Join Our WhatsApp Group

GIDAN GANDU Complete Hausa Novel Document by GIDAN GANDU


GIDAN GANDU

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 88561



GIDAN GANDU

Reading Time: 7 Hours

Added On: 08, May 2023

Author: Sadi Sakhna ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 09035784150.

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 385.72 kb

File Type: txt

Views: 3051+

Download: 1465+

Last download: 13 hours ago

Description/Story: GIDAN GANDU
Biebee Isa
Hausaebooks
Creat:- Shuraih Usman

Ku shiga shafinmu na facebook domin samun wasu kayatattun littatafan ta hanyar bibiyar wannan
adireshi na yanar gizo www.fb.com/hausaebooks

GIDAN GANDU
1⃣🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕
Tsaki Haneefa ta qara bugawa a karo na biyu,
yanzu mu kullum haka zata dinga samu latti?
Bilqeesu tace Aifah, inda sabo ai ya ci ace mun
saba, ta cika nawa, Hanifa tace wlh baxa ta sabu
ba, bari mu dawo daga makaranta wlh mu samu
Tsoho mu gaya mishi, Islahulkhair da ke gefen
su ba ta tanka musu ba, cikin damuwa Fadila
tace Mallam Audi donAllah ka qara mata horn,
kafin Mallam Audi ya qara Horn suka hangota
tana sauri cikin yanayinta na sayih ta fada cikin
mota qirar bus, Mallam Audi Ina kwana, ya

amsa mata cikin murmushi, tace kayi haquri
wlh banga Socks dina bane, yace ba komai shigo
muyi ta tafia kar mu bata wani lokacin. Ya ja
mota ya bar haraban wakeken gidan da ke
qunshe sashe sashe..
Kusa da Islahulkhair ta zauna gefenta Fadila ce
riqe da keypoint tana karatu, Ta ce hey Sisters,
sorry i kept u waiting, Fadila ta dago ta kalleta,
cike da zolaya tace Allah ya nuna mana ranar da
zamu daina jiran Maysah, kin cika nawa, tace
wlh banga safata bane ta kalli Islah tace yadai
sisi? Murmushi ta mata tace lafya u will never
change will u? Daria ta mata ta kama kunnenta
tace sorry, ta kalli su Hanifa da bilkis a gefe
tace duk ina kwananku, a tare suka buga tsaki
tare da hararta, ba ta damu ba don idan da sabo
ta saba. Mazan da ke zaune su hudu a chan baya
tace Whatsapp bro, daya kawai ya amsata
sauran 3 hararata sukayih. Ta kalli Na'imah da
bakinta ke sake tana jalalar da miyau tace
Nimcy a rufe bakin mana, kar ki bata gaban
hijabinki, cikin tsiwa nimcy tace anqi a rufe din,
sa'idawa masu bacci da ido daya, tace Allah baki
haquri ta ciro littafinta ta shiga dubawa don yau
suke fara NECO exams...
Jikokin Alhaji Musbahu Zailani kenan masu
rubuta Jarabbawar qarshe ta makarantar
Sakwandire na TopOnwards Science College
Maiduguri, Su 10 cif zasuyi graduation bana...
***************
Assalam Alaikum tsoho me ran qarfe, Tsohon
da ke zaune kan Sofa kyakyawan gaske ne,
kadan ya rage ya cika shekaru chasa'in cif a
duniya, tsufansa me kyau ne, gyara zaman
gilashisa yayi yace Hanifa ce da Balki? Eh mune,
amma bilkisu nake ba balki ba, yayi daria yace
ja'ira, ya jarabawar? Suka ce toh Alhamdulilahi,
duk suka yi shiru, Tsoho yace me bakin shan
qwai menene? Naga magana a bakin ki, Hanifa
ta zumburo baki, tace kaga dai tsoho ka bar ce
man me bakin shan qwai, yace toh ai naga kun
kasa magana, ku fada matsalarku a magance
maku ita, Ke Me Gadon zinare menene? Bilkisu
tace daman Tsoho qara muka kawo ma,
Haneefa tayi charaf tace tsoho mu dai mun gaji,
wao kullum sai Maysah ta samu latti, gashi mun
fara jarabawa, wlh idan bamu bi a sannu ba
wata rana sai an hana mu zana harabawa saboda
latti, Mu gaskia da sakel, a san yadda zaayi
damu, ko a sama mata me kaita ta qarata chan
da lattin ta, Tsoho yayi jimm yace kuyi haquri,
kunsanta da Nawar tsiya, zan mata fada, amma

