Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da su ka iya da. A hankali-ahankali ana sake koya mu su sai brain ɗin su ya dinga picking da sauri, waɗansu abun ma kafin a nuna musu sai su tuna da kan su. Najeeb ya fara tuna 'yan uwansa ne saboda sun fi kusa da shi. It will be odd ace daga farko-farko ya gane Farida tunda ba wai sun jima tare ba ne. Koda ya ke Najeeb ɗan duniya ne zai iya ganeta ma ya waske😂 i dont know, ba ri mu bi su mu ga ya za ta ƙare*


Najdah ne ta yi saurin cewa "she's your secretary" Daddy ya buge bakin ta.
Najeeb cigaba dai da kallon Farida yana son fahimtar miye ma'anar secretary da kuma dalilin da ya sa ita wannan secretary ɗin ta ke tareda shi koyaushe.

Dr Kenneth ya ce "za ka tunata a hankali. Yanzu ka tuna ya aka yi ka zo nan?"

Najeeb ya girgiza kai still idon sa na kan Farida da idon ta ke cike da hawaye amma tana ta dannesu kar su zubo.

"Ba ka san ya aka yi accident ɗin nan ya faru ba?" Najeeb ya sake girgiza kai.

"Ka tuna wani abu a iya kasancewar ka cikin yanayi na coma?"

"I dont know, there was darkness, then voices then her eyes" ya faɗa yana nuna Farida

"Za ka iya tuna voice ɗin da ka ke ji?"
Najeeb ya girgiza kai.
Dr Kenneth ya miƙa ma sa wani littafi ya ce duk abinda ya tuna ya rubuta a ciki.

Kafin Dr Kenneth ya fita sai da ya tabbatar mu su da kada su dinga damun sa da tambayoyi, su bari a hankali zai dinga tuno komai. Za dai su iya dinga yi ma sa labarin abinda ya ke so ko kuma su dinga nuna ma sa abubuwan da zai sa ƙwaƙwalwar sa ta yi saurin dawowa dai-dai...

Najeeb ya buɗe littafin ya fara zane. Idan akwai abinda ya farayi bayan ya fara iya riƙe biro to zane ne. Dan har yanzu ma rubutun sa bai dawo dai dai ba.

Dukkan su su ka zuba mishi ido su na ganin yadda ya ke zanen wani gida. Duk da freehand sketch ne hakan bai hana gidan ya fito da kyau ba. Da ya gama sai ya zana wata mace a bakin gidan tana murmushi wanda yanayin fiskar ya ɗan yi shige da fiskan Farida.

Farida kam ba zanen ta ke kallo ba tana tsaye ne amma ta yi nisan kiwo. Tunanin ta bai wuce ya za ta ji idan aka ce kwata-kwata Najeeb ya manta da ita kuma ya kasa tunowa da ita.

"Aisha" mom ta faɗa tana dafa kafaɗarta. Ta ɗanyi firgigit ta kalli Mom, Mom ta nuna ma ta Najeeb.
Idon ta ya sauka akan Najeeb da ke miƙa ma ta takarda. Hannu na rawa ta karɓi takardar. Duban zanen ta yi sai ta fashe da dariya wanda ya sa hawayen da ta ke ta ɓoyewa su ka samu damar saukowa.
Shima Najeeb ɗin murmushin yai.

Ba abin da ya fi ɗaukan hankalin Farida irin abinda ya rubuta a ƙasar zanen *Plz smile*

"Allah sarki yanajin ta ajikin sa ne fa" Daddy ya faɗa yana shafa kan ɗan na sa.

Najdah ta cika ta yi fam, tana ta hararan Farida ta gefen ido.

Mom ta ajiye album a gaban sa ta buɗe tana faɗin duk wanda ta tuna a ciki ya faɗa. Hoton baby tana jinjira ne a farko, ya fi minti biyu yana kallon hoton kafin ya ce Baby. Gaba ɗaya sai su ka sa dariya.
Hoto na gaba kuma na shi ne yana ɗan shekara huɗu anyi hoton a wani amusement park ne yana cikin motan wasan yara. Wannan kam bai ɗau lokaci ba ya nuna kan sa. Hoto na uku hoton shi da Sabreen ne lokacin da Sabreen ta yi graduation ɗin gama high school. Ya jima yana kallo, ya gane ta amma sunan ya maƙale ma sa. Kusan minti huɗu ya ce "Sa Sa Sabreen"...

