Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

firgita da yadda ya nuna ƙin cikin kai tsaye haka.Ya dafo kafaɗun Adnan yana bashi baki akan ya amshi cikin tunda da aure suka samesa, sannan haihuwa is a big blessing da Ubangiji ke wa bayinsa. Amma maimakon Adnan ya ɗauki shawaran doctor Peter sai ma ya sake ɗaukan zafi yana tabbatar masa da cewa dole cire cikin za a yi don baya buƙatar haihuwa a yanzu.Fitar Hannah a guje daga office ɗin tana gunjin kuka shi ya ja hankalin AD Dukku, ya bi bayanta cikin hanzarin bayan ya sake jaddada kalmar roƙo ga Doctor akan ya bashi ko wani magani ne da zata sha cikin fita tunda sati shida kacal ne.Doctor Peter bai samu amsa masa ba, AD ɗin ya fice don rufawa Hannah baya.

A jingine jikin motarsa ya sameta tana kuka sosai,ya ɓalla mata wani irin harara yana magana cikin tsawa yake faɗin, "Ni zaki fito ki bari a gaban likita ki zo nan kina kuka Hannah? Kukan cire cikin ki ke yi kona soyayyar da ki ke wa cikin da uban cikin? To bari kiji ko mutuwa zaki yi sai an cire cikinnan ban shirya haihuwa yanxu ba." Ya ƙare maganar yana komawa ciki ya barta a tsaye tana cigaba da kuka mai taɓa zuciya.Bata taɓa tsamannin Adnan zai ƙyamaci haɗa zuri'a da ita ba,duk da cewa ta san baya sonta amma hakan bai sa ta taɓa yin hasashen zai iya nuna bayason haihuwa da ita ba.Don abinda zuciyarta ta kimsa mata kawai shi ne ita ce da baya so, shiyasa ba zai so haihuwa da ita ba, ba wani maganar rashin son haihuwa yanzu bane ba yayi ɗin. Tana nan tsaye tana kuka ya dawo hannunsa riƙe da ledar magungunan da doctor ya rubuta ya saya,wanda a ciki har da takardan wani maganin zubda ciki da doctor Peter ya rubuta masa bayan ya tura masa kuɗi masu nauyi a account ɗinsa.Don da fari Doctor ɗin yaƙi bashi goyan baya akan a cire cikin,sai da yaji batun kuɗi sannan ya aminta da rubuta masa maganin da zai zubda cikin sauƙi idan ta sha.

A jikinta ya yi wurgi da ledar magungunan yana bin ta da wani mugun kallon tsana, kai kace ita ce ta yiwa kanta cikin ba shi ba.Hannah ta sunkuyar da kai tana cigaba da kuka mai sauti, hakan ya sanya shi daka mata tsawar da ya tsaida kukan babu shiri.Ta ɗago idanunta dake zuban hawaye ta ɗaura a kansa tana faɗin, "Don Allah Adnan kar kace sai an fidda cikinnan,wallahi ina son sa tamkar yadda nake son ka.Ka barni da abuna domin ba zan taɓa iya zubda da kyautar da ba kowa Ubangiji ke yiwa ba, don wasu na can na nema da kuɗi ido rufe ba a basu ba.Amma kai an baka kana so ka yiwa Allah butulci sabida kawai baka sona, shiyasa ba za ka so haɗa zuriyyah dani ba ko? Miye aibun soyayyar da nake maka Adnan, miye laifi don an jarabci zuciyata da soyayyarka...." Kukan da ya sake taho mata ne ya hanata ƙarisa kalamanta, ta dinga yinsa tana ji tamkar ta shiɗe sabida yadda zuciyarta ke tsananin zafi.Ga zazzaɓin da ya sake rufeta dukkanin jikinta na ɗaukar rawar sanyi, wanda sanyin AC dake kunne ke sake tunzara rawar da jikin nata ke yi.Adnan da ke saurarenta har ta dasa aya tana cigaba da kuka, ya kasa cewa da ita uffan don a yadda zuciyarsa ke tafasa da ɓacin ran samuwar cikin yanzu, yana cewa zai yi magana to ba alkhairy zai faɗi ba.

