Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


WASIKAR JINI!!!
Littafi na Daya (1)
Part A
A wani zamani can baya mai tsawo daya shude a
cikin daular kasashen larabawa anyi wani
shararren
sarki mai suna Aiyuba Ibinin Silhar.Masana
hasashe da masu bincike na wannan zamani sun
tabbatar
dacewa babu wani sarki a duniya kaf wanda yakai
sarki Aiyuba tarin dukiya da kuma karfin sihirin
tsafi,saidai kash,ko kadan bai kasance sadauki ba
ko jarumi mai karfin damtse da iya yaki,amma
saboda wannan dukiya daya tara da kuma karfin
sihirin tsafi sai ya zamo dodo ga dukkan
sarakunan dake nahiyar ya zamana cewa duk
tsoronsa sukeji.Komai yawan dakarun yakin sarki
da kuma jarumtakarsu indai sukace zasu yaki
sarki Aiyuba saidai su sha
kashi.Sarki Aiyuba yana da matar aure guda daya
rak mai suna Hufaira wacce sukayi auren saurayi
da budurwa tun kafin ya zamo sarki wato ya gaji
karagar mulki a wajen mahaifinsa kuma kafin ya
tara dukiya taban al'ajabi.Allah bai bawa sarki
Aiyuba haihuwa ba saida ya shekara daya akan
karagar
mulki a sannan idanunsa suka bude akan fadada
harkokinsa na kasuwanci izuwa ko ina a cikin
duniya,ya zamana cewa duk bangaren da mutum
yaje a duniya walau kasar larabawa,turawa da
bakaken fara da kuma bangaren kasar Hindu da
birnin Sin sai yaga gonaki,gidaje,da rumfuna Na
kasuwa anan na sarki Aiyuba Ibn Silhar.Kuma
gaba dayan fatakensa suna amfani da wani
hatimi guda
daya mai taswirar rakumi da takobi a jikin
kowacce irin haja tasa sai kaga wannan hatimi.
Dukkanin yaransa masu sarrafa duniya suna
tsananin tsoronsa
kuma suna adana masa dukiyar domin idan ka
kuskura kaci amanarsa tofa ka rinka ganin masifu
kenan iri iri na cututtuka masu azaba,kuma ka
rinka
shiga bala'i iri iri kenan har sai kazo gabansa ka
kawo wannan dukiya kuma ka tuba sannan zaka
samu kanka.
Wani babban hali na kirki a tare da
sarki Aiyuba shine ko kadan baya wasa da hakkin
yaransa yana biyansu ladan aikinsu kamar yadda
ya kamata,kuma indai ka shekara guda kana yi
masa bauta kaima ka fita daga sahun talakawa
saidai a
saka ka a sahun attajirai.
A shekarar farko daya hau karagar mulki ne
Matarsa Hufaira ta haifar masa 'ya mace
kyakkyawa ta gaban kwatance mai
sunaNuwaira,koda yake sarki Aiyuba yaso ace 'da
namiji ya samu domin ya gaje shi amma duk da
haka saida yayi farin ciki ainun kuma saida aka
shafe kwana saba'in kullum sai anyi walimar ta
farin cikin samun
wannan 'ya.Attajiran sarakai da matsafa saida
sukazo daga kowanne bangare na duniya suka
halacci wannan biki na murnar haihuwar gimbiya
Nuwaira.Batun maroka kuwa duk wanda ya sami
damar shiga gidan sarautar sarki Aiyuba kakarsa
ta yanke saka domin shi da talauci sunyi hannun
riga.Da yawan marokan haukacewa sukayi
saboda ganin irin tsananin dukiyar da suka samu
wacce bama suba hatta jikokinsu da tattaba
kunnensu sai sunci albarkaci,wasu kuwa kuka
suka kamayi domin basu san ta yadda zasu iya
diban dukiyar ba su tafi
da ita,bisa dole komai hadamar maroki yabar
wata dukiya ya kwashi iya wadda ya iya diba.Yan
fashi kuwa dake kan hanyoyin zuwa birnin
Lailatun Harus wato birnin sarki Aiyuba basu taba
samun ganima ba a rayuwarsu irin ta shekarar da
aka haifi Gimbiya
Nuwaira,wasu ma da yawansu sanadin daina yin
fashin su kenan.
