Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»Ώο»Ώ[23/04, 14:54] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—


✍🏻
*WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*Bissimillahi rahamanirrahim*


*Nafara da sunan Allah mai rahama mai Jin kai Allahu buwayi gagara Misali. Allah yanda kabani Ikon fara rubun littafin kasa na kammalashi lafiya*


πŸ‘ŒπŸ»A RASHI

WANNAN LITTAFIN QAGAGENE DAGA NI BINTA BANYI DAN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAIDAI DA YANAYIN RAYUWARSA TO A RASHIN SANI NEπŸ‘ŒπŸ»

*Ban yadda wani ko wata ta juya min littafi ba batare da izini na Dan haka a lura*


πŸ’‹Bakina bazai iya fadin irin godiyar da take cikin zuciyata ba Amma na barwa zuciyata komai tabbas nasan Akwai so na gaskiya a zuqatanku Ku kun San kan Ku ba sai na fadaba Allah ya bar kauna ta Dan AllahπŸ’‹


*Iyayena Abin Alfaharina Allah yaja min da ranku yakara muku lafiya Ameen*πŸ‘πŸ»



πŸ…Ώ 1




Wani matashin yaro ne zaune cikin Wani haddaden falo dashi da Abokanshi sun kaceme sai har gowa suke gefe guda kuma Abinci ne da Abinsa birjiki gasunan anci an barsu !


"Yana zaune kan kujera cikin wasu kananun kaya da sukayi masa bala'in kyau kafarshi daya kan daya kamar wani mace Hannusa riqe da *Sigari* yana busawa da kangashi Kaga Dan duniya domin ida nunshi a Bude suke dudu shekarunsa baza su haura 24 ba!

Yanada kudi sosai domin kafatanin danginshi basusan wani Abu ba waishi talauci "yan boko ne taimi dukkanisu duk Wanda ya kwana yatashi A family nasu sai yayi kararun boko basu damu da yin kara tun Addini ba sosai qalilan daga cikinsu ne suke mai da hankali suyi!!

To Shima *NASIR AL'HUSEN* yana cikin jerin waddanda basu damu da karatun Addini ba yafi mai da hankali a boko domin tun yana shekara Sha shida yake can America cikin turawa karatun boko ya samu shekara takwas a can Dan haka duk wasu munanan dabi'u a can ya dauko Abinshi. Idonshi idon Mata ne mutukar ya kyalla ido yaga mace mai kyau nan da nan zai rude zai iya kashe ko nawa ne a kanta domin samun biyan bukatarsa

Yana ta6a shaye shaye Amma baita shangiya ba har yanzu suma kayan mayen sai sun fita yawace yawacensu da Abokai yakesha ko in zai nemi matanshi baya ta6a yadda yasha wacce zata bugar dashi dayawa masu tsada yake Amfani dasu

Yana 6oyewa iyayenshi duk a zatonsa basu gane ba tuntuni dadyn dinshi ya fahimce shi shi dai kwai yana masa Addu'a
Mom d'inshi kuwa Sam bata Fuskanci komai ba dake macece mai son yara kwata kwata batason laifinsa duk Abinda yayi dai dai ne!
Shiyasa suke dasawa dashi. Dan yana sakewa da ita sosai bakamar dady nashi ba!!



*MRS AHAMAD GWADABE CE*
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

*INA TARE DAKU HAR KULLUM*
[23/04, 14:54] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—



*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*πŸ…Ώ2*



Mom' dinshi ma'ai kaciyar Lafiya ce a sibiti" da kowane lokaci tana zuwa Aiki 'sabe rana dare shiyasa duk sanda zata je Aikin kwana yake tsula tsiyarshi a gidan. Dan mata yake kawo wa suyi Abinda suka ga dama dashi da Abonkanshi gashi yanada wata baiwa da Allah yayi masa na farin jini! Babu maza babu mata babu yara kanana babu manya kowa yasan *Nasir* sabida yawan kyautarshi da wasa da dariya domin mutum ne shi mai yawan fara'a yana sakewa da kowa a family nasa sosai In kacire dady n shi gaisuwa ce kawai a tsakaninsu domin ko taro a ke irin na family bai zuwa sabida dandy dinshi ne shugaban taro to duk sanda yake gabatarwa a gurin a taron Sai yayiwa *Nasir* shagu6e A kan Yasan ya San Abinda yake Ai katawa a bayan fage shine dalilinda duk ranar daza a gabatar da taron yake kirkirar wani Abu domin yaki zuwa"


A kwai "yan mata Biyu Hasina da Mubina da suke mutuwar sonsa a family din Dan har fada suke da juna gami da gaba duk a kansa gashi sunayi shi Sam bai Sani ba su suke wahalar da Kansu domin shi a halin yanzu babu Maganar Aure yaruwarshi yake ci da tsinke!!

