Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba su taɓa irin haka ba, Rayyan ya na tsoro da shakkar Farida shi ya sa ko hannun ta bai taɓa riƙewa ba sai dai ko a rashin sani.
Yau ta samu first kiss ɗin ta, kuma da Sir Najeeb, Sir Najeeb fa. Ta sa hannu ta rufe bakin ta saboda tsikar jikan ta da ya tashi lokacin da ta tuna abinda ya ce "kiss me".

"Did they hurt you?"

Ai ta tafi duniyar tunani ba ta ma ji abinda ya ce ba. Duk wani cin mutunci da ta shirya za ta yiwa Sabreen lokacin ta na cell ta watsar da shi. Ƙwaƙwalwarta ba abinda ya ke tunowa sai wannan moment ɗin.

Chan ƙasan zuciyar sa ya ke neman dalilin da ya sa ya kissing ɗin ta amma ya rasa. Chan ya baiwa kan sa amsa da Sabreen. Yes ya yi haka ne saboda Sabreen, saboda ta gane cewa he's over her now. Amma must he resort to kissing her? Yanzu sai ta rena shi. Wata zuciyar ta ce but it was the best kiss you ever had. Ko dan ya jima bai yi kiss ba ne, dama da Sabreen ne kawai, no one else. First kiss na shi in 8yrs felt different. Kaman wani ƙaramin yaro haka ya lashe lips ɗin sa da harshe. Garin haka ma saura kaɗan ya buge wani mai Keke.

Har su ka isa gida ba wanda yai magana. Farida ce ta fara shigowa dan ta fita ta bar shi a mota. Tana tafiya tana jin ta a sama fiskar ta ɗauke da murmushi.

Najdah ne da wata tsohuwa a falon lokacin da ta shigo. Ba ta ma lura da su ba sai da tsohuwar ta ce "amarya lafiya?" Farida ta juyo sai ta ga tsohuwar duk da kuwa kuɗi sun ɗan ɓoye tsufan, amma kuma a yadda ta gan ta za ta haifi Daddy.

Ta yi saurin ƙarasawa wajen ta ta tsugunna "Hajiyata dan Allah ki yi haƙuri ban gan ki ba ne"

"Na ga alama ai, kin tafi birnin soyayya ko. Ina angon" kafin ta ba ta amsa sai ga Najeeb ya shigo.

Yana ganin Hajiya Mama ya washe baki " tsohuwa yaushe a gari?"

Yana ƙarasowa wajen ta ta ɗauki sandarta ta ɗaga sama za ta kwaɗa ma sa ya ja baya da sauri.

" ke fa tsohuwa kin dawo kenan za ki fara cin zalin mutane"

"Ungo na ka Najeebullahi, tun jiya na dawo amma shi ne ba za ka kawo min amarya na gan ta ba"

"To ke kiji da ƙafar ki ma na, amma sai shegen yawo"

Farida dai kallon Najeeb da Hajia Mama ta ke da su ke dramar su na Kaka da Jika. Najeeb was jovial amma ba kaman tsakanin sa da Mom ba wanda tun zuwan ta abin ke ɗaure ma ta kai.

Hajia Mama ta kalli Farida ta ce "kin ga mijin kin nan ke ce rufin asirin sa. Haka yai ta yawo ƙaton tuzuru da shi, sai da Allah ya kawo ki"

Farida ta yi murmushi.

"Sai ki kula da shi sosai dan ɗan duniya ne"....


Ta fito daga wanka bayan sallar Isha ta fara jin hayaniya a ƙasa. Ba ta tantance ko muryan su waye ba ne amma daga yadda maganar ta ke haɗakar larabci da turanci ta san ba zai wuce Sabreen ba ne...


"Big B mi ya sa ka ke bin bayan ta, kai kan ka ka san ita ta yi wannan abin and she needs to be punished for that"

" walau ita ta yi walau ba ita ba, dukkan ku biyu babu wanda ya ke da ikon arresting ɗin ta, especially you Sabreen. Ina so ki nisanci iyalina"

"Big B amma..."