Bayan an kwana saba'in ana walimar murnar
haihuwar ta gimbiya Nuwaira sai baki suka watse
suka koma izuwa kasashensu,a lokacin ne fa
labarin Gimbiya Nuwaira dana mahaifinta ya sake
yaduwa da fantsama a ko'ina cikin
duniya,sunayensu ya zamo abin kwantace,daukak
arsu ta shafe duk wani mai sharafi a zamanin.
Wani babban abin mamaki da yake daurewa
mutane kai dangane da sarki Aiyuba shine babu
wanda yasan a inda yake tara dukiyarsa ko
yake boyeta,
Amma duk sa'adda yaso yayi amfani da dinare
ko lu'u lu'u ko makamancin su kawai zaice aje
guri kaza ne a dauko,ana zuwa kuwa za'a ga
dukiyar koda yawanta yakai cikin gari guda,kuma
koda an san cewa babu komai a wajen,mafi
yawan
wuraren dayake cewa aje a debo dukiyar ma
wulakantattun wurare ne marasa daraka inda
babu
tsaro kamar kududdufai ko inda ake tara shara.
Haka dai arzikin sarki Aiyuba yaci gaba da
habaka ya zamana cewa kullum a cikin gyara
birninsa yake da gine gine na kawa da kasaita
har saida takai cewa a duniya kaf babu wata
kasa data kai tasa
kyawu,tsaruwa da kawa,fadarsa kuwa aljanar
duniya ake kiranta domin komai na cikinta da lu'u
lu'u aka yishi.
Lokacin da gimbiya Nuwaira takai shekara bakwai
a duniya sai kyawunta ya ninka nada,al'amarin da
yasa iyayenta suka kara son ta
kenan ainun fiye da koyaushe.'Yayan masu fada
a ji
kuwa tun daga sannan suka fara kamun kafa ta
neman aurenta saboda matsayin ubanta da kuma
kyawunta,amma sai sarki Aiyuba yayi biris da
bukatarsu komai irin dangantakar dake
tsakaninsa
da iyayensu kuwa,wannan shine abu na farko
daya fara jefa hassada a zukatan sarakunan dake
nahiyar suka fara tsanar sarki Aiyuba.
A yamma da birnin Lailatul Harus wato birnin
sarki Aiyuba akwai wata kasa mai suna
Hirama,sarkin dake mulkin kasar Hirama ya
kasance gagarumin sadauki mayaki mai tarwatsa
maza a filin daga,ana kiransa da suna
Murwatu,shima matsapi ne na gaske,amma bai
kama farcen kafar sarki Aiyuba ba,domin ya taba
jarraba karfin tsafinsa akan na sarki Aiyuba yaji
ba dadi,harma saida ya durkusa bisa gwiwoyinsa
a gaban sarki Aiyuba ya nemi gafara don kada ya
rasa rayuwarsa.
Al'amarin ya faru ne a wata shekara da akayi fari
a kasar Hirama ya zamana cewa
yunwa,fatara da talauci ya addabi mutanen kasar
har takai cewa kananun yara da masu rauni suna
mutuwa.Lokacin da al'amarin yayi tsamari ainun
sai sarki Marwatu yasa aka rubuta wasika ya
tashi
manzo izuwa ga sarki Aiyuba a cikin wasi kar ya
nemi taimakon abinci mai yawa gami da aron
kudade masu yawa domin ya bunkasa harkar
noma a kasar tasa,dama babbar matsalar kasar
itace kasarsu bata da dadin noma sai masana
kasa sunzo sunyi mata aiki sannan kuma suna da
karancin
ruwa,dole ne a buda hanyoyin ruwa daga
kasashen ketare su shigo,kuma a nemi iri mai
kyau na
shuka.