*wannan kenan*

********************

Wani Wanda suke kira da mansur shi yadawo kusa da *Nasir* ya zauna yana dariya kasa kasa yace yaya yau din kuwa zamu fitaa kasan Anyi sabuwar dauka!


Fuska yasaki kadan yace kai wasa ma kake Babah dole ne muje Ai muga ni Ammafa kasan ni bana son kananun yara nafi son manyan baby's yadda zanjini a ciki ruwa tsun dum ko ina da bayani!
Hannu Mansur ya bashi suka tafa yace kai *NASS*
kana San kan har kar shegen Sama wai maye sirri ne sabida na lura "dakansu suke kawo kansu wataran basai ka nema ba"

Le6anshi nakasa yasa a baki yana wani Murmushi yace Sirri ai daga nine Abokina ni na yadda da kaina sabida nasan duk macen da ta dandana taji sai ta zo da kafadunta
Wata Mahaukaciyar dariya Masur yafara yana nuna *NASS* da Hannunsa yace kayi min daidai *YARO DA KUDI* nasan dama da kudi ko babu zasuzo ko su biya Ayi musu

Le6enshi dai yake tsotsa Wanda suka Dan rine kadan sabida zuqar *SIGARI* yana lumshe ido yace Ai hakkinsu ne dole in bawa ko wace shegiya ko zata zubar ni A kwai "yar iskar da ta isa ta siye ni karya take duk macan da Kaga na kwanta da ita A kwai Abinda na hango!!


*MUJE ZUWA*



*MRS AHAMAD GWADABE*
[23/04, 14:55] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI🐾*
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—




*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*πŸ…Ώ3*


Daya daga cikinsu mai suna Anwar yace kwarai kuwa *NASS* Nasan ka da idon gane gane Dan Allah taya ya kake gane mace mai tes yaya sirrin yake ne Abokina ?

"Mikewa yayi yace babu Wani sirri baiwace kawai Allah yayi min kasan na karanchi mata kala kala So ganesu bazai min wata wahala ba son danake musu ne ma yasanya na tsaya na yi karatu a Kansu!
Yace bara in yi Wanka nafito mufi ta Yau A kwai casu sosai yafada gami da dukan kafar "Anwar din yana dariya!

Abdul latif dake zaune yana kallo bai tsoma baki n sa ba cikin maganar tasu sai yanzu yace Wallahi
*NASS* Karage So mata wai kai baka gajiya da yin sex kullum turawa sun 6ataka Allah zan fadawa dady Abinda kake shukawa a bayan fage kai ko gudun cuta ba kayi!

"Kai Dan Iska rabu dani yaruwarka ko tawa An so matan nace an so matan shikkenan sai in zauna spam ya kashe ni bazan je in zubar ba kaje kafadawa dadyn din in yaji yayi min Aure kowa ya huta!
Yafadi hakane sabida yasan dady nashi bayason yayi mishi Aure yanzu a cewarsa sai yakara hankali tunda yanzu dai shekarunsa 24 so yake yayi kamar 27 sannan yasan ya fuskanci yaruwa kwata kwata dadyn shi basan yana bin mata ba yafi gazgata Dan shaye shayen da yakeyi Wanda A halin da ake ci yanzu yake yaqi da ya rabashi dashi!


Abdul latif dai yaron kanin dadyn *NASIR* Tare suka taso dashi ya girmi Nasir din da "yan watanni Amma bazaka taba cewa ya girmeshi ba domin shi mai karamin jiki ne yayin da Nasir yake do go ga tsayi ga qiba Amma ba sosai jikinshi a murje kyakyawane sosai Mayan kananun kaya da manyan takalma sosai in ka lura da wuyanshi har wata sakarka ce siririya ta gwall a makale Askin kanshi kuwa "'irin na Mawaka n kan kasar America ne yayi wani tozo a tsakiya gefe da gefe a aske anyi mishi wani irin Aski "yan yatsunshi kuwa wasu manya manyan Azirfa ce masu bala'in tsada Wanda a kai musu a do da daimon a jiki
Haka yake matsewa cikin kananun kaya dake bashi da rama wataran in ya yi wata shigar sai ka rantse da Allah 2pac ne tsowon Mawaqin nan na kasar A America idan "yan wulakanchin na kusa dashi dashi kuwa har Dan kwali yake dauraw(Ban Dana)
Yasa wasu Uban safunan Hannu in kaganshi sai ka rantse black America ne domin kwata kwata baiyi kama da "yan Najiria ba!

*WANNAN KENAN*


Abdul latif yace dukana zakayi ne naga kana wani zabura!!


Tsaki yaja yana yayi masa banza ya maida idonshi kan su Anwar yace"guys ku jirani Dan Allah in fito Ku rabu da wan can mashiriricin!!!



*MUJE ZUWA*




*MRS AHAMAD GWADABE*
[23/04, 14:55] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—



*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*πŸ…Ώ4*


Babu Abinda Abdul latif yace masa Dan inda sabo yariga yasaba da iskancin Nasir!

Ya kalli su Anwar da Abbas yace wallahi Ku lura da dunyar nan naga kwata kwata Ba kwa wannan lissafin duniya fa Ba matabbata ce kuma duk Abinda ka shuka shi zaka girba Ku dinga Sara kuna duba bakin gatari duk Abinda kayiwa Dan wani to tabbata sai an wa naka!!

Nunashi da hannu sukayi suna dariya Abbas yace Malam Alaramma wa'azi kake mana ne kome kai fa kafiye Takawa nuna ma tsoron Allah zakayi kome?
Sunayi suna masa dariya tamkar sun samu mahaukaci sabon kamu!!

Girgiza kai kawai Abdul latif yayi yace ai duk kunyi Nisa bazaku ji kiran da nake yi muku!

Kai ya sayyadi A ramma ya isa haka Dan Allah cewar Anwar yaciga ba dacewa babu ruwanka damu ka wai ido ne naka Dan iska kawai munan dashi zai biyo sawunmu Amma yanzu yazo yanawa mutane wa'azi waishi mai tsoron Allah Mtssssssss!!

Mi kewa Abdul yayi domin fita yace Allah ya ki yayeni kuma da kukeyi Allah ya shirya minku babu India zan biku yawon iskanci Allah ya kiyaye hanya yayi ficewarsa daga falon!

Yana Fita Suka kyalkyale masa da dariya gami da tafawa Anwar yace dubeshi Dan Allah wai shi ustaz zaka biyo sawumu ne ai!

A haka Nasir yafito ya samesu suna tai wa Abdul iskanci!


Cikin wani irin taku Nasir din yakaro so inda suke yana wani irin Abu irin nasu na birni !!
Da sauri Anwar ya dunqule hannusa suka dinga wani irin Abu da hannuwan nasu shi da Nass din suna Dariya hade da dukan kafadun su!!!

"Abbas yace Kai Nass yaushe kahada wannan Wanka kwata kwata bansanka dasu bah!
Kaga yadda kayi kyau kuwa "Hande some "Lailai yau zaka hada go sulow mutumina!!


Yana Wani irin Abu irin nasu na nigogi gami da gyara wani tabkeken Agogo dake daure a hannusa mai bala'in tsada yace waddanan kayan ai sun Dade a ajiye ka wai banyi Amfani dasu bane!

"Kayi kyau sosai dole in kar6i kayannan nima in maqala "kasan Mutumi na ne 50 Cent na Lura shigarshi ka hada!!

Dariya Nasir yayi yace kwarai kuwa ni har yanzu duk mawaqr A America bani da gwani kamarshi kasan ya'iya raff"hippo)

Abbas yace a ganinka Ba!


Wasu Riga da wando ne jikin Nasir wandon iya gwuwa ne wani burgujeje yasha a do ajikinshi birjik da Alji wuna gaba da baya rigar kuwa me kamar vest ce mai kauri da yankakken hannu itama burgujejiya da photon wani tsohon mawaqin kasar America 50cent a jikinta tafkeke sai wasu iyayen sarkoki a wuyanshi sai sheqi suke da Wata shigiyar hana sallah mai bala'in tsada da yasa a kansa!

Humm Fadin tsadar takalimin da'ike sanye a qafarsa bata lokaci ne totally in zaka lissafa kudin wannan kwalliyar Nasir sun tassama dubbannin daruruwa domin shi kanshi takalmin ya kai dubu Dari da hamsin!!


"Cikin Nishadi suka Fita daga part din nsa ya sanya key ya kulle!!

Wata Shegiyar mota suka Nufa samanta a bude kalarta jace sosai tayi masifar haduwa dagani sabuwar zuwace domin bata baza gari Ba gashi dagani sai an sanya kudade masu nauyi za'a mallaketaa!!

Zama sukayi ciki kana Nasir yatashi motar hade da sakin waqar Mawaqiyar nan (Rihanna) tuni Harabar gurin ya karade da dukan sifiqa ji kake duff Duff!


Da Sauri Malm Yau mai gadi yatashi domin bude get ganin yadda Nasir ya fafaro motar kamar zai tashi sama!

Tana Zaune kan bai n ci kamar ko da yaushe takan fito ta zauna kusa da mahaifinta ta Dan tayashi hira!

Tunda ga Fitowarsu Nasir har shigarsu mota bata dauke idonta daga Kansu Ba tanajin wani irin mugun bakinciki ganin yadda suka yi shiga kamar Ba "ya"yan musulmai Ba
Ran tane yabaci ganin yadda Mahaifinta ya mike yana rawar jiki domin bude musu kofaa"

Daga yau ta dauki Alkawarin mutukar tananan bata tafi skull ba zata dingaa bude musu get din!!!


*MUJE ZUWA*πŸ’‹
[23/04, 14:55] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—



*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)


*πŸ…Ώ5*


Malam Ya'u nata kici kicin bude get da Sauri ta Mike takarasa gurin tafara kokarin tayashi budewa!
A tare suka bude get din ita dashi sannan ta matsa gefe guda tana Dan sauke nuffamfashi domin dai get din bana wasa bane!!
Abin Mamaki motar taga ta tsaya Nasir ya zuge glass din motar Fuskarsa a sake ya Mikwa malam Ya'u hannu yace Arrama barka da Safiya"
Shima malam Ya'u hannusa ya mikawa Nasir din cikin Mutmchi suka gaisa Malam Ya'u yace za'a fita ne Nasiru Don Allah A kula da duniyar nan ka rike sallah ka dinga yi kan lokacinta duk Abinda kake idan lokacinta yayi kabari kaje kayi!

In da Sabo Nasir yasaba da Wannan surutan da Malam Ya'u take masa indai zaifita sai ya tsayar dashi yana masa Wasu maganganu a cewarsa"

Dariya Nasir yayi kadan yana satar kallon inda take tsaye tayi Saurin dauke kai domin kwata kwata baya San su hada ido da yarinyar Sabida idonta kamar na mage ne kwayar idon blue yarinyar Kamar wata Al'jana Shiyasa in zasu hadu sau dubu baya gangancin kallonta Dan wani Sa'in in ya hada ido da'ita kwana yake da yini gabanshi na Faduwa yarasa gane wace irin Masifa CE wannan Shine dalilin da yasa ya daurawa yarinyar karan tsana!!

"Yace karkar kadamu Arrama zamu kiyaye in sha Allahu A cigaba da Addu'a yafada yana kara tashin Motar a karo na biyu!!

Malam Ya'u ya matsa gefe yabashi hanya yana daga Masa Hannu tare da yimin shi Addu'oi iri iri gami da Fatan Alkairi!


Ranta A mutukar 6ace taje ta zauna kan bainci tana zumbura baki!

Ma Haifinnata yazo ya zauna kusa da ita yace yaya A kayi ne Yarinyar kirki kina yimin magana banji Ba Mai A kace a siya a Makarantar!?


"Cikin Shagwaba tace wallahi Baba ina tausaya Maka in dai nayi kudi sai ka bar wannan Aikin qaskancin da kake yi zan sai mana gida mutashi daga Wannan!

Dariya Malam Ya'u yayi yana girgiza kai yace ta yaro kyau take bata karko Allah ya Amsa Addu'ar ki Maryam zan fison haka nima !!
Amma kisani Babu Abinda Alh' Huseen Zai nema ban mishi Ba A rayuwata Sabida mutum ne shi Dan Halak tun kafin A haifeki yayi min Hallicin da bazan ta6a man tawa Ba a rayuwata!!


********************
Asalin Malam Ya'u Malam Yau dai haifaffen kasar kamaru ne Ba fulatani ne tsantsan ko a can kasar tasu a cikin qwauye suke sosai shiyasa ko Kalmar A! Da Hausa basu sani bah!!



