Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su saboda Alhaji Matawalle ba ya so a je kotu domin ya na siyasa kuma ya na son fitowa takaran senator. Na biyu kuma Alhaji Tukur mahaifin Khalidah ba ya son wargaza alaƙar sa da Najeeb, 8% shares na shi a kamfanin shi ya san kuɗin da ya ke samu, shi ya sa shima ya zaɓi teburin sulhu.

Alhaji Matawalle zai biya kamfani taran miliyan ishirin ita kuma Khalidah za ta biya Farida miliyan biyu.

" 'yar uwa mun yi kuɗi fa. Dan Allah ayi kason da mu"

Farida murmushi kawai ta yi dan ba wannan ba ne damuwar ta.

Ranan duk wani ɗokin dawowa Kano da ta yi ta ji Kanon ya fita ma ta a kai. Da yamma bayan ta dawo Baba Sabuwa ke kiran ta akan 'yan uwan Najeeb sun kawo lefen ta yau da safe. Su kan su ba su san da zuwan ba ko karramawar kirki ba a mu su ba.
Farida kin ga kaya ki godewa Allah gaskiya domin an zuba dukiya a lefen ki. Yanzu ya za ayi? Za a kawo mi ki shi chan gidan kun ne ko ya?

"Baaba Sabuwa duk yadda ku ka yi" ta faɗi hakan ne saboda ko kaɗan maganar lefen bai sa ta ji raɗaɗin da ta ke ji ya ragu a zuciyar ta ba...

........................

Yana shigowa Daddy ya kirashi tambayar sa yai ko ya je ya duba Mom ya ce bai je ba.

"Yanzu Najeeb ka kyautawa kan ka, da girman ka da ilimin ka amma ba za ka kyautatawa mahaifiyar ka ba. Duk abinda ta yi ma ka bai kai ace tana kwance a asibiti yau kwana uku ka kasa zuwa ka dubata ba. Najeeb tsinuwa ka ke nemawa kan ka?"

Maganganun Daddy su na shiga su na fita ta ɗaya kunnen ne, saboda ba jin su ya ke ba hankalin sa ya tafi wani wajen. Jini kawai ya ke gani malale a ƙasa ga kuma gawar Aisha...

Daddy ya gama ma sa wa'azi sai Najeeb ya tashi ya fita ba tareda ya ce komai ba...


Tuƙi ya ke amma zuciyar sa na tuno ma sa abun da ya faru shekaru da su ka wuce. Duk da yanzu ya girma kuma ya san ƙaddarar Aisha ne ta zo da haka amma wannan trauma ɗin da ya dasu a ransa tun yana yaro ya ƙi sake shi...

***

Cikin Aisha na wata takwas abin ya faru. Immediately Adam ya saki Nabilah ta tattare yaranta ta bar ma sa gida. Sai dai hakan bai sa Najeeb ya dena zuwa wajen Aisha ba. Idan ya taso daga makaranta chan zai wuce sai dare ya dawo. Mom ta ma sa faɗan amma baya ji.
Ana haka sai ɗaya daga cikin ma su kula da Aisha ta yi tafiya saboda Maman ta da ta mutu. Ganin haka ya sa Najeeb ya dawo wajen Aisha da zama duk da kuwa akwai Mrs Beverly tareda ita. A kwana na uku da ya koma wajen Aisha, Mom ta zo da ƙarfin tsiya ta tafi da shi gida ta hana shi zuwa wajen Aisha. Abu da renon turawa sai ya fara maida ma ta magana akan ba ta isa ta hana shi fita ba, Ya fita da gudu.
Mom ta nemi restraining order daga kotu akan ba ta yadda ɗan ta ya je gidan Aisha ba saboda tana tunanin Aisha za ta ma sa lahani. Da ke Najeeb under 18 ne sai ya zama dole yana ƙarƙashin kulawar iyayen shi. Ranan da letter ɗin ta fito haka Mom da jami'an kotu su ka je su ka ɗauko Najeeb tareda faɗawa security ɗin gidan ko da wasa kar ya bari Najeeb ya shiga gidan.

Daren ranan yai wani mummunan mafarki akan Aisha ta mutu hakan ya sa da safe ya kira Daddy da ke Belgium a kan ya sa baki yana son zuwa wajen Aisha.
Mom ta ce indai ya na America yara za su zo wajen sa amma Yaran ta ba za su je wajen Aisha ba. Da Najeeb ya fita school bai je ba sai da ya fara biyawa wajen Aisha ya ga tana lafiya kafin ya tafi.
Yammacin ranan da ya dawo ya samu Mom tana masifa akan Aisha ta dameta da kira. Najeeb bai kulata ba sai da Najma ta dawo ta ke ce ma sa yau ta ji tausayin Aisha domin ta kira kusan so biyar amma saboda ba ta magana ba ta iya ba da saƙon da ta ke son faɗa ba. Ƙila tana son ganin ka ne.

Hankalin Najeeb ya tashi, tunda su ka raba gida Aisha ba ta taɓa kira ba. Ta kira sau biyar kam yana nufin tana cikin matsala ne. Haka ya fita da gudu ya je ya ɗau keken sa ya tafi gidan Aisha duk da kuwa Mom tana ƙwala ma sa kira akan ya dawo.
Da ya je gidan tun daga falo ya fara kiran Aisha amma ba ta fito ba ya duba Mrs Beverly a kitchen ba ta nan sai ya haura sama da gudu. Kai tsaye ɗakin Aisha ya shiga. Amma mi sai ya ji kukan jinjira, yana duba gefen sa ya ga Aisha kwance ga jini duk ya ɓata wajen. Irin jinin da ya gani sai da wani jiri ya kusa kada shi ya dafe gini na wasu mintuna kafin ya ƙarasa wajen ta yana jijjigata amma ba ta tashi ba. Cikin kuka ya je ƙasa da gudu ya kira emergency line na police...

Yana tsaye aka zo aka ɗauke gawan Aisha, duk abinda idon sa ke sa ma sa shine Mom ce ta kashe Aisha. Ranan shima asibiti ya kwana dan yana tsaye a wajen bayan ansa gawar Aisha a mota ya faɗi ya suma...

Ko da bayan autopsy na Aisha ya fito kan ba kashe ta aka yi ba, haihuwa ta yi ita kaɗai jini ya tsinke ma ta kuma rashin Mutum a kusa da ita ya sa ba a kawota asibiti da wuri ba har ta mutu.
Najeeb bai daina ganin Mom a matsayin wanda ta kashe Aisha ba. He was very traumatized a lokacin da har ta kasance baya iya bacci sai da magani. Ya jima yana visiting therapist kafin daga baya aka ce ya dawo normal amma still a hakan bai koma dai-dai da Mom ba.
Rasuwan Aisha ya sa Mom ta saduda da rayuwa, ta nemi Adam ya maidata dan ta kula da Najdah...

"She wanted her dead all along, she's evil" abin da ya faɗa kenan ya buga steering ɗin motar. Idon sa na buɗe amma duhu ya ke gani, yana ƙoƙarin saita motar ta shi wata babbar mota ta zo ta buge motar sa, motar Najeeb ta yi sama sannan ta dawo ta faɗi ƙasa...



*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




0️⃣3️⃣2️⃣





*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi, ga mai so zai iya tuntuɓar 08137311900*


*wannan page ɗin na ki ne ke kaɗai Anty nah Surayyah. Wishing you health, wealth, peace, grace, mercy and joy amin. Allah ya ƙarawa rayuwarki ta Oga da ta yaran ki albarka amin. Happy birthday🍾🥂🎂*



Tana zaune sai cika ta ke tana batsewa, abu ɗaya ta sani shi ne ta ajiye aiki da Najeeb sannan kuma dole ta rama abinda Sabreen ta ma ta. Ba za ta bar karuwan nan ta sha banza ba.
Tun tana duba agogo tana jiran Najeeb har bacci ya ɗauketa akan Sofa...