Sarki Marwatu ya dauki alkawarin cewa bayan ya
shekara guda zai dawo da duk kudin da aka ara
masa kuma zai bayar da riba kaso guda cikin
uku.
Lokacin da wannan wasika ta riski sarki Aiyuba
yana zaune akan karagar Mulki a fadarsa ana
tafiyar
da harkokin mulki,ga Gimbiya Nauwara zaune a
cinyarsa kumaga fadawansa da sauran jama'ar
gari sun kewayeshi.
A tsakiyar fadar wadansu kyawawan 'yan mata
ne su bakwai suna ta tikar rawa anayi musu kida
don debe kewa.
A wannan lokacin sarki Aiyuba yana cikin nishadi
da walwala don daka dubeshi kasan cewa farin
ciki ya cika zuciyarsa.Bayan magatakarda ya
gama karanta wasikar sarki Marwatu sai sarki
Aiyuba ya tuntsire da dariya irin tasu ta sarakai
masu jin izza sannan ya dubi 'yarsa Gimbiya
Nauwara yace,'yata kinji
bukatar da sarki Marwatu yazo mini da ita,shin
kin amince na taimaka masa ko kuwa na rabu
dashi?
Kisani cewa duk wannan dukiya dana tara a
duniya badan kowa na tara taba sai domin
ki,kece kadai
kike da ikon fadin abinda za'ayi da ita.Koda
fadawan sarki Aiyuba da sauran jama'arsa sukaji
wannan
batu sai suka cika da mamaki sukayi zaton ma
ko sarki Aiyuba ya sami dan tabin kwakwalwa ne
domin basu ga dalilin da zaiyi wani abu da
dukiyarsa sai ya tambayi 'yarsa wacce ta
kasance yarinya karama 'yar shekara bakwai.A
lokacin da gimbiya taji tambayar da mahaifinta
yayi mata saita yi murmushi sannan ta
dubi sarki tace,yakai Abbana kayi sani cewa kana
daarzikin da zaka iya ciyar da gaba dayan
kasashen dake nahiyar nan tamu kuma ka
wadatar dasu da arzikin da zasu tsira daga
talauci to amma nafi so
kayi taimako a inda ya dace abinda nake nufi
shine wannan sarki Marwatu yana daga cikin
wannan
sarki Marwatu yana daga cikin irin sarakunan da
sukayi maka girman kai,
baya daga cikin sarakunan da suke zuwa
gaisheka duk shekara duk wani abu na farin ciki
idan ya sameka baya zuwa ya tayaka sai yanzu
da bukatarsa ta taso sannan zai nemi
taimakonka.
To kasani cewa bazamuki taimakonsa ba,kasa
akai masa abinci mai yawan gaske kuma a bashi
kudade masu yawa wadanda zasu isheshi ya
gyara harkar noma amma bisa sharadin zai
biyaka kuma ya biya ka riba bayan cikar shekara
guda kamar yadda ya
sharadanta da kansa.In har ya karya wannan
alkawari to duk abinda ya biyo baya kada ya
zargo
kowa face kansa.
Baya ga wanann inaso ka gaya masa a cikin
amsar wasikarsa cewa kai mai arziki ne kuma
attajir uban sarakai inda ma ya nemi kyauta da
an bashi amma rashin biyayyarsa ce ta sanya a
bashi aro.
Koda Gimbiya Nauwara tazo nan a
zancentsa sai gaba dayan mutanen dake fadar
suka cika da tsananin mamaki bisa yadda akayi
Nauwara ta zamo yarinya mai kaifin hankali da
tunani haka, shi kuwa sarki Aiyuba sai ya kamu
da tsananin farin ciki ya dubi 'yan majalisa
yace,kunga wannan yarinyar dole ne ta kasance a
cikinku domin ko babu ni zata iya baku
shawarwari akan harkokin mulki wadanda zasu
amfane ku su amfani kasa gaba daya,kuma duk
abinda ya taso na kudi zata taimaka muku
dashi,saboda zata gaji duk dukiyarta bisa wannan
dalili daga yau dinnan na mika matsayin
Galadima a hannun Gimbiya Nauwara tunda shine
matsayi na kula da duk harkokin kasuwancinmu
da sarrafa kudaden kasa,koda jin wannan batu
sai idanun Galami suka zazzaro hankalinsa ya
dugunzuma kuma ransa ya baci.Ya dubi sarki
Aiyuba cikin alamun tsananin damuwa a lokacin
dayai sauri ya durkusa a gabansa zai fashe da
kuka yace,Haba yakai dan uwana ya za'ayi kace
gimbiya ce zata karbi matsayina alhalin
shekarunta basu kai ta ruke wannan mukamin ba
kuma idan ta karbi wannan
mukami ni kuma wane matsayi zan rike a wannan
majalisa ko kuwa so kake na karayin kasa ne?
Koda jin wannan batu sai sarki ya mike tsaye
daga kan karagarsa ta mulki ya sauko har kasa
inda galadima ke durkushe ya kama kafadunsa ya
tashe shi tsaye ya dubeshi cikin murmushi
yace,Yakai galadima kayi sani cewa har abada
bazan taba wulakantaka ko
kaskantar dakai ba saboda kaine kadai dan
uwana na jini daya rage a wannan duniya,a kan
wane dalili
zaka damu da mukami a cikin wannan fada
alhalin ko yanzu na fadi na mutu kaine zaka gaji
karagata,tunda babu yadda za'ayi gimbiya tayi
mulki bisa dokar wannan masarauta tamu?
Idan kana kwadayin dukiyar da take kai kawo ne
a ofishinka na
kasuwanci idan ka zama sarki komai na
hannunka,ka sani cewa gimbiya babbar
gudunmawa
zata bayar a gareka kuma da babban taimako na
kudi ko nawa ake bukata tunda arzikin da zan
barmata ya ninka duk arzikin dake cikin kasashen
nan na nahiyoyinmu sau goma,daga yau ka koma
matsayin wazirina tunda ka sani cewa tunda na
hau mulki kujerar wazirci babu kowa a kanta,koda
jin
wannan batu sai farin ciki ya lullube galadima ya
kama godiya kamar bazai daina ba,amma yana
hada idanu da gimbiya Nauwara sai ya murtuke
fuska kamar wanda aka aikowa da sakon
mutuwarsa,ita kuwa saita risina a gareshi kuma
ta tayashi murna bisa samun wannan sabon
mukami na waziri.
Nantake sarki Aiyuba yasa aka rubuta wasikar da
sarki Marwatu ya aiko da ita kuma akayi bayani a
cikinta kamar yadda Gimbiya Nauwara ta
bukata,daga nan
sai aka shirya buhunhunan abinci a kalla miliyan
uku bisa keken shanu da rakuma gami da
buhunhunan dinare duba arba'in bisa rakiyar
dakaru dubu dari aka baiwa manzo na sarki
Marwatu suka kama hanya suka durfafi birnin
Hirama..........
Dafatan littafin yayi.?
Kasancewar korape-korapen da najima ina samu
akan cewa ayi wani littapin yaki nikuma banida
lokaci daman kun sani, wannan dinma nayi
rubutun ne tun 2015 yana ajiye shiyasa nace to
ko akwai wanda basu karanta ba wasu kuma
zasu so sake karantawa...
Ina patan zaku bani hadin kanku mu gudu tare
mu zira tare.
WASIKAR JINI!!!
Littafi Na Daya (1)
Part B
.
Aka baiwa wannan manzo na sarki Marwatu suka
kama hanya suka durfafi birnin Hirama.