"Najdah!" Ya daka ma ta tsawa. Kallon shi ta yi sannan ta haura sama da gudu.

Ya juyo ya kalli Sabreen ya ce "next time ki ka yi ƙoƙarin taɓa lafiyar mata ta, i wont take it lightly"

Cike da tuƙuƙin baƙin ciki ta ce "you dont love her, do you"

Haɗiye miyau yai sannan ya ce "go back to Hollywood you dont belong here"...

Ɗakin Najdah ya fara zuwa Lokacin da ya haura sama, amma ta ki buɗe ma sa ƙofa. Dan haka ya juya ya shiga ɗakin su.

Yana shiga ɗakin ya gan ta bakin gado tana kuka. Jikin sa yai sanyi ya ƙarasa wajen ta yana tambayar minene dan a tunanin sa ko a cell ɗin an mata wani abu ne.

"Mi ya faru?"

Tana kuka tana jan majina ta ce "Baba ya rasu"
Kan sa ya ɗaure dan Anas ya taɓa ce ma sa Farida marainiya ce to yanzu kuma wani Baban ne ya rasu.

"Your father?" Ya sake tambaya.

"Kaka na ne"

Ya jawota jikin sa yana lallashin ta.

"Yanzu Ummi ta kira ni, dan Allah Sir Najeeb zan je Jos gobe"

Ya gyaɗa kai ya ce "its ok"


Sun jima tana kwance a jikin sa tana hawaye tana faɗa ma sa kyawawan halayen Baba. Bai bar wajen ta ba sai da ta yi bacci, lokacin kusan sha biyu saura na dare. Da ya gyara ma ta kwanciya sannan ya je yai wanka ya shirya cikin kayan bacci sannan ya zo ya kwanta amma kafin yai bacci sai kusan ƙarfe biyu. Tunani ya cika ma sa kwanya.


Washe gari da sassafe ta shirya, ya sa Iliya ya kaita har Jos. Lokacin da motar ta bar cikin compound ɗin ƙarfe shida da rabi na safe. Yana shigowa cikin gida Daddy ya kira shi, da ya je tambayar sa yai gameda abinda ya faru jiya dan ya ji maganar a wajen Mom.
Bayan ya ma sa bayani sai Daddy ya ce " ka yi katanga tsakanin ka da Sabreen, ban hana ka ƙara mace ba idan ka ga ba za ka iya zama da Aisha ita kaɗai ba, amma ka sani. Ba zan taɓa amincewa da Sabreen a matsayin suruka ba. Ba wai dan ta rabu da kai ta dawo ba, sai dan ba zan bari ka haɗa zuri'a da macen da zata iya gurɓata ma ka rayuwa ba. Ina sane da lokacin da Mahaifiyar ka ta ke kuka kullum saboda Sabreen ta na shirin auren wani kafiri ɗan ƙwallon ƙafa har ta ke sukan addinin musulunci da ya hana aure tsakanin kafiri namiji da mace musulma. A hira da aka yi da ita shekaru uku da su ka wuce, cewa ta yi sallah na takura ta, wai anata abu ɗaya kullum ba hutu. Wannan ba macen aure ba ne. Idan har ka nuna za ka auri Sabreen to za ka yi nisa da ni da iyalina. Za ta zauna a nan ne kawai saboda alaƙa ta jini da su ke da shi da Nabilah amma bayan nan ba na so wani abu ya kuma shiga tsakanin mu"

Najeeb ya gyaɗa kai.

"Ya maganan gidan ka, anyi interior decoration ɗin?"

"An kusa a gama"

"Ok Allah ya nuna ma na"...

Yau dai throughout a office jin sa ya ke wanni iri. Musamman idan ya zo fita ya ga ba ta kan kujeran ta.

