Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

faɗa wani lokaci kuma yai magana a hankali. Saɓanin da da ta ke maida ma sa magana yanzu kam ko mi zai ce ba ta kulashi.
Ta koma ba ruwan ta da kowa aikinta kawai. Ko sallah a office ɗin ta ta ke, balle wajen cin abinci kam ta dena zuwa...


"Sir ga resignation letter ɗi na" ta faɗi lokacin da ta ajiye ma sa takardar a gaban sa.

"Ok" iya abinda ya faɗa kenan ko ɗagowa bai yi ba balle ya kalli idon ta.
Ta yi mamaki dan Najeeb ɗin da ta sani da ba zai yi shiru ba.

"Allah ya sada mu da alkhairi Sir Najeeb. Na gode da taimako da kulawar ka"

Cikin zuciyar sa ya amsa da amin.




*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




0️⃣2️⃣2️⃣






Waɗanda ta ke mutunci da su kawai ta je ta yiwa sallama. Lokacin tashi yai ta haɗa yanata-yanata ta tattara office ɗin,ta ɗauko office laptop da Najeeb ya ba ta dawo ma sa da shi.

"Sir Najeeb zan tafi, ka yafeni dan Allah, na san a zaman da mu ka yi na yi laifuffuka dayawa amma ka yi haƙuri. Allah ya yafemu gaba ɗaya"

Shiru ne ya ratsa office ɗin na lokaci mai tsawo. Tun tana ganin Sir Najeeb zai buɗe baki yai magana har ta cire rai ta fita daga office ɗin.

Sai da ta fita daga office ɗin sannan ya ɗago idon sa ya ce " i'm not done with you yet Miss Salihu"....

Office ɗin Anas ta je dan ta ma sa sallamar ƙarshe.

"Yanzu ƙanwata shikenan kin bar aiki da mu?"

"Yaya na ai ana tare ko da bana aiki anan"

"Gaskiya ban ji daɗi ba, yanzu idan ki ka tafi wa za mu samo ya replacing ɗin ki. Ke ce the second longest surviving secretary a wajen Najeeb"

"Ya Anas kenan, ai da ƙyar mu ka sha mu ɗin ma"

" ba wani, da ƙyar dai Najeeb ya sha a wajen ki"

Dariya ta yi sannan ta ce " ya Amaryar ta mu?"

"Tana nan sai rigima"

"Ta kaini rigima"

Anas ya zaro ido yana dariya "ai Farida idan ta kai ki rigima bulaguro zan yi a garin. Irin ki ai sai su Najeeb"

"Hmm Ya Anas kenan. Nikam ina abokin adawar ka? Ko ya janye ne?"

"Ai tunda Daddy ya sa min stamp na yaƙice shi. Ga shi dama gimbiyar wannan ɗan baƙin kaɗai ta ke gani"

"Allah ya kaimu lokacin biki Yaya na"

"Amin ƙanwata, kar a manta da IV ɗin mu fa"

"Ai kune ƙarɓan fari".....


...................


Shirye-shiryen biki ake ba kama hannun yaro saura sati uku aure aka kawo lefen Farida kuma gaskiya Rayyan ya yi ƙoƙari sosai.
Farida ta duƙufa da gyaran jiki da shirye-shiryen yadda biki zai kasance.

Yau ana saura kwana goma sha takwas aure, Baffa Musa ya kirata.

"Wani shirme na ke ji za ki yi ranan Alhamis?"

"Baffa friends day za ayi ranan Alhamis tunda ka hana ayi kamu"

"Enemies day za ki yi ba friends day ba. Yanzu ke Farida ba za ki yiwa kan ki faɗa ba. Ayi miki walima salamun alaikum a kaiki ɗakin ki hankali kwance, sai kin bijiro da wani shirme"

"Baffa a cikin gidan nan fa za'ayi kuma iya mata ne ka san inada jama'a"

"Ungo na ki ke da jama'an na ki"

"Mun gode Baffa"

Taɓe baki yai kawai yana bin ta da kallo. Bakin tan nan yana fata ya zaunar da ita lafiya a gidan ta, ba ya kawo fitina ba.

"Baffa ina ka amince?"

"Ya na iya uwata. Allah ya kaimu lokacin ya kuma kaɗe fitina"

"Baffa thank you" ta faɗa tana tashi da sauri...


................


Duk yadda ta ke ji gameda auren sai da auren ya zama saura sati ɗaya sai jikinta yai sanyi. Haka kawai sai tsoro ya shigeta gani ta ke kamar za a kuma wani chakwakiyar kamar yadda aka yi lokacin Lukman. Ummi ta zo amma su Nanna sai Alhamis za su shigo. Ranan talata da safe ta wuce Najeeb constructions. Ta fara biya wa office ɗin Sister Munibat ta ba ta katin gayyata tareda cewa idan ba ta zo ba to sun ɓata.

"Sister Aisha kenan, ai indai ina da rai da lafiya to bikin ki da mu za ayi"

Farida ta ɗan harareta " kaman da gaske, kin sayi ashobe na kuwa?"

Sister Munibat ta fara sosa kai.

" hmmm ai dama na sani, Dan Allah ki daure ki zo"

"Insha Allah sister Aisha zan zo"


Daga wajen Sister Munibat ta wuce wajen Anas. Ta jima a wajen sa, inda ya ke ba ta labarin sakataren da aka ɗauka bayan ta tafi.

"Farida kwanan sa huɗu ya ajiye aiki, wai ba zai iya ba"

"Ai Sir Najeeb idan ba jan wuya ba ba mai iyawa da shi"

"Jan wuya kamar ki ba"

"I'in ai mun sha fama da shi"......

Lokacin da ta shiga office ɗin sa yana jikin shelf ya na neman wasu files. Ta tsaya tana kallon yadda ya ke ta dibi-dibi a wajen. Da ta na nan yanzu da ita ke wannan aiki.

"Sir Najeeb mai ka ke nema?" Muryan da bai yi zatan jin sa ba ya ji a ta bayan sa. Bai san lokacin da ya sake file ɗin ya faɗo ba. Tsayawa yai yana kallonta, ta wani yi haske tana sheƙi, ga wani ƙanshi mai daɗi da jikinta ke fitarwa.
Tsugunnawa ta yi ta ɗauka file ɗin sannan ta miƙa ma sa. "Ga shi na ma ka aikin ƙarshe"
Bai amsa file ɗin ba sai ma juyawa da yai ya je ya zauna a kujerar sa.

"Iko sai Lillahi, daga ganin Sarkin Fawa sai miya ta yi zaƙi. Sir Najeeb ba fa aiki na zo ba da za ka min jan ajin da ka saba"

"Oh really"

"Gashi, dama IV na kawo ma ka" ta yi saurin ajiye file ɗin tareda ciro IV ta ajiye ma sa.

"Dan Allah a daure a zo. Duk da ma dai i'm just a secretary"

Ta ɗan yi dariya ta ce " was just a secretary"


"Congratulations Miss Salihu"

"Thank you Sir Najeeb"

Ya ɗan kurɓi coffee da ke gaban sa sannan ya ci gaba da latsa laptop.

"Sir Najeeb ina da magana. Dan Allah ka ɗan rage halin kan nan. Ka ga ba kowa bane zai iya jurewa. Ni ma da ƙyar na sha a wajen ka. Allah, watarana idan na koma gida daga office har ƙaramin zazzaɓi na ke saboda stress da zafin kai. Kai ba a maka gwanin ta sannan..."

"Out"

"Ka ga irin halin na ka ko"

"Miss Salihu get out"

Ta yi shiru tana kallon sa sai da ta ga zai sake ɗaukan mug ɗin coffee ɗin sannan ta yi wuff ta ɗauke.
Ta kai baki da nufin ta kurɓe duka lokaci guda sai ta ji shi da zafi sosai. Ta ɗan kurɓi kaɗan ta sake kurɓa sannan ta ajiye ma sa.
Dariya ta yi saboda yadda ta ga ya zaro ido.

"Sir Najeeb tsokalar ƙarshe ne fa. Na tafi"

Harta juya sai kuma ta juyo ta ce "Sir Najeeb a yafe mu"...
Sai da ta rufe ƙofa ya ce "devil in a dress" ya jawo wani dogon envelop ya buɗe, hotuna ne guda uku a ciki " happy never marriage Miss Salihu" ya faɗa a fili.

(🙄Sir Najeeb ya dai?)


.......................

Farida na komawa gida ta tarar da Maijiddah ta zo.

"Kai-kai Jiddah mi ki ke ci haka? Kin ganki kuwa"

"Kai Anty Farida"


"Zo zo mu shiga ɗaki ki gaya min sirrin"

Sai da su ka zauna ta ce " Jidddah ciki gareki, wannan ƙiban da walakin"

Maijiddah ta rufe ido tana murmushi.

"Masha Allah, Allah ya raba lafiya. Ina kishiyar ki? Har yanzu tana Abuja?"

"E, amma yanzu sau biyu ta ke zuwa a wata"

" 'yar kusun'wa, za ta ma ajiye aikin ta dawo gidan ta, ko kuma ta ji ta a silencer dan mune ma su gidan yanzu"

"Na gode Anty. Kayan da ki ka bani sun min rana"

"Zauna a wajen, ai mazan yanzu sai da shigar bariki. Nima na je Jos na kwaso nawa suna nan jingim"....


Biki na matsowa jikin Farida na ƙara sanyi kullun ta yi bacci sai ta yi mafarkin an fasa aurenta. Abin ya dameta ta gayawa Ummi, Ummi ta ce ta dinga addu'a. Itama ɗin Ummin Allah-Allah ta ke ayi bikin lafiya ba tareda wata matsala ba.
Ranan Alhamis aka je aka yiwa Farida jere a gidan Rayyan. Rayyan ya gina 3-bedroom flat mai kyau. Baffa yai ƙoƙari dan ya kashe kuɗi sosai wajen sayen ma ta kaya, 'yan uwan Ummi ma sun yi ƙoƙari gaskiya...



........... ..........


Ya na zuwa ƙofar gidan ya sa yaro ya kira ma sa maigidan. Da yaron ya fito ya ce yana zuwa...

Musabaha su ka yi da dattijon sannan su ka gaisa.

"Yi haƙuri ban ganeka ba"

Ya miƙa masa envelop sannan ya ce " ɗan ka zai yi aure ranan Asabat ɗin nan ko?"

"Insha Allahu"

"Matar da zai aura ba matar aure ba ce"

"Ban gane ba"

"Ka dubi cikin envelop ɗin nan za ka ga zahiri" daga haka ya juya ya tafi.


.....................


Anyi friends day lafiya kuma ba laifi ƙawayen ta na Jos sun zozzo, anci an sha kuma an girgije.

Ƙarfe goma sha ɗaya na dare lokacin ba ta fi 'yan mituna kaɗan da kwantawa ba kiran Rayyan ya tashe ta. Tana ɗauka ya ce ta fito waje yana ƙofan gidan su.

"My Ray lafiya ka zo da daddaren nan?"

"Ki fito Farida akwai saƙon da zan ba ki ne"

Maganar saƙo da ya ce sai ta ji zuciyar ta ya buga. Ta tashi ta sa hijabi ta fito.
Akwai wa su baƙi da ke kwance a barandar tsakar gidan su na hira, da ke ba su jima da tattara tsakar gidan ba.

"Amarya ina zuwa haka?"

"Ƙofar gida zan je an kawo min saƙo"

"Samarin zamani dai, angon ne ya ka sa hakuri haka"

Ita dai ba ta sauraresu ba ta fita.

Wajen motar sa ta je ya buɗe ta shiga.

"My Ray minene, hankalina ya mugun tashi fa"

Da ke dare ne ba iya kallon fiskarsa ta yi sosai ba balle ta ga yanayin sa.

"Farida ashe za ki iya cin amana ta"

Dum ta ji ƙirjin ta ya yi.

"Wallahi ban ɗauka za ki min haka ba"

"Na shiga uku ni Farida ba dai za a kuma ba. Rayyan mi na yi?"

"Ashe soyayya ku ke da Ogan ki. Ashe duk yadda ki ke zagin sa a gabana iya fatar baki ta tsaya"

"Rayyan dan Allah kar ka sa zuciyata ta buga yanzu. Idan ma wasa ka ke ka dena please "

"Da kan sa ya je gida ya ce wa Baba ke karuwarsa ce"

"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun, Lahaula wala ƙuwwata illa billah. Sir Najeeb ne ya faɗi hakan?"


Miƙa ma ta wayarsa yai ya ce ga hotunan da ya kawo. Ina tunanin ma waɗannan lokacin da ku ka je Lagos tarene ku ka yi holewarku achan.
Ta amshi wayar ta fara kallon hotunan. Hoton farko tana zaune kan cinyar Najeeb ta sa hannayen ta a kafaɗun sa tana murmushi, ɗaya kuma suna tsaye ya rungumeta ta baya, lips ɗin sa a daidai wuyan ta. Ta swipping na gaba wanda tana kallo hawaye na ɗiga a jikin wayar. Suna rungume da juna bakinsu a haɗe kamar suna kissing.

"Ba ni bane, wallahi ba ni bane. Wannan sharri ne. Rayyan ka yarda da ni"

"Dama na zo na faɗa miki ne da kaina kafin gobe a zo gida a faɗa. Na fasa auren ki Farida, ina son ki amma ba zan iya auren ki ba. Najeeb yana da kyau yana da kuɗi, ko bayan mun yi aure idan ya neme ki za ki amince da shi. Ba zan iya aure da zargi a ciki ba"

Bakin ta ne ya fara rawa, tana so ta yi magana amma ko me ya taho zai fito sai ya maƙale a wuyan ta. *"Na fasa auren ki Farida"* shine maganar da ke ta maimaituwa a ƙwaƙwalwarta.

"Gobe za su zo su karɓi sadaki da lefe, sauran abubuwan na yafe. Na gode da Allah ya tona asirin ki kafin ma ayi auren, dama Umma ta sha faɗamin ba ta yarda da ke ba dan 'yan Jos ɗin nan yawancin ku 'yan iska ne"...

Ba ta san ya akayi ta buɗe ƙofa ba, ba ta san kuma ya akayi ta shiga gida ba. Zuwa ta yi ta zauna a bakin gado hawayen da ta ke yi ma ya tsaya. So take ta gane mafarki ta ke yi ko gaske ne. Bacci kam ranan ba bu shi a idon Farida.

Washe gari da safe aka tashi da shirye-shiryen walima. Farida ta kasa magana ta kasa faɗan abinda ya faru jiya, ita har lokacin gani ta ke mummunan mafarki ta yi jiya da dare.

Zuwa ƙarfe goma sai ga Baffa ya shigo yana faɗace-faɗace. Kiran Ummi da Nanna da Baaba Sabuwa yai zuwa falon sa. The next thing da akaji sai kukan Ummi. 'Yan gulma su ka yi falon da sauri Baffa musa ya fatattake su.

"Amina ki dena kuka, ni ban yarda da abin da su ka ce ba, kuma koma hakanne dole sai na aurar da 'ya ta gobe. Ba zai yiwu a fasa aurenta har sau biyu ba, sai duniya ta zageni. Ni nawa 'ya'yan ina aurar da su lafiya ita kuma da ta ke amana gareni ake samun matsala duk lokacin bikin ta"

Nanna da ita kaɗai ce ba ta fara kuka ba ta ce "yanzu wa za ta aura?"

"Yakubu, Yakubu zai aureta, ku cigaba da shirye-shirye Allah ya kaimu goben"...

Farida na ɗaki har lokacin tana zaune jugum, Maijiddah ta yi tambayar duniyar nan amma ba ta kulata ba.

Ummi ta shigo ɗakin tana hawaye. Zuwa ta yi ta tsugunna gaban Farida ta ce "faɗa min gaskiya Farida, akwai abinda ke tsakanin ki da Ogan ki?"

Farida ta kalli Ummi da rinannun idanuwan ta ta ce "da gaske ne ko? Da gaske Rayyan ya fasa aurena?. Ummi banida sa'a a rayuwa kenan? Ummi ina son na yi aure, ina son na samu gidan kai na, ina so na haihu na tara 'ya'ya, ina so na samu ladan biyayyar aure, ina so na cika miki burin ki Ummi. Ummi ko dai aure ba ya cikin ƙaddara ta ne?"

Ummi ka sa magana ta yi sai kuka.....

Zuwa ƙarfe shabiyu 'yan gidan su Rayyan su ka zo karɓan kaya. Daga wajen ma su ke cewa aje a kwashe tarkacen da aka jera a gidan ɗan su. Abubuwa dai su ka rinchaɓe a wajen.

Kowa a gidan da abinda ke ran sa, wassu baƙin na shirin komawa amma da su ka ji Baaba Sabuwa ta ce aure ba fashi za ayi, sai su ka tsaya dan su ga ƙarshen Farida.

Farida tun safe ko sau ɗaya ba ta fito a ɗaki ba, ko wanka ba ta iya yi ba balle abinci kam ba a zancen sa.
Da yamma Yakubu ya dawo daga wajen aiki sai a lokacin ya ke jin labarin abinda ke faruwa. Baaba Sabuwa ce ta ma sa maganar auren Farida da ya koma kan sa. Duk da bai shirya aure yanzu ba sannan bai taɓa kawo auren Farida a ransa ba amma indai dan ya cececi mutuncin 'yar uwar sa ne to zai aureta da gudu ma. Abinda ya ƙara ɗaure ma sa kai baifi yadda aka ce wai 'yan gidan su Rayyan sun ce wai FARIDA karuwar Ogan ta ba ne. Ya san Farida kuma ya san Sir Najeeb, ko da dai chan ƙasar zuciyar sa yana zargin Sir Najeeb na son Farida amma bai kai har ace wai suna neman junan su ba.

Yana cikin wannan tunanin ya ji wayar sa na ringing. Yana dubawa ya ga Farida ai da sauri ga ɗauki kiran.

"Dan Allah Yakubu ka sameni a ƙofar gida"

Da sauri ya tashi ya fita.
Lokacin da ya ganta wani tausayinta ne ya kuma shigan sa. Lokaci guda Farida ta chanja ta zama wata iri, fiskanta ya kumbura ga idon ta da su ka ƙanƙance saboda kuka. Tunowa yai da shekara uku da su ka wuce exactly haka ta lalace lokacin da aka raba aurenta da Lukman. Gara lokacin da sauƙi tunda matsalar daga Lukman ne to yanzu fa.

Ya ƙarasa wajenta yana faɗin "Farida dan Allah ki yi haƙuri, ki kwantar da hankalin ki komai zai wuce"

"Ka kaini gidan su Sir Najeeb" abinda ta faɗa kenan cikin muryarta da baya fitowa sosai saboda dashewa da yai...


Adama ce ta buɗe ƙofa lokacin da ta danna doorbell ɗin.
"Daddy na nan?"

"Eh ki shigo"

A tsaye ƙiƙam ta tsaya idon ta na kallon ƙasa, kan ta ke sarawa, duk yadda ta ɗaga kan sai ta ji wani raɗaɗi.

Mom ce ta fara saukowa ganin yadda Farida ta ke ya sa tasan yarinyar na cikin damuwa.

" 'yan mata ki zauna mana" ta faɗa da Hausanta da bai gama nuna ba.

Farida ba ta ce komai ba sannan ba ta zauna ɗin ba. Kitchen Mom ta wuce ganin Farida ba ta cikin hayyacinta.

Minti huɗu sai ga Daddy ya sauko.

"Ina wuni Daddy" ta faɗa da disashshiyar muryarta.

"A'a Aisha Amarya?"

"Na'am Daddy"

"Lafiya dai ko?, shekaranjiya Baban ki ya kawo min katin biki, ina ce ba wata matsala ba ne ta taso ?"


"Daddy kai uba ne na gari amma ɗan ka bai ɗauko hali na gari ba. Najeeb ya min sharri, ya raba ni da farin ciki na. Ya sa min tabo a rayuwata wanda ban san ranan da wannan tabo zai gogu ba. Ni marainiya ce, ba ni da gatan da ya wuce Allah, kuma na haɗa Najeeb da Allah. A kamfanin sa ban tsira ba, na bar aiki da shi ma ban tsira ba. Allah zai saka min" ta fashe da kuka ta fice daga gidan da gudu. Daddy yana kiran ta amma ba ta tsaya ba. Daddy kan shi ya ɗaure dan bai gane ina maganganun Farida su ka dosa ba.

Tana fitowa ta tsaya ta goge hawaye sannan ta fara tafiya duk da kuwa ba ta da ƙwari a jikinta. Ta kusa isowa wajen Yakubu da ke jiran ta jiri ya ɗebeta ta faɗi ta suma. Yakubu ya yiwo kan ta da gudu...





*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




0️⃣2️⃣3️⃣








Maigadi da dreba da su ke zaune a benchi su ka taso da gudu.
Ce ma sa su ka yi ya kai ta mota yayinda Iliya dreba yai sauri ya shiga gidan don ya faɗawa Daddy.
Daddy na falo har lokacin yana waya da Anas.

Ya na ma sa bayani Daddy ya ce muje-muje.

Daddy na gaba Yakubu na baya ɗauke da Farida wanda har lokacin ba ta farfaɗo ba duk da kuwa sun yayyafa ma ta ruwa. Kafin su isa asibitin ta farfaɗo amma ba ta san inda ta ke ba....

Chan gida kuma Baffa ne ya ke ta faɗa kan miyasa za'a bar Farida ta fita a wannan halin. Maijiddah ne ta ce tare su ka fita da Yakubu. Sai a sannan yai shiru ya zaro wayar sa a aljihu ya fara kiran numbar Yakubun amma bai ɗauka ba.

"Shima ɗan gatan'wa, ko ina ya shiga oho"...



Ruwa aka ɗaura ma ta aka ma ta alluran bacci dan sun ce jinin ta ne ya hau. Sai da ta fara bacci tukunna Yakubu ya samu damar kiran gida ya faɗa mu su.

Daddy ya dubi Yakubu ya ce " mi ya ke faruwa ne? mi Najeeb ya ma ta?"

Da kaman ba zai faɗa ma sa ba,sai dai girman Daddy da kwarjininsa ya fi gaban ya ƙi ma sa magana. Duk abinda ake ciki ya tsirge mi shi tundaga farko har ƙarshe.

Da ya gama bashi labarin Daddy ya ɗauko waya ya kira wata number.

"Anas ka na ina ne?"

Yakubu bai ji mi ake ciki ba ya dai ji ya ce "muna room 18 a sama"

Ba'a jima ba sai ga Anas ya shigo. Ganin Farida a kwance ya sa shi mamakin mi ya faru.

"Yakubu ya jikinta?, mi ya sameta?"

Da sauƙi kawai Yakubu ya iya ce masa.

"Ina ɗan banzan nan ya ke?"

Daddy ya tambayi Anas.

Ya gane Najeeb ya ke nema dan haka yai saurin cewa yana office nima daga office ɗin na ke.

"Har da kai ake rusa rayuwar mutane ko?"

Anas ya zaro ido ya ce "A'a Daddy"

Daddy ya miƙe ya ce "Yakubu Allah ya bata lafiya, ina nan dawowa anjima"

Yana Fita daga ɗakin Anas ga bi bayanshi da sauri.
A motan Anas ɗin su ka wuce Najeeb constructions.

Ya jima yana tunanin ko wani hali ta ke ciki. Wani ɓangare na zuciyar sa na faɗa ma sa bai kyauta ba wani ɓangaren na nuna ma sa ya yi dai-dai.
"She deserve it" ya furta a fili.
Yana ƙoƙarin duba wasu takardu da aka submitting ma sa tun da safe amma ya kasa fahimtar komai. Haka kawai zuciyar sa ke ma sa ƙunci....

A hanya Daddy ke sanar da Anas abinda Najeeb yai, Anas ya kaman salati yana salallami.

"Daddy ban san Najeeb zai iya yin haka ba especially saboda zargin da na ke masa akan yana son Faridan"

"Dan uban sa dan yana son ta sai ya mata sharri"

Anas dai shiru yai yayinda Daddy ke ta surfa ma sa masifa kaman wanda shi yai laifin.

Da ke an riga an tashi wajen shiru ka ke ji. Daddy da Anas su ka haura third floor.

Ya kifa kan sa akan kujera saboda wani zazzaɓi da ya rufeshi lokaci guda, ya rasa mi ya sa shi shiga wannan yanayi. He supposed to be happy ya rama kaɗan daga cikin asaran da Miss Salihu ta sa ya yi. But instead his sad.

Buɗe ƙofar office na shi da aka yi ya sa ya ɗago kan sa da sauri.
Ganin Daddy da Anas sai ya miƙe. "Dad " kaɗai ya iya faɗa kafin saukan mari ya sa ya haɗiye koma mi ya ke shirin faɗa.
A karo na biyu Daddy ya kuma marin sa, ji ka ke taas. Anas na gefe ya sha jinin jikin sa dan faɗan uba da ɗa sai Allah.

"I'm ashamed to call you my son"

"Dad" Najeeb ya faɗa a hankali

"Ashe tarin shekarun ne kawai akan ka ba hankali. Mahaukacin banza Mahaumacin wofi. Sai ka samu me idan ka hanata auren? Tukunna ma, miye dalilin yi ma ta sharri? Miye dalili? "

"she deserve it Dad, she wanted to ruin me. Na rasa big contract saboda ita saboda haka 2 project da mu ka fara su ka soke contract da mu. She tarnished my image and the repeatition of my company"

Wani marin Daddy ya kai ma sa. " i didnt know i have a monster son. Asaran kamfaninka yana dai-dai da ruguza mutuncin mutum kenan?. Shin ka yi tunanin halin da yarinyar nan za ta shiga? What if she died of shock, sai ka haɗa party kana murna ko"

Ya nuna shi da ɗan yatsa yace " Anas, kalli banzan yaron nan fa,8yrs ago da Sabreena ta gudu ta barshi kafin auren su he almost died, he was depressed for months. Ya je theraphy section na watanni huɗu kafin daga baya ya warke ya dawo Nigeria. Do you know that this fool here yana shan antidepressant drugs har yau saboda baƙin cikin yarinyar nan. Amma shi ne ya ke da guts da zai je ya hana auren 'yar mutane"

"Najeeb" ya ka sa magana ma saboda baƙinciki da ya tokare ma sa wuya.
Daddy juyawa yai ya fita, Anas ya kalli Najeeb, kallon ka bani mamaki sannan ya bi bayan Daddy da sauri.


Gidan su Rayyan Daddy ya ce Anas ya kai shi. Da su ka je su ka sa a yi sallama da Baban Rayyan ɗin, aka ce mu su yana kasuwa. Numbar sa su ka karɓa su ka kirashi jin sunan Alhaji Adam Jibo ne ya sa mahaifin Rayyan ya ce yana nan zuwa. Haka su ka zauna zaman jiran sa, kafin ya dawo ma an fara kiran sallan maghrib su ka yi sallah a masallacin anguwar.
A ƙofar gidan aka shimfiɗa mu su tabarma lokacin da Baban Rayyan ya zo.

Daddy bai ɓata lokaci ba ya ma sa bayanin ko shi waye da kuma abinda ya ke tafe da su.

"Malam Abdullahi, wannan hoto da aka kawo muku ba tare su ka ɗauka ba, editting na shi aka yi, kasan yanzu fasahar zamani ba abinda ba ayi. Wannan yarinya ta na da tarbiya kuma kowa ya shaideta da haka. Duk abinda Najeeb ya zo ya faɗa muku to wallahi ƙarya ne, ya yi hakan ne dan ya cimma wani banzan burinsa. Ku yi haƙuri a maida maganar auren yaron ku da Aisha"

Yadda Daddy ya ke magana cikin kwantar da murya ya sa Malam Abdullahi yarda da maganar sa domin Daddy babban mutum ne a gari kai a ma ƙasar gaba ɗaya ba zai yiwu ya zo wajen sa dan kawai ya ma sa ƙarya ba.

"Alhaji na fahimceka, sai dai gaskiya al'amarin nan ya riga ya ɓaci.

Please Login or Register in order to submit comment