maganar raba tafiya duk bata taso ba, tun
lokacin yayyunku da sukayi aure tare ake kaisu
makaranta kunga lokaci guda ba za a bar
wannan qaidar ba, Hmm ai daman munsan baka
san laifinta ka fi sonta cikin jikoki, da sauri yace
haba yan jikoki na, wlh duk daya na dauke ku,
ku bari zanyi shawara da iyayenku, ku saurareni
kunji? Sukayi godia suka mai Sallama.
*******
Ta kalleshi tace Tsoho tunda nagama karanta
ma Jaridar bari naje nayi karatu dukda bamu da
paper Gobe sai Jibi, yace RUMAISA'U Meyasa
kike sa 'yan uwanki latti? Kullum ke kadai suke
jira, ko so kuke a hanaku shiga makarantar! Duk
cikin lallabi yake mata magana, ta yi raurau da
fuska tace, kayi haquri InshaAllah zan daina,
yauma don safata ta shige wani gurin ne ai da
bansamu latti ba, yacr donAllah ki daina kinji?
Tace InshaAllah, yace yauwa idan kin shiga cikin
gida ki kiramin Hajia Babba, tace toh Tsoho ta
miqe ta fita, a ranta tace InshaAllah sai na riga
kowa shirin makaranta jibi, ba za a qara jirana
ba sai dai na jira...Tayi Sassan Matan tsoho
domin kiran Hajia Babba, da Sallama ta shiga
dakin Hajia babba ce da Abida (Maman Hanifa)
a dakin, suna ganinta sun ka bata fuska, ta gaida
su ba wanda ya amsata, tace Hajia Babba tsoho
na kiranki, ba ta jira ta ce komai ba, ta fice don
bata son jin zagin da za a jefi kakar ta dashi ba.
Anty Abida ta buga tsaki tace jikar Mayu kawai.
Hajia Babba taja tsaki tace wanda suka gaji tsiya
game da miqewa don ansa kiran mijinta Tsoho.
*******
Gidan Alhaji Musbahu Zailani, wanda yan
unguwa da sauran mutane ke ma laqabi da
GIDAN YAWA, gida ne katon gaske gari guda ne,
me qunshe da sashe sashe, su biyu kachal
mahaifan su suka haifa, shida Qaninshi me suna
Rabi'u iyayensu asalin yan qasar Chadi ne yan
Shuwa Arab, Shekara 2 kachal ya ba qanenshi.
İyayensa sunyi hijira zuwa qasar Nigeria garin
Maiduguri inda suke sana'ar sirfani da
dinki,Bayan Rasuwan Mahaifansu Musbahu ya
rungunmi qaninsa suka cigaba da wannan
sanaar dinki, har Allah ya buda musu, sun samu
İlimi me inganci na arabi da boko. Kafin suka
fara habaka Sanoin su ta wani sigar.. Har suka
zama matasan Attajirai.
A kasuwan da suke Sanaarsu, Akwai Wata
yarinya Karime da ke kawo musu tallan fura
fura, yau da gobe ya sa suka saba da Musbahu
har suka fara Soyayyah, ba ayi wata wata ba ya