Sannan yana ganin tunda Doctor ya rubuta masa maganin zubda cikin, gani yake yi cikin ma ya zube ya gama.Don haka bashi da lokacin ɓatawa wajen sake jaddada mata ƙudirinsa. Ya yi biris da ita tana faman kukan da ke sake ƙona zuciyarsa,amma bai sake tanka taba har suka isa wajen wani babban pharmacy ya faka motar.Ya fita cikin zafin nama yana barin Hannah da bin bayansa da kallo, zuciyarta na sake matsewa da wani irin abu mai nauyin gaske.Bai jima ba ya fito hannunsa riƙe da wani ƙaramin leda, ya buɗe motar ya shiga ya tayar suna hawa kan kwalta.Kallo ɗaya ya sake mata ya ɗauke kai,bai sake duban inda take ba har suka isa gida.Ta rigashi ficewa daga motar ta nufi cikin gidan da gudu-gudu tana cigaba da kuka sosai.A ɗakinta da ke sama ta zube bisa bed tana ji tamkar kanta zai rabe gida biyu, ga zuciyarta da tayi mata mugun nauyin da take ji tamkar an ɗaura mata bulo.Dukkanin jikinta na sake ɗaukar rawar zazzaɓin da ke huda cikin ƙashinta.A haka ya turo ƙofa ya sameta, ya cilla ledar magungunan bisa kan gado yana magana cikin dakiya ya furta, "Ki tashi ki nemi wani abu kici sai ki sha magungunan zazzaɓin gasu nan,sannan ki tabbatar dukkaninsu kika sha zan yi wanka da sallah in dawo don ganin kinyi yadda nace ɗin.Daga haka ya fice daga ɗakin ya bar Hannah na cigaba rasgar kuka, tayi mai isarta kafin ta lallaɓa ta yo wanka ta fito ɗaure da alwala.Da ƙyar a zaune ta gabatar da sallar magriba da ya riskesu akan hanya,ta idar da sallar tana jan jiki ta koma gado.Wayanta ta ɗauka ta kira Diana ta ce ta kawo mata fresh milk mara sanyi, ta kuma yi mata warming meat pie da ke fridge.Koda Diana ta kawo mata kaɗan ta iya cin meat ɗin ta sha madarar mai yawa ta aje.Ledar magungunan ta janyo tana duba su ɗaya bayan ɗaya,ta tsaida idanunta akan ƙaramin ledar da ya fito dashi daga pharmacy ɗin da suka tsaya dashi a hanya.Haka kawai ta ji a jikinta maganin bai kwanta mata ba, sai ta ware shi daban tana ƙin shan sa, ta ɓalli sauran ta sha tana komawa ta kwanta hawaye na cigaba da kwaranyowa daga cikin idanunta........✍🏻



*Pay 500 in to this account number👇🏻*
*0504192664 Ibrahim Aisha Dansabo GTbank*
*OR*
*PAY IN TO DIS ANOTHER ACCOUNT* 👇🏻
*8167768704 AISHA* *DANSABO IBRAHIM*
*ACCOUNT NAME:OPAY*
*Evidence of payment to this number:08167768704*


🤳🏻 *INA MASU RIƘE DA WAYAR HANNU KUNA TA'AMMULI DA KAFAFEN SADARWA? TO ALBISHIRINKU DOMIN KUWA GA A.ƊANSABO DATA SERVICES.* *TA ZO MUKU DA TSARIN SAYEN DATA AKAN FARASHI MAI SAUƘI. DATA BUNDLES KAMAR NA👇🏻*
*MTN*
*GLO*
*AIRTEL*
*9MOBILE*
*MONTHLY VADILITY 💃🏻*

*DUK AKAN FARASHI MAI SAUƘI KUMA A SAUƘAƘE.KE DAI KAWAI KI NEMI A.ƊANSABO DATA SERVICES AKAN WANNAN LAYIN NATA 08167768704 DOMIN ƘARIN BAYANI KO BIYAN KUƊINKI DOMIN SAYEN DATARKI A SAUƘAƘE* 💃🏻💃🏻💃🏻



#Lovestory#
#Najma#
#Aysha Ɗansabo Lemu🥰
[3/11, 1:35 PM] Aysha Dansabo Lemu😘😘: 📱 *NUFIN ALLAH...!* 🤲🏻
*Arewabooks@ayshadansabo*