Daddy kam bayan fitan Najeeb kiran matar sa yai su ka yi hira, da ke jikin tan da sauƙi, dan likitan ya ce za'a iya sallamarta gobe.

Ƙarfe shaɗaya na dare wayar sa ta fara ringing, daga kan gado ya sa hannu ya lalubota ya ɗara a kunne dan ko gama gane numban da ya kira bai yi ba.
Abin da aka ce ma sa ne ya sa ya tashi zaune yana maimaita Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raju'oun jikin sa na ɓari.
Ɗaukan key yai ya fita daga ɗakin da sauri duk da kuwa pyjamas ne a jikin sa...


Tunda aka shigo da shi ake ƙoƙarin tsaida jini, yadda jini ke zuba a jikin sa da ma gefen kansa ka ce duka jikin sa zai tsiyaya zuwa ɗan ƙanƙanin lokaci.

Wani na ganin Najeeb Adam Jibo a jikin ID card ɗinsa ya gane ko ɗan waye, shi ya sa aka kira numban Daddy...

Yadda Daddy ke jinsa gani ya ke ba zai iya jira har Iliya ya taso daga BQ ya zo ya kai shi ba duk da an hana shi tuƙi da dare saboda idon sa.
Yana fitowa yana ƙwala sunan Malam Aminu maigadi akan ya buɗe gate, yadda ya ke kiran, shi kan sa Maigadi sai da ya tsorata... Ikon Allah ne kawai ya kai shi asibitin lafiya amma ƙila da shi ma hatsarin zai yi.

Yana zuwa aka ce har lokacin likitoci na kan sa. Jikin sa rawa ya ke bai iya zama ba yana safa da marwa zuciyar sa cike da addu'o'i. Tsabar rikicewa ko fitowa da wayar sa bai yi ba daga mota...

Anas ƙarfe huɗu da rabi na asuba aka kira shi, ya fito daga banɗaki kenan ya yi alwala ya ji kira kafin ya ɗauka ta katse. Ganin Daddy sai hankalin sa ya tashi, lokaci guda zuciyar sa ta raya ma sa ƙila Mom ce ta rasu. Duk da kuwa jiya da ya je dubata ya ga jikin ta da sauƙi sosai, to amma mutuwa ko da ciwo ko ba ciwo sai an tafi. Yana ƙoƙarin sake kiran Daddy kiranshi ya kuma shigowa ya ɗauka da sauri.

Maimakon Daddy ya ce ma sa wani abu ne ya samu Mom sai yai ma sa maganar Najeeb, Najeeb da su ka rabu lafiya ƙalau jiya.
"Daddy ya rasu ko?" Ya faɗa hawayen da su ka cika idon sa su na gangarowa.

Daga ɓangaren Daddy ya ce " a'a, yanzu likitocin su ka fito amma bai farfaɗo ba har yanzu"

Yai hamdala tareda cewa gashi nan zuwa...

Zuwa ƙarfe bakwai na safe asibitin ya cika da 'yan uwa. A wannan lokacin ne Uncle Sulaiman ya sa aka maida Daddy gida saboda ya chanja kaya.


.....................

Farida ba ta farka ba sai ƙarfe biyar lokacin da alarm ɗin ta yai ta ruri ba kakkautawa. Da ƙyar ta sa hannu ta jawo wayar ta katse alarm ɗin. Mafarki mai daɗi ta yi, itada Najeeb su na zaune a wani lambu, kanta na kan cinyar sa yana wasa da gashin ta.

" I love you Aysherh" ya faɗa idon sa cikin na ta.

"I love you too Sir Najeeb"

Hannun sa ya sa ya ɗan matse bakin ta ya ce "ba na hana Sir Najeeb ɗin nan ba"

"Sorry my champ"
Ta ɗan ɗago kanta ta kissing goshin sa sannan kumatun sa sannan hanci. Ganin ta tsaya ya sa yatsa ya nuna lips ɗin sa.