*MUJE ZUWA*
πŸ’‹πŸ’‹



*MRS AHAMAD GWADABE*
[23/04, 14:55] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—



*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*πŸ…Ώ6*



'A zahirin Gaskiya ya'u suna fama da kanta ta talauchi sai a wayi gari su rasa Abinda zasu saka a bakin salati ga mahaifinsa karfinsa ya qare shannusa da yake kiwo dasu duk ya kadar da wasu duk domin Asirinsu ya lullubu mahaifiyarshi ya Findu tana da lalaura ta rashin gani gashi kurma ce bataji sosai sai anyi magana da kyau sannan!

Tare suke fadi tashi da Maihafinsa da sauran "yan uwansa har ta kai takawo suka hana maihafin nasu fita kiwo sabida girma da yafara kamashi rannan suna tafiya shida "yan Uwansa ya kallesu yace cikin fillanchi nifa ina tunanin in bar garin nan zan fita nema ko Allah zai sa a dace Amma ina tunanin fadawa Baffah Ba lailai ne ya yadda bah"


Wani yayan shi jibo yace kayi tunani mai kyau Ya'u kasamu baffa kayi masa bayani watakila ta Amince kasan Arzikin bawa baya wuceshi kila wani Alkairin ne yake kiranka!
Yaci gaba dacewa kai yanzu idan kabar nan wane gari zaka tafi ko in ce wace kasa kake son zuwa domin naiman kudi!

"Ya'u yace zan tafi Najeria ne kawai naji Ana cewa cibiyar kasuwanchi ce mussaman wata jaha a cikin jahohin Najeria mai suna Kano naji su "Ilu suna fadin Wai ko baka da ko sisi kashiga wannan jahar zaka samu Alkairi sannan zaka SHIGA kasuwanni kasan cewar tanada manyan kasuwanni zaka shiga kayi buge bugenka babu mai hanaka in kanada rabo sai kasamu uban gida da zai tallafa maka har ka tsaya da kafafunka" duk cikin fillanci suke magana!


Babban cikinsu yace kayi dabara nima sai naji ina sha'awar binka to Amma mu muna da iyali baza mu tafi gari yagari kamar wannan Ba mubarsu wqzai kular mana dasu da iyayenmu kai din dai dama dabaka da Aure kai Yagi ldacewa kaje din zan samu Baffah in yimasa bayani Sosaoi"
Ya'u yaji dadin qarfin gwiwar da "yan Uwansa suka bashi yayi ta Farin ciki sosai!!



To koda Jibo yafadawa baffah qudirin Ya'u nabarin kasartasu ta gado Abin mamaki basu Sha wata wahalar shawo kanshi Ba yaAmince yace yaji dadi da hakan Allah yasa Alkairi ne yake kiransa yace dasu suka shanu biyu a kasuwa domin a bawa Ya'u kidin guziri da Abinda baza'arasa Ba Abinda yayi saura a hannushi sai yafara Sana'a ko ta turawa a baro ce!!



Batare da bata lokaci bah a kasiyar da Shanu a kahadawa Ya'u kudi ranka ta kaff Ana jiran ranar tafiya

A kwai Abokinsa ilu tare zasu tafi ilu yadan fi Ya'u wayewa yanaji Hausa kadan kadan kasancewarsa mutum ne mai kurda kurda Ba Lamar Ya'u Ba ya kanshiga cikin kasuwannin cikin garinnasu yayi buge bugensa to A nan yake Dan tsintar ya rirrika daban daban!


Allah buwayi gagara Misali kamar jira a ke su Ya'u subar wannan kauyen nasu Annoba ta sauka a garin ta Ambaliyar ruwa Wanda ta tafi da bukkokin Al'uma gami da rayukan jama'a Wanda kafatin dangi da iyayen Ya'u suka shafe kamar babu su a doran duniya Ruwa ya tafi dasu

*inna lillahi wa'inna ilaiyi raji'un*


*MUJE ZUWA*



*MRS AHAMAD GWADABE*
[23/04, 14:56] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾

πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—



*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*πŸ…Ώ7*



Lokacin da labari ya iski su Ya'u sun shiga halin dimuwa da tashin hankali To haka suka hakura suka fawwalawa Allah domin ko dasu kayi yunkurin koma grain nasu mutumin da yakawo musu labarin faruwar hakan yace ko sunje babu wanda zasu samu domin qauyen ya shafe waddanda suke da shauran shan ruwansu a duniya suna gadon Asibiti sannan gwamnnatin kasar tana Aiki a gurin!