Al'amarin waziri Ridwan bin Silhar kuwa lokacin
da fada ta watsa sai ya tafi izuwa gidansa cikin
tsananin farinciki tamkar an mallaka masa
duniyar gaba daya
nan take yasa aka shirya walima ta musamman
ya gaiyaci duk manyan abokansa na birnin da
kauye. Washe gari kuwa gidansa ya cika makil ya
batse da jama'a maza da mata,ba'a fara walimar
ba sai bayan anje fada an gama bikin
nadashi,babban abinda ya bakantawa waziri
Ridwan rai shine ba sarki ne ya nada masa
rawani ba na wazirci,Gimbiya Nauwara ce ta
wakilci sarki kuma tun a fada yaga komai ya
sauya na irin ikonsa da karfinsa akan harkokin
arziki na kasa.Hatta dukiyar da ake ajiyewa a
Baitul Mali a gabansa mai kula da dukiyar yazo
gaban gimbiya da lissafin komai kuma yayi bata
bayanin yadda ake sarrafa dukiyar bisa tsarin
tsohon galadima,koda ta fahimci cewa tsari ne
nason kai da son zuciya,domin akwai wadansu
kudade da suke shiga aljihun galadima a banza
maimakon su rinka zuwa hannun talakawa
mabukata,sai ta dubi ma'ajin baitul Malin
tace,yau zan canja tsarin komai na dukiyar dake
cikin baitul Mali kuma zan kirawoka na baka
komai a rubuce bisa yadda nakeson a rinka
tafiyar dashi.
Koda waziri yaji wannan jawabi na gimbiya sai
zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone
kuma yaji ya sake tsanar gimbiya fiye da ko
yaushe,ba komai ne ya janyo hakan ba face ya
san cewa da zarar gimbiya ta sauya tsarin komai
na
dukiyar baitul mali shike nan ya daina samun
kudade masu yawan gaske wadanda dasu ne
yake sharholiyarsa a garin yake yin duk abinda
yaso har ma ake shakkarsa.
Da farko attajiran garin sun dauke
cewa sarki Aiyuba ne yake baiwa dan uwansa
Ridwan kudade shi yasa yake tafiyar da rayuwar
mai
mugun tsada a gidansa da harkokinsa,amma a
yanzu da aka sauke shi daga matsayinsa na mai
kula da bailtu mali sai komai ya sauya ya kasa
cigaba da bushasha kamar yadda ya saba duk da
ci
gaba daya samu a majalisa ba baya ba.
Bayan an dawo daga fada an fara walima mutane
maza da mata,sarakai da attajirai,da masu fada
aji suna ta ciye ciye da shaye shaye a cikin
babban falon gidan Waziri Ridwan amma shi mai
gaiyatar babu shi a wajen sai matarsa Gimbiya
Ra'isa wacce itace take
karbar baki tana sawa ana kaisu inda ya kamata
su zauna,koda Ra'isa taga an shafe kusan rabin
sa'a da fara walimar amma mijinta bai gama
shirin ba ya fito daga cikin turakarsa sai ta tafi
izuwa turakar tasa da sauri.Tana shiga sai ta
iske shi a zaune bisa kujera
ya kifa kansa akan tebur yana ta sheshshekar
kuka,al'amarin daya dugunzuma hankalinta kenan
ta ruga gareshi ta dago da kansa suka dubi juna
tace,Haba yakai Abul Zainur yaya zaka zauna
anan kana kuka alhalin yau rana ce ta farin ciki
bisa babban mukamin daka samu,ga masoyanka
can fa
sun taru a falo ana tayaka murna.Koda jin
wannan batu sai waziri Ridwan ya kyalkyale da
mahaukaciyar dariya,al'amarin daya firgita Ra'isa
kenan ta danja da baya ta kura masa idanu
kawai.Take Ridwan ya tsuke bakinsa ga barin yin
dariyar ya dubeta cikin
yanayi na bakin ciki a lokacin da hawaye ya zubo
masa yace,Yake matata kiyi sani cewa dan uwana
sarki Aiyuba ba matsayi ya kara mini ba tauyeni
yayi domin wannan kujera ta waziri daidai take
da ajiye ice ko dutse abinda bashi da rai wanda
bazai iyayin
ko motsin komai ba,kin sani cewa bani da wani
buri a wannan duniya face na zamo gagarumin
attajiri
wanda babu kamarsa a duniya a tarin dukiya
dajin dadin komai na barwa duniya abin tarihin da
baza'a
taba mancewa dashi ba.