Ta girgiza kan ta. Ya ɗan yi ƙanƙan da ido alamar tausayi. Murmushi ta yi tareda haɗe bakin su...


Ta tashi jiki a mace ta shige banɗaki, wannan mafarki da ta yi ya sa ta sassauta jin haushin sa da ta ke ji.

Lokacin da ta zo gaban madubi, kallon kanta ta yi ta fara gwada maganan da za ta yiwa Najeeb ta yadda zai tabbatar ran ta ya ɓaci ya kuma ɗauki maganarta serious.
A hankali tana fari da ido ta ce "Sir Najeeb, gaskiya idan Sabreen za ta yi aiki a kamfanin ka to ni zan ajiye aiki na"
Ta yi tsaki ta ce ba haka bane barin sake. Wannan karan ta haɗa rai ta ce "Sir Najeeb zan ajiye aiki na"

Sai ta kwaikwayi muryan sa ta ce " good for you"

"Good for you kawai za ka ce min? Ka na tunanin idan na ajiye aikin akwai wanda zai iya yi ne?"

Da muryar sa ta ce "dayawa ma"

" Sir Najeeb, Allah ni kaɗai ce za ka iya jura. Ba wanda zai iya juran faɗan ka. Kai ba mace ba amma sai shegen mita"

"Aysherh" ta ji muryan sa a bayanta. Da sauri ta juya amma ba kowa. Ta rufe ido tana tuno kiss ɗin su na ranan...


Saboda ta tsara ba za ta koma aiki ba shiya sa da ta gama azkar ɗin ta ta sauko dan ta taya Adama aiki.
Tana saukowa ta haɗu da Daddy wanda shigowar sa kenan, ganin sa sanye da kayan bacci ga kuma damuwa shimfiɗe a fiskar sa ta yi tunanin ko wani abu ne ya samu Mom.

"Daddy ya jikin Mom" ta faɗa cike da tararrajin mi zai ce

"Alhamdulillah da sauƙi 'ya ta"

"Lah ba mu ma gaisa ba" ta faɗa tana tsugunnawa ta na mi shi ina kwana.

Tausayin ta ne ya kama Daddy. A yadda ya ga Najeeb ɗazu zuciyar sa ta karaya. Yanzu idan Najeeb ya rasu wanni hali Aisha za ta shiga? Auren da bai wuce sati shida ba.

"Aisha ki shirya yanzu, idan na fito za mu je asibiti Najeeb ba lafiya"

Dum ƙirjinta ya buga "Najeeb ba lafiya, mi ya same shi?. Allah sarki ashe shi ya sa bai kwana a gida jiya ba." Tambayar da ke yawo a kanta kenan.
Amma duk yadda aka yi rashin lafiyar Najeeb mai tsanani ce dan kuwa Daddy ba zai damu har haka ba idan minor abu ne.
Komawa ɗaki ta yi dan ta ɗau gyale da jakar ta...

Iliya ne ya ke jan su, cikin motar shiru ka ke ji. Ganin yadda Daddy ke ta yawaita faɗin Lahaula Wala Ƙuwwata Illah Billah lokaci zuwa lokaci sai Farida ta ƙara tsorata da lamarin. Ba dai Najeeb ya rasu ba ne, idan Najeeb ya rasu ina za ta sa kan ta...

Sai da su ka isa asibitin sannan Daddy ya ce " 'ya ta ina so ki kwantar da hankalin ki dan Allah. Insha Allah komai zai zo da sauƙi, Najeeb ya yi hatsari jiya da dare"

Dafe ƙirjinta ta yi da sauri lokaci guda kuma numfashin ta ya tafi hucin gadi na 'yan wasu sakanni.
Hawaye ne su ka fara zirya a idon ta su na gangarowa.

"Ba kuka za ki ma sa ba, addu'a za ki ma sa Aisha"

Tafiya su ke amma ƙafafuwanta ji ta ke kaman ba ajikin ta su ke ba, she's not feeling them ko kaɗan.
Har su ka isa wajen su Anas hawaye ta ke. Yadda ta ga an cika wajen sai hankalin ta ya ƙara tashi.

Daddy ya tambayi ɗanuwan sa ko likitan ya ce wani abu. Uncle Sulaiman ya ce sun ce ƙarfe tara za a ma sa CT-scan aga mi ya hana shi farfaɗowa dan sun ce su na zargin ƙwaƙwalwar sa ta kumbura ne.

Anas ya raka Farida gallery na theater room ɗin inda ta hango Najeeb kwance ansa ma sa life support system. A lokacin ta fashe da wani irin kuka mai taɓa zuciya. Anas ya ɗan dafa ta ya ce " dan Allah ki dena kuka addu'a za ki ma sa abinda ya ke buƙata kenan"

"Mutuwa zai yi ko?, mutuwa zai yi tun ban nuna ma sa yadda na ke son shi ba ko?, Ya Anas ba zan iya jure rashin sa ba"

Shi ma dai Anas daurewa kawai ya ke amma ya karaya da halin da ya ga abokin na shi....

Zuwa yamma an tabbatar mu su da cewa akwai jini da ya daskare a ƙwaƙwalwar Najeeb wanda idan ba acire ba ƙwaƙwalwar za ta yi ta kumbura ne har kuma ta iya jawo ta dena aiki gaba ɗaya wanda ƙarshen zancen dai mutuwa ce.

Abun ka da ma su dukiya tuni aka kira Dr Sajid Usman Abdallah dan ya zo ya jagoranci aikin da za a ma sa. ( ga wanda ba su san Dr Sajid ba an bar ku a baya 😂 ku karanta Mutum mugu ne. Yana nan a wattpad, za ku ga yadda Angon Zaytunah da Naziha ya sha goggonmayar rayuwa. Yai fama da zafin kishin Zayty da kuma rashin kamun kan ta. Sannan ya zo yai dakon soyayyar Ziha yarinyar da shekara ashirin da biyar cur ya ba ta, But aka ce love is blind☺)

Ranan Alhamis aka saka aikin kuma har lokacin Najeeb is in comatose. Kwana biyun nan Farida ta yi su ne akan sallaya. Kaso biyu cikin uku na daren sun tafi a sallah da roƙon Allah ne sauran kaso ɗaya kuma ya tafi a kuka da tunani.
Mom ma da aka sallamota wani tashin hankalin ta shiga dan sai da ta suma lokacin da ta je ta ga ɗan ta kwance a asibiti rai a hannun Allah...

Sun yi aikin awa shaɗaya akan Najeeb kuma Alhamdulillah an cire jinin da ya daskare ba matsala.
Sai dai Dr Sajid ya ce akwai yiwuwar Najeeb zai cigaba da zama cikin coma na tsawon lokaci. Amma, ba abinda ya fi ƙarfin addu'a...

Wata ɗaya kenan da ta wuce, wata ɗaya na kuka da roƙon Allah, wata ɗaya da tun ana cewa zai iya farfaɗowa gobe har aka zubawa sarautar Allah ido.
An tabbatar da case ɗin Najeeb ta shiga PVS (persistent vegetative state) yanzu kam sai randa ya farfaɗo kawai amma ba maganar ana tsammanta zai tashi nan kusa.

Duk wani wanda ya san Najeeb Adam Jibo sai da su ka tausaya ma sa. Shi ba mai bacci ba, shi ba mutuwa ba. Yana nan yana numfashi amma gashi a kwance ba abinda zai iya yi.

Wannan wata ɗayan da a ka yi Farida ta zama certified nurse a wajen kula da Najeeb. Tunda aka dawo da shi ɗaki na musamman da aka gyara saboda shi Farida ta koma kwana da shi. Duk yadda Daddy ya hana ta ƙi. Ita ke goge ma sa jiki safe da kuma yamma, har turaren sa ta je ta kwaso tana fesa ma sa. Ta ce Sir Najeeb ba ya son ƙazanta kuma yana son ƙanshi.

Zuwa yanzu ta rage yawan kuka da ta ke. Tana asibiti yanzu 24/7 duk da kuwa an ce ba sai an zauna da shi ba tunda ba wai tashi zai yi ya buƙaci abu ba kamar normal mai jinya. Idan ka ga ta je gida to ta je ɗauko wassu kaya ne. Kullum da safe da kuma dare sai Daddy da Mom sun zo sun duba ta tareda duba Najeeb da fatan cewa ko da na ɗan ƙaramin lokaci ne zai buɗe idon sa.

Farida ta chanja ta zama silent. Ko Sabreen ne ta zo duba Najeeb ba ta kulata, fita ma ta ke ta ba ta waje har ta gama tsiyarta ta tafi. Wanda iya ka daɗewar ta minti ishirin ne...


Yau ma ta na kwance gefensa tana ɗan shafa gashin sa da ya fara tohowa saboda lokacin da za a masa aiki aske gashin aka yi yai ƙwaranƙwal.
Taɗi ta ke ma sa kamar yadda ta saba yi.

"Sir Najeeb a ina ma mu ke"

Ta ɗan yi murmushi ta ce "yawwa na tuna, ranan da na fara jin wani abu gameda kai shine ranan da aka zo aka rescueing na mu daga hannun su Joseph. Ban ganewa zuciyata ba tun daga ranan. Ko da na dawo office kullum idan na kalli idon ka sai na ji wani abu ya taso min daga chan ƙasan zuciya ta, shi ya sa ko ina magana da kai na ke avoiding haɗa ido da kai. Ko da yaushe ina ƙoƙarin yaƙi da zuciyata saboda wani sabon al'amari da ya dinga taso min da shi gameda kai ba mai yiwuwa ba ne, na dinga tabbatar wa kaina ka fi ƙarfi na, na dinga nunawa kai na, Najeeb Adam Jibo ya fi ƙarfin Aisha Farida Salihu. Amma ka san me? Bayan ƙaddarar aure ta shiga tsakanin mu sai...."

Sallamar Anas ya katseta daga labarin da ta ke wa Najeeb.

Sai da su ka gaisa ta ke tambayar sa ya aiki?

" 'yar uwa abubuwa fa ba daɗi. Riƙe kamfani kaman Najeeb constructions sai ma su zafi irin Najeeb ɗin. Kin san Allah daga jin zancen halin da Najeeb ya ke sai kowa ya fara fidda asalin halin sa. Aka dena bawa aiki mahimmanci ana sako-sako da duk wani ayyuka da ake yi. Can you imagine wai anyi board meeting akan wai ba su yarda na jagoranci kamfani ba"

Farida ta zaro ido " to amma Ya Anas ba kai ke riƙeta ba idan Najeeb ba ya nan?"

"Haka ne amma kin san na 'yan kwanaki ne wannan. Najeeb bai taɓa tafiyar da ta wuce sati biyu ba. Yanzu kuma wata ɗaya da sati uku kenan ba ya nan. Farida abubuwa sun fara ja baya. Ba ni da zafi kaman Najeeb hakan ya sa kowa ya fara abinda ya ga dama"

"Amma ka gayawa Daddy?" Ta tambaya tana mamakin wannan al'amari, ba mutuwa Najeeb yai ba amma har an fara juya ma sa baya, Mutane kenan

"Mun tattauna da Daddy kuma ya amince da shawarar da na kawo, ya ce mu yi magana da ke ɗin"

Ta ɗan gyara zama dan ta fahimci zancen sosai.

"Farida riƙe Najeeb constructions ba zai tafi dai-dai ba sai iron man kaman Najeeb. Ki na da zafi, za ki iya taka kowa sannan za ki iya shugabanci. Kin zauna da Najeeb kin ga yadda ya ke gudanar da al'amuran sa i'm sure kin tsinci ilimin shugabanci a tareda shi. Farida ki koma aiki, wannan karan ba matsayin sakatariya ba sai matsayin CEO"

"Allah ya kiyaye Ya Anas. Wani zance ne wannan. Saboda ni ce na kawo son shugabanci duniya sai mijina na asibiti ba lafiya sai na tsallakeshi na tafi wajen aiki" ta goge hawaye ta ce " ina nan da shi anan har ranan da zai farfaɗo"

"Farida na san ki na so ki kasance tareda Najeeb, amma ba kya ganin kina da hakki akan kula da dukiyar sa. Barin gaya mi ki halin da mu ke ciki yanzu. Kamfanin da ta ke da major shares bayan Najeeb tana so ta janye hannun jarinta ko kuma mu mu sake sayar ma ta da kaso arba'in a ciki. Kin san mi hakan ke nufi? Yana nufin su na so su mallaki kamfanin ta ƙarfi, zai zama Najeeb 35% ne kawai na shi a ciki kuma kinga kamfani ta bar hannun Najeeb. Ke 'yar kasuwa ce kin san yadda za ki yi ki kawo cigaba a wannan kamfani ki kuma ceceta. Ni Architect ne ban da wani ilimi mai zurfi a wannan fanni. Najeeb da ki ke gani bayan karatun Engineering da Architecture da ya yi yana da degree a fannin kasuwanci sannan yana da certificates dayawa a ɓangarori ma su yawa musamman leadership. Hakan ya sa komai ke tafiya ma sa dai-dai"

"Ya Anas ba zai yiwu ba. A nemi wani ko cikin cousins ɗin Najeeb amma ban da ni. Ba zan iya ba"....

"Farida......"

.................................


Wata baƙar Marcedez benz ce ta shigo Kamfanin Najeeb constructions. Lokacin da motar ta tsaya an kai kusan minti biyu kafin aka buɗe ƙofa. Wata haɗaɗɗiyar mata ce ta fito daga ciki ta owners corner. Tun daga takun ta ka san mace ce mai aji da kuma girma. Kai tsaye ta shige kamfanin security ɗin wajen yana mata good morning ta amsa ma sa ta hanyar ɗaga hannu.
Anas ne ya nufota yana gaisheta lokacin da ta iso top floor ɗin. Tare su ka jera su ka wuce conference hall ɗin inda za ayi board meeting.

Kujeran da ta zauna an rubuta CEO a jiki waje ne da Najeeb ke zama lokacin yana da lafiya. Waje ne da bayanshi ba wanda ya taɓa zama a wajen idan ana taro haka.

Sai da ta ja numfashi ta sauke sannan ta ce *"suna na Aisha Farida Salihu, Mrs Najeeb Adam Jibo kuma acting CEO Najeeb constructions har zuwa lokacin da miji na zai samu lafiya ya dawo"*
Ta kalli fuskokinsu mai cike da tarin tambayoyi ta ce *ko da me ja?*....


*Tantarantarantaran. Daga secretary sai CEO wannan ƙarin matsayi har haka @team Farida kuna da aiki a gaban ku. @team Najeeb, sorry Najeebullahi ya tafi hutu, sai kun ganshi kawai dan nima ban san ranan dawowar sa ba😀*





*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


0️⃣3️⃣3️⃣




*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi, ga mai so zai iya tuntuɓar 08137311900*



"Excuse me, ba za mu amince da wannan ba. Ta ya za ace za ki jagoranci kamfani kamar wannan ki na matsayin sakatariya. I bet wannan kamfani za
ta ruguje kafin nan da wata ɗaya. Duk da ki na matsayin matar Sir Najeeb hakan ba zai sa ki ma ye gurbin sa a wannan kamfani ba. You are incompetent and clueless" wani a ciki ya faɗa yana huhhura hanci.

Ba tareda ta karaya ko nuna damuwa ba ta kalli mutumin ta ce " mi ye matsayin ka a wannan kamfani?"

Mutumin

Please Login or Register in order to submit comment