Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɗin Sir Najeeb ta wuce ranta cike da masifa. Ta san ba makawa takardar kora zai ba ta sai dai wannan karan za ta karɓa za ta bar Najeeb constructions amma sai ta wanke sunan ta.

Kaman ba abinda ya faru haka ta ganshi yana zaune yana duba wa su takardu.

"Sir Najeeb, na san ka ji abinda aka ce na faɗa amma ka sani ba muryata ba ce wallahi, ba ni ba ne"

Ɗagowa yai ya kalleta ya ce " Miss Salihu, let it be the last time da za ki maida Kamfanina wajen faɗa"

"Sir Najeeb, wallahi a liƙa min sharri kam ba zan zauna haka ba. Kowaye sai na ci kutumar uban sa, hakan ma sai hukuma ta shiga tsakani. Haka kawai dan an sanni da yawar surutu sai a kwaikwayi muryata a faɗi abin da ban faɗa ba"

Kafe ta da ido yai yana gani tana banbami kaman za ta ci babu.

Miƙa ma ta file yai ya ce " take this file to Anas, kuma ki sanar da Admin na HR inada zama da su anjima"

Mamaki ya kamata. Ta haɗiye miyau ta ce " ba korata za ka yi ba?"

"Ki na so na kore ki ne?"

Ta yi saurin girgiza kai ta ce " ba ka ji recording ɗin nan ba ne"

" muryan ki ne?"

" wallahi ba ni bane" ta faɗa da sauri

"Good. Then get back to work"

Ta ɗau file ɗin ta ce " wani lokaci idan ka yi abu kaman Salihin mutum, Sir Najeeb"

"Miss Salihu!"

Ai da sauri ta bar gaban shi tana dariya.

...........

Zuwa ta yi ta ajiye file ɗin a table ɗin Anas ta juya za ta tafi saboda ba ta son ko haɗa ido da shi.

"Aisha dan Allah ki tsaya"

Ai dama jira ta ke yai magana ta fara masifa " Ya Anas dama zumuncin kenan, idan na yi laifi a tureni gefe kamar wata kayan wanki balle ma banyi laifi ba. Iya zama na da ku yau wata ɗaya da sati uku amma har ka ji a zuciyarka zan iya maka ƙazafi, ai ba zama mai kyau ake ba kenan..."


"Dan Allah ƙanwata ki yi haƙuri. I was blind by anger, maganganun sun girgizani sosai to the extend na ka sa ma tsayawa na lura cewa ba muryan ki bane. Im really sorry ƙanwata"

"Ba wani, kai dai tabarmar kunya kawai ka ke son naɗewa da hauka. Ni ka ma barni na faɗi abinda ke raina dan abinda zai sa na huce kenan"

"To faɗa ina jin ki"

Yadda yai maganar sai ta ɗan ji kunyar sa.

"Shikenan Ya Anas na haƙura amma tsakani da Allah na ji haushin abinda ka yi min"

"Dan Allah ki yi haƙuri my ƙanwa"...


Farida na komawa office ɗin ta ta ji saƙo ya shigo wayarta tana buɗewa ta ga numbar NJ, ta yi tsaki sannan ta buɗe saƙon

*bai kamata ki watsar da kan ki ta hanyar yin dambe da wacce ba ta kai ki daraja ba Aysherh, kin fi ƙarfin haka. Ko kin manta ke matar aure ce ..... N J*

"Mtsww, wannan NJ ɗin ma wallahi sai na binciko shi a wannan kamfani, mutum sai shegen na ci, kai ba za ka kira ba idan kuma an kira ba zai shiga ba" ... ta ajiye wayar ta cigaba da aikin da ta ke.




..............

Turo ƙofar aka yi da ƙarfi. Najeeb ya ɗago ido da sauri don ganin wannan mai karambanin. Farida ma da ke jera wasu files a shelf ɗin Najeeb ta juyo da sauri.