*Paid book:500*

*Chapter 15*

_Free page_

Tamkar wacce aka dallawa mari haka ta tashi zumbur ta diro daga bed ɗin, sabida tunawa da tayi da cewa zai shigo tabbas ya duba kota sha maganin.Ta san halinsa sarai duk abinda ya faɗesa sai ya cika shi, don baya magana biyu ko faɗin abinda ba haka yake a zuciyarsa ba.Ta janyo ledar maganin da bata sha ɗin ba ta ɓalli guda biyu kamar yadda aka rubuta,ta nufi toilet tayi flushing ɗinsu ta dawo ta kwanta. Koda da ya shigo ya sameta a kwance idanunta a lumshe hawaye na kwarara daga cikinsu,sai ya nufi inda magungunan suke yaba duba one by one.Ganin duka ta ɓalla ta sha ya sanya shi sauke a jiyar zuciyar da ta jiyo sautinsa,hakan ya sake tabbatar mata da cewa a kwai wata a ƙasa kenan.Sai ta sake rintse idanunta tana hana kanta yin duk wani motsi da zai gane idanunta biyu ne.Ya tako zuwa bakin bed ɗin ya yi tsaye yana ƙare mata kallo, kafin a hankali ya zame ya zauna daga bakin gadon.Hannu ya kai ya janye rufan da tayi sabida sanyin da take ji na zazzaɓi, ya aza hannayensa duka biyu ya tadota zaune.Har lokacin ta kasa buɗe idanunta da sukai masifar yi mata nauyi, sai da taji hannunsa cikin rigarta sannan tayi saurin buɗe idanunta da suka ɗan kumbura ta aza a kan kyakykyawar fuskarsa da ya tamketa sam babu annuri. Bai kalleta ba ya sauke rigarta zuwa ƙasa yana yin baya da hannunsa ya ɓalle huck ɗin bra ɗin da ke jikinta,tsayayyun ƙirjinta da suka sake cika suka bayyana a fili.Ya dinga binsu da kallo tamkar mai son gano wani abu a jikinsu,kafin a hankal ya kai baki ya sumbacesu yana faɗin, "Ban shirya bane Hannatu, sam ban shirya zama Daddy a daidai wannan time ɗin ba.Dole cikinnan a cireshi don ba zan iya amsarsa yanzu alhali duka ban gama morarki ta yadda za a ce har kin yi ciki ba." Ya ƙarisa maganar yana kai bakinsa kan ƙirjinta ya yi musu wani irin sumbatar da ya sanya ajiyan zuciya ƙwacewa Hannah.Kalamansa suka dinga ƙona zuciyarta tana ji sam bata ƙaunar ganinsa ma a gabanta.Ganin yana son raina mata wayo da salonsa ya sanya ta sakar masa kuka tana faɗin, "Banaso AD, please ka daina taɓani bana son hakan tunda kana ƙyamar haɗa jini dani, don kawai baka ƙaunata." Yadda tayi maganar ta motsa zuciyarsa da gaske,amma bai bari ta gane hakan ba don ya riga ya sanyawa ransa ƙin cikin da kuma ɗaukar alwashin rabata dashi.Don haka bai sake cewa komi ba ya tureta daga jikinsa bayan ya gama yamutsa ƙirjinta da tsotsesu son ransa.Ya fita ya barta tana kuka sosai mai asalin cin rai da motsa zuciyar duk wani mai sauraranta.Tunda ya yi wannan fitar bata sake jin ɗuriyarsa a cikin gidan ba har ta kwanta bacci, ta farka ne cikin tsakiyar dare sakamakon wani amai da ya tadata ta nufi toilet ta dinga kwarashi.Ta fito daga toilet ɗin kenan bayan ta wanko baki da fuskarta ta jiyo shigowar motarsa cikin gidan.Ta dubi agogon ɗakinta wanda ke nuni da ƙarfe biyu ne har da rabi na dare, ta janyo ƙafa zuwa bakin gadonta tana ji zuciyarta na sake ɗaukar zafi da ƙuna.Tana jiyosa ya hawo upstairs ɗin ya nufi ɗakinsa, tamkar ta bisa ta ga idanunsa amma takaicin yadda yake ƙin cikin jikinta da rashin ƙaunarsa gareta ya hanata yin hakan.Sai ta koma ta kwanta zuciyarta na kisima mata abubuwa da yawa a kansa, sannan batun cire cikin na zaune daram a zuciyarta tana tunanin yadda zasu kwashe dashi zuwa gobe idan ya gane bata sha maganin ba.Ta dinga faman tunanin hanyar da zata bi don ganin ta tseratar da cikin jikinta daga bazaranar da AD ke yi, na sai an zubda shi dole.Tunaninta ya tsaya akan ta kira Momynsa da safe ta sanar da ita halin da ake ciki, don ita kaɗaice ke sanya shi abu ya yi ko baya so.Amma baya ga ita baya jin magana ko shakkar kowa, yin kominsa yake gaba gaɗi musamman da ya samu kakarsa ta ɗaure masa gindi bata son ɓacin ransa ko ƙanƙani.Da wannan decision ɗin da ta yanke na sanar da Momynsa halin da ake ciki, ta samu bacci ya sace ta ba tare da tayi tunanin bi ta kan AD Dukku da ya dawo cikin wannan tsakiyar daren ba.Sabida ba yau ne karon farko ba,ya rigada ya zame masa sabo yawon dare zuwa club ya dawo cikin tsakiyar dare.