kai gaisuwa gun iyayenta, yace ba su da kowa a
Qasar nan sai qaninshi. Mahaifin karime yace
bakomi an bashi karime, ana haka ne diyar
kishiyar Maman karime ta shigo daga tallan
Goro, ta gaidasu, Baban yace sannu Hajjo kin
sha rana shiga kan kabad ki dauko samira na
nan da abinci kici tace to, Rabiu ya bi bayanta da
kallo chan yace Baba wannan fa? Yace hajara
kenan, qanwar Karime ce, amma ba uwarsu
daya ba, uwarta ta rasu, sukace Allah ya ji
qanta, Baban ya miqe yace ina zuwa, ya shige
ciki, Musbahu ya lura Akwai magana bakin
qanenshi, yace yaya dai Rabiu? Yace Yaya
wannan yarinyan ta man, bansan ko babanta ze
ban ita ba, Musbahu yace bari yazo a kwatanta
daman gwara kayi auten kaima, ko da baban ya
dawo Musbahu ya sanar dashi buqatar qaninsa,
Mallam yayi shiru yace baqi taku ba, amma
Hajjo bata da kowa sai Allaj sai ni, Hajjo tasha
wahalar kishiyar uwa, ta na kan sha, Zan baka
hajjo amma sai kayi man Alqawarin cewa zaka
riqe man ita da amana, da sauri Rabiu yace
wallahi na amince baba, zan riqe maka ita da
amana. Yace toh shikenan na baka ita bayan Sati
2 kuzo a daura aure. Sunyi murna gaba ki dayan
su...
*******
Da daddare Mallam ke gayama maman karime
yadda sukayi da meson Karime, murna fal
ranta, Allahu Akabar, ashe zan ga Auren Karime
nah, kai madalla madallah, yace ai ba auren
karime kadai zaki gani ba, harda na hajjo, take
Annurin fuskarta ya dauje dif, tace bangane ba,
yace Qanin Musbahu ke son Hajjo kuma har na
bashi ita, maman karime ta daka tsalle ta re da
riqe qugu tace Kam babban balaeen chan....
2⃣🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕 by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Sai kuma ta
fashe da kuka, yanzu mallam ni zaka tona wa
asiri? Eyi? Yace bangane tona miki asiri ba, dan
ka ga ba ni na haifi hajjo ba shine zaka aurar da
ita ko neman shawara bakayi? Ynx idan tayi
aure wazai na kai mun talla? Ko ni kakeso na
fita tallan da kaina? Takaici ya hana mallam
magana sai kawai ya fice ya bar dakin...
*****
Tadihn su sukeyi irin ta masoyan da, Hajjo ta
shigo da Sallama a fuskarta, Musbahu ya amsa
da murmushi, yace Amaryarmu, nan da nan
karime ta hada gabas da yamma, tace wato
Rabiu ba xai janye ba koh? Me zaayi da wanda
ba a san asalinsu ba? Hajjo ta shige cikin gidan
da sauri tana matsar qwallah, Musbahu ya bata

rai yace haba karime me yasa kike haka neh?
Sai kace ba Mahaifinku daya ba? Charrr uban,
Allah ya sawwaqe, daman wayace ma baban mu
daya? To tsaya kajih yanda abun yake, da ita
kishiyar maman mu ta shigo gidan nan, Agola
ce, kuma da ta rasu, shine babana ya riqeta, ni
kadai ral mahaifana suka haifa, Musbahu yace
najih dai, be kamata kina nuna qyamarki gareta
a fili ba, ko kina kishi ne don ta fiko kyau, wani
mugun ashar ta lalayo ta dinga zage zage da
qyar ya lallabata tayi shiru. Ya shaida mata gobe
zasu je Chadi don sanar da kawunninsu auren
su, ta mai Allah ya kiyaye
******
Ko da Su Musbahu suka isa qasar Chadi suka
tarar da Kanin Mahaifinsu Ya rasu me dakinshi
batafi wata 2 ba itama ta rasu, Musbahu ya kalli
Rabiu yace kaga Rabiu inaga mu tafi da su
Mudassir da labaran Nigeria, yara ne ba su fi
shekaru 10 ba su da kowa yanzu sai mu, yace
Yaya duk yanda kace hakan zaayi...
Haka kuwa akayi Washegari suka kama hanyar
Nigeria. bayan kwana 2 aka daura auren
Musbahu da Karime, da kuma Rabiu da Hajjo.
Dan madaidaicin Gida ya kama musu, suka
zauna tare da yanuwansu Labaran da Mudassiru,
Musbahu yace Karime ta riqe su, fir taqi ita
bazatayi bautan yara ba tun kafin ta fara samun
nata, haka Rabiu ya kwashe su ya kaima Hajjo
su, ta amshe su hannu bibiyu.
*****
Bayan Shekara daya.
A daddafe ta szuwa ta kai kanta bangaren
Karime, kuka takeyi tana kiran Yaya ki
taimakeni, bayana zai balle, Karime da ke zaune
tana tamnar cingam ko kallo bata isheta ba, nan
Hajjo ta xube tana murqususu, amma karime
bata ce mata ci kanki ba, Tunda Hajjo ta samu
ciki Karime ta ji wani tsanarta ya shigeta, jin
haushinta daya ya zaayi hajjo ta samu ciki? Ita
bata samu ba? Ta sha kai ma cikin hari tun yana
qarami amma bata samu nasara ba, Kishinta
takeyi Sai kace kishiyoyi, ta dinga juyi a qasa
amma ko kallo bata samu ba daga karime,
maqociyarsu ce Umm Afeef ta shigo gidan da
Sallama, ganin hajjo a qasa yasa ta qarasa gunta
tana sallami, me ya sameki haka? Ko naqudar
ce? Sannu, ta kalli karime tace kedai bakiji
dadin rayuwarki ba, wai shin mini daya kuke
aure da zaki nuna mata wannan halin ko in
kula? Karime tace Maman Afeef wlh ki fita
idona zamu kwashi yan kallo dake. Cikin