"Najeeb wanni walaƙancin ne wannan? Ga wacce ta ma ka sharri amma ba ka ɗau mataki a kanta ba sai Halima. Ka manta Wannan Jakar har dukan Halima ta yi. You're supposed to sack her"

" ina ganin ba ki shiga office ɗin ki ba har yanzu. Go back to your office akwai saƙo da na sa aka ajiye mi ki"

"Najeeb i'm serious bai kamata ka kori Halima ba she didnt deserve it"

Ko kallonta bai yi ba ya ce " ki je office ɗin ki ki duba saƙona"

Ta juya a fusace ta bar office ɗin.
Farida ta fara dariya dan ta san saƙon, tunda ita ya ce ta typing suspension later ɗin Khalidan.
Ganin dariyan na ta ya ƙi ƙarewa ya sa ya daka ma ta tsawa.
"Miss Salihu!"

"Sorry Sir" ta faɗi tana ƙoƙarin gimtse dariyan...

Ta gama abinda ta ke amma ta fake dan tana son ganin reaction ɗin Khalidah idan ta dawo.
Ai kuwa sai ga Khalidan ta zo a rikice.
Ta cilla wa Najeeb takardar hannunta tana faɗin " Najeeb explain this"

" ba ki iya karatu ba ne ko me?"

"Najeeb one month suspension a kan me?"

Shiru yai bai kulata ba.

"Najeeb a wani dalilin za ka min haka"

Still Najeeb bai yi magana

"Najeeb magana fa na ke. I'm calling my Dad right now"

Tana ƙoƙarin kiran mahaifin na ta ta ji Najeeb yana magana.

"Alhaji Tukur na bawa 'yar ka Khalidah Siraj Tukur suspension na wata ɗaya, ko kana da ja akai?"

Saboda wayar a handsfree ta ke sai kawai Khalidah ta ji Babanta yana cewa "ba ni da ja My Engineer. Komai ka yi dai-dai ne"
Najeeb ya sa hannu ya katse kiran ko ɗagowa bai yi ba balle ya ga yadda Khalidah ta taƙune fiska.

"Shikechar inji wani almajirin mu. Asha hutun wata ɗaya lafiya ko, dama ance idan za ka gina ramin mugunta ka gina dai-dai kai" ta ƙarasa maganar tana dariya

Khalidah ta zo gaban Farida ta nunata da yatsa ta ce " sai na ga ƙarshen ki Farida, you'll see"

"Allah raka taki gona Anty Big"

Tsaki Khalidah ta ja sannan ta fice a office ɗin.

Tana cikin dariya Najeeb ya daka ma ta tsawa.

"Get out"
Simi-simi ta fita a office ɗin sa.


..............

An kawo lefen Maijiddah kuma ba ƙarya AbdulWahab ya kashe kuɗi wajen haɗa kayan nan. A wajen ƙarɓan kaya ma Farida ta ka sa ta tsare dan ganin komai ya tafi dai-dai.

Anty Hanne ƙiri-ƙiri ta nuna kishinta a fili saboda kayan da akaiwa Maijiddah ko rabinsa ba aiwa 'ya'yanta da aka aurar ba.
Baaba Sabuwa kam farin ciki fal ranta.


Ranan sunday da dare AbdulWahab ya zo yiwa Maijiddah sallama da ke ya zo weekend.
Farida ce ta tsarawa Maijiddan kwalliya ta kuma zaɓa ma ta kayan da za ta sa.

Falon Baffa Musa aka saukeshi. Wannan zuwan sa gidan kenan na biyu tun haɗuwar su.

Tareda Farida su ka zo bayan sun gaisa da shi sannan ta fita ta basu waje.

"Ina yini" ta faɗa a hankali dan ita har yanzu ta kasa sake jiki da shi.

"Lafiya gimbiya ta"...

Hiran na su yawanci shi ya ke maganar dan Maijiddah kam kunya ta hanata sakewa.

Ya ɗan taɓa abinda aka kawo ma sa sannan ya tashi akan zai tafi.