**********
*Kaduna.*

Najma a part ɗinsu Nasreen ta tare har dare, sai hiransu suke yi da Nabeelah wacce har tafi Nasreen son hira ma sosai. Sai around 10pm ta tashi zata koma part ɗin Gwaggo amma sai Momy ta hana, ta ce mata kawai ta kwana anan ɗin don Daddy ya ce ma gabaki ɗaya zata dawo side ɗin da zama ne wajen ƴan uwanta su Nasreen. Suka cigaba da hiransu rabi kuma suna kallo, gefe guda kuma su Nasreen hankalinsu na kan wayoyin hannunsu suna chart da friends ɗinsu.Kiran Anty Jiddah ne ya shigo wayar Nasreen vid call, ta ɗaga da murmushi akan fuskarta tana faɗin, "Sweethrt sai yau kika tuna damu? Ina ta kira wayarki a kashe so nake in nuna miki sabuwar Sis da muka yi a gidan fa." Nasreen tayi maganar da wani irin shagwaɓar da ya bai wa Najma mamaki.Ta dubi Nasreen ɗin lokacin da muryar Jiddah ya ratsa kunnuwarsu tana faɗin, "Sorry dear! Hubby ne ya kashe wayan ya amshesa don ya ce bani da time ɗinsa sai na kiran waya gida kamar a kaina aka fara nesa da ƴan uwa.Yanzu haka ya fita ne ya barni da ƙyar na gano inda ya jefa min wayar, shi ne fa yanzu na kira." Nasreen ta jinjina kai tana faɗin, "Lallai ne Uncle Muhsin, so ya london hope kina enjoying?" Jiddah ta furta, "Sosai Sis, ina Momy ne? Na kira wayarta busy." Nasreen ta bata amsa da faɗin, "Yanzu ta shige room may be suna waya da Daddy ne." Jiddah ta gyaɗa kai tana komawa kan batun Nasreen na cewa sunyi sabuwar Sis.Nasreen ta haska mata fuskar Najma da hankalinta ke kan TV tana faɗin, "Hey! Najma ɗago ku gaisa da Anty Jiddah." Najma ta waiwayo da murmushi akan fuskarta tana kallon allon screen ɗin wayar, suka gaisa da Jiddah cikin fara'a sosai,don ita ma yawan murmushi gareta tamkar Momy. Sun jima suna hira tsakanin Nasreen da Anty Jiddah, sannan Nabeey ta amshi wayar ita ma suka yi maganar tana sanar da Jiddah lallai a siyo mata tsarabar london.Najma ta dubi Nasreen bayan sun kammala wayar da Anty Jiddah ta ce, "Gaskiya Sis Anty Jiddah duk ta fiku kyau!" Nasreen ta saki murmushi tana faɗin, "Ita kuma duk kyawunta Yaya AD ya fita ba." Najma tayi murmushi tana jinjina kai ta ce, "Taɓ! Lallai kam kyakykyawane idan har yafi Anty Jiddah kyau." Nasreen ta saki smile tana faɗin, "Zaki gansa ai watarana da idonki Najma, daga lokacin zaki tantance cewa ya fita kyan.Amma fa Yayan namu ba ƙaramin tsoronsa muke ba, don fitinanne na bugawa a jarida." Cikin nuna halin ko'inkula Najma ta jinjina kai ta ce, "Dama su Maza haka suke idan sun ga sune manya a gida, sai suyi ta takurawa ƴan matan gidan da nuna musu shegen son girma da isa.Su Yaya Auwalun gidan Baba Hakimi ma haka suke wa ƙanninsu su Lubah mazurai, ni kaɗaice basawa hakan wallahi." Najma ta kai ƙarshen maganar tana tunowa da aminanta su Lubah, waɗanda suka gama shan waya dasu ɗazu suna ta taya ta murnar tayi waya.Nasreen ta sake sakin ƙaramin murmushi tana duban Najma kai tsaye ta ce, "Hmm! Sis ke dai kawai ayi shiru, amma duk yadda zamu kwatanta miki waye Yaya AD ba zaki gane ba." Daga haka suka rufe chapter ɗinsa Najma na basu labarin kalar rayuwar da suka yi a makarantar ƴan mata dake basawa.Nabeelah ta dinga tuntsura dariyar yadda Najma ta sha wuya a hannun jeniors kafin ta gyare, ita kuma Nasreen birgeta Najma ta dinga yi tana yaba sanyi da daɗin amon muryarta da ke fita a nutse.Sai ƙarfe 11pm na dare suka nufi room ɗin Nasreen don kwanciya, ita kuma Nabeey ta wuce nata room ɗin da ke manne dana Momy daga ciki.

