunty Gausiya dan itace sanadin tada asthmar Mamanmu."

            Fita mukayi nida Rahila, har muna ture juna, muka samu tana sallah, a ɗ'akin mukayi  sallar muna idarwa muka zuɓe a jikinta tare da sake kuka, rungumeta mukayi sai kuka muke, kamar wani abu zai sameta.
             Shafa kanmu tayi, cikin nutsuwa tace.
"Ya isa haka! Yan ukuna bagani nan a raye ba. Toh ya isa haka ba kuka zakuyi addu'a zaku tayi min Allah ya kara min lafiya."

             Kallonta Rahila tayi cikin kuka, sannan tace.
"Wato da Rahima, bata shigo ba dashi knn sai dai musa mi mugun sako, Don Allah Mama ki daina saka damuwa a ranki."

        Shafa kanmu tayi cikin jin daɗi tace.
"Toh nadaina."

     "Toh karya mana ita zakuyi, Auta da yan biyu."

      Mikewa mukayi, muna dariya dan Babban Yayan Hayat na ya shigo rike da basket, zama yayi cikin nutsuwa. Mikewa nayi na amshi basket ɗin na kai kusada ita, gaisheshi mukayi ya amsa, yana murmushi yace.
"Mama ashe abinda ya faru knn? Amma ai an gaya miki ki rage iza damuwa cikin ranki, banda kwanarki na gaba Allah ya kawo Rahima ai da bamu kai labari ba, don Allah ki cire al'amarin Gausiya, a ranki ko muma Yaranki zamu sami nutsuwa."

    "Yayansu! Ai ba wai narike damuwarta bane kawai ciwone ya tashi min, amma zan kiyayye gaba."

      Lekowa Umma tayi tana kallonmu yanda mukayi rashe rashe, a cinyar Mama.
 
     "Mmm! Zaman jiranku zanyi ne? Ko kun manta kuna da mkrantane. Ga wanke wanke can."
    Da sauri muka mike, zuwa waje aikinmu kowa ya kama, dan munsan da aikin.

      Nike wanke wanke da shirya kayan karyawa, Rahila sharan ɗakunan Iyayenmu da wanke ban ɗakinsu da kuma namu, Rahima kuwa da ita ake girki, shima juya abin ake, turn by turn.

       Karfe bakwai da arba'in muka gama kome, sai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment