Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ba.
"Delu tayi murmushi tace sojan kenan hajiya komai nasu ai daban...

"Abba na zaune yana kallon program din good morning Nigeria a NTA Haidar yayi sallama ya shigo, Abba ya amsa gamida maida dubansa ga Haidar...
"Gefen Abba ya zauna a 'kasa kana ya gaisheshi....
"Har an gama fushin ne? Abba ya tambaya..
"Murmushi Haidar yayi gamida shafa sumansa kana yace" a'a Abba ai dama ba fushi nake ba, hukunci da kuka yanke yayi daidai Abba inshaa Allah zaku sameni ina maiyi maku biyayya....
"Wani sanyi ne ya ziyarci zuciyan Abba kana ya shafa kan Haidar yace" Allah yayi maka albarka Aliyu yanda kayi mana biyayya Allah ya baka yaran da zasu maka kaima..
"Ameen Abba " ya fa'di a ta'kaice....
"Nan Abba ya fada masa duk yanda tsarin abin yake Haidar ya nuna yayi na'am.
"Ya btun aikin naka yaushe ne dama zaka koma...
"Gobe nake son komawa dan munada tafiya a satinnan.

"Shiru Abba yayi kaman mai nazari kana yace toh ya batun daurin auren naka bazaka samu halarta ba kenan ko 'ka'aka...
"Eh Abba ai babu matsala za'a iya daura auren ko bananan.... zan turawa Anty Hiba kudi ta account dinta saita saya lefen...
"Abba yayi murmushi kana yace Allah maka albarka... toh ya batun tafiya da matar taka kaga next week zasu rubuta final examz dinsu...
"Saida Haidar yaji wani dumm da Abba ya ambaci Hanifa da matarsa, ya dan sosa kai kana yace babu matsala Abba sati uku kawai zanyi na dawo idan na dawo sai muga yanda abin zai kasance....
"Sosai Abba yaji dadin yanda Haidar ya kwantar da hankalinsa ya nuna masa ya isa dashi, haka suka dan ta'ba hira kafin Haidar ya mike ya fice zuciyarsa cike da tsanar Hanifa, ya dau awashin sai ya saitata bisa hanya....
"Washe gari Haidar ya 'daga zuwa Lag....

"Su mamy kam shiryeshirye suke kan yi Anty Hiba kuw abun ba'a cewa komi, bata sama bata 'kasa tuni ta iso kano kullum tana kasuwa ana sayayya.
"Yau suna zaune ita da mamy hira suke wanda ya shafi bikin.
"Nifa sai inaga kaman bamuyi ma Hanifa adalci ba ya kamata mujira muji ta bakinta dan ballaline wannan hukunci ya mata, sannan ko kadan dama jinin Hanifa da Haidar kwatakwata bai jutuwa, beside sai inaga tayi karama ma aure gaba daya tausayinta nake.... mamy ta fadi sanda take duban Hiba.
"Anty Hiba tayi shiru kana tace "mamy ki rika kyautata zato inshaAllah wann aure zai jure zai zame mana abin alfahari nan gaba, dama wuyanta na miji ya amince ne mace kam nata mai sauki ne, sannan a hankali sai kiga sunso junansu.. mudai fatanmu Allah ya tabbatar da alkhairinsa.... ameen sukace gaba dayansu....

"Duk wann bidiri da ake Hanifa na can sch suna rubuta jarabawa babban burinta kiwa bai wuce ta fita da sakamako mai kyau ba dan farantawa iyayenta....

_Friday 5th June_
Yayi daidai da ranan da aka daura auren Haneefah da Aliyu Haidar a babban masallacin central mosque bayan saukowa daga sallan juma'a, hakan kuma yayi daidai da rananr su ta 'karshe na rubuta jarabawan kammala sakandari... mamy kam tasha kuka wanda ta rasa kukan na farin ciki ne kona akasin haka.

👸🏻Queen Samy😍💄💋.........
[5/9, 6:18 AM] 🌹 Muhammad🌺kabeer🌹: 🌹🌹🌹 *Mijin Haneefah*🌹🌹🌹
15

Tun kafin su iso gida take murna yau zataga mamynta duk ta ishesu a motan banda zumu'di bata komai.
"Sumy tayi gyaran murya tace Hany are you sure BUK kike so, kai nikam gaskiya I preferred ATBU shinema first choice dina.
"Wa nifa kinsan bazan kuma yin nesa da mamy ba, from now on nothing will tear us apart. We will always be together.
"Shema daketa duba slumbook dinta sai lokacin tayi magana " lallaima kid sis and does that mean zaki zauna da mamy for the rest of your Life, what about if you get married, are you going to live together with her and the husband....
"Gajeren tsaki Hanifa tayi kana tace " Com'on sis Shema there you go again, da zaran anyi magana saiki kawo maganan aure wa mutum, and who told you ni auren nake sonyi....
"Eh mana she's right baby sis Sady ta fadi.... yatsina fuska Hanifa tayi snn tace" whatever!....