Washegary Nasreen na bacci Najma ta sulale ta koma part ɗin Gwaggo, ba tare da ta jira kowa ya tashi daga sashinsa ba.Ita ma kuma bata yi karanbanin sake zuwar ma su Rabi kitchen neman tayin aiki ba, duk da cewa abin na ranta tana kuma da burin son ta iya girke-girke kala-kala.Ko anan part ɗin Gwaggo ta tadda babu motsin kowa ya tashi a cikinsu,hakan ya sanya ta lallaɓa ta shige room ɗinsu ta samu Inna Mairo bisa gado ita ma tana faman juyi.Don ita ma ba gwanar komawa baccin safen bace, don haka sai suka ɓige da hiransu har gari ya sake wayewa sosai rana ya fito.Wanka suka yi duka suka shirya cikin shiga mai kyau na tsadaddun suturun da aka siya musu.Sosai Najma ta sha kyau cikin wasu skat da riga ƴan kanti masu shegen kyau! Rigar a sake take bata kama jikinta ba, amma kuma ta bayyana tudu da cikar ƙirjinta sosai.Waɗanda suke a tsaye cur cikin push-up bra da ya sake ɗagosu ya tsayar. Ba gwanar yin kwalliya bace don bata ma iya ba kai tsaye za a ce, tunda bata karambanin yinsa ma.Iyakarta shafa powder ta sanya kwalli da man baki, hodar ma fara tafi shafawa don ta kance baƙin fuskarta da farar powder zata fi dacewa.Sai dai a yanzu ta ƙaryata hakan, tunda ta shafa haɗaɗɗiyar powder ɗin mary kay mai tsadar da Nasreen ta saya mata. Sai ta ga tabi baƙar fuskarta tayi mata kyau,don kalar da aka zaɓar mata dama don irin su baƙaƙen fata aka yisa.A yanzu ɗin ma powdar kaɗai ta shafa ta goga man baki, ko tozalin ma bata sanya ba don babu shi a cikin kayan shafan da aka siya mata.Tare da Inna Mairo da tayi shar cikin jar doguwar rigar atamfar holland suka fito xuwa falon Gwaggon,sunyi xaman kamar mintuna goma sannan Gwaggon ta fito.Tayi kyau cikin riga da zani na wani irin material da suka kasa bambace voile ne ko kuma wani abin daban.Ta zauna a kujeran da tayi sabo da zama a kai, idanunta akan Najma wacce tayi mata mugun kyau da shigar jikinta, ta dinga kallonta tana amsa gaisuwar da Najmar ke mata.Inna Mairo ma suka gaisa da Gwaggo cikin girmamawa, Gwaggon na tambayar Najma amma dai gudowa tayi bata bari su Nasreen sun tashi ba? Najma tayi murmushi kawai ba tare da ta iya cewa komi ba.Suka haɗu sukai breakfast a nan tsakiyar falon Gwaggon, wanda aka shinfiɗa babbar ledar cin abinci kamar ko yaushe a saman carfet ɗin dake tsakiyar falon. Suna kammalawa Nasreen na shigowa cikin shirin fita skull,ta sha gayu cikin wani haɗaɗɗen gown na lace.Wanda kallo ɗaya zakai ma lace ɗin da ɗinkin da ya samu kasan cewa kuɗi sunyi kuka.Sannan colour ɗin lace ɗin da ya kasance black and silver ya haske farar fatar Nasreen ɗin, ya yi mata mugun kyau tamkar ka saceta ka gudu.Ta samu waje ta ɗosana ɗuwawunta tana gaida su Inna Mairo cike da ladabi,suka amsa da fara'a Inna na tambayar cewa halan skull xata wuce? Nasreen ta bata amsa da cewa, "Eh!" Najma ta dubi Nasreen tana ɗan yin ƙasa da murya ta ce, "Morning Sis, hope kin tashi lafiya?" Nasreen ta ballawa Najma harara tana faɗin, "Bansani ba ƴar rainin sense, kawai saina dinga tashi bacci bana ganinki kin ɓace ɓat a sashin baki ɗaya kin gudo nan kamar wacce ta kwana a ƙaya." Najma ta saki dariyarta mai kyau ta ce, "Sorry Sis! Ni ban iya wannan baccin safen bane shiyasa na gudu wajen Innata kawai." Nasreen ta sake hararanta tana miƙewa tsaye tare da gyara zaman veil ɗinta ta ce, "Ni xan wuce skull Sis sai 4 zan dawo yau,kinga kenan zanyi missing ɗinki." Najma da ƙaunar Nasreen ke sake kamata, sai ta saki murmushi mai faɗi tana faɗin, "Nima haka, but ayi karatu da yawa Sis sai kin dawo." Nasreen ta ɓata fuska tana cewa, "Babu ma rakiya kenan ko?" Najma da su Gwaggo suka sanya dariyar yadda Nasreen ɗin tayi maganar cike da shagwaɓarta na sabo.Najma ta tashi tana duban Inna ta ce, "Inna bari na rakata, daga can zan shiga mu gaisa da Momy." Inna Mairo ta jinjina kai ta ce, "Adawo lafiya, nima ki ce ina gaidata kafin in shigo." Daga haka Najma suka jera da Nasreen suka fito har zuwa parking space na gidan.Najma na sake yaba tsaruwar gidan da kyawunsa duk idan ta fito harabar gidan.Sai da motar Nasreen ta fice daga gate ɗin gidan sannan ta juya ta nufi part ɗin Momy ɗin.