Har lokacin da Farida ta zame jiki ta bar ɗakin ba su ankara ba. Tafiya ta ke amma ba abinda ke yawo a ƙwaƙwalwarta irin sunan da Najeeb ya ambata.
Wato ya iya tuna Sabreen amma ita bai tuna ta ba, Sabreen fa!...

Hoton Aisha aka buɗe ma sa lokaci guda idon sa ya fara kawo ma sa hoton ta kwance cikin jini. Dafe kan sa yai yana numfashi da ƙyar nan kuma seizure ya kama shi ya fara jijjiga. Su Najma su ka fita kiran likita, bayan seizure ɗin ya tsaya Dad ya gyara ma sa kwanciya ya maida shi kwance ta gefen sa...


...................

Tana zuwa ɗakin su gado ta hau, kukan ma da ta ke son yin ma ta kasa. Zazzaɓi ne ya rufeta tun tana rawan sanyi har bacci ya tafi da ita. A ƙalla ta yi awa uku tana bacci kafin ringing ɗin wayar ta ya tashi.

Ta ɗau wayar tana mai goge gumin da ke goshinta da ɗaya hannun.

"Aisha ki na ina?"

"Ina gida Mom"

"Yaushe za ki dawo?"

"Sai dare"

"Ok"

Sai da ta ajiye wayan ta tashi da ƙyar. Ko'ina a jikin ta ciwo ya ke a haka ta shige banɗaki dan ta yi wanka...


Da dare da ta isa ta tarar da abun mamaki. Mom na tsaye gaban Najeeb tana hawaye tana bashi haƙuri, shi kuma ya kauda kai gefe.
Daddy baya nan dan ya bar asibitin tun da yamma. Najdah ne a wajen bayan Mom, itama Sallah ta ke yi.

Mom ta zagayo gaban Najeeb ta tsugunna har ƙasa. Da gudu Farida ta ƙarasa wajen tana ƙoƙarin ɗaga Mom.
"Mom so ki ke ki ja ma sa bala'i. Bai kamata ki tsugunna ma sa ba"

"Ki bar ni Aisha, ya tuno abinda na yi ya ce baya son ganina. Plz ki ce ya yafe min, ba zan iya rayuwa ba tareda ina kusa da shi ba"

Farida sai da ta tabbatar ta ɗaga Mom kafin ta sa hannu ta fara goge ma ta hawaye.
"Dan Allah ki dena kuka, kukan ki masifa ce a gareshi"
Da ƙyar Mom ta iya haɗiye kukan ta yi shiru.

Farida ta juya ta kalli Najeeb da ya ƙura ma ta ido, cikin ɗaga murya ta ce "kai Sir Najeeb, ka kiyayi fushin mahaifiyar ka. Kar ka ga dan kana cikin wannan yanayi ana tausaya ma ka ka maida mu bamu san mi mu ke ba, ka sanni sarai zafi gareni, kuma idan ba ka shiga taitayinka ba duk abinda ke cikin ƙwal..."

"To kashe ma na shi. Munafuka, kin san yana cikin wani hali amma ba za ki bari hankalin sa ya kwanta ba, kashe shi tunda abinda ki ke so kenan, dan ki gaji dukiyar sa ko"


"Najdah!" Mom ta daka ma ta tsawa.

"Mom ki ga abinda ta ke ma sa fa, anan ɗazu ya shiga wani hali saboda wani abu ya tuno amma yanzu ta dinga ma sa masifa kaman wani ɗan ta"

Shikan ido ya ke bin su da shi. Yadda Farida ke masifa haka ya dinga ji ƙwaƙwalwarsa na tuno ma sa wassu masifan da ta yi a baya. Abin ya confusing na shi, domin yana ta ƙoƙarin gano a ina abubuwan nan su ka faru kuma yaushe su ka faru.

"Ki tafi ki bamu waje zamu iya jinyar sa" Najdah ta faɗa tana kallon Farida ido cikin ido.

"Yarinya kenan, ki je ki yi aure za ki fahimci minene tsakanin miji da mata. Jinya kuma ko uwar da ta haifeshi ba ta ma sa ɗawainiyar da na ma sa ba."

"Mom kin ji maganar banzan da ta ke yi ko?"

Mom ta ce "gaskiya ta faɗa. Babu wanda yai wa Najeeb hidima kaman ta, kuma ba abinda za mu saka ma ta da shi sai addu'a. She's the only one that never stop believing in him kuma na tabbata da ya yi shekaru a haka to a hakan Faridan za ta jira shi"

Najdah haushin maganan Mom da ta ji ya sa ta je ta ɗau jakan ta fuuuu ta fita ko sallama babu.


"Koyaushe haka ki ke da faɗa?" Najeeb ya tambaya yana kallon Farida

"Haka na ke, a haka ka sanni dan haka idan za ka tuno ka tuno, idan ma ba ka tuno ba to zamu cigaba daga inda mu ka tsaya"


"Son please forgive me" Mom ta faɗa tana haɗa hannun ta alamar magiya.

"Ka san Allah Sir Najeeb ba inda za ta je sai ka ce ka yi haƙuri"

Dariya yarinyar ta bashi.
"A matsayin ki na wa?"

Confidently ta ce "a matsayina na matar ka"

"Mata na?" Ya tambaya looking confused

"Yes ni matar ka ce" ...


.........................

Bai gama yadda da maganar Farida ba sai da Washegari da Najdah ta zo ya tambayeta ya aka yi ya auri Farida ba Sabreen ba. Da ke tana jin haushin Farida ba ta faɗi laifin Sabreen ba, sai ta ce Daddy ne ya aura ma sa Farida kuma ba son ta ya ke ba.
Maimakon ya bibiyi miya faru. Sai zuciyar sa ta fara kawo ma sa soyayyar sa da Sabreen, take kuma tausayin Sabreen ya kama shi. Sai dai kasancewa bai gama gane abinda ya faru da shi ba ya sa yai shiru...

Duk da ya tuno abinda ya haɗa su da Mom amma tundaga ranan da Farida ta ma sa masifa sai ya dena ɗaure ma ta fiska amma dai still ya kasa sake jiki da ita.

A kwanan sa na talatin da bakwai da farfaɗowa sai ga Sabreen. Shi da Farida da therapist ɗin sa ne a chan wani fili, yana gwada tafiya da walking stick ɗaya maimakon biyu da ya ke amfani da su da.

Najdah da Sabreen ne su ka nufo su. Sabreen na ƙara tabbatar wa idon ta ga Najeeb nan a raye kuma yana tafiya ta yanka da gudu ta je ta faɗa jikin sa.

"Noory you're back, i miss you Noory, i miss you"

Ji ta yi an damƙi gashinta da ƙarfi, dama ɗan gudun da ta yi ya sa gyalen da ta yafa ya faɗi.

"Ah Ah...Noory help" Sabreen ta faɗa tana ƙoƙarin ƙwatan kan ta. Amma ba ƙaramin damƙa Farida ta yiwa gashin ba.

"Wallahil Azim ko ki koma inda ki ka fito ko na lahira ya fiki jin daɗi. Idan ma hauka ke kan ki to nawa sun fi na ki"

Ganin yadda idon Sabreen ya firfito, goshinta yai ja, jijiyinta su ka mimmike ya sa Dr Kenneth ya fara bawa Farida haƙuri akan ta sake ta za ta illata Sabreen.

Najeeb kam tsayawa yai a gefe yana kallon ikon Allah.
Da ƙyar Farida ta haƙura ta sake Sabreen wanda ta faɗi ƙasa tana numfashin wahala, har da hawaye.

Cikin zuciyar sa ya ke tunanin ashe Najdah ta yi gaskiya da ta ce ma sa Farida is mentally not stable.

Zuwa yai zai taimakawa Sabreen ta tashi. Farida ta riƙe shi " inka ɗaga ta na mutu kafira"
Bai ɗaga tan ba sai ma Dr kenneth ne da Najdah su ka ɗaga ta...

Ranan dai Sabreen ba ta sake dawowa ba sai washegari.
Duk zuwan ta gaishe shi sai dai ta zo da Najdah dai-dai lokacin da Mom ko Daddy ke wajen sa. Shegiya ta ji damƙan manya😂...

Har yanzu dai bai gama tuno komai ba, yadda memory ɗin ke dawo ma sa tsilla tsille ne ba direct ya ke tuno abu ba. Wani lokaci sai anyi magana sai abinda aka faɗa ya triggering ma sa wani memory.

Yau ma magana ya ke da likitan sa a office likitan ya excusing kan sa yana amsa waya. Juyawar da zai yi ya kalli Tv da ke ɗakin likitan sai ga Sabreen a cikin TV. A church su ke ana ɗaura ma ta aure da wani, bayan priest ya ce you may now kiss the bride sai ga shi ɗaya actor ɗin ya kama waist ɗin Sabreen su na kissing. Najeeb ya rintse ido wassu abubuwa na dawo ma sa....





*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


0️⃣4️⃣1️⃣





Dafe kan sa yai yana jin wani irin zogi. Komai ne ke son dawo ma sa lokaci guda. Likitan ne ya lura da yanayin sa.

"Are you Ok?"

Da kyar Najeeb ya ɗago kan sa idon sa sun yi ja.

"Mr Najeeb ka dinga yi a hankali, kar ka takura wa kan ka, ahankali za ka tuno komai"

Najeeb ya gyaɗa kai...


Tun bayan abinda ya tuno gameda Sabreen ƙoƙari ya ke ya tuno ya su ka yi zaman auren su da Farida. Although Najdah ta gaya ma sa ba auren soyayya su ka yi ba, he still wants to remember something gameda auren su. Yawancin abubuwan da ya ke ɗan tunowa gameda ita time to time bai wuce aikin su tare a office ba. Tun ranan da ya tuno abinda Mom tayiwa Aisha ya ke ƙoƙarin ɓoye wasu abubuwan da ya tuno. Ko ranan da ya tuno accident ɗin da yai bai gaya mu su ba, he pretends bai tuna ba.

Farida ce bashi abinci, su biyu ne a ɗakin. Duk da yanzu yanada ƙarfin jiki sosai zai iya cin abinci da kan sa amma Farida sam ta hana. Dole sai dai ita ta feeding ɗin sa, su yi ta daru akan rashin son cin abincinsa. Yana cin kaɗan idan ya ce ya isa Farida za ta hau shi da faɗa. Wani lokaci idan ta takura ya kan ƙara kaɗan amma ma fi yawancin lokutan kau da kai gefe yakeyi ya ƙi ci.

Yau ma ɗin ita ke bashi abinci.
"Aysherh" ya kira sunan ta. Ranan da ya fara kiranta da wannan suna ya ga farinciki da ɗoki tattare da fiskar ta, har da cewa "My Champ sake kira dan Allah"

Lokacin da ya tambayeta ko ya ya ke kiranta da kafin wannan abu ya sameshi ƙin gaya ma sa ta yi, tace ya kira ta da Aishern kawai. Shi kam sai ya ke ji kamar ba Aysherh ya ke kiranta ba. Sunan a bakin sa ya yi daban, like there's more to sunan Aysherh da ya ke kira.

Yayi gyaran murya ya ce "Ehm Aysherh...Ehm....did we?" Ya sake gyaran murya
"Have we.....?"

"Ina jin ka mijina" ta faɗa tana goge ma sa baki da tissue.

Wannan karan daurewa yai ya ce "lokacin da mu ka yi zaman aure da ke muntaɓayin wani abu?"

Dariya ne ya cika ta amma ta gimtse ta ce "wani abu kuma?"

Sai da yai gyaran murya kafin ya ce "abun aure"

"Abun aure ai dayawa My Champ. Wanne a ciki?"

Ya marairaice ido ya ce "please Aysherh. Kin san abun da na ke nufi fa"

Daɗi kashe ni. Abin da zuciyarta ya faɗa kenan, wai Najeeb na hira da ita, hiran ma irin hiran su ta da.

"I'm serious Aysherh"

"Abubuwan aure ai dayawa My Champ. Akwai cin abinci tare, wanka tare, wasa da dariya tare, akwai kuma abubuwan da ake yi da dare, ko kuma ayi abun idan ɗaya ya ji abu sai ya taƙali ɗayan sai a haɗu ayi abubuwa. So wanne aciki ka ke tambaya?"

Maganan nan ya tuno ma sa da wassu abubuwa amma har yanzu bai iya tuno ko sunyi abun da shi ya ke tambaya ba.

"So, we did everything that couples do?"

"Mun yi komai hadda gyara"

Zaro ido yai lokaci guda kuma ya sa hannu yana tare gaban sa.

Farida ta fashe da dariya tana faɗin "to na nawa kuma. Bayan angama ganin komai"

Har lokacin bai ɗaga hannun sa ba ya ce " you're lying"

Tana cikin dariya Anas ya shigo.

"Wannan dariya haka, Farida ko dai ya tuno komai ne?"

Farida ta girgiza kai. As usual ya kawo ma ta wasu documents ne ta duba.

Anas ya gaida Najeeb wanda har lokacin yana kare gaban sa da hannu.

"Abokina ya dai? ko wani abu ya samu wajen ne?"

Pillow ya jawo ya sa a wajen kafin yai wa Anas wani mugun kallo.

"Mutumina ka godewa Allah da ya ba ka jarumar mace. Ba dan ita ba da kamfanin ka ta samu matsala"


"Ko a wanni duniyan ne secretary ta ke zama Oga oho?"

Ya kalli Farida da ido ya ce "what did you know Miss Salihu?"

Farida ta zaro ido, shi kuwa murmushin yaƙe ya mata ya maida hankalin sa kan Anas.

Abubuwa dayawa ne ke yawo a cikin ƙwaƙwalwarta. Kenan Najeeb ya tunata, komai ya tuna? ko kuma dai ba komai ba.

"Alhamdulillah mutumina. Ka tuna Miss Salihun ka, the stubborn Miss Salihu"

"Ko ba Miss Salihu ba ne ta sa min superglue a seat?"

Anas ya kwashe da dariya. Ita kuwa Farida jikinta ne yai sanyi.
Najeeb ba wai ya tuna abin ba ne da kan sa. Ranan ne Najdah ta nuna ma sa video ɗin da Anas ya nuna mu su ranan birthday ɗin sa, yana gani kuma wassu abubuwa su ka dinga dawo ma sa gameda Farida, musamman lokacin su na office...

Bayan Anas ya tafi, Farida ta ce " My Champ ka tuna komai ne?"

"The last time i remember ba da wannan suna ki ke kirana ba. What changed?"

Da gayya ya gaya ma ta haka, shima rama abinda ta ma sa ɗazu yai.

"Saboda..." sai kuma ta kasa magana.

Ranan gaba ɗaya gwiwarta yai sanyi. Duk yadda ta yi dan ta fahimci ko ya tuno komai na rayuwar su amma ta ka sa. Sai ya dinga gwaleta idan ta tambayeshi...

Washe gari da safe ƙarfe goma sai ga Lukman. Bayan ya yiwa Najeeb ya jiki sai ya ke faɗa ma sa cewa gaskiya ya riƙe Farida da kyau domin ta ma sa abinda ba ko wacce macce ne za ta iya yi ba.

"Oh! and how do you know?"

Lukman ya ƙaƙaro murmushin dole ya ce "saboda na gani da ido na"

"Nagode da gaisuwa, Dr Lukman right?"

Lukman ya gyaɗa ma sa kai tareda barin ɗakin, chan ƙasan zuciyarsa kishi na cin sa...


"Shi kuma wannan daga ina ya ke?" Ya tambaya yana tsare Farida da ido

Ba tareda ta kalli idon sa ba ta ce "he's my ex husband"

"Ashe ma bazawara na aura ban sani ba"

Ɗago rinannun idanunta ta yi tana ma sa wani kallo. Abinda ma zai ce ma ta kenan wai bazawara. Anya za ta taɓa samun matsayi a wajen Najeeb musamman yanzu da bai gama gane kan sa ba...

...............................

Bayan anyi sunan ɗan Maijiddah da kwana uku AbdulWahab ya koma Lagos. Bai samu Aneesa a gida ba, dama ta ce ma sa Abuja za ta je. A washe garin ranan da ya dawo ta dawo. Ita ba ta ma san ya dawo ba...

Tana zaune a falo tana kallo tana cin pringles sai ga kiran wata ƙawar ta.

Bayan sun gaisa ƙawar ke tambayarta ya kishiyar ta.

" shegiyar fa haihuwa ta yi, namiji kuma"

Ɓangaren ƙawar ta ke ma ta faɗa akan ta yi sake da har ta bari Maijiddah ta haihu a gidanta.

"To ya zan yi Binta, kwanan baya har cikin ƙarya na ce ina da shi dan na samu attention ɗin AbdulWahab kuma na samu a lokacin. Daga baya na mata sharri akan ta tureni cikin ya zube. Da farko ya yarda daga baya ya ƙaryata zancen. I really dont know what to do again..."

Ko mi ƙawar ta ce oho. Aneesa dai cewa ta yi "ni kin san ba na son shige-shigen nan. Ka je ma duk su ci kuɗin ka a banza ba biyan buƙata"

Jayayya su ka fara yi da ƙawar akan zuwa wajen Boka, daga ƙarshe Aneesa ta kashe wayan tareda cewa za ta yi tunani akai.

"Nonye....Nonye"
Ta fara kiran mai aikin ta. Jin shiru ya sa ta miƙe tsaye, ai kuwa da sauri takoma ta zauna daɓas tana riƙe baki.

"Sweetheart" ta faɗa baki na rawa.

Yana tsaye ya harɗe hannuwan sa a ƙirji yana kallon ta, idon sa yai wani irin ja.

"Aneesa why? Why? Ki rasa abinda za ki yi sai ƙarya"


"I can explain AbdulWahab, please" ta faɗa tana haɗa hannuwan ta biyu.

"Wajen Boka ko, ki je Allah ya bada sa'a" yana faɗin haka ya haura sama.

Jikin ta na rawa ta tashi ta bishi da sauri...

Buga ƙofar sa ta ke yi amma bai kulata ba balle ya buɗe, ta zauna a bakin ƙofar tana ba shi haƙuri tana hawaye...

Kwanaki uku su ka gifta amma kalma ɗaya ba ta ji daga bakin AbdulWahab ba. Ta yi kukan ta bada haƙurin amma bai ma kulata ba balle ta san ko ya yafe ko bai yafe ba.
A rana ta biyar ya ce ma ta idan har ta zaɓi zama da shi to za ta ajiye aikin ta ta zauna ta kula da shi da kuma yaranta, amma idan ta zaɓi aikin ta to zai sawwaƙe ma ta.

It was a very tough decision for her. Tana son AbdulWahab tana kuma son aurenta. Duk da dai ta san ba ƙaramin asara za ta yi ba idan ta ajiye aiki amma kuma ba za taɓa zama bazawara saboda aiki ba. Ta kira Mama neman shawara, inda Maman ta ce ma ta ta zaɓi abinda ta ga ya fi ma ta, amma ta sani ba za ta taɓa samun wani miji kamar AbdulWahab ba musamman ma a shekarun da ta ke yanzu.
Ƙarshe dai shawaran da ta yankewa kanta shine ta ajiye aiki...

Duk da ta ajiye aiki hakan bai sa AbdulWahab ya koma ma ta kamar da ba. Cewa ma yai ta je ta bawa Maijiddah haƙuri. Girman kai ba zai bar ta ba, ta girmi Maijiddah sosai, kusan shekara shashida ta bata. Da ta ga uwar bari dole dai sai da ta kira Maijiddan a waya ta ba ta haƙuri. Maijiddah kam ta yafe tuntuni tunda mijinta ya gane gaskiya kuma ya yarda da ita ai an wuce wajen... kafin Aneesa ta samo kan mijinta sai da ta kai wajen wata ɗaya...



.................................


Yau aka sallami Najeeb daga asibiti bayan kwanaki hamsin da huɗu da yai da farfaɗowa. A report ɗin da su ka bayar sun nuna cewa ba shida matsala, a hankali zai dawo da dukkan ƙarfin sa, haka kuma bisaga tambayoyi da kuma shaidar 'yan uwansa sun tabbatar da cewa ya tuno kaso tamanin na rayuwar sa ta baya kuma a hankali zai ƙarasa tuna komai...

Gefen sa na dama Farida ɗayan kuma Najdah a haka su ka fito daga asibitin Daddy da Mom kuma na gaba farinciki yana nan tattare da fiskokin su. Motar Farida su ka shiga, yadda Najdah ke maƙalewa Najeeb ba dan su Daddy na wajen ba da ta gaya ma ta maganar banza.

Maimakon Najdah ta bi motar su Daddy sai ta shiga tasu motar.
Su uku ne a baya sun sa shi a tsakiya.
"Dan Allah ki fita ki bamu waje, mata da miji suna son ganawa da junan su"

"Wayaga mata. Ba inda zan je. Yaya na son kasancewa da ƙanwar sa"

"Tunda sirrin miji da mata ki ke son gani, Bismillah" ta faɗa tana hawa kan cinyar Najeeb, kafin ya ce wani abu ta haɗe bakin su, yana so ya tureta daga jikin sa saboda Najdah da ke motar amma gangan jikin sa ya betraying ɗin sa. Maimakon ya tureta sai ma ƙara matseta yai a jikin sa, yayinda kuma hannunsa duka biyu su ka fara yawo tsakanin bayan ta zuwa hips ɗin ta.

"Dreba tsaya zan fita" Najdah ta faɗa tana jan tsaki.
Sun fito daga gate ɗin asibitin kenan ko nisa ba su yi ba.
Ya samu waje yai parking

"Karuwa kawai" ta faɗa tareda banko mu su ƙofar motar.
Abdullahi dreba ya fara dariya ƙasa-ƙasa yana faɗin "to kema miji ya kwanta a asibiti tsawon watanni ba lafiya, yanzu ya samu lafiya ki zo ki liƙe ma sa, ai duk abinda ki ka gani ke ki ka jawo"


Lokacin da ta ji Najdah ta fita ta fara ƙoƙarin janye bakinta.
"My Champ" ta faɗa cikin sarƙewan numfashi tana nuna ma sa ƙeyar dreba wanda bawan Allah kam kiɗa ma ya sa a motar ya ƙure volume sosai, dan kar kunnen sa ya jiyo ma sa ba dai-dai ba.

Kallon-kallo su ka fara yiwa junan su, idon Najeeb yai wani ja guguwar sha'awa ta bugeshi.
Ya san a mota su ke amma kuma duk wani ƙoƙarin hana jikin sa aikata wannan abu ya ka sa, jikin sa har rawa ya ke yi. Ƙoƙarin tashi ta ke yi daga jikin sa gaba ɗaya. Ya maidata da sauri, "My Ch..." Najeeb bai bari ta ƙarasa ba ya jagoranci wannan kiss ɗin, wannan karan da zafi zafin sa ya ke yi, ya cire ɗankwalin ta ya sa hannun sa cikin gashin ta yana shafawa. Kafin ta ankara yai wani juyawa da ita sai gashi tana ƙasa yana samanta still bakin su haɗe da na juna. Ta san glass ɗin motar tinted ne amma kuma ko da Abdullahi dreba bai juyo ya leƙa su ba, ya san dole su na aikata wani abu a bayan motar.

Ƙoƙarin zuge

Please Login or Register in order to submit comment