Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

MUMMUNAN ZATO Book 3 Complete Hausa Novel Document by MUMMUNAN ZATO Book 3


MUMMUNAN ZATO Book 3

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 40950



MUMMUNAN ZATO Book 3

Reading Time: 3 Hours

Added On: 14, Jun 2024

Author: Halima K Mashi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 199.11 kb

File Type: txt

Views: 910+

Download: 756+

Last download: 20 hours ago

Description/Story:
MUMMUNAN ZATO BOOK 3

*📔📔📔 Page 1*

Da gudu ya fito yana kiran "Jabir! Jabir!!" Dai dai lokacin da Jabir ke fitowa daga garejin motoci, inda ya ajiye motar da suka shigo yanzun nan,ya ji muryar Ogan nashi cikin wani firgici, da gudu ya nufo ƙofar falon inda suka yi kiciɓis da maigidan nashi ɗauke da A'isha ga jini na zuba. A guje ya koma ya fito da mota ya shiga suka fizgi motar a guje, duk da haka Uncle gani yake tamkar Jabir ba gudu ya ke ba, ya ce "Jabiru mu yi sauri fa,ƙila ma ta cika."

Suna isa da gudu ya ɗauke ta bai damu da jinin da yake zuba jikinshi ba, ya shiga asibitin yana kiran "Doctor! Doctor!?" Nurses ɗin da suka ganshi tuni suka nufi gurin da ake aje gadon da ake tura marasa lafiya, kafin su iso ai shi tuni ya kai Office ɗin Doctor. Bakin ƙofa suka ci karo da Likitan, shima ya firgita da ganin jinin. Nurse's suka iso tuni ya zube ta kan gadon, suka tura da gudu sai Emergency,shima ya bi su amma kafin ya shiga tuni an turo ƙofa, sauran Nurse's ɗin suka ce "Yallaɓai kayi haƙuri ka jira Doctor za ya yi aikinshi, lokacinne ya kalli jikinshi tun daga rigarshi har wandonshi jini ne. Nan take zuciyarshi ya yanke cewa cikinshi ya zube, ya dunƙule hannunshi ya kai ma bango duka ya kifa kai jikin bangon yana mai jin wani irin raɗaɗi a zuciyarshi.

"Oh Allah! Dama ba zan ga ɗan kaina ba?" Wata zuciyar ta ce "kada ka yi saɓo." Nan take ya ce, "Allahumma ajirni fi musibati." Sai ya saka dangana cikin zuciyarshi,ya yarda Allah da ya bashi wannan shi ne zai bashi wani,ya saka hannu cikin aljihun wandonshi ya ciro wayarshi,layin Alhajinmu ya kira, lokacin da yaji muryarshi yana cewa, "Abubakar ya ya?" Zuciyarshi ta karye ko yaushe in yana gaban mahaifanshi ko yana waya da su ya kan ji shi tamkar yaro ƙarami. Cikin rawar murya tamkar Zai fashe da kuka, ya ce "Alhaji A'isha tayi ɓari muna nan asibiti." Tamkar ya soka mishi ƙaho a cikin zuciyarshi, ya ce,me ka ce Abubakar? Kana nufin meɗakin ka ce ta yi ɓari?" Ya amsa da cewa "Eh muna asibiti." Jabiru yana ta kallon maigidan nashi cikin tausayawa. Bayan ya gama wayar da Alhajinmu ya kira Nafisa ya sanar da ita, Jabiru ya ce maigida ko zamu je ka canza kayan nan? Cikin ko in kula ya ce kada ka damu Jabir, bari mu ga yanda jikin A'ishan yake."

Sai ga Hajiya Jummai da Hadiza sun shigo da sauri, Jummai ta soma kuka tana kallon kayan jikinshi. "Alhaji me zan gani haka? Alhaji ba dai ɓari tayi ba?" Hadiza ma cikin matsananciyar damuwa ta ce "Mun shiga uku ni Dija, yanzun ina A'ishan ta ke?" Yanda suka nuna damuwarsu sai shi ne ya koma yana lallashinsu. A haka Alhajinmu ya same su can sai ga Nafisa, duk da kukan da Jummai ke yi da tagumin da Hadiza ta yi bai sa zuciyar Nafisa yarda da su ba, shiru-shiru Likita sai dai Nurse ta fito da gudu ta ɗauko wancan ta zo da gudu ta koma ciki, don haka sai ya soma fitar da rai da rayuwar A'isha. Nafisa ta zo ta dafashi, "Kayi haƙuri Bros, Allah yana tare damu, insha Allahu Allah zai isar mana komai." Ya saka hannun shi a kafaɗarta, amma bai iya cewa komai ba, sai dai girgiza kai kaɗan yake yi,jim kaɗan Likitan ya fito, Nurse's na biye dashi sun turo ta a kan gado Uncle ya nufo shi yana cewa, "Ya ya Doctor?" Likitan ya ce "jira ni" cikin Office ya shiga,ɗakin da za'a ƙwantar da ita, Nurse's suka turo ta ciki,sai da suka sa ta a gado tare da ruwa sannan Likitan ya ce, "Nurse ɗin su gyara ta da ƙyau, sannan kada su bari kowa ya shigo in da take. Ya fito ya nufi office ɗin shi inda ya samu su Uncle cirko-cirko a tsaye, ya shiga ya zauna yana cewa "Ranka ya daɗe bismilla,ku zauna." Ya ɗauki wani handkachief ya share zufar da ta zubo mishi a fuska, ya ajiye ya dube su. "Ranka ya daɗe yanzun dai muna buƙatar jini ne
" Alhajinmu ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "To sai a gwada mu,in bai yi ba sai a nemo." Likitan ya ce "Ranka ya daɗe ai kai ko ya yi ba zamu ɗibi naka ba saboda girma, sai dai na "Yallaɓai." Uncle wanda tunani da damuwa ta hana shi magana,ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya, ya ce dama kai ba za'a taɓa jininka ba, sai dai nawa" ya ci gaba" Likita cikin ya fita ko?" Cikin ƙarfin hali Likitan ya ce, "Ba zan tantance ba yanzun,da so ma muke musha kan jinin da ke zuba." Uncle ya miƙe "muje gurin ɗiban jinin." Likita ma ya miƙe yana cewa, "Sai mun je an gwada." Ya ce jinina zan iya ba kowa, Likita ya ce "to shikenan,sai mu ɗiba mu gwada lafiyar shi, sannan mu tace."

