Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar Gidan tsohuwa_😅)



Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*AM BACK AGAIN BY THE GRECE OF ALLAH*



_Alherin da ke ciki Allah yasadani dashi, shairin dake ciki Allah ya tsareni dashi_
_Muje zuwa masoya ana bugun tare🤝🏻_ *UMMU SAFWAN CE*






*1*









Cikin sand'a tashigo cikin zauren gidansu, tana wasar b'uya, ita da k'awayenta

Lab'ewa tayi tasha jinin jinkinta kamar wacce tayi k'arya, tana tafiya a hankali yanda baxaka iyajin sautin takun k'afartaba."

Gafda zata shiga cikin gidan ne
Saiji tayi taci karo da wani abun,a gabanta."
turus tayi,
Taja ta tsaya gefe d'aya tana turo baki kasan cewar zauren gidan duhu ke gareshi,

Ta d'auka *Kaka* ne, kaka Kwaishi da fitinar tsuha,
Tashiga gunguni tana magana k'asa k'asa, " kai wannan tsohun kacika rigima yazaka taka min k'afa, idan kuma akace da kai ka kusan mutuwa, ka d'ora hannu a kai kace kai ba yanzun zaka mutuba."

Shuru taji anyi Bataji antanka mata ba."

Dogon tsaki taja harda d'an murgud'a baki taci gaba da tafiya
zata shiga cikin gidan kenan taji ta kuma taka k'afar mutum a karo na biyu."

Jikinta ya soma rawa fitsari ya fara d'iga a wandonta, saka makon marin da taji an kwad'a mata a fuska."

Wata irin k'ara tasaki ta fad'i k'asa tana birgima, "Wayyo idona na shiga uku tsohuwa kizo ki ceceni."

Mahmud dake tsaye cike da takaicinta, yace "Ke wace irin yarinya ce,wadda bata kallon gabanta, tunda kika shigo soron gidan nan naketa k'ok'arin naga na kauce mki amma duk da hakan saida kika taka min k'afa."
Oh kin d'auka *kaka* ne da kike fad'awa magana yanda kikaga dama?"
to bashi bane ni kika tak'ewa k'afa, wawuya kawai marar hankali wadda bata kallon gabanta bare bayanta,
Ni maganin rashin kunyarki zanyi kafin na bar gidan nan."

Tsohuwa dake sallah,
Sallamewarta kenan taji sautin kukan Dije a zaure."

Da sauri ta mik'e tsaye tafito daga d'akin tana fad'in "deejama wani mugunne ya dakeki?"

Ai kuwa deejama najin muryar tsuhuwa ta kuma bud'e baki had'ida sanya hannu d'aya ta dafe b idonta d'aya, "wayyo idona nashiga uku tsuhuwa idona ya tsiyaye."

Mahmud tsaye yayi ya tsura mata ido yana kallon ikon Allah, k'azafi takeso tayi mashi yanaji yana gani."

Ta mik'e tsaye dafe da ido sai kuwa takeyi tana tsalle tana fad'uwa, sai da tazo dafdashi ta kuma taka masa k'afa da k'arfi
ta xuba a guje tanufi wurin tsohuwa dake tsaye a k'ofar d'aki tana ruwan masifa."

Tanufi wurin tsohuwa tana fad'in "wayyo idona tsohuwa ki taimakeni yaya muhmud ya tsiyayar min da ido d'aya."

"Tsohuwa tace "burinka ya cika mamuda ka tsiyaye mata ido d'aya saika zuba ruwa k'asa kasha,
Ni wlh bnsan irin k'iyayyar da kakeyiwa deejama ba,
kwata kwata baka k'aunar ka bud"e ido ka ganta tana walwala a gida ko a waje."

Tunda burinka ya cika ka makantar da ita, saikazo ka kwashe kayanka ka koma gidanku. Mungode da ziyarar Allah amfana."

Muhmud da zaifita, jin k'azafinda dijana tayi masa yasashi dawowa ya fasa fitar.

Yace "Allah tsohuwa ki daina biyewa wannan yarinya, kwata kwata batajin magana kuma batada kunya. Tun da nazo garin nan kullum sai ankawo maki k'arar dijama, amma kullum sai d'aure mata kikeyi bata laifi."