wahalaliyar muryan hajjo tace umm afeef
marata, bayana, ta fita da gudu tana fadin ina
zuwa Bata tsaya ko ina ba sai gidan Unguwan
zoman garin Ummu Anisa, ta ce ki temaka
haihuwa tazo ma hajjo, ai ko da gudu suka fito
suka nufa gidan, har ynx hajjo na qasa ta na
mutsu mutsu, maman Anisa tace kamata
mukaita ciki, Karime tace Waaa? Ai wlh ba zaa
shiha da najasa dakina ba, ummu Afeef ta buga
tsaki tace in fitsari banza ne, kaza ma tayi,
Ummu anisa tace rabu da marar tausayin nan
kamata mu kaita bangarenta, nan suka bar
karime na ta zazaga masifa. Suna ko shiga daki
Hajjo tayi wani yunkuri ta santalo danta, Kai
Masha.. Maman afeef ba ta rufe baki ba sai ga
wani dan ya fito, cikin murna tace Yan biyu-- sai
ga wani dan ya kuma fitowa, Guda maman afeef
ta sake da qarfih, ummu aneesa sai sannu take
ma hajjo, kafin aka gyara hajjo. Da yaranta
maza kyawawa kamar babansu. Ummu Afeef ta
fita waje da sauri taga karime na labe tana
leqe, ummu afeef tayi shewa tace samun Yan
uku sai 'yar baiwa, Karime ta dafe qirji tace na
shiga uku, Yan uku? Maman afeef na fita ta
samu almajiri kayi maza kaje kasuwa kace ma
malam Rabiu hajjo ta haihu ta samu yan uku.
Da gudu almajiri ya ruga.
Karime kuwa kamar tayi hauka, sai sambatu
take tayi, Hajjo ta haihu? Ta samu yan uku?
Kuma maza? Jar ubanchan, wlh bazata sabu ba.
Da balaee nima sai na haihu cikin watan nan
hka ta dinga haukanta...
Da gudu Rabiu da Musbahu suka shigo gidan,
kallo daya zaka musu zaka san suna dauke da
tsantsar farin ciki, Hajjo har tayi wanka tayi
kyau abunta, Rabiu ya kwaso yayan ya rungume,
ya miqa ma yayanshi, Musbahu ya amshesu
tare da musu addua, Allah shi rayaku.. Nan
ummu aneesa tace a bar hajjo ta samu bacci,
Yan gidan kuwa Labaran da mudassiru sai
murna suke tayi Nene Hajjo ta haihu.
Musbahu ya shiga cikin Gidanshi jiki na rawa
yake ta qwalawa Karime kira yana Karime
karime, Hajjo ta haihu har daki ya bita yana
gaya mata, Yan uku ta samu, kuma duka maza,
Bata san lokacin da ta fashe da kuka ba, shi be
ma lura da yanayinta ba, yace wai baki san hajjo
ta haihu bane ba? Cikin tsawa da masifa tace
Tou Sai Me? Ya dan kallota, karime lafiya? Ta
miqe tace ita ta kawo hakan, ta sabi zaninta ta
bar gidan, shiko Musbahu tunani yake me yayi
zafi haka?