"Tarba na mussaman mamy tayiwa girls din nata, murna a wajensu ranan ba'a bayani, Inna kam baki ya kasa rufuwa ranan gaba daya jikokin nata sun girma sun zama 'yan mata sosai.
"Suna can sashen Inna suna zuba surutu Abba ya dawo wai zo kaga murna wajen girls din mamy haka sukaje suka ri'ka zuba masa shagwaban da suka saba shi kuwa sai biyesu yake dama yayi missing hakan. Mamy kam gaba daya batada walwala wani mugun tausayin Hanifa takeji. Walima maiji da lafiya Abba da mamy suka shirya masu, omo com see pretty ladies😍. Abun sai wanda ya gani....

"Babu yanda Abba beyiba a sanar da Hanifa maganan aurenta amma fir mamy ta'ki haka tayita rokon Abba ya dakata tukunna, a cewan ta ya dan kara lokaci bata gama shiryawa ba...

_Two weeks later_
"Kwanakin nan duk haka mamy keyin su cikin zullumi, ko kadan Hanifa kam bata kawo komi ba, su Shema kam suna son gano wani abu dan rannan sunji Inna da mamy suna maga kaman kuma akan Hanifa ne, Inna tana cewa gwara a sanar da yarinya tanada aure yanzu, mamy kuma na rokon Inna a dan kara mata lokaci dan bata son Hanifa tasan cewa ba itace ta haifeta ba....
"Toh tambayan a nan shine SU WAYE IYAYEN HANIFA SANN AURE AKAYI MATA? toh idan kuwa hakane SHIN WANENE *MIJIN HANEEFAH* wannan tambaya shine ya tsaya a ransu...

"Mamy da Anty Hiba zaune can kuryan dakin mamy, mamy tayi jigum abun duniya duk ya isheta. Anty Hiba ta rike hannun mamy tace pls mamy ki bari a fadawa Haneefa kafin Haidar ya iso gari... Girgiza kai mamy ta soma hawaye na bin kuncinta tace no Hiba noo... banyi shirin ganin irin wann rana ba, ban shirya cewa Hanifa am not her real biological mother ba. She's my daughter she's my child. ?. Kuka sosai ya kufce mata, Anty Hiba ta share kwallan daya zubo mata snn tace " you will always be her mother mamy, you're her mother pls lets end up this'boye 'boye sooner or later she will learn the truth. Snn akwai auren Haidar a kanta so dole a sanar da ita..... daidai nan suka bude kofa suka shigo su ukun "Shema'u Sadiya da kuma Sumayya... kallon kallon suka shig yiwa Anty Hiba da Mamy. Tabbas sunji komai take idanunsu ya ciko da kwalla.
"Shema ce tayi karfin halin cewa "Mamy wacece Haneefah sann YaHaidar shine *Mijin Haneefah*? Anty Hiba ta mike ta riko hannayensu kana ta tura kofan dakin ta rufe, zaunar dasu tayi bisa carpet gaba daya suna fiskantan mamy da Anty Hiba...
"Mamy ta goge hawayen idonta kana tace a yau zan fayyace maku sirrin daya jima a binne sirrin dabuku san dashi ba... gaba daya suka zubawa mamy ido suna saurarenta......

👸🏻Queen Samy😍💄💋.......
[5/9, 6:18 AM] 🌹 Muhammad🌺kabeer🌹: 🌹🌹🌹 *Mijin Haneefah*🌹🌹🌹
16 and 17