"Saboda kana jin zafinta shiyasa ka tsiyayar mata da ido d'aya?"
Tafad'i hakan had'ida kamo dijama dake gefenta tsaye kamar ta shige mata a ciki dafe da ido d'aya."

Ta janye hannun deejama daga kan idon nata tana fad'in naga idon naki dije, idan ta kama mutafi asibity sai na kira ubanshi duk inda yake yazo ya d'aukemu ya kaimu asibitin."

Ganin babu abunda idon nata yayi, tsohuwa ta kuma kallon muhmud dake tsaye gefe d'aya yana kallon ikon Allah.

"To burinka bai cikaba baka makantar da itaba."

tarik'a hannunta "mutafi deejamar tsohuwa kisha hura ki nemi wuri ki kwanta kirabu da wancan Azzalumin."

Kallon mahmud deejama tayi ta fakaici idon tsohuwa tayi masa gwalo had'ida murgud'a mashi baki."

Nuni yayi mata da hannu a lamar zanrik'eki."

Bai d'aga daga inda yakeba. Sai sallama yaji anayi,
wata mata ce tashigo da yaronta janye a hannunta wanda bai wuce shekara goma ba da bokitin markad'e a hannunta duk ya b'aci da k'asa alamar b'ari yayi."

Tana fad'in "ina tsohuwa take?"
Fito fito dan yau na rantse da Allah bazanyi asaraba. Kullum na aiki yarona wurin markad'e sai dijama ta tareshi a hanya tayi mashi dukan tsiya sannan daga k'arshe ta zubar min da markad'e to yau hak'urina ya k'are Dan bazanyi asaraba sai anbiyani ehe "

Mahmud yadubi matar yace "d'aga murya kwarai yanda zasujiki suna ciki yanzun suka shiga."

Tsohuwa tafito deejama ta biyo bayanta,
Tsohuwa tace Abu mai waina mekike fad'i?"
Me kuma deejama tayi?"

Abu mai waina tarik'e k'ugu, ta maimaita mata b'arnar da deejama tayi mata."

Tsuhuwa itama ta hau masifa tana fad'in Sam ba Deejama ta aikata hakan ba."

"Na lura a garin nan babu wanda aka sanyawa ido irin deejama, yarinyar da na aika tasayomin sikari. Tayaya zatabi ta k'ofar gidanku?"

to Wani irin sokon yaro ne gareki da har zai saki baki,
Deejama tayi masa duka kuma har ta zubar mashi da markad'e." dan Allah Abu mai waina kifita a gidan nan tun cikin muna mu biyu, dan babu wani ranko da zan maki ehe."

Ai kuwa Abu mai waina tashiga ruwan bala'i,
"Ayi maka asara kuma baxa'a baka hak'uriba, to yau duk yanda za'ayi sai dai ayi amma sai anbiyani markad'ena."

Mahmud da yaji fad'an ba mai k'arewa bane, ransa ya b'aci yaciro d'ari biyar ya mik'awa Abu mai waina had'ida bata hak'uri."

Baki ta bud'e ta fara dariya takarb'i kud'in tana godiya,
Sai ta koma yin magana cikin lalama da taushin murya, "aisu yaran ne basajin magana, amma ya kamata a k'ara jawa deejama kunne saboda kaf a cikin k'auyen nan ta hana yara walwala idan ta fito kowa tsoronta yakeji."
Babu Wanda ya kuma tanka mata, sai Deejama da tace "kedai ki wuce kiba mutane wuri, tunda anbiyaki kud'in markad'anki, karki damemu da suruto."

Ta dubi Sale yaron Abu mai waina, ta harareshi tace "kai kuma sale duk na rik'aka saina karye maka k'afa d'aya."

Abu mai waina najin hakan kuma tasan halin dijama zata iya, zata fara wata sabuwar masifar mahmud ya bata hak'uri. SnnTa tafi,

a hasale yanufi wurin dijama zai daketa tsohuwa ta turata d'aki tana fad'in wlh karka daketa. Meye ruwanka, to muddun ka daketa saina sab'a maka a gidan nan."

Mahmud ya dawo baya, yana hararar dijama yana fad'in zan rik'akine saina d'ebi d'arina biyar a jikinki. Dan bazan biya mki kud'i a banzaba."

Yanajin tsohuwa ta fara ruwan masifa ya fito ya baro masu gidan."

Bayan sallar isha'i kamar yanda suka saba kowace yarinya zataci ado tanufi dandali,
Haka dijama tayi kwalliya tasanya atamfa riga daban Zane da d'ankwali daban, tazane fuskarta da kwalliya kasan cewar dijama kyakkyawace kuma bafulatana ce, domin ba sosai hausarta ke fitowaba."
An d'aure k'ugu da gyale."

Da gudu tafito gidansu tana rera wak'a, k'awayenta najin sautin wak'arta kowa ya fito daga gidansu suka tareta
Suna fad'in ga 'yar gidan tsohuwa nan ta fito, aikuwa da murna suka tareta suka jera suka nufi dandali."

Dijama ce gaba k'awayenta suwaiba da lantana da ladidi, da luba a bayanta suntake mata baya domin itace boos duk Wanda yaja magana ita ke tare mashi."

Gefe d'aya suka samu suka zauna a kusa da wani mai kifi,
Mai kifin yana ganinsu , Sai da ya kuma dallara fitila ya duba da kyau ya tabbatar da sune,
Ya sauke wani numfashi a ransa yace "Ashe yau zanyi kwantai bazan samu cinikiba. Saboda wad'an nan hatsibiban yaran."

'Dijama ta turo ido had'ida turo baki cikin tsiwa ta dubi mai kifi tace "lafiya meya faru kake haske mana ido da fitila?"

Mai kifi da saida gabanshi ya fad'i dajin maganar dijama, dan ba k'aramin aikinta bane ta bad'e basa kifi da k'asa taja masa asara kuma ba yanda zaiyi. Ya k'ak'aro dariyar dole yace "yi hak'uri 'yar gidan tsohuwa ai bansan kece ba."

Ya d'auko leda yasanya mata kifi. Yace 'yar gidan tsohuwa ga wannan kici,
Ta dubeshi ta ya mutse fuska tace "ya'u kabar kifinka kawai yau bana ra'ayin cin kifin."

Abokananta suna su, amma saboda tsoron da suke mata yasa ko wacce ta had'iya yawunta."

Ya'u mai kifi yana ganin haka yatashi tsam ya d'auki tiren kifinshi ya bar wurin ya canza wurin zama yayi nesa da su sosai."

Dijama bata lura dashiba, hankalinta yatafi wurin kallon wani saurayi da budurwa dasuke hira da alama saurayin bak'one zuwa yayi."

Dariya tayi ta girgiza kai irin yanda ta hangosu saurayin sai wani kakkab'ar jiki yakeyi da hankicif, yana wani ya mutsa fuska wai shi d'an gaye."

Gaba d'aya ta nunawa k'awayenta shi, suka tuntsire da dariya,
Dijama tace "yawwa lantana jeki d'aukomin macijin robar nan naki Wanda yayanki yaje binni ya sawo maki."

Lantana ta zuba da gudu taje gida ta d'auko ta kawowa dijama."

Tace yawwa kuzo kuji abunda zamuyiwa wancan gayen."

Suka had'a kai wuri d'aya abu na basu umurni suna girgiza kai alamar sun fahimta
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)



Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)






*2*







Dijama ta nuna masu inda zasuje su lab'e,
Sai data tabbatar da sun b'oye, sannan
A hankali ta lallab'a tanufi wurin saurayin da budurwar wad'anda suka samu wuri a gefen dakali suka zauna, suna hira suna dariya,

basu lura da itaba sunyi nisa wurin hirarsu ta masoya, ta lallab'a taje bayansu ta d'ora masu macijin robar Wanda aka sanyawa batur sai wutsil wutsil yakeyi kamar macijin gaske,
ta lallab'o ta baro wurin tayo wurin k'awayenta su lantana da suke lab'e wuri d'aya suna lekenta suna dariya."

Itama b'oyewar tayi tashiga lek'awa domin ganin yanda d'an gaye zaiyi."

Ganin basu lura da macijin a bayansu ba,
yasata fitowa tanufi wurinsu tayi kamar wucewa zatayi, sai da tazo daf dasu ta kurma ihu tana nuna bayansu "wayyo Allah maciji a bayanku."

Yahaya gaye yana waigawa yaci karo da maciji a bayanshi,
ai baisan lokacin da ya b'urka tusaba ya kurma ihu ya zubar da talkamin k'afarshi Ya zuba a guje yana fad'in wayyo Allah maciji jama'a Ku kawo min agaji."