A da nayi tunanin cewa da zarar dan uwana sarki
Aiyuba ya mutu zan cika wannan buri nawa tunda
ni kadai nake da gadon duk abinda ya mallaka
amma a yanzu daya sami haihuwa sai dukkan
burina ya ruguje tunda gimbiya Nauwara zata
gaje dukiyar ce wacce a halin yanzu babu wani
mahaluki a doron kasa daya mallaki a
dadinta.bani da ikon batar da gimbiya Nauwara
ko na kashe ta domin duk abinda zan aikata a
boye sai ya gani da karfin sihirinsa na tsafi.
Babban abin bakin cikina shine na fuskanci cewa
wannan matsayi
na galadima da sarki ya rabani dashi yafi
kowanne mukami daraja da muhimmanci akasar
hatta karagar sarki kuwa...
Dalilin da yasa na fada miki haka shine gaba
daya harkokin kudi na kasar yana cikin wannan
matsayi haka kuma galadima shine da jan
ragama ta zabin sarki kuma shine mai baiwa
sarki shawara akan harkokin mulki,kinga kenan ko
na hau kan karagar mulki gimbiya Nauwara ce
mai jagorantar mutane a fakaice idan tayi aure ta
sami haihuwar 'da
namiji,danta zai iya zama sarki kinga kenan a
karshe nida duk iyalina zamu tashi a tutar babu,ki
tuna cewa a yanzu danmu Yarima Zainur da
shekaru biyu kadai ya girmi Gimbiya
Nauwara,yaushe ne
shima zai girma kuma yaushe ne nima zan hau
karagar mulkin kasar nan har ya gajeni?
Koda Waziri Ridwan yazo nan a zancensa sai ya
fashe da kuka,al'amarin daya karya zuciyar Ra'isa
kenan taji ta kamu da tsananin tausayinsa don
haka sai ta rungumeshi ta shiga rarrashinsa tana
cewa,
Ka kwantar da hankalinka yakai Mijina kayi sani
cewa komai nisan jifa kasa zai fado tunda idan
babu
mutuwa ai akwai tsufa da cuta,da sannu lokaci
zaizo wanda sarki Aiyuba yanaji yana gani
daukakarsa ko ikonsa zasu dakushe kuma ko
yana so ko baya so dole ne ya mutu yabar
wannan karagar mulki da dukiya daya tara a
hannunka tunda dai yanzu ya fara
tsufa kuma 'yar nan tasa yarinya ce karama
kaine kadai shakikinsa idan bai danka amanarsa a
hannunka ba saidai ya barta a hannun bare
wanda zai sami banza ya kwashe tsuntsu daga
sama gasasshe.
Koda Ra'isa tazo nan a zancenta sai fuskar
Ridwan ta fadada da murmushi take yaji wani irin
farin ciki ya lullube shi,kawai sai ya dubi Ra'isa
cikin murya yana cewa yake matata hakika ba
karamin hangen nesa kikayi ba yanzu domin na
tsaya na yi nazari naga cewa duk abinda kika
fada gaskiya ne,kuma banga hanyar da sarki
Aiyuba zai iya tsallake duk wadannan abubuwa
da kika fada ba,koda jin haka sai duk su biyun
suka kyalkyale da dariyar mugunta sukayi ta
dariyar kamar bazasu daina ba.
.
YARIMA ZAINUR ya taso a cikin wani irin hali
wanda yasha bambam dana mahaifinsa waziri
Ridwan domin shi ko kadan bashi da son abin
duniya kuma harkokin sarauta ma basa gabansa,
a rayuwarsa
babu abinda yakeso sama da farauta da kuma
jarumtaka bisa wannan dalili ne ya mannanewa
sarkin yakin birini wanda ake kira Haiman bin
Husein ya rinka bashi horon yaki kuma suka rinka
fita
farauta daji tare.