Haka su Ya'u suka hakura suka cigaba da yiwa "iyayensu da "yan uwansu addu'ar samun rahamar Allah suka cigaba da yawon buge buge cikin kasuwanni kafin Hausa ta zauna bakin Ya'u sai da aka yara sannan yafara ji da mayarwa Sukafara harkar sai da ruwa (garuwa) suna bin Unguwanni sun samu Alkairi sosai da sosai suka samu suka kama hayar shago suna kwana ciki shida ilu rannan ilu yace mai zaihana mu shiga kasuwa ne da waddan kudin da muka Tara da na hannunka sai mu sari takalma murinqa turawa ko a baro ne! Ya'u yace hakan yayi kyau gobe idan Allah ya kaimu sai mufita da Wuri! Allah kasa mufara Asa'a
Allah mai iko A kwai wasu "yan shayeshaye dasuke makalewa jikin katangar gidan da su Ya'u suka kama hayar shago Ashe sunji duk Abinda suke cewa suka biyo dare suka kwashe kudin nan tas sai wayar gari sukayi suka babu kudi inda suka'aje Neman duniya basu gansu bah
*innalillahi wa'inna'illahi raji'u*
Kuka wurjajan ilu yake yakasa daurewa!
Shi ko Ya'u na zucci yake yana tabawa ilu hakuri Amma ina ilu yaki yin ta wakkali!!


Ilu yana kuka yace yanzu kai Ya'u wakake tunanin zai sace mana kudin nan naga kamar bakadamu Ba wai kai ko da hadin bakinka aka sace mana kudine!

Cikin Mamaki Ya'u yake kallon ilu yace haba ilu wannan wace irin magana kakeyi kudinka fa basukai yawan nawa kudin fa dawa kake tunanin zan hada baki wana Sani a nan garin Dan Allah kacire wannan zargin cikin zuciyarka!



Ilu yace babu wani zargi Ai gaskiyace gashi nan baka damu Ba kamar yadda na damu to waye zai shi go yayi mana sata tunda dakin A kullle yake wallahi Kaine ka dauke ko kasa a dauke sai bayan kwana biyu kafito dasu kace tarawa kayi!


Wani bakinci da bacin rai ne yakama Ya'u ganin yadda ilu ya hakikance yana shirya masa qazafi domin shine zai zargi ilun a kan sace kudin in hakane sabida nasa kudin sun nunka na shi yawa Amma dubi Abinda yake fitowa daga bakinshi Dan rashin tawakkali!!




*MRS AHAMAD GWADABE*
[23/04, 14:56] +234 808 996 5176: πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—
*🐾YARO DA KUDI*🐾
πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—πŸ΅πŸŽ—



*✍🏻WRITTEN BY*
Binta Umar
(MAMAN ABDUL WAHABU)



*πŸ…Ώ8*


Haka ilu ya kwana yanawa Ya'u bala'i gami da bakaken mangaganu karshe Dai Ya'u da yagaji shima yafara mai da martani ganin cin mutuchin da Ilu yake masa


Haka suka cigabah da rayuwa babu mai kula da Dan uwansa in gari ya waye ko wanne zai fita har kokinsa gurin kwanciya ne kawai duke haduwa Ilu ya dauki Ya'u da gabah sosai yayinda Ya'u yake bin sa sannu sannu yana mamakin halin ilu na rashin tawakkalinsa Yana masa magana shi domin yafi shi hankali!


Wataran Ya'u ya fito da safe domin tafiya cikin kasuwa sabida sun kwana da Aiki Sauri Sauri yake tafiya Cikin tsautsayi Yazo tsallaka titi wata mota ta kunnu kai ta yi gabah dashi!


Cikin Sauri Mutumin dake cikin motar ya fito cikin tashin hankali yana wa drevar shi fada yace Na Hana irin wannan tukin ganganci Nura wai mai yasa kake yin haka

Kafin Alhji huseen ya karasa gurin tuni Nura Drever ya je yadaga Ya'u yana masa sannu gami da duddubah jikinsa
Alhji ya karaso gurin yana fadi kamashi mutafi a sibiti a dubashi kana Neman ka jawo mana wanin tashin hankalin"


Ya'u ya mike da kafafunsa yana karkade jiki yace babu ciwo a jiki Alh kuyi tafiyarku haka nagode yafada
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On YARO DA KUDI
avatar
magaji-2

4 months ago

Reply

Allah Yakara budi

Please Login or Register in order to submit comment