Da ke Jummu'a ne kuma ranan hutu ne an haɗa ƙwarya-ƙwaryan party amma bai iya tsayawa a wajen ba. Anas ne ya tsaya ya wakilce shi, daga sallar jummu'a gida ya wuce yana jin jikin sa ba daɗi. Ba wai ba shi da lafiya ba ne amma kuma jikin sa is weak.
Yana shiga ɗakin sai ya ji ɗakin ya ma sa faɗi kaman ba ɗakin sa ba, there's something missing. Ƙanshin ɗakin ya sauya tun zuwan Farida saboda haɗuwar turarukan sa da na ta kalolin turaren. Har ta fasalin ɗakin ya sauya. Ya tuna ranan da ya shigo ya ga tana chanja arrangement na wasu abubuwan a ɗakin.
"Sir Najeeb ɗakin ka yana buƙatan polish"

Ya tuna yadda yai ta gwaleta yana cewa ta hargitsa ma sa ɗaki.

Ya na shiga wajen closet ya tuna ranan da ya ke chanja kaya ta shigo lokacin gajeren wando na jeans ne a jikin sa ba riga.

" Sir Najeeb, idan ka na gida sai ka yi ta sa gajerun wanduna kaman wani ɗan firamare"

Yai murmushi tunowa da yai da kalolin tusa da ta lissafto ma sa ranan...

Lokacin da ya gama abubuwan da zai yi yana kishingiɗe a kan gado ya ji gadon ya ma sa daban. Tun da ta zo kullum za su kwanta akwai pillow a tsakanin su, jiya ne kawai su ka kwana ba pillow.
A hankali ya sa hannu ya fara shafa gefen da ta ke kwana wanda ya ke empty yanzu. Ya tuno ranan farko da za su kwana a kan gadon faɗan da su ka yi, daga ƙarshe da tunanin kissing ɗin da su ka yi jiya bacci ya tafi da shi.

Washe gari da safe Daddy ya ce su je su yiwa Baffa Musa ta'aziya. Tare su ka je a chan ne ana taɗi wanda tsakanin Daddy da Baffa Musan ne dan shi banda ya haƙuri da ya ce bai kuma cewa komai ba. Cikin taɗin su Baffa Musa ke kawo rayuwar da Farida ta yi. Daga wannan gida zuwa wannan gida kafin daga baya ta zauna a wajen Kakannin ta.

Daddy ya tambayeshi ko miyasa bai ɗauki Farida tun da wuri ba. Baffa Musa ya ce "Hmm Faridan, tun tana yarinya ta ke da baki. Ko hutu aka kawota sai ta yi ta ƙorafi, Baffa garin ku akwai zafi, ba zan zauna ba"...

Lokacin da za su tafi Baffa ya ce da Najeeb " ka kula min da ita dan Allah. Ka da ranan gobe Ubanta ya ce ban riƙe amanar tilon 'yar sa ba"

Najeeb ya ce Insha Allah...


........................

Yau sati ɗaya kenan da ba ta nan. Cikin sati ɗayan nan ya rasa ganewa kan sa. Bai ma cika son fita ba, dama wajen aiki ke ɗebe ma sa lokaci to yanzu ana hutu. Sabreen washe garin da Farida ta tafi itama ta yi tafiya, bai san inda ta je ba kuma bai damu ba dan shi idan ta tashi ne to kar ta ƙara dawowa.

Yau da ya je wajen Hajia Mama ne ta ke cewa ya kira ma ta Farida ta ma ta ta'aziya.

Kwana uku da Farida ta yi a Jos ta yi su cikin rashin jin daɗi, na farko ga rashi da su ka yi, na biyu kuma Sir Najeeb da ya shareta. Kullum da tunanin sa ta ke kwana ta tashi, amma shi ko text bai ma ta ba balle ya kira ya ma ta ta'aziya. Duk da kuwa ranan da ta taho ta tura ma sa text akan sun isa lafiya amma ko reply bai yi ba. Wasu lokutan har mafarkin suna tare ta ke, haka kawai tana zaune sai ta ji kaman muryarsa a kunnen ta yana faɗin "kiss me" har tunanin ko ta fara hauka ta ke yadda waɗannan kalmomin biyu ke sa ta jin wani nishaɗi da farin ciki...