***Rannan suna Yara sukaci suna Hassan
Hussaini da Gambo, Yaran nan abun so ne gurin
Jamaa, har yau Karime bata leqo ta gansu ba,
Rabiu wani kuka ta musamman yake ba
matarshi, Hajjo na shan wahaln yan ukun nan,
ba wanda ke tayata da rainonsu, sai Mudassiru
da Labaran, ganin hakan ne Karime ta sami
Rabiu da kuka wai ita dai a bata mudassir da
labaran, ita tana cikin kadaici, waye waye, Rabiu
be ce komi ba yace su koma gun karimen,
Musbahu ya so tambayar ba a si kawai sai ya
share. Karime ta cigaba da riqonsu don kawai
kar Hajjo ta moresu, a hankali a hankali ta
dinga chusa masu tsanar Hajjo.
*******
Abu na Allah cikin Shekaru yaran hajjo 6 har
da yanuku kasancewar duk shekara take
haihuwa wani abun Allah yaranta duka maxa,
Bayan Yan uku ta samu Ahmad da Ibrahim, sai
auta Hafiz har yau Karime ko batan wata ba ta
taba yi ba, an bi Malaman anbi yan tsibbu da
bokaye amma a banza. Musbahu na san Yaran
Yanuwansa sosai, ya sa yan uku da Amad
makaranta Islamiya..
***
A bakin kogi me kallon boader ya hango er
yarinya na kuka gashin kanta ya rufe mata
fuskarta da sauri ya qarasa yace ke me akayi
maki? Dago kanta tayi Ya Salam!! Aljana ce ko
mutun? Cikin hausarta da be fita tace wlh
mutun ce ni, ya sunanki? Sunana Aishalle daga
ina kike? Masu kamen bayih ne suka kamo mu
shine ni na gudo nayo nan, ke er wace qasa ce?
Tace kamaru, yace ina iyayenki? Ta matse
qwallah tace sun rasu da dadewa, yace ta shi na
siya miki abinci, na saki kwalekwalen da zai
kaiki har kamaru, da sauri ta girgiza mai
kai,Tace wlh ba zanje ba, banda kowa a chan,
bauta mukeyi a gidan sarki, kuma na gudu da na
koma zaa fille mun kai. Ka barni a nan kawai,
Musbahu ya tausaya mata qwarai, yace zakije
gidana? Da sauri ta daga mai kai, yace toh biyo
ni, ba gaddama ta bishi, sunyi tafiya kadan kafin
suka isa gida, tun daga soro yake qwala ma
karime kira, ta fito, kai mallam ya kake kwala
man kira kamar wani watan ramadana-- turus ta
tsaya ganin Alajana da gudu tayi daki ta na fadin
bayanka Musbahu bayanka Aljana, yayi daria
yace keee mutum ce, ta dan leqo tace daga ina?
Ya kwashe komai ya gaya mata, shine nace ta zo
ta xauna a gidan nan, Ashar ta saki, Wannan
Alajanar zata zauna dani? Wannan Mayyar? A

gidan nan? Wlh ba dai gidan nan ba, Musbahu ya
fusata yace Gidan ki ne ko nawa? Toh sai ki
hanata xama gidan nan idan kin isa.. Zuciya ta ci
karime ta daka tsalle ta damqo gashin Aishalle
Add 3⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕 GIDAN GANDU💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Aishalle ta sake
ihun wahala, Musbahu ya chapko karime ya
hadata da bango, ya ja hannun Aishalle yayi
waje da ita, karime na kwance kasa amma
bakinta be daina furta zagih da batanci ga
Musbahu ba, Wurin Hajjo ya kaita, tayi sauri fa
lullube jikinta da zanih, yace hajjo ga yarinya
nan danAllah aba ta abinci kuma tayi wanka a
bata kaya, Hjjo tace toh Yaya, Yace Aishalle ki
saki jikin ki, ba abunda...


Read / Download GIDAN GANDU

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album