"Allah ya tsare hanya, ya kai ka gida lafiya. Ka gaida su Baby da Alizah"

"Amin tawan. Shikenan gimbiya ba wani ɗan abu da za ki bani"

"Abban Alizah mi ka ke so"

Ɗan matsowa yai kusa da ita ya riƙe hannunta ɗaya yana ɗan murzawa. Ya sa hannu ya saukar da gyalen da ta yane kan ta da shi sannan ya tufke ɗankwalin,
warware gashin da ta tufke yai sannan ya fara shafa gashin wanda ya zubo har tsakiyar bayanta ƙanshin man da ta shafa wanda ke fitar da ƙanshin mint leaf kaman kuma lemon grass. Ya kai hancinsa yana shaƙar ƙanshin.
Hannunta da ke trembling cikin na sa da kuma yadda bugun ƙirjinta ya ƙaro saboda closeness na su ya sa ya saita kan sa yai gyaran murya bayan ya miƙe tsaye sannan ya ce " Allah ya kaimu kwana ashirin da tara gimbiyata"....



....................

Yakubu ta sa ya ciro ma ta kuɗi bayan ta ga cikakken alert ɗin ta wannan karan Sir Najeeb bai cire komai ba.
Karfe goma saura kwata ta shiga falon Baffa dan bai jima da dawowa ba, sai da ta ba shi lokaci kafin nan ya ci abinci.
Ɗan gefe da shi ta zauna suna gaisawa.

"Baffana na kai na. Allah ya ja zamaninka ya ƙara ma ka lafiya amin"

"Amin 'yar Baffa"

Hannu biyu ta sa ta miƙa ma sa kuɗi. "Baffa a sa mana albarka"

" wannan bai yi yawa ba Farida"

"Baffa na so ya fi haka ma sai dai ka san mu mata sai a hankali, kuɗin na wa na sayo gwanjo da su kuma ban gama haɗa kan kuɗin ba"

"Allah ya miki albarka Farida" ta amsa da amin.



"Dubu hamsin yai yawa Farida, ba dai duka albashin na ki ki ka kawo ba?" Baffa ya faɗa lokacin da ya gama irga kuɗin.

"A'a Baffa"


Shiru ne ya biyo baya na minti biyu kafin ta ce " Baffa dama na ce tunda wannan shekaran ka yi bikin su Salima ga na Jiddah nan da wata ɗaya mi zai hana nawan a barshi wata shekaran kaga kafin nan ka tara wani abu"


" A'a Farida, idan na yi haka na ci amanar mahaifin ki. Duk cikin 'ya'ya na ba wadda ta wuce shekara ashirin na aurar da ita, Maijiddah ce ma har ta kai ishirin ɗin. Idan ba ƙaddara da ta faɗa miki ba ai da tun shekaru uku da su ka wuce anyi bikin ki"

"Baffa Allah ba matsala ka bari irin watan uku na wata shekara sai ayi kafin nan komai ya dawo normal"

"A'a Farida ko da duka gonakaina zan sayar dan na samu kuɗin yi miki aure zan sayar. Ai idan na bari wata shekara sai duniya ta zageni. Idan ba su iyayen yaron sun ce bai gama shiryawa ba ai da tareda Maijiddan zan haɗaki"

"Baffa dai" ta faɗa kaman za ta yi kuka.

"Tashi ki je ki kwanta. Allah ya kaimu watan December"

"Baffa nikam..."

"Tashi na ce" ya faɗa da ɗan ƙarfi.

Ta tashi tana guna-guni ta bar falon.

Sai da ta fita Baffa ya ƙara godewa Allah domin halin Salihu na kyauta kam Farida ta ɗauko, dan lokacin yana raye bashida rowa ko kaɗan, zai iya bayar da abu shi ya rasa kuma hakan bai dame shi ba...

................


Lagos


Ranan Monday da safe ya isa Lagos, kai tsaye office ya wuce kasancewa dama shi ɗaya ya je ya bar su Alizah a gidan maƙocin sa kuma abokin aikin sa Mr AbdulRazaƙ.
Bai ɗauka Aneesa za ta zo ba tunda ya gaya ma ta zai je Kano kuma zai bar yaran a wajen maƙota.
Ƙarfe takwas da rabi na dare ya isa gidan Mr AbdulRazaƙ dan ɗauko yaranshi. Sai dai da ya je ake ce ma sa Aneesa ta zo ta ɗauke su.
A take a wajen ya kira Aneesa amma ba ta ɗauka ba. Hankalinsa bai tashi ba sai da ya je gida mai' aikin su ta ce Aneesa ta wuce da yaran Abuja. Yai ta kiran numbar Aneesan amma ba a ɗauka. Ƙarshe dole ya kira numbar ƙaninta Nazir ya ce ya kaiwa Aneesa.

Minti biyar sai ga kiran Aneesa a wayarsa.

"Wannan wanni irin iskanci ne Aneesa za ki ɗauke min yara ba tareda kin sanar da ni ba"

"Iskanci kuma AbdulWahab, Ni da 'ya'ya na. For your information, kai da su Baby sai ka janye maganar auren ka. Ko kuma su zauna tare da ni anan amaryarka ta haifa ma ka wasu"

"Anny kin san yaran nan suna Makaranta fa"

"And so, zan sa su a wani anan"

"Look Aneesa, ki maido min da yarana gobe-goben nan ko kuma..."
Ƙiiit ta kashe kiran.

*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*



*Free page*

0️⃣1️⃣3️⃣



Kwana biyu Aneesa ba ta turo ma sa yaran ba dan haka dole ya kira Alhaji, mijin Maman Aneesan kenan, ya ma sa bayanin komai shi baya ma gari dan haka bai san su Alizah na gidan sa ba. Ya jima yana yiwa Aneesa faɗa akan ta ajiye aiki ta je ta zauna da yaranta amma ta ƙi. Kasancewa Maman ta ba ta bashi goyon baya ba shi ya sa yai shiru ya zuba mu su ido. Ya auri Hajiya Salma ne lokacin Aneesa na da shekara goma shabiyu ƙaninta kuma na shekara tara. Bai taɓa banbanta su da 'ya'yan sa na cikin sa ba, makaranta mai tsada su ka yi da ta gama sakandare ya turata karatu ƙasar waje.

Aneesa ta haɗu da AbdulWahab ne a cikin jirgi, daga Lagos za ta wuce Abuja. Sun kusan shekara biyu su na soyayya kafin su ka yi aure saboda dagewa da Aneesan ta yi akan za ta yi masters kafin ta yi aure. Bayan sun yi aure ta fara aiki da wani Kamfani a Lagos. Shekaru biyu da su ka wuce Kamfanin su ka buɗe wani branch a Abuja kuma su ka nemi Aneesa ta koma wajen. Ƙarin matsayi da albashi su suka ruɗi Aneesa ta tsallake mijinta da 'ya'yanta ta wuce Abuja. Abdulwahab ya yi faɗan ya yi fishin amma duk a banza. Haka ya kira Maman Aneesan ya mata bayani akan ba da yawunsa Aneesa ta koma Abuja ba. Buɗan bakin Maman sai ta ce "AbdulWahab idan ta ajiye aikin za ka iya ba ta dubu ɗari shida da hamsin a wata ne (650,000)?" Wannan maganar shi ya sa AbdulWahab ya sauke makaman yaƙin sa ya haƙura ba dan ya so ba, sai dan inda ya ke ganin za a mata faɗan ma goyon bayanta ake. Bai faɗawa iyayen sa ba sai da ƙannensa su ka je ma sa hutu bagtatan su ka tarar Aneesa ba ta nan da farko ce mu su yai ta je gida ne kawai daga baya su ka gano komai, nan Hajiya Yelwa ta ce ba ta san zance ba ta ya za'ayi yana Lagos matar sa na Abuja wai sai ƙarshen wata za ta zo...

Alhaji yai waya ya ce maza Nazir ya maida yaran Lagos. Kasancewa Aneesa ta fita wajen aiki sannan Mama ma ta fita ya sa ya ɗau yaran ba tareda wanni cikin su ya hanashi ba. Ya na samun tiketin jirgi sai Lagos. Baby da Alizah sai murna dan dama sun ƙagu su koma school sannan su ka Dad ɗin su.

...................


Shirye-shiryen biki ake ba kama hannun yaro, duk da dai abubuwan sun zo a tsukekken lokaci amma hakan bai hana Baffa ko Baaba Sabuwa yin ƙoƙari wajen yiwa 'yar su gata ba. Da ke AbdulWahab na da gida a Kano anan za a ma ta jeren kayan ta.
Farida kam abun ya haɗu ya ma ta yawa kwana biyu su na aiki sosai a kamfani da ke akwai wani sabon contract da Kamfanin ya samu ga kuma shirye-shiryen biki. Har ɗan rama ta yi saboda zirga-zirga. A cewarta Maijiddah tana da gidadanci ba kaman ƙannen ta da idon su ya buɗe ba, dan haka ta ke sa'ido akan komai saboda ayi komai na zamani...


Gulma kam a Najeeb constructions sai ma abinda ya ƙaru musamman da aka kori Halima sannan aka ba wa Khalidah suspensio. Dayawa su na tafiya da cewa Najeeb da Farida su na soyayya ne musamman kasancewa har yanzu bai koreta ba duk da kuwa irin karya dokoki da ta ke. Sai dai duk gulman a bayan fage a keyi dan ba mai iya tunkaran Najeeb ko Farida. Irin dukan da Faridan ta yiwa Halima ma ya sa su ke tunanin ƙila Farida na da taɓin hankali...

Ɗan baccin da ba ta samu sosai cikin kwanakin nan saboda matsowar bikin Maijiddah shi ta ke yanzu a office. Sallaya ta shimfiɗa a ƙasa ta kwanta tana narkan bacci hankali kwance.

Ya kira telephone ba a ɗaga ba, ya kira wayarta still ba a ɗauka ba. Computer ɗin sa ya jawo ya duba ko ta fita ne sai ya hangota chan ƙasa tana bacci. Ya jima yana kallonta kafin ya tashi ya ɗau key da wayarsa ya fita.

"Miss Salihu" ya faɗa da ɗan karfi lokacin ya tsugunna kusa da ita. Sai da ya kirata a na uku sannan ta tashi a firgice. Ganin shi tsugunne ya zuba ma ta ido ya sa ta ɗan goge fiskarta ta ce " sannu Sir Najeeb"

"Bacci a bakin aiki Miss Salihu"

"Yanzu sai ka ce acikin albashina. To ka yi haƙuri gajiya na yi"

Yadda ta yi maganar ya bashi dariya sai dai haɗa rai yai ya miƙe ya ce ta tashi za su fita.

Bin sa ta yi zuwa office ya nuna ma ta takardun da za ta ɗauka. Bacci bai gama saketa ba amma haka ta tattaro takardun ta biyoshi. Tsabar mugunta sai ya ƙi ya bi lifter ya bi stairs.
Suna saukowa ta fito da biro ta ɗan ƙara sauri ta caka ma sa biro a bayan wuyan sa. Hannu ya sa ya shafa wajen ba tareda ya juyo ba. Ƙaramar tsaki ta ja ta sake kai hannu za ta sake caka ma sa sai kuwa ƙiris ya juyo.
"Wayyo Allah na!....Wayyo!" Ta faɗi cikin ihu, ta zubar da files ɗin hannunta ta koma baya da gudu.

Irin yadda ya ga ta tsorata ta fita da gudu sai abin ya sa shi dariya. Sometimes ya kan yi tunanin yarinyar nan na da taɓin hankali...

Kai tsaye office ɗin Anas ta je. Tana magana tana haki ta ce " Ya Anas.... ka taimakeni... yau na tsokano tsuliyar dodo"

"Mi ya faru? Mi ki ka yi?"

Ba ta bashi amsa ba sai ma ta cigaba " wallahi ba zan sake ba. Ni ban ma san ya akayi na ma sa haka ba, dan Allah ka je ka bashi haƙuri"

"Me ki ka yiwa Najeeb"

Ta ɗan yi ajiyar zuciya ta ce "biro na chaka ma sa a wuyan sa"

"Biro" Anas ya maimaita sannan ya kwashe da dariya.

"Ya Anas ba dariya za ka yi ba fa, haƙuri za ka je ka bashi"

"Yanzu ke Farida a wanni dalilin za ki ma sa haka?"