"Mamy taci gaba da fadin, shekaru goma sha takwas da suka wuce Allah yayima iyayenmu rasuwa nida 'yan uwana guda biyu tak Deena da kuma Hiba. Tun bayan rasuwan mahaifanmu rikon deena da hiba kannena ya dawo hannuna a lokacin ni kadai keda aure cikinsu dan nice babbarsu dama.
"Mahaifinku yanada 'kani guda daya tak a duniya me suna Umar, Umar na yawan zama a gidan wansa wani sa'in yana gidan Inna toh a haka ne har Allah yasa suka fahimci juna shida deena har ta kaisu da aure, lokacin da akayi auren kuwa Umar ya samu aikin banki a meduguri dan dama ya kammala karatunsa. Haka akayi biki aka kai amarya dakinta can meduguri. Shekara guda da aurensu deena ta haifo yarinyarta kyakywa wacce ta shiga ran jama'a da dama aka sanya mata suna Haneefah. Haneefah ta kasance 'yar lele wajen iyayenta da dangi baki daya. Lokacin da takai shekara daya da rabi deena da umar suka yanke shawarin kawo nan kano wajena dan in yayeta. Hakan kuwa akayi, tunda suka kawo mun Haneefa na hadata da ku soyayyanta ya shiga raina har inajin sonta fiye da 'ya'yan da na haifa hakan ne ta kasance a wajen Abbanku ma. A wann lokaci kunada shekaru biyu a duniya yayinda 'Danmasani yake dan shekara uku yayanku Haidar kuma yanada shekaru gomasha daya a duniya, snn cikinku shi kadai ne yasan wnn labari da nake fada maku a yanzu dan kuwa shine yayi girman da zai sani.
"Rana da Hanifa ta cika sati biyu a wajena a ranan sukayi shiri cikinnzumudin zuwa 'daukan 'diyarsu..... kuka ya kuma kufce wa mamy saida tayi mai isanta kafin ta tsagaita kana ta ci gaba.... " zuwan da basuyi ba knn ganin 'diyarsu da basuyiba knn dan kuwa a hanya suka hadu da mummunan ha'darin mota wanda yayi sanadiyan rasa rayukansu....... kuka ya kuma kufce wa mamy yayinda Anty Hiba dasu Shema suke tayata....
"Tundaga wann lokaci mukayi alkawarin rike Hanifa tamkar mu muka haifeta tinda dama abinda yayita shi yayimu baki daya saidai yanzu ya zama dole tasan labarin asalinta dan kuwa a halin yanzu Haidar yayanku shine mijinta, shi kadai ne zai iya rike mana amanrta shida Hanifa duka abu daya ne.... ta rungumo hannayensu snn taci gaba da fadin Hanifa kanwarku ce, First Cousin dinku ce nida mahaifiyarta uwanmu daya ubanmu daya haka nan mahaifinta da mahaifinku iyayensu daya. Har a yanzu babu abunda zai canza tsakaninku.... Sosai su Shema ke kuka dan kuwa ko kadan basu taba kawo hakan a ransu ba... a hankali Sadiya ta mike tana share kwallan idanunta dan kuwa mugun tausayin Hanifa ne ya dira mata, ta sani ko kadan yaHaidar da Hanifa basa jituwa balle ace an masu ure zasu zauna gida guda matsayin miji da mata, tana bude kofa tayi tozali da Hanifa wacce ta durkushe a wajen tana kuka maras sauti alamun taji komai... da sauri su Shema suka karaso basu iya cewa komi ba sai rungumeta da sukayi suna kuka mai tsuma rai, Anty Hiba da mamy ma kukan suke... kusan minti babu wanda ya iya bawa dan uwansa hakuri gameda kukan da suke yi.
"A hankali ta goge hawayen idanunta ta karaso kan carpet yanda mamy ke zaune, zama tayi kan gwiwoyinta ta riko hannu mamy gam cikin hanunta, mamy kam kasa hada ido tayi da ita saima kallon gefe da take yi, a hankali ta soma furta.
"Mamy mamy na dan Allah ki kalleni mamy na, kice mun kece mamyna kinji mamy I love you mamy..... gaba daya kuka ya kufce masu Hanifa rungume mamy tayi tana kuka me tsuma rai mamy ma kukan take.
"Da kyar mamy ta iya saita kanta kana ta soma fadin "we're so sorry daughter ki yafe mana nida Abbanki na boye maki wann sirri har na stawon lokaci, it was never our intention to hurt you, we did this because we do love you dear. And maganan aurenki da Haidar idan baki so dole a warware shi kinji swthrt.... girgiza kai Haneefa ta soma yi kana tasa tafin hanunta ta rufe bakin mamy snn tace "mamy dan Allah ki dena bani hakuri ni kun gama min komai keda Abba banida abinda zan saka maku dashi nan gidan duniya sai addu'a, mamy ban ta'ba kukan maraici ba hasalima ba santa ba, kun nuna mun so fiye da 'ya'yan da kuka haifa kun rikeni bisa gaskiya da amana Allah ubangiji ya saka maku da mafificin alkhairi..... ta 'danja fasali kana taci gaba da fadin "aurena da yaHaidar kuma.. sai ta danyi shiru kana tace "mamy ku kuka fi cancanta ku za'ba mun miji na gari, Allah yasa hakan shine mana alkhairi..... kuka take sanda ta kifa kanta bisa cinyan mamy..
"Allah ya maki Albarka daughter Allah baki zaman lafia me daurewa a gidan aurenki Allah kema ya baki yaran da zasu maki biyayya yanda kika mana, mamy ta fadi sanda murmushin farin ciki ya mamaye fuskanta...

"Can dakin Inna ta tafi ta kwanta tunanin rayuwan dake shirin tinkaranta take, yaHaidar ya tsaneta fiye da komai a duniya, itama ta tsanesa bata kaunan koda ganinsa ne amma ya ta iya bazata iya watsawa su Abba kasa a ido ba mutanen da suka zame mata sutura a rayuwa.... tana a haka 'yan uku suka turo kofan daki take ta rufe idonta kaman me barci gaba daya tausayin Hanifa suke sosai dan haka suka fice suka bart tayi bacci, suna fita wani sabon kuka ya kufce mata shiknn yanzu zata rabu da 'yan uwanta, 'yan uwanta da suke tare koda yaushe dare da rana safe da yamma, ta goge hawayen idonta sanda Inna tayi sallama ta shigo.
"Abinci ne a plate Inna ta shiga lalla'bata taci, fir Hanifa ta kasa cin abinci inna tayi tayi haka Anty Hiba ma duk taki saida mamy tazo da kanta snn ta samu ta saka wani abu a cikinta..
"Washe gari Haidar ya iso gari bayan Abba ya masa tuni kan magann su, shi kam gaba daya ya mance da wani aurwn Hanifa a kansa, abu daya yake tunawa yayi murmushi shine zai koya wa Hanifa hankali zai saita tabyanda bazata kuma kodankallon banza bane wa mutane balle har ta kaita ga masu rashin kunya...

"Jere na gani a fada Abba yayima Hanifa a gidanta na Kano, babu yanda su Shema basuyi ba kan Hanifa ta yarda a danyi koda walima ce amma fir taki, gaba daya ba isheshen lafia bane ma da ita, tunda yaHaidar ya iso gari dir taki su hadu.
"Yau tana zaune bayan Anty Hiba ta tilasta mata shan pepper soup, haka ta sha kadan duk jinta take batada appetite yayi sallama ya shigo.
"Take gaban Hanifa ya shiga dukan taratara, Anty Hiba ce ta iya amsa sallaman kana Haidar ya shigo yana sanye da jampa blue da hula zanna bukar, sai kamshin Dolce n Gabbana ne ke tashi ajikinsa.
"Woh wann wani irin angone da bazai bari a kai masa mayarba sai yazo ya dame mutane, cewan Anty Hiba teasingly.
"Murmushi Haidar yayi hannunsa na nade a kirji kana ya saci kallon Hanifa da gaba daya ta kasa daga kanta sai faman bin plate din hanunta take da kallo. Anty Hiba ta mike tace toh maza kasata taci tunda ka shigo, sai snn Hanifa ta dago kanta tana duban shi amma me, wani mugun faduwan gaba taji tayi saurin sunkuyar da kanta. Daga haka Anty hiba kam ta fice abunta.
"Hanifa kam kiris ya rage numfashinta bai daukeba dan tsoro, Haidar yayi taku kadan ya karaso gabanta. Kallonta yake dan rabonshi da ganinta yakai 2yrs.
"Kwanto da kanshi yayi daidai saitin kunnenta take ta soma ja da baya dan kuwa 'bari jikinta ya soma, yayi murmushin cin nasara kana. Ina zakije ko kin mance mijinki ne a gabanki abinda ya fada knn cikin dakewa.
"Bata fasa matsawa ba saida ta isa kuryan gado, kafa yasa ya take kafanta wanda ya hanata karasawa karshen gadon, dukda zafinnda taji hakan baisata uffa komi ba sai hawayen dake kokarin ciko idonta.
" hannu yasa ya cire hijabin dake jikinta, take ta shiga rike hijabin tana fasin "dan Allah yaHaidar kayi hakuri.... Shiii! Ya daura hannu a bakinshi alamun tayi shiru ya karasa cire hijabin ita kam Hanifa rumtse idonta tayi ga kirjinta dake barazanar tarwtsewa, 'yar karamar rigace a jikinta wanda ya nuna komai na jikinta, take yaji bezai iya jure kallonta a haka ba, dan kuwa wani irin yarrr yaji gaba daya illahirin jikinsa, tasa hannunta ta shiga kare kirjinta... tsaki yayi gamida jefa mata hijabin jikinta yace" meye kike boyewa a wajen, kina tunanin kinda abinda ni Haidar zai burge ni ne, never. So nake na fada maki ki shirya zama a gidan yari dan kuwa na tanadar maki rayuwa mafi kunci a gidana, mayya idan banda mayya dasu Abba suka tambayeki ko kinason auren ai ce masu zakiyi baki so, amma dashike ke mayya ce 'yar 'karama dake kina son sanin namiji shine zakice masu kin amince, yayi wani murmushin mugunta kana yace "this is the huge mistake you made, I'll make your life so miserable ta yanda sai kin tsane rayuwarki. Is not too late for you little Brad zaki iya zuwa kice masu baki son auren, am just warning you kar kiyi mistake din zuwa gidan Haidar idan kunne yaji jiki ya tsira. Daga haka ya fice zuciyansa fes...
"Kwanciya tayi bisa pillow din dake gefenta ta shiga rusa kuka me tsuma zuciya....

"Washi gari idanun Hanifa duk sun kumbura saboda kuka, Anty Hiba ta gama hada mata kayanta da wasu turarruka da ta hada mata, dan jirgin karfe 12:00pm zasu bi,
"Tana zaune gefen Abba a kasa bayan ya gama mata nasiha da fatan alkhairi tare da saka mata Albarka, Haidar yayi sallama ya shigo parlorn, saida zuciyanta ya tsinke da jin sallaman yaHaidar shiknn da gaske ne zata tafi ta bar su mamynta.
"Haidar ya karasa ya gaida Abba, Abba ya masa nasiha sosai shima kana ya hadasu baki daya ya masu nasiha mai tsuma zuciya. Haidar ya saci kallon Hanifa data sunkuya tana hawaye, murmushin side yayi na mugunta a ranshi yace yarinya bakima yi kuka ba tukunna.
"Haidar ne ya fara mikewa yayi sallama da Abba kana ya fice ya nufi sashen mamy, nasiha mamy ma ta masa sann tace sun mallaka masa amanan Hanifa, Hanifa amana ce a garesu dan haka sun dauki wnn amana sun mallaka masa. Har airport suka raka su gaba daya mutanen gidan idan ka dauke Abba, sosai Hanifa tasha kuka ta rungumesu Shema gwanin ban tausayi, ana fara kiran garuruwa mamy ta rungume Hanifa sanda aka kira garin Lagos Haidar yayi sallama dasu mamy kana Hanifa tabi bayansa tana sanye cikin bakar abaya ta yane kanta da mayadin kayan, haka sukata waving wa junansu har ta shige.....