**********
*Port Harcourt.*

Lafiya lau ta tashi ta gabatar da sallar asuba,jikinta bata jin ciwon komi sai kasala da tarin damuwa da tunanin da suka cunkushe zuciyarta.Don ji take yi sam ba zata yadda AD ya samu nasarar rabata da cikin jikinta ba,don tana tsananin son cikin da gaske. Wayarta ta janyo ta turawa Momynsa text tana sanar da ita halin da take ciki, ta dinga bin saƙon da kallo bayan ta tabbatar da tafiyarsa.Zuciyarta taji na ɗan yin sanyi,domin tasan matuƙar saƙon ya isa ga Momynsa ta kuma karanta to tabbas cikin ya tsira ya gama.Ta miƙe da ƙyar ta isa ga bed tana son sake rintsawa kafin 6:30am ta cika ta fita don sama masa abinda zai ci kafin ya wuce office.Wani irin bacci ne mai ƙarfi ya ɗauketa, bata tashi farkawa ba sai 7:30am.Ta diro a gigice daga bed ɗin tana kallon time, zuciyarta na bugawa da tunanin yana dab da fitowa don wucewa office. Kusan a guje ta sauka zuwa down stairs don shirya masa abu mai sauƙi da zai ci.Ta tadda Diana kusan duk ta kammala aikin gyaran downstairs ɗin,ko'ina na fidda sassanyar ƙamshi mai ratsa zuciya.Toasting bread tayi masa ta dafa ruwan tea ta soya egg, ta juye komi a inda ya dace ta ɗakko zuwa dining area dake nan ƙasa.Tana aje tray ɗin yana ƙarisowa wajen cikin shirinsa tsaf!Daddaɗan ƙamshinsa na cika wajen yana ratsa kafofin hancinta.Ta ɗaga idanunta tayi masa kallo ɗaya tana mai saurin yin ƙasa da kanta,don wani irin tashin hankali ta shiga da ganin kallon da ya jefo mata.Da ƙyar ta iya gaida shi ƙirjinta na faman bugun da ta kasa dubansa, sai ma ɗauke kai da ta sake yi tana jin wani fargaba na sake shigarta.Ya ja kujera ya zauna yana fara haɗa tea da kansa ba tare da ya jira ta haɗa masa ba,ganin hakan ya sanya ta saurin ɗago kai ta saci dubansa zuciyarta na sake shiga tashin hankali.Plate ɗin da ta zubo masa toested bread with egg ta tura gabansa,cikin aro jarumta ta furta, "Sorry na tashi late ne Hubby, wannan ɗin kaɗai na samu yi." Bai tanka ba sai ma siffing tea ɗinsa da ya fara yi hankali kwance.Ta sunkuyar da kanta ƙasa tana ji bugun zuciyarta na ƙaruwa, don wannan shirun nasa ta san bana lafiya bane.Wajen ya ɗauki shiru sai ƙamshinsa da ke shiga hancinta ke sake haifar mata da shiga wani