Tana ganin wanda ya kirata mamaki haɗe da wani farin ciki ya mamayeta, sai da wayar ta kusa katsewa sannan ta ɗauka.

"Sir Najeeb shi ne sai yau?"

"Aishatu, kuna lafiya ya haƙuri?" Muryan Hajia Mama ya doki kunnen ta maimakon muryan Najeeb...

Hajia Mama na kashe wayan ta kaiwa Najeeb sanda.
"Ashe ko ta'aziya ba ka je mu su ba. Kakan matar ta kan"

"Kai Tsohuwa, ba munje gidan uncle ɗin ta ba. Miye sai mun je har Jos. Will that bring back the dead?"

Hajia ta sa ke ɗaga sanda yai gefe da sauri yana dariya...


Kaman yadda Hajia Mama ta nema kuma ta sa Daddy ya ma sa magana dole ya shirya zai je Jos. Shi sau ɗaya ya taɓa zuwa garin kuma aiki ne ya kaishi.

Ya fito kenan ya tarar da Anas da Najdah a falo su na magana.
"Kai ba na son takurawa fa, she's still in school" Najeeb ya faɗa yana hararan Anas.

Anas ya ce " an gaya ma ka ni irin ka ne da sai na zauna har 35yrs. Ai ni kafin watan shidan sabuwar shekaran nan zan angonce"

"Shege, to Baby sai ta ƙare karatu tukunna"

"Wallahi ba ka isa ba, ka san tun yaushe mu ke shan ruwan kanwa kuwa"

"Ɗan iska, to ka bi ni a hankali ko in hanaka, dama Musty yana gaba dani saboda na hana shi, ka ga idan ka yi wasa sai na bashi ita"

"Kai na a ƙasa babban yaya, mu na neman tubarrakin ku"...

Sai da su ka jima su na wasa da dariya kafin daga baya bayan Najdah ta bar falon Anas ya shiga bayanin abinda ya kawoshi.

"Najeeb, Farida ita ke da gaskiya da kai da kamfani you owed her apology"

Najeeb ya gyara zama yana sauraron sa.

"Khalidah da Alhaji Matawalle su su ka kitsa komai. The money from VESTAC inc. Alhaji Matawalle ne ya sa aka tura supported by Khalidah. Shi ya shirya yadda za a sace ma ka takardun zanen ka a kuma ɓata modelling da ka yi. On the other hand kuma Khalidah ita ta kawo shawaran a framing Farida. Duka evidences da mu ka haɗa yana nan" ya miƙa ma sa wata ƙatuwar envelope.

Idon Najeeb ya rine yai ja tsanar Khalidah da Alhaji Matawalle na ƙara shiga ran sa.

"Kai ka san wani mataki ko hukunci za ka ɗauka idan aka koma aiki ranan monday" ...

..............
Ba dan ya riga ya shirya tafiya ba da ba abin da zai sa ya tafi. Ƙusan ƙarfe uku ya isa Jos, address ɗin da Yakubu ya bashi ya bi, da tambaya kuma ya isa har layin su. Bai gama shan mamakin layin ba sai da ya isa gidan. He cant believe a irin wannan gida Farida ta yi rayuwa. Ba wai dan bai saba ganin gidaje haka ba a'a sai dan yadda Farida ke gudanar da rayuwar ta with boldness and cofidence, ba ta shayin shiga ko'ina. A ko yaushe ji ta ke dai-dai ta ke da kowa, duk daraja ko kuɗin ka kuwa.

Yaro ya kira ya ce a ma sa magana da Farida dan tun a bakin layi ya ajiye mota saboda mota ba ta shiga layin.

Ana yiwa Farida kitso yaro ya shigo wai ana sallama da Anty Farida.

"Ni kuma? Waye?"

"Bai gaya min ba"

"Ya yake" Farida ta sake tambaya tana sawa ranta kwaɗayin ya kasance Sir Najeeb ne ya zo.