"Kawai haushi na ji ya tashe ni a bacci kuma ya ce wai mu sauko ta stairs"

Cikin zuciyarsa ya ce "lallai Farida na jinjina mi ki"

A fili kuwa cewa yai " yanzu dai kin amince kin yi laifi?"

"Na yi. Wallahi na yi"

"Shikenan, mu je na same shi"

"A'a kai ka fara zuwa tukunna, ni zan jira ka anan"

"Ki zo mu je ba abinda zai mi ki"

Jiki a sanyaye ta bi bayan Anas su ka wuce office ɗin Najeeb.

A zaune su ka sameshi yana waya. Daga bakin ƙofa Farida ta tsaya dan idan ma wani abin zai ma ta za ta samu ta gudu da wuri. Anas ya ƙarasa wajen sa ya zauna yana ɗan dariya ƙasa-ƙasa.
Yana ajiye wayan Anas ya ce "Yallaɓai mun zo biko, ƙanwar mu ta yi laifi kuma ta gane kuskurenta. Ayi haƙuri"

Shiru yai na ɗan daƙiƙai sannan ya ce " ta gaya ma abinda ta yi?"

"Ta gaya min, kuma na ma ta faɗa sosai"

"Good, akwai psychiatrist da na kira yanzu, zai zo ya gwada min ita dan ban yarda da lafiyar ƙwaƙwalwar ta ba"

Daga inda ta ke tsaye ta ce " haba Sir Najeeb, psychiatrist kuma. Sai kace mai taɓin hankali"

Kallon Anas yai ya ce " idan aka tabbatar min da lafiyarta ƙalau, then she can work with me. Idan tanada matsala kuma sai ta je ayi treating ɗin ta, dan ba zan iya aiki da mahaukaciya ba"

"Sir ka rama abin da na ma ka idan haka ne" ta faɗi da ɗan ƙarfi

Shiru yai yana kallonta sai chan kuma ya ɗau biro ya miƙe tsaye. Tana ganin ya nufota da biro a hannu ta tsume, wai a dole ba ta damuba irin ta surrender ɗin nan. Sai dai saura taku kaɗan ya isota ta buɗe ƙofa ta fita da sauri.

Najeeb ya ce " you see, she's crazy"

Anas yana dariya ya ce " she's just funny. Dan Allah kar ka ma ta komai"...


Fitan Aisha Farida kam ai sai gida, dan ba ta yadda ta tsaya ba. Sai da ta je ta tuna ai ko wayarta ba ta tsaya ɗauka ba jakarta kawai ta ɗauka. Ta yi tsaki sannan ta yi amfani da wayar Jiddah ta kira Yakubu ta ce ya je ya ɗauko ma ta wayarta a office.

"Yanzu ke tafiya gida ki ka yi ba tareda an tashi ba, Sir Najeeb ya sani?"

"Ya sani mana, kai dai je ka ɗauko min wayata kawai"...

Najeeb ya fito daga office ɗin sa zai fita ya ji wayar Farida na ringing, ganin bai ga jakarta ba yai tunanin ta tafi ne. Zuwa yai ya ɗau wayar amma kafin ya ɗauka kiran ya yanke, take kuma aka sake kira sai ya ga sunan mai kiran an saving da *My Ray*. Tsaki ya ja sannan ya saka wayar a Aljihu ya fita.
Yakubu da ya zo bai ga waya ba ya kira Farida ya gaya ma ta. Ita kuwa ta rantse indai aka sace ma ta waya a Najeeb constructions to za ayi ƙaramin yaƙi dan kuwa ba za ta yadda ba sai an fito ma ta da waya...


..................

"Yanzu kinga wannan jakar, duk kayan ciki na ki ne. Na fi awa ɗaya ina zaƙulo waɗannan kayan a wajen ma su gwanjo. Wallahi ko manya-manyan boutique ki ka je ba za ki samu kaya ma su kyaun wannan ba, ai gwanjo rufin asiri ne. Sai ki samu kayan da har ki gama yayinsa ba za ki taɓa ganin irin sa ajikin wani ba"

Maijiddah ta buɗe jakar ta fara fiddo kayan da ke ciki. Duk wanda ta ɗaga sai ta yi saurin ajiyewa saboda yanayin kayan sun bata kunya.