yanayi.Kamar daga sama ta jiyo muryarsa a dake yana kiran sunanta, "Hannatu!" Ta ɗago kanta da sauri tana duban fuskarsa, wanda ya haɗeta tamkar bai taɓa sanin wani abu wai fara'a bare dariya ba a duniya.Take taji ƙirjinta na sake sauya bugu da matsanancin tsoron abinda zai faru, ta amsa cikin karyewar murya hawaye na cika idanunta.Bai dubeta ba ya ɗaura da cewa, "Ki zaɓa ko cigaba da zama da AD Dukku ko kuma cikin jikinki,cikin biyu dole ki zaɓi ɗaya tunda har kika yi gangancin kai ƙarata wajen Momy!" Yadda ya yi maganan hankali kwance yana jifanta da wani irin kallon tsananin jin zafinta, sai hakan ya sake kiɗima zuciyarta.Hawayen da take riƙewa suka ɓalle mata,ta buɗe baki cikin harɗewar murya da rawar harshe ta ce, "Na zaɓi dukan ku AD, na zaɓi zama da kai sannan na zaɓi cikin jikina domin ina tsananin ƙaunarku kai da cikin.Don Allah kar hukuntani da abinda bani na bai wa kaina ba, Allah ya bamu wannan kyautar don haka kayi haƙuri mu am....." Tsawar da ya daka mata ne ya hanata ƙarisa kalamanta.Ya nuna ta da yatsarsa lokacin da yake miƙewa tsaye ya ce, "Sai kin zaɓa Hannatu, dole sai kin zaɓa koni ko cikin jikinki domin ban shirya amsarsa ba.Ina magungunan da aka baki, baki sha duka bako?To bari kiji tunda kika kai ƙarata kika haɗoni da Momy sai ki zaɓa koni ko cikin,idan kuma ba hakan ba karki bari ma na dawo daga office na sameki a cikin gidannan na taddaki yau!" Yana gama maganar ya kwashi wayoyinsa ya bar mata wajen ya yi tafiyarsa don wucewa office. Hannah da ta bisa da kallo zuciyarta na sake mutuwa a ƙaunarsa, bata san lokacin da wani gigitaccen kuka ya ƙwace mata ba. Ta nufi upstairs tana yinsa tamkar ba za ta daina ba.Kira da ke shigowa wayarta ya sanyata tsaida kukan tana ɗakko wayar don ganin mai kiran haka da safen nan,don ba a saba kiranta da sassafe haka ba.Sunan Momynsa da tayi saving da Momyn AD ta gani,hakan ya sanyata ɗaga wayar tana sake sakin wani sabon kukan mai sauti sosai.A cikin yin kukan take gaida Momyn tana sake faɗi mata abinda AD ya ce mata kafin ya fice daga gidan.Ta ɗauki tsayin mintuna shiru tana sauraren abinda Momyn nasa ke faɗi mata daga ɓangarenta.Zuwa wani lokaci

Please Login or Register in order to submit comment