Yaron ya ce " fari ne, dogo, kaman balarabe ya ke amma ya iya Hausa" ai yaro bai gama bayani ba ta tashi daga gaban Umma Binta ƙanwar Ummi da ke ma ta kitso.

"Ka je da gudu ka ce ma sa ina fitowa yanzu"

"O'o amaren zamani kenan, Farida wannan zumuɗi haka"
Ai ba ta ji me Umma Binta ke cewa ba ta riga ta shige ɗaki za ta ɗau hijabi...

Ya bawa ƙofan gidan baya yana tsaye hannayen sa duka biyu su na cikin aljihu, hankalin sa ya tafi wajen wassu yaran Birom da ke wasa a ta wajen kwata yana mamakin yadda yaran ba sa ƙyanƙyamin wajen.
Yana sanye da baƙar shirt da baƙin hoodie jacket sai baƙin jeans.

"Sir Najeeb" muryan ta ya doki kunnen sa. A hankali ya juyo yana kallon ta, ba ta wani chanja ba sai dai idon ta ya ɗan nuna rama may be saboda kuka ne dan ya san ba ta wasa da abinci.

"Ashe za ka zo, shi ne ko ka faɗa min. Mu shiga ciki"

Sai da ya ɗau minti ɗaya ya na kallon ta kafin ya bi bayanta su ka shiga gidan...


Da ke kwana na tara kenan da rasuwan duk an watse sai iyalin sa kawai. A daddafe ya gaisa da su. Kusan awa ɗaya yai a gidan saboda yadda 'yan uwa da maƙota ke zuwa gaida mijin Farida wanda yawanci gulma su ke zuwa saboda su ga mutumin da ya sa aka fasa aurenta da Rayyan, su ga ya ya ke. Sai dai kowa ya zo da Masha Allah ya ke tafiya baki buɗe. Sun ga kyau, sun ga kuɗi, sun ga aji, sun ga ƙasaita...


Lokacin da zai tafi bayan ta raka shi wajen motar sa ya ce " za'a koma aiki monday yaushe za ki dawo?"

"O'o ni Aisha Farida, dan aiki kawai za a neme ni. Ni kam dole idan na koma a chanja min matsayi ya kamata a upgrading ɗi na, na bar matsayin sakatariya"

" ki na son ƙarin matsayi ne?"

"Haba Sir Najeeb wa ya ƙi cigaba a duniya"

Bai san ya ake zuwa gai da sarakai ba shi ya sa bai zo da komai ba. Ya dai bar musu dubu ɗari a gefen ɗrinks ɗin da su ka kawo ma sa wanda ko taɓawa bai yi ba...

Har motar sa ta ƙule Farida ba ta bar wajen ba. Tana ƙissima abubuwa dayawa a ranta. Zuwan Najeeb ya sa Najeeb ya ƙara samun wani matsayi na daban a zuciyar ta...





*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




0️⃣3️⃣1️⃣




*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi, ga mai so zai iya tuntuɓar 08137311900*




Yana hanya ta kirashi lokacin koma fita daga Jos bai yi ba. Ya saƙala bluetooth ya amsa kiran.

"Sir Najeeb shi ne har da ɗawaiyina haka. Mun gode Allah ya ƙara buɗi. Allah ya kai ka lafiya"
Amin kawai ya ce ya kashe kiran.


Da ya isa Kano yana so ya kira ta amma ya ka sa. Sai ya ɗauko wayar zai danna numbar ta sai ya fasa ya ajiye, ana huɗu da yai haka sai ga text ɗin ta ya shigo tana ma sa ya hanna da fatan ya isa lafiya.
"Na isa" kawai ya daure ya rubuta ya ma ta reply da shi. Maimakon ta haƙura a haka sai ta kuma turo da wanni text ɗin.
"Sir N mi zan taho ma ka da shi? ina son zuwa Wase gobe"

Bai san ina ne Wase ba, dan haka ya minimizing wayar ya browsing sunan nan ya gane wata ƙaramar hukuma ne a Jos.

Ya ma ta reply da "ok"

Ta sake turo wani saƙon " Sir N ba ka faɗi abinda zan kawo ma ka ba"

Ya na so ya ajiye wayar ya shareta amma zuciyar sa ta hanashi

"Kan ki" ya tura ma ta ba tareda ya gama tantance ma'anar faɗin hakan ba.

"Kan kifi? Sir N kan wani irin kifi?"

Ganin reply ɗin ta ya sa shi murmushi. Ya ɗan jima kafin ya tura ma ta "Mrs Jibo sleep"

Good night kawai ta sake turowa daga nan ba ta kuma turo da wani saƙon ba. Shi ma ya ajiye wayar sa gefe ya kwanta.

.......................

Safiyar Sunday ya aika ma ta da Iliya driver akan ya je ya ɗauko ta. Ita kam tana chan tana kan haɗa kayan tsaraba da za ta zo da shi. Sai da Iliya ya kusa isa cikin Jos sannan ya kira ta ya ce ya kusa isowa.
Wani matsayi ta ke kuma hangowa kan ta idan ta koma Kano. Ya sa an kawota da mota ya kuma turo ma ta driver ya dawo da ita. Wannan karramawar sai Mrs Jibo ai...

Lokacin da su ka isa gida ana kiran sallar maghrib. Iliya ya je ya kira Friday su ka shiga da buhun dankalin turawa da ta zo da shi da kuma wata ƙatuwar jakan ghana-must-go.

Ɗakin Mom ta je dan ta gaidata ta samu ba ta nan, ta wuce ɗaki ta shirya ta yi sallar la'asar da magariba...

Ƙarfe tara ta sauko ƙasa dan ta nemi abinda za ta ci, ba komai a dining ɗin hakan ya sa ta shiga kitchen shi ma wayam. Yunwa ta ke ji dan haka ta tsaya ta girka noodles da soyayyan ƙwai, ta fito ɗauke da plate ɗin shi kuma Najeeb ya shigo.

"Sir Najeeb" ta kira sunan sa. Juyowa yai ya ganta tsaye riƙe da plate da cup

Sai da ya gama kallon ta daga sama har ƙasa sannan ya juya ya tafi. Ta bi bayan sa da baki buɗe.

A dining ta zauna ta ci abincin ta dan idan ta haura sama za ta ji ƙiwuyar saukowa, sai da ta gama ci sannan ta wuce ɗaki.

"Sir Najeeb irin ba ka ji daɗin ganina ɗin nan ba, ko sannu da zuwa babu"
Bai kulata ba hakan ya sa ta gane akwai abinda ke damun sa dan bayan bai kulatan ba fiskar sa ya nuna yana cikin damuwa.

"Sir Najeeb ba ka da lafiya ne?"

"Please stop talking" abinda ya iya faɗa kenan ya gyara kwanciya a kan gado.
Tabbas akwai abinda ke damun shi dan Najeeb ba ya bacci da wuri, sannan duk rintsi sai ya yi wanka ya sa kayan bacci kafin ya kwanta.

Kaman yadda ya buƙata ɗin, shirun ta yi tana tunanin ko me ke damun shi.
Har ta kwanta Najeeb bai tashi ba, ba kuma baccin ya ke ba dan idon sa a buɗe lokacin da ta leƙa shi...



Washegari da ta shirya ta fito ne ta haɗu da Tasallah a kitchen wanda ke shaida ma ta Mom ba lafiya an ba t gado.
"Ayya ashe shiya sa jiya da na dawo na ji gidan shiru. Ya jikin ta?"
Tasallah ta ce da sauƙi. Maimakon office da ta yi niyyar zuwa sai ta wuce asibitin lokacin Iliya ya kawo Adama za ta ɗauki wassu kayan buƙatu sai su ka tafi tare.

Ta yi mamakin yadda Mom ta faɗa haka. A wajen Najdah ke cewa " tunda yanzu ke ki ke juya Big B sai ki sa ya zo ya ga Mom. Kin wani yanko ƙafa kin zo irin son a sani ɗin nan"

Farida ta kalli Najdan sannan ta kalli Mom da ke kwance tana bacci.

"Na san da cewa ba kya son ganina tareda yayan ki, amma ki sani shi ya kawo ni gidan ku ba ni na kawo kai na ba. Tun farko-farkon zuwa na ki ke ta ƙananun magana akai na, ban tanka mi ki ba. Kar ki sa na kalle ki da idon Aisha Farida dan ba za ki ji daɗi ba. Ki bini a hankali mu tafi a yadda mu ke yanzu"

Najdah ta yi tsaki, ta ɗau waya ta fara latsawa.

Farida ta fice daga ɗakin gudun kar ta fara masifa ta tada Mom daga bacci. Amma tabbas za ta ware lokacin Najdah nan ba da daɗewa ba...

Kai tsaye Najeeb constructions ta wuce sai dai da ta je office ɗinta kama baki ta yi saboda chanji da ta gani, office ɗin ta da na Najeeb ya koma kusan guda ɗaya, maimakon gini da ke tsakanin su yanzu wani tinted glass ne ya raba su wanda daga office ɗin sa yana iya hango komai a na ta office ɗin amma ita kuma ba za ta ga na sa ba.

" ba dai wannan Sir Najeeb ya ke nufi da matsayi ba"

Ba ta gama zama ba Najeeb ya shigo ran sa a ɓace. Yanzu ya fito daga board meeting.

"Sir Najeeb ashe Mom ba lafiya shi ne ba ka gaya mun ba"

"Get back to work Mrs Jibo"
Gwiwanta yai sanyi ba dai duk wani zumuɗi da zaƙalewan da ta ke yi a kan sa duk na banza ba ne.

"Noory" muryan Sabreen ya dawo da ita daga tunanin da ta ke.

Murmushi Sabreen ta yi ganin Farida a wajen. Da alama itama daga wajen da Najeeb ɗin ya fito ta fito.

Ganin Sabreen ya sa ta ma tuna da zancen ta, ita harga Allah ta manta da wata Sabreen.

"Noory, you are just taking it personal, i'm here to work"

"Kar ki sake kirana da wannan sunan. Here and anywhere else i am Najeeb to you"

Ta ɗan ji haushi saboda a gaban Farida ya faɗa. Amma ta dake ta ce "fine"

Farida ta fice daga office ɗin ta koma na ta duk da ta san daga inda ta ke su na kallon ta.

Wani yanayi ta tsinci kan ta ciki. Sabreen ta fara aiki anan, mi hakan ya ke nufi? Kenan watarana Sir Najeeb zai aiketa wajen Sabreen ko Sabreen ɗin ta ba ta saƙo dan ta kaiwa Sir Naheeb. Ba zai yiwu ba, dole ta ajiye aikin nan. Ba za ta yi aiki tana ƙarƙashin Sabreen ba, wannan cin fuska ne.

"Congratulations 'yar uwa. Finally gaskiya ta fito" muryan Anas ya doki kunnen ta.

"Wani gaskiyar?" Ta tambaya tana ƙoƙarin ɓoye damuwar ta.

Zama yai zai ma ta bayani sai ga Sabreen ta fito.

Tana ganin su ta yi wani murmushi sannan ta juya tana catwalking ta fita.

Anas ya juyo ya kalli Farida wanda itama bin bayan Sabreen ɗin ta yi da kallo.
Ya ce "asirin wanda su ka kitsa mi ki sharri ya tonu. Gaskiyar zance ta fito"

"Haba! Yaya na wani ɗan Alatsinen ne ya ke son ganin baya na"

"Wallahi Khalidah ce"

"Ban yi mamaki ba dan za ta rina"

Nan ga shiga labarta ma ta yadda aka yi gaskiya ta fito.
Da kotu za su shiga amma an settling case ɗin tsakanin Kamfani da

Please Login or Register in order to submit comment