Ladiyo dayake tasan halin dijama bataji tsoroba illah ta mik'e a hasale tanufesu,
Suna ganinta tayo kansu suka zuba a guje suna dariya harda rik'e ciki, suna fad'in wasa mukeyi
macijin roba ne."

Yahaya gaye da saida yayi nisa sosai da wurin sannan ya tsaya yana zarar ido yana maida numfashi sama sama, a can yajiyo sautin dariyarsu dijama suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne."
A hasale shima ya nufesu, cike dajin haushin muzantashi da sukayi a gaban budurwanshi, bugu da k'ari ga gudun da yayi harda tusa yasaki."

Aikuwa ya tunkarosu gadan gadan, dijama na ganin haka ta d'aga murya da k'arfi tace "kowa yayi ta kansa."
Suka zuba da gudu ko wannensu yanemi hanyar tsira."

Juyawar da zatayi ta gudu, taji tayi karo da mutum a dai dai lokacin da yahaya gaye yanufota, aikuwa ta mak'alk'ale mutumin wanda batasan kowaye shiba,
D'aga idon da zatayi sai taga Ashe yaya Mahmud ne."

Mari ya kwad'a mata, ya rik'a hannunta ya mik'awa yahaya gaye yace "gata kaci ubanta,
Domin ko mu kanmu mungaji da ita, mungaji da hali irin nata, kayi mata dukan tsiya ninace."

Yahaya gaye babu abunda yakeyi sai ruwan masifa,
Ladiyo ta matso kusa da ita ta xungure mata kai tace "kinci darajar yayanki da yau sai na lahira yafiki jin dad'i,
Dijama da sai zarar ido takeyi tana kallon fuskar yahaya gaye tanaso tayi dariya amma ba hali."

Mahmud yaja hannunta yana rankwashinta a kai yana mata fad'a, sai da sukazo k'ofar gida ta kwace hannunta da k'arfi tashige gida tana fad'in Allah ya isa mugu kawai."

Da Sauri yabita cikin gidan yana Neman ya rik'ata, aikuwa ta fad'a d'akin tsohuwa da gudu,
tsohuwa na ganinta tayi saurin tashi zaune tace "babu Wanda zaibiyoki sai mamuda domin nasan shi kad'ai ke k'ok'arin yaganki bakya motsi, hakan yayi dai dai da zuwanshi k'ofar d'akin yana huci, tsohuwa tace "karka kuskura ka shigo min d'aki
kaji na fad'a maka."

Yaja yayi tsaye a k'ofar d'aki yana huci,
Saida dijama ta kalli fuskarshi ta tuntsire da dariya harda rik'e ciki, dariya takeyi sosai, sai ta kuma kallonshi ta kuma tuntsirewa da dariya,
Ya kuma hasala, tana ganin ya hasala sosai tace "yaya kasan ko menakeyiwa dariya?"

Ya wurga mata harara had'ida girgiza kai."

Tace "ba komai yake bani dariya ba sai yahaya gaye, yanda yasaki tusa ya zuba a guje."

Shima kanshi gudun da yaga yahaya gaye nayi sai da yabashi dariya kasan Cewar duk abunda sukeyi a kan idonshi,
Dariya taso sub'uce mashi yayi saurin barin wurin, yanufi d'akinshi, yana fad'in idan kingama dariyar saiki kawo min abincina ina jiranki."

Yitayi kamar bata jishiba, tashiga bawa tsohuwa labari suna dariya."

Tsohuwa tace "tashi kije ki d'auki abincin yayanki ki kaimasa yana can yana jiranki."

Ta turo baki tace "ni tsohuwa bazanjeba saboda duka na zaiyi."

Tsohuwa tace "baxai dokeki ba aina riga nayi mashi magana, nace karya dakeki kuma kinsan mamuda yanada jin maganar mutane, Wurin nan yana burgeni."

Sannan ta tashi tana turo bki tanufi kicin ta d'auki abincin shi tanufi d'akinshi,
Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi sallama ba,
ta tarar dashi zaune a kan katifarshi dagashi sai best da gajeran wando, jikinshi ko ta ina gashi gashine yayi kwance akan kyakkyawar fatar jikinkinshi fara fes.

hankalinta ya tashi jikinta yasoma rawa aduniya bata tab'a ganin namiji a hakanba,
Tsawa ya doka mata wadda tasanyata tadawo natsuwarta yace "ubnwaye yabaki izinin kishigo min d'aki batare da kinyi sallama ba?"
Maxa kikoma kiyi sallama sannan ki kuma shigowa."

