Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira)

*ZUCIYA*
_kowa da irin tasa_

© *NA AYUSHER MUHD*

1⃣
Duk yanda yaso ya taka burki abun ya gagara gashi a kan gada yake sannan ga motoci na wucewa, cikin rikicewa ya zuro da hannunsa ta window yanawa mutane alamar su matsa akwai matsala, wasu sun fahimceshi wasu kuwa basusan ma me yake nufi ba, wani yaro ya gani ya taho gadan gadan yana kokarin tsallake titi horn ya shiga yima yaran hakan yasa yaran ya kalli motar sai dai kasancewar yarone karami kawai sai duk ya daburce ya rasa ina zai nufa tsoro yasa shi ya karkata kan motar wanda tsautsayi yasa ya afka cikin kokin jikake tim mota ta fada ciki nan fa mutane suka taru dan neman yanda za'ai sai dai inaa mota tuni ta tafi can kasan koki, rukicewa yai ganin motar ta cika taf da ruwa, shi kanshi duk ruwa ya fara cikamai baki nan ya fara kokarin fitowa ta glass din motar wanda yai sa'a a bud'e yake, dakyar ya fito sai dai yana fitowa yaji ya bugi wani abu wanda baisan menene ba ga ruwa ya shakka dayawa wanda yasa ya suma.....



_A Rigar Datti_

Nafi ta d'ago ta kalli mahaifinta wanda yasata a gaba yana zabga mata masifa cikin yarensu na fulani tace " Baffa kayi hakuri wlh ni bansan ya akai kajin nan suka faracin geron nan ba."
Wanda ta kira da Baffa wato mahaifinta cikin tsananin masifa yace " kedai wannan yarinya baki da mutunci dan tsabar wulakanci da asarar abinci har kaza ta samu matsayin cimin gero na? Wanda nine nake wahalar neman kayana bake ba bakuma waccan balagazazziyar uwar taki ba wacce ta d'au kaninki ko kunya ta saida saniya ta ta had'a ta tafi wai saudiya yin takaranci ba? Ni dai wannan masifa ta faru ne tunda na auri waccan tambad'ad'iyar uwar taki wacce ban tambatar da tsatson ta ba."

Nafi ta share kwallar ta tace " Baffa kayi hakuri nasan inna taba kyau...."
"Gafaracan ni munafuka yimin shiru ai kinji a sara nayi mamakin da zata gudu menene dalilinta na barinki tadau namiji yanzu da alama na fara fahimta."
Ya maida numfashi sannan ya cigaba " kidahumar banza kidahumar wofi to wallahi a hir d'inki da min almubazaranci."
Yana kainan yai waje a fusace, hawaye ta share sannan ta mike ta d'au kwarya ta tafi garken shannun baffa dan yin tatsa.
Tana yi tana 'yan wakenta na fulani, kasan zuciyarta kuwa takaicin tafiyar uwarta da kaninta take sun barta ita kadai a wannan rigar tasu ko tausayinta basayi.
Kasancewar Mahaifinta mutum ne mai bala'in gaske in nace bala'i to fa lalai ina nufin bala'i baya ganin mutuncin komai a rayuwarsa banda na dukiyarsa ko da wasa wani ya tab'amai dabba to fa lalai ya shiga uku, saboda tsabar masifarsar ne yasa ya bar cikin mutane ya dawo can gefen kogi ya dasa nasa gidan wanda ake kira da rigar Datti.

*Dattin* sunan mahaifin Nafi kenan, Mahaifiyar Nafi ba karamin hakuri tai da Datti ba, auren soyayya sukai sai dai kasancewar ita ba bafulatana bace (Kad'o suke kiran hausawa.)ta samu kalubale da dama gun danginsa, har sukazo suka hakura saboda tsantsar mutuncin ta wanda ya ninka na d'an nasu.


Duk yawan shanu da kaji da zabi irin na datti ko da wasa bazakaga an yi abinci mai mutunci agidanba bare har akai da zancen yanka kaxa, koda kuwa ciwo zai kama ta, ya gwammace ya d'au dabbar dabatada lafiya ya fita ya siyar, girkinsu dai baya wuce abin gero ko dawa dan ko shinkafa ba bari yake a ci ba.
Iya tsananin hakuri Matarsa tayi dashi ganin bazai tab'a canzawa ba haushi ya kamata ta d'au saniyarsa ta saida ta kuma dauke karamin danta kanin nafi ta gudu dashi Saudiya inda 'yar uwarta take da zama tana kasuwanci (Takaru).

Samari da dama suna san Nafi dan in taje Talla cikin gari abin shawa duk da ba kaya dayawa gareta ba sai dai zakaga kayanta kullum tsaf tsaf gata ba laifi tanada kyau.
Duk yanda samari suka kai ga santa babu mai iya tunkarar ta dan kowa na tsoron hada zuri'a da Datti acewarsu duk wanda ya aureta sai dai yai kayan daki da kansa sannan har cikin gidansa Datti zai dinga zuwa yana zazzaga masifa.

Nafi kam haka nan take zaune da mahaifinta a rana duk shiga da fitar da zaiyi da masifar dazai mata.


******
Ajiyar zuciya Nafi tai a sanda ta gama yin tatsar, ta mike ta dau bokitin tai cikin gida.

Tana ajiyewa a ciki ta dau wani bokitin dan d'eboma dabobi ruwa da kuka daura sanwar dare.

Tad'anyi tafiya kadan ta isa babban kogi wanda ke bayan gidansu kadan, kallan katon kogin tai yau sam ba kowa ko fulanuwa masu kiwo da suke tsayawa ba dabobinsu ruwa yau basanan, tadanyi tsaki kadan cikin yaransu na filo tace " yau dai da alama banida sa'a ko mutanen da muke 'yar hira dasu wani sa'in ban tarar ba." Takarasa maganar tareda gangarawa kasan Kogin.

Zama tai adan bakin kogin tasa kafafuwanta acikin ruwar tanadan bubugasu kadan waka take dan yi tana murmushi ita kadai, rayuwarsu da mahaufiyarta da kaninta Gaddafi take tunowa.

Ganin rana na neman faduwa yasa ta mike tadau d'an karamin kokonta ta shiga deban ruwan tana zubawa a bokiti, ta dau bokitinta da niyyar tafiya daga d'an gefe inda ruwa ke korowa taga kamar takalmi, mamaki ya kamata can kuma tadan girgiza kai kadan tace " Oh ni Nafi yanzu kila wani bafulatanin ne ya manta da Takalminsa, ba mamaki gobe yazo yai ta neman inda yake."

Karasawa tai kusa da takalmin tana cewa " bari ni in dauka tunda akusa nake sai in ajiye gobe na fito in rataye musus ko a bishiya ne."

Mamakinta ya tsaya ca a sanda tasa hannu dan ciro takalmi sannan a daidai lokacin ruwa ya koro sannan ya koma hakan ya bata damar ganin ashe kafa ce ta mutum kwance a cikin ruwa.
Da sauri ta saki ta kalmin sannan ta kurma wanu ihu mai kara wanda ruwan sai daya amsa, sai dai abin haushi babu kowa agun, idanunta a runtse suke tam ta had'a hannayenta biyu alamar roko tana cewa " Yahkuri Aljanin ruwa wallahi Allah bansan kai bane kake hutawa, natuba kwai ka yafemin wallahi ba ruwana ba kuma zan sake ba."

Tana gama rokonta na shirme ta dan bud'e ido daya cikin tsananin tsoro sai dai yananan a yanda ta barshi, baya ta danyi tana cewa " Kayi hakuri dan Allag ka koma makwancinka in ma fatalwa ne ni wallahi ba ruwana da kai."

Nan ma tad'an sake kyalla ido kadan, sai dai yananan a inda yake, dabarace ta fado mata akan lale ta mike ta falfala da gudu hakan zai fi mata sauki, juyawa tai ta ga lalai fa ba kowa ai kuwa da wayau ta tattare zaninta ta juya tai baya a guje kai kace Zaki ne ya biyota ko bokitin ruwan bata tuna dashi ba.

Gida ta nufa da uban gudunta, tana shiga ta shiga yin haki na tsabar tsoro, Datti dake tsaye a tsakar gida ya kalleta cikin takaici yace " To dabba da alama kema bakida maraba da tinkiya meye hakan kuma?"

A tsorace ta daidaita tsayuwarta tace " Baffa aljani na....."

Yace kiga abinda yafi aljani ma makaryaciyar banza da wofi dan tsabar iskanci dama ba ruwa kika tafi debowa ba? Ai kin sani sarai dabobbi ba ruwa a gunsu."

Sai a lokacin ta tuna da abinda ta fita yi cikin sanyin jiki ta fita, tana tafi tana dan share kwallarta aganinta ya kamata mahaifinta yaji a wani hali take ciki.

Da komawarta idanunta suka sake dira kan wannan mutumin, har ta dau ruwanta zata tafi wata zuciyar tace "Yanzu Nafi in mutum ne fa ya fada ruwa?"
Da sauri ta kara kallan gun, tsoro ne fal a ranta, addu'a ta shiga yi tana takawa a hankali idanunta kuma a rufe wai ita a dole so take inta isa idanun nata na rufe zata zare mai takalma ta gani ko da kafafu.

Haka tai ta tafiya idanu a rufe jitai ta yi tuntube kafarta ta harde saboda tsoro jikake tim ta fada kan wani abu, bata San sanda ta bud'e idanunta ba cikin tsoro ta kalli inda ta fada, itadai tasan lalai akan abu ta fada hakan yasa ta kallin kasa, ganinta kwance akan mutum yasa ta kara calla wani kara mai sauti......

*THE INNOCENT TEAM*

*ZUCIYA*
_kowa da irin tasa_

© *NA AYUSHER MUHD*

2⃣


Kanta ta sake cusawa kan mutumin duk ta rikice, can ta tuna inda tasa kanta hakan yasa ta mike da sauri, jikinta na rawa, sai dai a wannan lokacin tsoronta yadan ragu ba kamar da ba.

Hannu tasa ta zare takalmi mai saucikin dake kafarsa, sannan ta zare safar kafa ta gani kamar ta mutum sai kuma tausayin wanda ke kwance ya kamata, hannunsa ta kamo ta shiga kokarin jawoshi daga cikin ruwan, da kyar da nishi ta samu tadan jawoshi kadan, nan fa ta shiga kokarin murgunashi, nan ma da kyar da numfarfashi ta samu ta juyashi, tsugunawa tai a gabansa tana kallanshi.

Tsoro ta fara ji kardai ya mutu? Nan tasa hannunta a sai tin hancinsa ta dan dade kadan jin baya numfashi yasa tsoro ya kara kamata, idanunta suka fara tara kwalla, hannunta tasa a saitin zuciyarsa, dariya ce ta bayanna a fuskarta a lokacin dataji bugun zuciyarsa.

Ta rufe fuskarta alamar kunya tace " Da ranta wallahi." Ta sake yin dariya tace " Wlh da ranta Allah da gaske."
Ta sake dariya.

Fuskarta ta zuro daf da tashi tana kallo, ba fari bane sannan kuma ba baki bane yanada kyau, hancinsa dogone, ta d'an yi murmushi sannan ta kalli kayansa tace " Kad'o ne wannan kam, sannan da alama bama dan nan garin bane daga birni yake." Baki tad'an turo kadan ganin ita kadai take maganarta sannan ta shiga tunanin yanda zatai ta dawo da numfashinsa.

Hannu tasa ta shiga danna mai kirji tana san ruwan daya shakka ya futo, sai dai ina, ya shaka da yawa duk yanda ta zake tana dannawa ba alamar motsi a tattare dashi.

Idanunta ne suka ciciko, ta kalleshi tace " Dan Birni ya zanyi?"

Ga ba kowa a gun, ta kafeshi da ido tana kallo jitake kamar tai ihu, tunawa tai sanda wasu fulanuwa suka ciro wani yaro daya fada ruwa kwanaki, tana kallo bayan sun danna mai kirji bai farfado ba sai wanda ya danna mai kirjin yasa bakinsa a nasa ya huramai iska alokacin mutane sukai ta ce masa dan iska, babar yaran tazo ta kwace danta itama tana masifa.

A hankali ta matso itama da shirin kai bakinta, sai kuma ta tsaya ta kalleshi tace " Dan Birni ba iskanci zan maka ba kawai iska zan hurama, kaji? inka warke xan baka hakuri."

Nan ta sa bakinta cikin nasa ta shiga huramai iska iyakar karfinta, sai datai tayi sannan can sai yadanyi tari sai ga ruwa dayawa ya zubo daga bakinsa, idanunsa ya bude a hankali ya kalleta, ta kifkiftamai ido tace " Hannu? Kin ganni?"

Gani tai ya maida idanunsa ya rufe, sai dai yanzu numfashinsa na fita sai dai dad'an sauri yake fita, tai shiru tace " ya zanyi? Bacci yake? Ga dare nayi?"
Jijigashi ta shiga yi tana cewa " Karkiyi bacci anan dan Allah kiyi hakuri ki tashi."

Sam bataga alamar motsi a tattare dashi ba, ga gari ya fara rufewa, da sauri ta mike ta suri bokitin ruwanta ta nufi gida, tana shiga ta waiga taga bataga Baffa ba, ajiye ruwan tai ta karasa gun dabobbi ta dauko baro ta fito da sauri.

Inda ta barshi anan yake babu alamun ya motsa, nan fa ta shiga kokarin d'orashi akan baron, sai dai ina.....sam ta kasa.
Duk wani karfi datake tunanin tanadashi ta sake akan mutumin sai dai daga ta dagoshi sai su fad'i tare, saboda rinjayarta dayake yi, duk su biyon sunyu butu butu dasu da jikakkiyar kasa, banda numfashin wahala ba abinda takeyi, ga duhu ya kawo kai, nan ta cigaba da gwadawa, dakyar da sid'in goshin wahala ta samu ta d'aurashi, tana daurashi hannunta ya kume ajikin baron.

Kara tad'anyi saboda zafin dataji, sai dai tsoron rafin ta keyi dan duhu ya fara rufewa, da sauri ta shiga tura baron, sai dai dakyar shima take turawa kasancewar ba siminti bane ko kwalta a gun, iya wahala Nafi taji a wannan lokacin, har ta samu ta isa gida, tai sa'a baffa na kewaye (ban d'aki ) hakan yasa ta tura baron zuwa d'akinta tasani sarai mahaifinta ko wani ne zai mutu bazai taba yanda a kawoshi gidanshi ba koda kuwa dan uwansa ne bare wannan dabatasan inda ya fito ba.

Can gefen dakinta ta sa tabirmar datake kwanciya a kai ta shimfida zannuwa guda uku sannan ta shiga kokarin saukeshi, wannan karan batasha wahala sosai ba sai dai shi yadan kumu da bango garin saukeshi.

Nan tasamai pillow ta kwantar dashi, itama nan ta zube ta kwanta dan tasha bakar wahala.

Batai minti 3 a kwance ba taji muryar Baffa yana kwalla mata kira " Ke Nafi kina inane?"
Dasauri ta mike ta kara jan labulen dakinta tai waje tace " ganinan Baffa."
Yai tsaki yace " Bakida hankali ne zaki d'ebo ruwa baki zubama dabobin ba shinr zaki dangwarar anan? Ko ni kike jira in kai musu?"

Kallan ruwan tai tadan yi kasa dakai tace " cikinane yadan murdamin kadan shiyasa......"
"Ciki? Zancen banza kenan, dan cikinki ya murd'a sai ki barmin dabobi da kishi ruwa? Sannan ba madai kina nufin bokiti dayan nan kadai kika d'ebo ba ko?"

Idanu tadan kifta na mara gaskiya, Datti ya shiga tafa hannu na mamaki yace " Lalai zance kwal ubanki kuwa a gidan nan, banza wacce mahaifiyarta ta gudu da kayan sata, sannan da auranta ta tafi yawan karuwanci."

Idanun Nafi ne suka ciciko tai saurin yin kasa da idanunta a hankali tace " kayi hakuri Baffa wlh ba h......"

"Billahilazi kika b'atamin rai goben nan sai in nemi wani can in aura miki, ni dama na gaji da ciyar dake abincin da bakisan darajarsa ba."
Yanakainan yai waje a zuciye.
Tsugunnawa tai agun ta shiga wani irin kuka mai tsuma zuciya, tadade agun kafin taje ta maka alwalarta wacce batasan ko hakan akeyi ba, itadai kawai tasan ana wanke fuska, hannu da kafa, ta mike ta shigo daki tayi dunguren sallarta da batasan me ake cewa ba.

Tana idarwa ta matso kusa da dan birni, kansa takai hannunta sai dai da sauri tadauke hannunta jin wani mugun zafi datai, Mikewa tai da sauri tace " Hande inboni!! Karfa kad'on nan ya mutumin adaki in shiga uku?"
Dasuri tai waje ta shiga lelekawa, abin haushi a can gefe suke wanda inzakaje rigar kusa dasu sai kayi tafiya mai dan yawa, gashi tana tsoron mahaifinta kar ya dawo yaga ba tannan.

Komawa tai ciki, ta nufi d'akin baffa nan ta shiga duba gayayyakin magani ko zataga na zazzabi, tai sa'a kuwa ta samu nan ta sato rigarsa ta fito daga dakin, wuf ta shige d'akin ta.


Tofa nan ake yinta gani take jikaken kayan dake jikinsa ne ya jawo mai zazzabin nan, shiyasa ta dauko kayan baffa, to amma taya zata ciremai kayan dake jikinsa ta samai wannan?

Tsayuwa tai akansa tai tsuru tsuru da ido tana tunani, maganin ta dauko ta jika a kofi sannan ta matso kusa dashi ta shiga bashi a hankali da cokali, wani yana shiga bakinsa wani kuma zubewa yake.

Bayan ta gama ne ta kalleshi cikin kalaar tausayi tace ya zanyi dake?




*THE INNOCENT TEAM*

*ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com

3⃣


Duk ta rud'e ta zauna kusa dashi tare da daura hannunta akan goshinsa, tsoro da fargaba ne suka cika mata zuciya jin yanda jikinshi yai zafi dauuu.
Yawo ta had'iya sannan tace " bazamuyi ta zama a haka ba d'an birni kiyi hakuri bazan kalleki ba, zan cire miki riga idanuna a rufe, kinji?"

Tana fadar haka ta ajiye rigar Baffa a kusa da ita ta matso kusa tare da rufe ido, irin rigarnan mai dogon hannu da kwala ce, sai botir dake jikin rigar daga sama har kasa, nan ta shiga b'allewa idanunta na rufe tana yi tana magana, "yanzu kaga bana kallanka, sannan namaki laifi guda biyu, na farko nasa bakina a naki sannan yanzu ina cire miki rifa, sai dai inaso karki manta wallahi ba asan raina duk nai hakan ba, banaso ne ki mutu kinji?"

Tana kainan ta shiga kokarin zare rigar, jin ta kasa zarewa yasa ta manta ta bud'e idanunta kallansa ta shiga yi, sam ta manta, yauce rana ta farko data tab'a kallan jikin namiji dan kaninta tun daya tasa mahaifiyarsu ta raba musu d'aki, ita ba gurin wasan shad'i ake barinta taje ba, nan ne dai tasan maza basa sa riga sai wando, to ita inama take zuwa banda ta mika nono da madara cikin gari inda mahaifinta yake saidawa, dan rashin yadda irin na datti bai yadda ace wani yasai da mai abu sai dai shi dakanshi, nan shago ya bud'e yake saida madara da nonon shanu.

Ganin yanda gabanta ke fad'uwa yasa tai saurin rufe idanunta sai dai wannan karan ta guntse bakinta gum, haka tasamai riga sannan ta fito waje da sauri.

Sam bata kula da Baffa dake zaune akan tabirma ba, ta tsaya a waje tare da rik'e inda zuciyarta take, a tsaye take kamar gunki, jitai ance " Wato Nafi kin fara zarewa ko?"

Dasauri ta kalli inda maganar ta fito, Baffa ta gani a zaune, hannunta ta zare cikin tsoro ta kalleshi tsoru tsuru tace " Baffa.."
" Inajiyoki daga d'aki kina magana ke kadai wato zama ke kadai a gida yasa kin fara zarewa ko? "

Tai kasa dakai cikin tsoro batace komai ba, baffa yai tsaki sannan ya juya kansa yace " damomin fura insha dare nayi."

Cikin rawar murya tace " to Baffa yauma bazamuci abinci ba......"
Katseta yai cikin masifa yace " Inkin gaji dashan fura da nono kiyi zuciya kiyi aure, nifa banga dalilin dazaisa yarinya kin kai aure incigaba da ciyar dake ba, sannan haka kawai inada shanaye dayawa bazanje insai abinci ba ah to."

Nafi bata amsa ba ta juya dan shiga d'akin dasuke ajiye fura, nan ta debo, ta d'ebo nono a kwarya ta zauna ta dama, itakam yanzu warin nono ma yafara damunta, tunda uwarta tabar kasar nan kullum abincin da suke ci kenan, sam Baffa ya rufe ido ita kuma tasan inya fita shago yana siyan shinkafa yaci amma ita kullum abinda takesha kenan.

Tana gamawa ta zubomai a langa ta rufe ta daura ludayi ta kawomai, sannan ta dauki nata tai d'aki, kallan mutumin dake kwance tai, tace " Nasan kaima yunwa kake ji ko?"
Matsawa tai ta kara tab'a goshinsa, da zafi har yanzu, nan ta matsa kusa dashi ta dan dagoshi kadan tasa kafarta ta tareshi, ta dinga deban furar data dama tana bashi a hankali da cokali, wani yasha wani ya zube, ganin yadan sha dayawa yasa ta mik'e jiki a sanyaye ta zare zanen data shimfida na saman ta goge mai jikinsa sannan ta dauke numfashinta itama tasha, dan sam batasan sha.


Waje ta fito da kwaryar sannan ta koma ciki tare da tura kofarta ta rufe, kusa da mara lafiyar ta koma ta zauna, ta hard'e cinyoyinta kallansa kawai takeyi, sai dai tunaninta nakan mahaifiyarta, a haka har bacci yai awun gaba da ita.


Wajen gabanin asuba ya bud'e idanunsa a hankali, yarinya ya gani kwance kusa dashi ta dan dukunkune jiki tana baccinta, kallanta yai sannan ya shiga kallan dakin, mamaki yashiga yi a ina yake hakan? Yadauka ya mutu shikam, Nan ya shiga juye juye, tare da kallan d'akin dakyau "wannan kuma inane hakan?"
Gashidai kamar d'aki sai dai gaba daya baisan dame akai rufin dakin ba, sannan ba komai a dakin banda ta birmar dayake kai sai gefe kuma bakko da 'yan samiru, kokarin mik'ewa ya fara sai kuma yaga kamar yarinyar tana neman tashi, dasauri ya maida idanunsa ya rufe.

Nafi ta mik'e zaune tare da sa hannu akan goshinsa, murmushi ne ya bayyana a fuskarta jin zazzabin yaragu sosai, ta kalleshi fuskarta dauke da murmushi tace " Zazzabin ya ragu aradu, dan binni ya kamata ka farfado ko na samu in baka hakurin abinda nai maka."
Tai kasa dakai tana murmushi tace " kaga sanda na sa bakina a naka a bakin ruwa wannan taimakon ka nai. "


DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA
avatar
sadiyayunusa

7 months ago

Reply

Inaso sosai

Please Login or Register in order to submit comment