Saida takai cewa dare da rana Yarima Zainur na
tare da sarkin yaki Haiman,kai watarana ma a
gidan sarkin yaki yake kwana,da yake matar
sarkin yaki bata taba haihuwa ba sai taji ta
kaunaci yarima zainur tamkar dan data haifa a
cikinta,kuma ta rinka kyautata masa
ainun,Al'amarin
daya janyo Yarima Zainur ya shaku da Lahisa
kenan ainun da kuma mijinta Haiman har yaji yafi
kaunarsu a kan iyayensa,sabida ra'ayinsu yazo
daidai da irin nasa na rashin damuwa da duniya
sabanin iyayensa wanda babu abinda suke so
sama dasu tara dukiya mai yawan tsiya kuma su
shagala a cikin jin dadi suyi facala da
warwasawa. Hakance tasa Yarima Zainur yaji
yafison yayi rayuwarsa a gidan sarkin yaki
Haiman.Nan da nan kuwa Yarima Zainur ya taso
da hazaka a bangaren iya yaki da farauta har ya
zamana cewa shi kansa sarkin yaki yana
mamakin irin baiwar da Allah ya yiwa Zainur,
sadaukantaka
tun yana yaro karami da tsananin jure wahalar
karbar horo ko kuma wahalar daji ya shafe lokaci
mai
tsawo na jure gudu,yunwa da kishirwa gami da
taurin kai,kafewar zuciya da tsananin rashin
tsoro.
Lokacin da Yarima Zainur ya cika shekara goma
sha hudu sai ya fara yin abubuwan al'ajabi
wadanda sukasa nan danan labarinsa ya bazu
ko'ina a nahiyar domin a wannan lokaci ne ya
shiga wani daji dake yamma da birnin Lailatul
Hawas wanda a cikin sane wadansu arnan daji
suka kafa sansaninsu.Ance yawan arnan dajin
yakai miliyan uku da doriya,kuma sunfi shekara
dari da wani abu a wannan daji,amma babu wani
abu a wannan daji,amma babu wani sarki daya
taba tunanin ya murkushe su su zama bayinsa
ko kuma ya rinka karbar haraji a hannunsu,gashi
dai ana harkokon kasuwanci dasu na cinikayyar
fatun dabbobi da sauran kayayyaki amma kuma
babu wata
kyakyawar alaka a tsakaninsu da mutanen birnin
Lailatus Hurus walau ta aure ko ta zumunci haka
zalika duk mutumin daya sake ya shiga cikin
iyakarsu yayi farauta koya debo wani amfanin
gona kona daji to kuwa bazai fito a raye ba saidai
gawarsa ta dawo amma sai gashi Jarumi Zainur
ya karya wannan alkadari nasu.
Abinda ya faru ne a wata safiya sa'adda jarumi
Zainur ya shiga daji
domin yin farauta a wannan lokaci yana sanye da
wata tsangalalliyar rigar fata iya cibiyarsa mai
yankakken hannu,wandon jikinsa na fata ne dogo
kuma matsatstse,takalman dake kafarsa ma na
fata
ne masu madauri iya gwiwa yana ruke da wata
baka babba mai kyau da daraja kuma ya rataya
kuttun
kibiyoyo a bayansa.
A gefen cinyarsa ta hagu da dama akwai
wadansu gajerun adduna guda biyu a daure kuma
a cikin kufensu da yake Allah ya yiwa Yarima
Zainur kira mai kyau gashi dogo kuma mai
matsakaicin kaurin jiki ga tarin gwanji kuma a
murde
yake duk wanda ya ganshi a wannan lokaci sai ya
burgeshi kuma sai yayi masa kwarjini.Saida
yarima Zainur ya shafe kusan sa'a hudu a cikin
dajin yana farauta amma bai hadu da wata
dabbar kirki ba face kananun dabbobin daji kamar
zomaye da tsuntsaye,al'amarin daya bata masa
rai kenan domin a rayuwarsa babu abinda yakeso
idan ya shiga
farauta face ya hadu da babbar dabba irin su
zaki,kura,damisa da sauransu wadanda zai fafata
dasu ya murkushe su da karfin tsiya ya kashe
sannan ya murkushe su da karfin tsiya ya kashe
sannan ya fede su ya kwashe abubuwan dake da
amfani a jikinsu yakai su kasuwa ya siyar.Wani
lokacin kuma dabbar da ranta zai daureta ramau
ya sabota a kafadarsa ya shiga da ita cikin gari
saidai kaga jama'a nata binsa du....ana mamakin
irin
wannan tsananin jarumtaka tasa.