👸🏻Queen Samy😍💄💋......🌹🌹🌹 *Mijin Haneefah*🌹🌹🌹
18 and 19

"Suna shiga cikin jirgi bayan sun zazzauna kowa bisa seat dinsa aka soma announcing su 'daura belt, Hanifa sai kiciniyan 'daura nata take amma ta kasa. Haidar ya kalleta ta wutsiyan ido takaici ya kuma kama shi even seat belt ma bata iya 'daurawa ba, yayi gajeren tsaki kana ya sunkuyo kansa na gogan fuskanta hannunsu na shafa na juna ya rike belt din, gaba daya saida shock ya ziyarci jikkunansu, kirjinta kuwa yaci gaba da lugude kaman ana daka dan bugu. A daidai saitin kunnenta ya ra'da mata " So dama all this rashin kunya da tsaurin ido naki even seat belt you don't know how to tie it, what a surprise. Yayi wani murmushin mugunta kana ya daura mata seat belt din sann ya gyara zamansa.
"Hanifa kam babu bakin maga dan this is her first time da ta ta'ba shiga jirgi, kuma sarai yaHaidar ya sani kawai dai salon wulakancin sa ne. Lumshe ido tayi kaman me bacci sanda jirgi take shirin tashi kuwa a razane ta hantsila jikin Haidar gamida 'kan'kanme sa ta tura kanta cikin jikinsa, sosai yaji a jikinsa da irin rikon data masa dan kuwa sakwanni ne da dama suka jiyarci illahirin jikinsa.
"Kallonta yake ganin yanda ta wani razana, be ce mata komai ba har lokacin tana nan makale cikin jikinsa wanda ita kanta batasan tayi hakan ba, saida ya bari jirgi ta daidaita a sama kana ya matse 'kugunta cikin jikinsa snn ya kai bakinsa saitin kunnenta a hankali yake ra'da mata " Saurin me kike ne Witch, saboda tsaban son maza irin naki shine bazaki iya bari mu isa ba saikin gwada wa kowa in public you're in need of namiji ko. A razane ta dago tana dubansa nan fa ta tuna ashe a jikinsa take, take ta shiga kiciniyan kwace kanta... matseta ya kuma yi cikin jikinsa kana yace" Saidai kash burinki na kwadayin namiji bazai cika ba dan ni Haidar kam na maki wuya I don't feel anything for you, to me you're nothing but a piece of trash, taba jikina ma da kika yi yanzu ji nake kaman na ganni a gida na samu na wanke jikina dan kar alargy ya feso mun, daga haka ya saketa ya komar da kansa bisa seeat kana ya lumshe idonsa.
" Shiru tayi sai zuciyanta dake mata mugun 'kuna wai shi meye ya 'dauketa da yaketa jifanta da wnn muggan kalamai, hawayene taji na kokarin ciko idanunta take ta shiga karanto duk addu'an da yazo bakinta....

_Lagos_
"Suna fitowa daga Arrival driver din shi ya karaso gamida sara masa yana fadin "welcome sir, gaisawa sukayi kana ya karbi jakan kayansu ya karasa dashi yanda yayi parking mota, bayan ya zuba kayan a boot ya budewa Haidar front sea ya shige dan dama shi baison zama baya kullum a gaba yake zama koda driver ne ke jansa.
"Philips ya budewa Haneefa back seat gamida sara mata snn ya koma mazaunin dreba yajasu zuwa Maritime.

"Sanin yaune zai dawo yasata canca'da ado cikin 'kanan kaya 'yar karamar rigar da bata wuce cinya ba. Tana zaune tana kallo ya turo kfan gamida sallama ya shigo.
"Da gudu Latifa ta 'karasa ta haye jikin Haidar tanai masa oyoyo, Hanifa kam kallon ikon Allah ta tsaya yi da mugun mamaki take binsu da kallo baki sake.
"Oh I miss you dear thank God you're back, da baka dawo yau ba dana bika dan gaskiya I can't help it. Sarai Haidar yasan Hanifa na kallonsu dan haka da gangan ya tallabo ha'ban Latifa ya ri'ko kunkuminta yanda ta manne tsam ajinkinsa sann ya soma fa'din, "I miss you too my Latifa, kin 'kara kyau sosai. Murmushi ta soma da jin kalaman Haidar dan kuwa tunda suke tare bata ta'ba jin ya yabeta ba sai yau bata ankara ba taji yasa bakinsa cikin nata, nan ya shiga aikamata sa'kwannin dake tafiya da ita wani duniya daban.
"Hanifa dake tsaye gefe abun tsoro ya soma bata, take tayi saurin juyawa da niyyan fita kawai ta ture flower vase nan yayi interrupting su Haidar daga duniyan da suka lula. Sai snn Latifa tayi tazolai da kyakywan yarinyar dake tsaye.
"Da mamki ta 'dago tana kallon Haidar kana tace "dear who's this young lady, ina ka samota.
"Haidar ya juya gamida yatsina fuska yana kallon Hanifa like a piece of trash kana yace" Oh this ya nunata da yatsa snn yaci gaba da fa'din she's my maid.
"Ke! Ya daka mata tsawa kana yace baki iya gaisuwa bane.
"Tab'di waye zai gaishe da karuwa Allah ya kiyaye" ta fa'di a zuciyanta.
"Am talking to you jor! Ya kuma daka mata tsawa. Ina wuni ta fadi a dakile, Latifa ta amsa a yatsine tana mata wani wula'kanceccen kallo.
"Guestroom Haidar ya nuna mata kana yace ta kai kayanta can, cikin sauri da kosawa taja trolly dinta ta wuce. Daki ne mai kyau well punished. Luggage dinta ta bude ta dito da kayan ciki kana ta dau towel ta fada bathroom danyin wanka.

DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MIJIN HANEEFA
avatar
aisha-musa

1 year ago

Reply

Please Login or Register in order to submit comment