Da Sauri ta juya ta koma jikinta na rawa."

Yana ganin fitarta yayi saurin mik'ewa tsaye ya d'auko jallabiyarshi ya sanya."

Sallama tayi sannan ya amsa mata had'ida bata umurnin shigowa, sannan ta shigo,

Kallon yabita dashi yana harararta domin cike yake da jin haushinta, yanuna mata wni tebur yace "wuce ki ajiye a can."
Kizo inaso zanyi magana dake, kuma kika kuskura kika gudu ko kika yimin ihu saina k'arye maki hannu d'aya idan na rik'aki."

Sum sum ta wuce ta ajiye harda wani sunkuyar dakai kamar ta Allah, tazo kusa dashi ta durk'usa had'ida sunkuyar da kanta k'asa."

Ya Matso daf da ita ya kama kunnenta ya murd'a sosai saida tasaki fitsari saboda azaba,
Yace "maimaita abunda kikace d'azun.
Ni kikeyiwa Allah ya isa baki yafeba?"

Rantse rantse tashigayi ita batayi Allah ya isaba"don Allah kayi hakuri karka ciremin kunne, banyi maka Allah ya isaba."

"Idan kika kuskura aka kuma sake kawo k'ararki a gidan nan saina farfasa maki baki kinyarda."
Tayi saurin d'aga kanta alamar "eh." Idanta na zubar da hawaye."

Ganin fitsarin dake d'iga a zanenta yasa yayi saurin sakinta yaja da baya da sauri ya d'auko bulala yanufota yace "koki goge fitsarin nan ko yanzun na lahira yafiki jin dad'i."

Da Sauri ta mik'e tsaye, saiga takarda ta fad'o a zanenta, ya doka mata tsawa yace "ke zonan takardar meye?"

zaro ido tayi waje takai durk'ushe tana matsar hawaye tana fad'in dan Allah yaya kayi hak"uri bazan sakeba."

Tsawa ya Doka mata yace "ba kuka nace kiyi ba tambayarki nayi."

Cikin rawar murya tace "Anty bushira ce antyn suwaiba k'awata tace nakawo maka."

Ya wurga mata harara yace "bud'e karanta abunda ke ciki,
Da sauri ta bud'e takardar tashiga karanta masa, jin kalaman soyayya ne alamar tana sonshi, yayi saurin doka mata tsawa yace "rufe min bakinki kiyi min shuru,
Bari nafaracin k'aniyarki ke 'yar aiken kamun naje ga Wanda ta aikoki."
Ke fitsararriya marar kunya ke ake aikowa da takarda kikawo min?"
Tashi ki kama kunnanki."

Tana hawaye tana fad'in "Dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba."

Yasin sai kin kama kunnenki, yayo kanta da bulala a hannunshi,
Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye takama kunnenta sai kuka takeyi tana bashi hak'uri."

Abincinsa ya jawo ya fara ci, yana kammalawa ya haye katifarshi yajawo jarida ya Shiga karantawa, ganin ta wahala sosai ya dubeta yace "tashi kiwuce kiba mutane wuri."

Tayi kuka idanunta sunyi jajir har sunfara kumbura, ya dubeta yace "ko gobe idan wata ta kuma aikoki da takarda da sunan kikawata kenan? Mami tazaro ido waje ni inbaka daman kataka matarka!? Afusace yafinciki briefcase dinsa yafita yabarsu agun,

Sam bayason Mami take hadashi da nafisa amaganan aure yafison suyi mu'amala da ita matsayin yaya da qanwa don duk familyn Su bawanda yafi shiri da ita irin nafisan

Tunda yafito daga cikin mota yake gaisawa da mutane har yashiga office, sister Amina yatarar tana shirya folder yaja kujera yazauna tadan rusuna tana makale murya tagaisheshi ko kallonta baiyiba ya amasa aggagauce yana duba wani file, kimanin Awanni hudu yadauka a office din ya shiga word a bakin qofa sukayi kicibus da Baba, "sannu likita da murmushi ya amsa da "sannu Baba ya maijikin dai? a wlh jiki Alhadulillah "ta tashi ne? "Eh ta tashi likita har tana dan cin Abinci, nagode likita wlh har bansan mezance makaba sai dawainiya akeyi damu tunjiya ake takawo mana Abinci Niki Niki ALLAH ya maka Albarka kaida iyalanka, "Ameen Baba ALLAH yaqara mata lfy munje inganta,

Yana gaba Baban nabiye dashi har jiki gadonta, bacci take amma yaga alamun sauqi sosai afuskanta, yajima yana kallonta yana nazartan yanayin fitan numfashinta yanadan rubuce rubuce, kafin yakai dubanshi ga mama jummai yace "jiya da yaushe tafarka? "Kusan magriba taci Abinci alokacin? "a'a maltina kawai tasha amma yau da safe tadan ci, ya gyada kansa "baccifa tayi da daddare? "Eh tayi sosai ma, sai da yagama "yace idan ta farka za'azo akaita can wajen masu xray, yazaro kodi mai yawa yamiqa wa mama jummai takarba sai zabga godiya take yajuya ya fita zuwa yanzu kam Baba yafara tsananin mamakin likitan dama anasamun irin wa'innan mutanen abirni? 馃 yatambayi kansa

Sai can bayan la'asar tafarka da sauri mama jummai ta tariketa tana tambayanta zaki zagane? ta girgiza kai gyaramata Zama tayi dai dai lokacin Baba Garba yashigo da katan din maltina da kayan tea wai gashi inji Doctor KB Dija kam gyara zama tayi tana kallonsu suna magana tana tambayan kanta to ko sudin suwaye? Tunda tafarka taga mama jummai tana ta hidima da ita datayi motsi zata matso ta tambayeta me takeso?

TOFA MUJE ZUWA MASOYA AKWAI MAGANA AGABA

TAKU UMMU FATIMA 馃槝
[3:46PM, 4/23/2018] 鈥�+234 806 573 1897鈥�: 馃尶馃馃尶馃馃尶馃馃尶馃馃尶馃
*DIJAH* *QAYA*

馃尶馃馃尶馃馃尶馃馃尶馃馃尶馃
*BY ASMA'U GALADIMA*
馃馃尶馃馃尶馃馃尶馃馃尶馃馃尶

馃 馃
馃 馃 馃 馃


*MAY* *ALLAH HELP OUR COUNTRY NIGERIA*馃嚦馃嚦馃嚞

*ISLAM MY RELIGION* 馃槝馃晪

馃寛 *KAINUWA* *WRITTERS* *ASSOCIATION*

Girma, daukaka, Imani, zaman lfy, Allah ya qaroshi awannan qungiya mai Albarka, .................. *Dashen* *Allah* 馃憜馃徎



*page* 2鈨�


Mama jummai ta mik'omata wani dogon Riga da Baffa yasayomata ak'ofan asibiti, rigan fari ne yana da manyan zanen flawowi ajiki jajaye,

Tafito shar da ita ko karyawa kasa yi tayi don dokin yau zata tafi gida, tana zaune abakin gado, likitoci sukafara round kallonsa takeyi bako k'yafta ido, itadai tabbas tasan wannan fuskan sai dai takasa tuna a'ina tasanshi,


Cikin nitsiwa yake zaga gadanje sanye yake da suit bak'ak'e da bulue shirt ta ciki bak'ramin amsan sa kayan yayiba Kaman irin black American d'innan, wani sassanyan k'amshi nafita ajikinsa,

Yana daf da gadon ta tafara tunoshi ahankali Abun da yafaru atsakaninsu yadawomata,


Mutuminnanne Wanda bai San darajan D'an Adam ba tabass shine, zuciyanta ta jaddada mata wani kallon tsana tabishi dashi,

Cikin taku d'ad'd'ai ya k'araso gadonta shikad'ansa sauran suna d'ayan gadon suna rubuta report,

Gwiwan hanunsa yasa ya dogara da jikin gadonta ya harde kafansa hanunsa d'aya na cikin aljihun wandonsa,

Yad'an ran k'ofo kad'an yana kallon dara daran idonta yace "yajikin naki?
Yanzu inane yakemiki ciwo?

Wani mugun kallo tamasa ta sunkuyar da kanta batare
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment