Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

FITAR TSIRO Complete Hausa Novel Document by FITAR TSIRO


FITAR TSIRO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 30058



FITAR TSIRO

Reading Time: 2 Hours

Added On: 18, Oct 2024

Author: Rufaida Omar ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 09034973645

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 151.78 kb

File Type: txt

Views: 1074+

Download: 762+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: FITAR TSIRO

Rufaida Umar

Paid book: 500
Account details: 7145096012 Ibrahim Rufaida Umar. FCMB

Phone number: 09034973645

Free page 1



Bismillahir Rahmaanir Raheem.

Ina roƙon Allah yanda muka fara ya bani ikon kammala maku lafiya. Allah ya baku ikon riƙe amanar labarina, ku bar shi a inda ku ka gani ku karanta. Nagode da kauna, Allah ya bar zumunci. Ameen.

***

Ta ɗaga idanunta tarr ta sauke saman mahaifinta wanda ke tsaye riƙe da belt yana huci, zuciyarta ta zo iya wuya ta soma magana a kausashe.

"Wallahi sai dai ka kashe mu, amma har abada ba zan taɓa yarda da auren nan ba. Idan kuwa ka takuramin sai na tona asirin ƙazamin sana'arka wajen hukuma idan ya so ka tsire ni da raina!"

Bai san lokacin da ya saki belt din ba, a razane wannan karon yake dubanta kafin ya maida duba ga Mahaifiyarta wacce ke kuka ga jikinta duk a fashe tsabar dukan da ta ci a hannunsa. Ya ƙara duban ɗiyarsa karo na biyu, babu ko digon tsoro ko fargaba a kwayar idanunta sai ma wani ƙarfin gwuiwa da jarumta. Da rawar murya ya soma magana bayan ya maida duba ga Mahaifiyarta.

"Na'ima...ni kika tonawa asiri wajen ɗiyarki?"

Yana maganar yana matsowa kusa da ita, ji ta yi numfashinta ya kusan ɗaukewa tsabar tsoro da tashin hankali. Tana kuka tana ja baya tana girgiza kai.

"Wallahi wallahi ban sanar da ita komai ba. Ban san a inda ta ji ba. Haulatu, a ina kika ji?"

Yarinyar da aka kira da Haulatu ta dubi Mahaifiyarta hawaye kace-kace saman fuskarta ga wani malolon abu da ya tokare mata wuya tsabar takaicin irin wannan shakkar da Ummanta ke yiwa Baban, mutumin da bai dauke su a komai ba face wani nauyin wahala da yake buƙatar yakicewa ta kowane hali. Sai ta ji gaba ɗaya ma ta kasa magana, tamkar wacce aka naɗewa harshe. Ta miƙe kawai ta shige ɗaki a fusace. Ta yi zaton zai ƙara kai hannu jikin Ummanta da zummar duka sai kuma ta ji shiru. Karshe ta ji an buga ƙyauren gidan da ƙarfi shaidar ya fice kawai sai ta haɗa kai da gwuiwa ta shiga rusa kuka. A wannan yanayin Umman ta shigo dakin, cike da tashin hankali ta hau jijjigata idanu waje.

"Haulatu, faɗamin a inda kika san wannan baƙar sana'ar ta mahaifinki? Wa ya fadamaki?"  Ta ɗago tana sheshsheka ta ce.

"Umma don Allah ki rage tsoron wannan mutumin. Ki yarda mu gudu mu bar masa gidansa. Wallahi idan ya dage zai aurar da ni ga Nazifi za ki neme ni ki rasa, ni zan tseratar da rayuwata tunda kin ji kin gani za ki iya rayuwa da shi."

Ta yi shiru kawai tana duban ɗiyarta, ta kasa ce mata komai sai ruwan hawayenta dake fita gami da numfashin da take saukewa lokaci zuwa lokaci ga uban radadi da jikinta ke yi wanda ba domin ba a sabo da wahala ba sai ace ya ci ace ta saba.

Haulatu ta ƙara duban Umma da rinannun kwayar idanuwanta yayinda take wani ɗan murmushin takaici.

"Na sani, dama wannan shirun da kika saba yi a duk sadda na nemi mu gudu, shi za ki yi. Shikenan, Umma ki cigaba da shirun idan har kina ganin wannan ne mafitar da kika zaɓamana. Kin fi kaunar yanda nake rayuwa a makaranta ana tsangwamata saboda halayyar mahaifina, toh shikenan, zan cigaba da rayuwa da ke a unguwar da ko makwafta ba sa shiga harkar mu su na mana kallon mutunen banza duk adalilin mijinki, babu wanda ke ganinmu da mutunci sai ƴan daba dake dandazo a kowace rana a ƙofar gidan nan suna taya ɓera ɓari, su na ƙara yiwa mijinki kirari da Oga kansa yana fasuwa.  Zan cigaba da zama watarana nima na bi sahunsa na zama mai siye da siyarwar ƙwayo..."

"Yimin shiru Haulatu! Rufemin baki tun ban zubarmaki da haƙora ba!"

Tsawar Umman ta katse zantukan da take yi kusan ba'a hayyacinta ba, sai kuma jikin Umman ya yi sanyi, tana kukan ta rungume Haulatu a jikinta. Ita kaɗai tilo ɗiyar da ta haifa ban da cikin da mijinta ya dinga zubar mata har sau shida, samun Haulatu da ta yi Allah ne ya ƙaddara sai ta fito duniya.
Itama Haulatun tana kuka ta rungume Umman, a duniya babu wacce ta fi ta a wurinta. Tana mata so da kaunar da har abada ba ta ji za ta iya nunawa ga wanda yake amsa sunan mahaifinta, mutumin da har abada ba ta jin za ta ba shi wannan ragamar. Tana da burin ace watarana ta kwatarwa Umman ƴancinta ta kuma ga ƙarshen wannan zaluncin da ya ke yi musu. Tauye haƙƙoki ba iyaka, sun shallake tunanin dukkan mai tunani, ana zama ne don ba wata inuwar da za'a raɓa a ji sanyi, wannan inuwar ta zama ta dole amma hakikanin gaskiya abin ya soma kai ta maƙura.

"Umma don Allah kar ki bari ya aurar da ni ga Alhaji Nazifi. Wallahi mutuwa zan yi."

Ta ɗago fuskar ɗiyarta tana share mata hawaye lokaci guda tana mai girgiza kai.

"Ba za ki mutu ki bar ni ba Haulatu, in sha Allahu za ki yi rayuwa mai tsawo, za ki samu farin cikin da nake yawan mafarkinki da shi. Aurennan kuma ba zai yiwu ba, ina ji a jikina daga yau an bar maganarsa. Mahaifinki ba zai ƙara tayarwa ba."

Haulatu ta runtse idanu, zafi take ji na gaske a kirjinta, duk sadda aka alaƙanta sunanta da shi takan ji tamkar ta tsire kanta, ita fa ba ta kaunar a kirashi da mahaifinta. Ta dai ji abin da Umman ta furta amma fa ba don ta gamsu ba sai ma ta shiga al'ajabin ta yanda Umman ta aminta ɗari bisa ɗari cewar an bar zancen gaba ɗaya.
  Kiraye-kirayen sallar la'asar ne ya katse musu shirun, Umma ta miƙe ta fita don ɗora alwala yayinda Haulatu ta ja jiki ta jingina jikin bangon ɗakin.

   Har Umma ta shigo ta shimfida abin sallah a gefenta ba ta sani ba, ta dube ta sosai, jinkirta lokacin sallah ba wani abu ne sabo a rayuwar ɗiyarta ba, wannan yana daga cikin abin da yake ci mata tuwo a ƙwarya, ta sani kamar yanda kakarta ta wajen uwa ta faɗi mata kafin mutuwa ta raba, sallah babu musibar da ba ta magancewa hakan yasa duk runtsi take matukar kokarin yi akan lokaci ta kuma dage wurin gani Haulatun itama tana yi, sai dai tana mamaki yanda koyaushe sai an sha fama kafin ta miƙe ta yi. Tana tsoron ace ta dauki wannan mummunan ɗabi'ar na mahaifinta wanda sallar ma ba ta dame shi ba. Hakan yana daga cikin dalilin da ta tsaya ka'in da na'in take kokarin ganin Haulatun ba ta yi wasa da zuwa Islamiyya ba. Wasu lokutan ta je, wasu lokutan kuma ta fake da cutar ƙarya ta lafe a gida.
  
"Haulatu."

Kiran sunanta da ta yi ya sanya ta firgigit ta dube ta. Wani abu ya tsirgawa Umma a zuciya, ta danne ta hanyar haɗiye miyau. Da muryarta mai nuni da rauninta ƙarara ta ce.

"Maza tashi ki ɗauro alwala ki yi sallah, wannan tunanin da koke-koken babu amfanin da zasu yi maki. Kinji ko?"

Ta yamutsa fuska sannan ta miƙe gami da jan ƙaramin tsaki, ba ta ce uffan ba ta fice daga ɗakin. Idan da sabo da wannan halayyar ta komai aka ce ta yi tsaki, Umman ta saba, ita dai tana kokarin ganin yarinyar ba ta sauka a kan turba ba, daidai gwargwado tana yi mata gyara a wasu guraren na kalolin rashin kunya ko ace tarbiyya, amma ta sani ƙarfe ɗaya ba ya amo. Addu'a ita ke maganin komai.

Da wannan ta share zantukan zucin, ta tayar da sallar. Kafin ta idar itama Haulatun ta iso ta zura hijabinta ta tayar. Umman ta riga ta miƙewa ta fice tsakar gidan don kama aikace-aikace. Ita kuwa Haulatu koda ta fito sai ta nemi wuri ta zauna gami da zubawa uwar idanu yayinda take kiciniyar kaɗa omo don fara wanke-wanke.
  Doguwar mace mai hasken fata da kyawun dirin halitta don idan suka jera ba za ka ce ita ta haife ta ba sai dai ko a kirata da yayarta ko kuma ƙanwar uwa saboda irin matan nan ne masu baiwar jiki mai kyau. Ta tabbatar da ace su na gudanar da rayuwa ne ta daula ko kuma rufin asiri ko yaya, da Allah ne kadai ya san irin gogewa da tsantsar kyawun halittar da za'a ga mahaifiyarta da shi. Sai ta ji murmushi ya suɓuce mata wanda nan take ya mantar da ita matsalolin da suke ciki, ta tafi hasko kawunansu cikin rayuwar da take da buri da mafarki a koyaushe. Wai ace ga su nan a gida mai kyau da tsari, Ummanta na daga zaune ga ma'aikata sai hidima suke yi. Duk
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download FITAR TSIRO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album