"Jiddah ya na ga kina wani yanƙwane fiska kaman kin ga kashi?"

"Anty Farida wannan kayan ai...."

"Ai me? Na ce ai me?. Dan Uban ki ina siya mi ki mutunci kina cewa ke tsiya ki ke so. Wannan kayan da ki ke gani da su ake cin gari. Balle ke da ki ke da kishiya, kishiyar ma wayayyiya 'yar boko"

"To Anty kuma sai insa wannan kayan in fito?"

Wani kallon banza Farida ta ma ta sannan ta ce " idan kin ga dama ki sa, idan kin ga dama kuma ki ƙona su idan kin je chan. Ni dai na san watarana sai kin kirani kince Anty Farida zan iya samun irin kayan nan wallahi ko nawa zan biya ki nemo min su. Lokacin ni kuma sai na karɓi kuɗi mai tsoka a wajen ki kafin na nemo mi ki"

"Ki yi haƙuri Anty"

"Ba batun haƙuri ba ne Jiddah, so na ke ki waye ki shigo gari kema. Idan kin je kin mallake zuciyan maigidan gaba ɗaya. And Wallahi zan faɗa mi ki gaskiya ba da hijabi ko manyan kaya ake sace zuciyan miji ba"


"Anty Farida wani mai ƙatuwar mota yana kiran ki a waje. Maijiddah ke kuma wai inji Rashidan Bala wai za ta samu kitso?"

"Zo nan Sadiƙ" Farida ta faɗa tana kallon molelen kan yaron da ya sha aski.
Yana zuwa ta kama shi ta ma sa dundu uku a baya.
"Ban hana ku kiran Maijiddah da sunan ta ba? Eh. Mi na ce ku dinga ce ma ta?"

Yaron cikin kuka ya ce "Anty Maijiddah"

"Good boy. Yanzu ka je ka cewa Rashida, Anty Maijiddah ta dena kitso"

Yaron ya fita yana kuka yana ƙoƙarin sosa bayan sa....


Ba ta gane motar wayeba amma ta san koma waye to babba ne. Ba ta tunanin kuma Alhaji Hussaini ne, wanda ta haɗu da shi a wajen aiki ya zo wajen Sir Najeeb ya nace ya nemi numbarta, sai da ta sissilleshi sannan ya haƙura ya dena kiran ta.

Tana ƙarasawa jikin motar ta zagaya wajen driver ta ƙwanƙwasa glass ɗin saboda tinted ce ba ta ga wanda ke ciki ba. Ɗan sauke glass ɗin aka yi sannan aka miƙo ma ta waya, tana ganin hannun ta ce "Sir Najeeb!" sai kuma ta yi saurin rufe baki tunowa da ta yi da abinda ta yi a office yau.

Ƙarasa sauke window ɗin yai sannan ya ce " Miss Salihu karɓi wayan ki"

Ta yi saurin karɓan wayan sannan ta ce "na gode Sir" bai ce komai ba ya ja motar sa ya tafi...



"Kaman motar Sir Najeeb na gani ɗazu a ƙofar gida"

"Shine. Waya ta ya kawomin"

Da mamaki Yakubu ya ce " Sir Najeeb ɗin?

"Iyi"

"Sir Najeeb ya kawo mi ki waya har gida"

"To miye aciki, ni ba sakatariyar sa ba ce"

Shiru Yakubu yai yana tunanin ko dai gulman da ake yi a office gaskiya ne. To idan ba haka ba Sir Najeeb ɗin da ya sani a da kam bai damu da damuwar kowa ba, kan sa kawai ya sani. To idan kuma akwai abu a tsakanin su fa? Baba ya ce a ƙarshen watan December za ayi bikin Farida.
Farida ce ta katse shi da cewa "yawwa Yakubu ka san numbar nan?" Ta nuna ma sa numbar NJ. Ɗaukan numbar yai ya sa a wayarsa sai dai bai da irin numbar ma a wayarsa...

...................

Fitowar sa kenan daga wanka ya ganta zaune abakin gadon sa.

"What are you

Please Login or Register in order to submit comment