Cikin ƙanƙanin lokaci suka ɗaurawa A'isha jini, duk mai imani in ya ga A'isha sai ya tausaya mata, don haka suka hana kowa zuwa gurinta.

Ƙwance take tamkar gawa, sannan jini ana sa wani, wani na fita. Alhajinmu da ya je ma da Hajiyarmu da labarin halin da ake ciki, bayan sallar isha'i ta ce da Alhajinmu su je ta duba ta.

Ta tsura mata idanu tana kallonta lokacin da Likitan suka shigo da Uncle, Alhajinmu ya dubi Likitan ya ce "Doctor wane ci gaba aka samu zuwa yanzu?" Likitan cikin karaya ya ce, "Sai dai godiyar Allah, amma lamarin ya ruɗani, don muna toshe nanne can na ɓallewa." Hajiyarmu ta matsa kusa da ita, ta kama hannunta ta dubi Likitan ta ce "Kai ɗannan gaya min gaskiya,ko dai yarinyar nan bata ne?" Likita ya ce tana da rai Hajiya bata rasu ba." Ta ce Innalillahi wa'inna ilaihir'raji'un, wannan kuma wanne irin ciwo ne haka?" Alhajinmu ya ce "Likita yanzun menene shawarar ka?" Likita ya ce "Addu'a kawai ce mafita,don ni ban taɓa karo da irin wannan matsalar ba."

Uncle ya jingina da bango don ya kula zaya iya faɗuwa. Duk da (AC) ɗin dake ɗakin bai hana shi zufa ta yi mishi wanka ba, Alhajinmu ya ce, "wannan sai dai mu ƙara,don kullum cikinta muke." Ya dubi Hajiyarmu "Ina ganin ko zan samu su Malam Yakubu ne?" Ta ce, "Za'a iya samun su ɗin, tunda suma waɗannan mutanan babu abinda ba sa saka ɗan Adam a ciki." Su Alhaji Bello sune suka yi ta ba Uncle magana, lokacin da yake cewa, shi dama tuni yasan A'isha ba zata tashi ba, saboda shi duk matar da ya aura mutuwa take. Yanzun me zai ce da Mustapha? Alhaji Bello da Alhaji Salisu suka ce, "ka daina wannan maganar, kada ka manta cewa, kai Musulmi ne."

Nafisa da Uncle suka ƙwanta gurinta,don anyi-anyi ya je gida ya ƙi, Hajiya Jummai ma da ƙyar su Hajiyarmu suka iya lallashinta, irin kukan da take yi ta so ta ƙwana aka lallaɓata suka tafi (kun ji makirci).

Tun shida na safe Alhajinmu suka iso da su Malam Yakubu, lokacin sun samu Nurse's suna gyarata, suna cire kayan shinfiɗar da na jikinta don haka dole suka jira, Nafisa ta fito ta sanar da su an gama, suka shiga addu'a suka soma yi suna tofa mata, cikin ikon Allah sai ta soma motsi,tana motsa ƙafa, ganin haka sai suka soma karatu,nan ta soma mutsu-mutsu, suka umarci Uncle ya riƙe ta kada ta faɗo. Suna ta karatu can ta soma gunji,suka yi, suka yi ko wanene ya yi magana, amma shiru. Sai dai can suka ga ta miƙe tana hamma, suka yi addu'o'i suka tofa mata, sannan suka ce ya fita ya dai ƙi yin magana ne. Sannan suka tafi da ƙudurin cewa zasu aiko mata magani, suka kuma sake bada shawara game da yawan karatu, sannan ta daina ƙwanciyar la'asar,in zata ƙwanta. To ta ƙwanta kamar da azahar zuwa la'asar, zatayi baccinta hankali ƙwance ga kuma lada.

Bayan tafiyarsu, Likitan ya iso,nan ya duba ta,ya cika da mamakin ganin ta tana numfashi, kuma numfashin ma irin na masu lafiya, Nan suka sanar da shi komai, ya ce "To mun gode ma Allah da yasa aka gano bakin zaren, yanzun in ta ɗan huta sai mu duba lafiyarta." Uncle ya yi hanzarin cewa, "Likita kana ganin za'a samu cikin nan?" Doctor ya dubeta cikin karaya, sannan ya kalleshi "Yallaɓai ba zan iya tabbatar wa ba, saboda ta zubar da jini har da guda-guda,ban sani ba ko har da ɗan tunda yanzun bai wuce ɗan guda ɗin ba."

Uncle ya yi ajiyar zuciya,dama shi tuni ya cire rai sai dai yana roƙo
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download MUMMUNAN ZATO Book 3

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album