Sa'adda Yarima Zainur ya shafe kusan sa'a hudu
yana farauta ya
sami nasarar harbo wani tsuntsi daga sama koda
tsuntsun ya fado kasa matacce sai murna ta
kama
Zainur saboda dama a wannan lokaci ya fara jin
yunwa nan take Zainur ya fige tsuntsun tas
sannan
ya shiga hada wuta ya fara gashi,shi dai wannan
tsuntsun kato ne mai tsoka sosai,kuma namansa
yana da matukar dadi da tsada a kasuwa koda
tsuntsun ya fara gasuwa yana digar maiko sai
Yarima Zainur yaji alamin takun sawaye a
bayansa,cikin hanzari ya mike tsaye ya zare
addunansa guda biyu yana mai gyara tsayuwa dif
sai yaji shiru wato takun sawun ya dauke tamkar
daukewar ruwan sama.Zainur ya cigaba da
tsayuwa
a inda yake batare daya motsa ba,kwatsam sai
yaga wadansu arnan daji sama dasu dari bakwai
suna
fitowa gaba dayansu kawai sai babbansu wani
narkeken kato abin kwatance ya tunkari inda
wannan
tsuntsu na Zainur yake,kawai sai ya dauke
tsuntsun ya yagi cinya guda ya kuma ci,al'amarin
daya fusata yarima Zainur kenan ya dakawa
narkeken katon tsawa yace dashi ya aje masa
namansa kada ya
cinye.Koda jin haka sai katon ya dubi sauran yan
uwansa ya tuntsire da dariyar mugunta
maimakon ma ya ci gaba da cin naman tsuntsun
sai ya jefa
naman cikin wani bakin ruwan tabo ya tattakeshi
da kafafunsa kuma ya cigaba da kyalkyalawa
Zainur dariyar mugunta.
A wannan lokaci ne fa jikin Yarima Zainur ya
kama tsuma kamar maijin sanyi zuciyarsa kuwa
ta kara tafarfasa kamar zata kone,kwatsam ba
zato ba tsammani sai arnan dajin sukaga Zainur
ya daka tsalle sama daga inda yake tsaye tamkar
an cilloshi daga cikin BAKA,kafin wani daga cikin
arnan dajin
yayi wani yunkuri tuni Zaiyanu yasa addarsa ya
sare wuyan wannan kato wanda ya bata masa
naman daya gasa,take kan katon yayi sama a
lokacin da jini
yayi feshi daga cikin dungulmin wuyan ya bata
wasu daga cikin yan uwansa.Koda ganin abinda
ya faru
sai ragowar arnan dajin suka afkawa yarima
Zainur gaba dayansu sukayi masa rundugu da
niyar suyi gutsun gutsun da sassan jikinsa.
Kaico tsautsayi ba'a sa masa rana kuma ita
masifa a kwance take duk wanda ya tsokanota
akansa takan kare,koda Yarima Zainur yaga
wadannan miyagun arnan daji masu naci kamar
suci babu sun afko masa gaba dayansu sai ya
durkushe kasa yayi wata irin
katantanwa yana mai zabtare musu kafafu a
lokaci guda kuma ya doki kasa da hannunsa
guda yayi
tsalle a sama kai kadan ya fafe cikin da yawansu
da addunansa biyu,sai gashi ya tarwatsa su da
karfin tsiya,ai kuwa sai ya sami dama ya rinka
kutsawa ta cikinsu yana sara da suka cikin wani
irin bakin zafin nama tamkar jikinsa bana jini da
tsoka bane,duk
inda yasa gabansa saidai kaga maza na zubewa
kasa kamar ana sassabe a gona.
Babu abinda
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On WASIKAR JINI 1 to 8
avatar
abdulrasheed-yusuf

4 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment