Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

iya ƙwallafa rai na a kan sa ba"

"Shikenan, ki zauna, ki zuba ido har Sabreen ta ci galaba akan ki. Idan hakan ta faru ina tabbatar mi ki da cewa ƙeyar Najeeb sai ya miki wuyar kallo"

Daga haka ya tashi ya fita.

Tunanin maganganun Anas ta shiga yi. Tana kokonton maganar amma wani ɓangare na zuciyarta na son gaskata hakan...


Ranan ba su dawo tareba saboda ta rigashi tafiya, ta barshi suna tattaunawa da Anas, ta san ba zai wuce akan fara aiki da Sabreen ta ce za ta yi da su bane.

A gajiye ta shiga gidan sai taga Sabreen da Mom su na hira a falo. Mom kawai ta gaisar ta wuce sama bayan ta aikawa Sabreen harara.

Tana ɗan jin ciwon ciki amma ba wannan ba ne a gaban ta yanzu. Mafita ta ke nema wa kan ta, ko da ba za ta samu Najeeb ba amma ba za ta bari Sabreen ta sameshi ba, dan Najeeb bai dace da karuwa ba. Ko yaushe ta fara damuwa da Najeeb oho...


As usual sai dare ya dawo, tana kwance akan gadon ya shigo. Ba ta kulashi ba dan ta kanta ta ke, tun da magriba ciwon cikin ta yai tsanani kuma ta duba ba ta da magani.

Bayan ya shirya ya sa Najdah ta kawo ma sa lemon tea. Ya zauna yana aiki a laptop yana sipping tea ɗin.

Tun ɗazu ta ke juye-juye a kan gadon bai lura da ita ba. Ta tashi zaune, ta yi rub da ciki, ta yi gotso duk saboda yadda ciwon mara da ciki ke jijjigata. Ƙarshe dai ƙasan gado ta sauko ta yi kamar sujjada tana ɗan jijjiga jikinta.

Ya gama abinda zai yi ya hau gado sai ya ga bai gan ta ba. Ɗazu dai ya gan ta a kwance kuma bai ji ƙaran buɗe ƙofar banɗaki ba balle yai tunanin wajen ta shiga. Ya share zancen ƙila kaya ta je chanjawa. Bai yi 5seconds da sake zancen ba ya ji nishinta.
Fara dube-dube ya ke har ya mirgino zuwa gefenta ya leƙa ƙasa ya ganta.

"Are you Ok?"

Girgiza kai kawai ta yi.

"Mi ya sameki?"

"Ina ruwan ka da ni. Ka damu da ni ne?"

Juyawa yai ya ƙyaleta.

Ta ɗan jawo pillow ta danne cikin ta da shi ta cigaba da nishi. Bata ankara ba sai ta ga ya kashe wutan ɗakin. Wani tuƙuƙin baƙin ciki ya zo ma ta har wuya, wato da gaske bai damu da ita ba.

"Wayyo Ummina, Wayyo Allah gatan marainiya. Wayyo Ummi"

Kunna wutar ɗakin yai ya tashi ya zo ya ɗauketa ya maidata kan gadon. Ya ce "mi ya ke damun ki?"

Ba ta kulashi ba ta cigaba da murƙusu a kan gadon. Lokaci guda ya tashi kaman an tsikare shi ya fita daga ɗakin. Minti biyar sai gashi ya shigo ɗauke da mug.

"Tashi ki sha magani"

"Ni ka bar ni, ka san abinda ke damuna ne?"

"Get up" ya faɗa da ɗan ƙarfi.

Ibrufen tab ya miƙa ma ta tareda ruwan ɗumi, ta amsa ta sha.

Ya ce " ki shanye ruwan"

Ta cigaba da shan ruwan ɗumin har ya ƙare. Ta miƙa ma sa mug ɗin ya karɓa ya ajiye a saman bedside drawer.

"Kwanta"


Kwantawa ta yi da bayan ta tana kallon idon sa. Rigan baccin da ta sa riga da wando ne masu laushi, wandon iya gwiwa ya ke.
Hannu ya sa ya kamo ƙafafuwanta biyu. Ta challa ƙara " Sir Najeeb me ka ke shirin yi?"

Wanni kallo ya watsa ma ta ta yi shiru. Ƙafafuwanta ya kama sannan ya tanƙwasu ta yadda cinyoyinta sai da su ka taɓa cikinta gwiwan kuma na taɓa nonuwanta. Ya sake stretching ƙafafun sannan ya sake tanƙwasasu. Haka ya ke yi har sai da yai kaman sau goma sannan ya sauke ƙafafun, ya sake ɗaga ƙafa ɗaya ya tanƙwasashi gefe. Ƙafar ta yi kaman triangle, sannan ya tanƙwasa ta koma ɗaya ɓangaren haka yai ta yi har sau goma sannan yai wa ɗaya ƙafan ma haka. Hannu ya sa zai ɗaga hips ɗin ta sama Farida ta yi saurin cewa "Sir Najeeb ina abu fa, kuma ba a abu idan ana abu"

Ya gimtse dariyar da ta zo ma sa ya ce " Bakin ki ne abu ai, ni ma ba na abu idan ba na so na yi abu musamman ma da wadda ba ta da abu"

Ya tallafo hips ɗinta ya ɗan ɗaga sama sannan ya mai da su ya sake ɗaga su a haka sai da yai sau goma.
Yana sake wani form of stretching ɗin ta yi saurin cewa " Sir Najeeb ka yi a hankali wandona zai yage"

Tsayawa yai yana kallon ta. Sometimes yana mamakin wai yarinyar nan ta yi makaranta. Most at times tana yin wassu abubuwan kamar 'yar ƙauye.

Sai da ya gama yi ma ta yoga dan ta samu relieve sannan ya kashe wuta ya kwanta.
A cikin duhun Farida ta dubi gefen sa ta ce "Sir Najeeb ya aka yi ka iya wannan abin, Allah na ji sauƙi sosai"

"Sleep Mrs Jibo" ...


...................

Kamar yadda Sabreen ta nema haka washe gari aka ware ma ta office a second floor. Da ta zo ta gani ta ce ba ta so sai a top floor inda office ɗin Najeeb ya ke. Anas ya ce sai dai ta yi manage ahaka zuwa kwana biyu. Ba ta da haƙurin kwana biyu dan haka ta ce ba za ta zauna ba.

Kamar yadda Anas yaiwa Farida alkawari hakan ya sa ya kira Yakubu su ka fara reviewing ɗin case ɗin Farida da aka yi kwanan baya.

Najeeb ya jima yana zaune yana aiki, Sabreen ta sa shi a gaba da kallo. Ya ce ta tafi ta ƙi tafiya sai yai kamar bai san da zaman ta ba a wajen.
Farida ba ta office lokacin da Sabreen ta zo ta wuce. Ta dawo daga kai saƙo ta zauna tana yin aiki sai ta tuna ya kamata ta chanja pad. Ta ɗau jakar ta ta nufi office ɗin Sir Najeeb tunda banɗakin sa ya fi clean.


Yana zaune ya ji hannun Sabreen a kafaɗar sa. Ya juyo a fusace.
"Whats the meaning of this?"

"I know you missed my touch Noory" ta faɗa tana ƙara shigewa jikin sa.

"To karuwancin har a office" muryan Farida ta dakatar da ita.

Dukkan su su ka kalli Farida da ke tsaye ta sa hannu a kafaɗa.

"Miss celebrity you're stepping beyond your boundary" ta ƙaraso har gaban ta ta nuna ta da yatsa.
Kamar yadda ta ce mata she has his heart haka itama ta kwaikwayi maganan ta ta ce " fuck off old woman, i am his wife"

Sabreen ta cize leɓe tana huci.

"As as as, mai guri ta zo sai mai tabarma ta naɗe"

"Wow! I like your courage" ta faɗa tana haɗiye duk wani baƙin ciki da ta ke ji.
Har ta fita Farida ba ta bar cewa as as as ba.

Ta juyo ta kalli Najeeb da ya zuba ma ta ido yana ganin shaƙiyancin da ta ke wa Sabreen. Not minding ko waye Sabreen ɗin.

"An dai ji kunya, mace ta gudu ta barka shekara takwas amma ka gan ta yanzu jikin ka ya fara rawa kamar mazari" ta yi wani juyi sannan ta wuce banɗaki.

....................


A hankali ta fara barbaɗa tankaɗaɗɗen yajin da ke hannunta, tun daga pillow zuwa duka bedsheet ɗin. Bedsheet ɗin ba fari bane balle a gane. Tana gamawa ta fice daga ɗakin ta maida roban yajin zuwa kitchen. Ta haura sama abinta.
Sabreen ta dawo tayi wanka ta shirya cikin rigan baccinta ɗan filili da shi. Ta kwanta akan gado. Juyawar da za tayi sai ta ji zafi a wuyanta da cinyoyinta da ke buɗe. Ta sa hannu ta sosa wuyar ai sai ya zama kamar ƙara zafi ta yi wa wajen. Ta yi wuf ta tashi tana sosa ko'ina ajikinta...


Farida ta baza kunne tana sauraron ko saƙonta ya kai inda ya ta ke so, saboda haka ma ba ta kunna Tv ba, Shi kuma Najeeb na aiki a laptop. Lokaci ɗaya su ka ji an kurma ihu.
Da farko Najeeb ya ɗauka ko ƙaran daga TV ɗin Najdah ne tunda ya ga Farida ba ta kunna Tv ɗin su ba. Ihu da ƙaran ya cigaba da ƙaruwa hakan ya sa ya miƙe zumɓur ya fita, Farida ta bi bayan shi da sauri.
Lokacin da su ka isa ƙasa su Daddy da Mom ma sun iso ƙasan su na kan Sabreen da ke ta soshe-soshe tana ihu...


*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




0️⃣2️⃣9️⃣





*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi, ga mai so zai iya tuntuɓar 08137311900*

Sabreen na ganin Najeeb, ta yi kan sa tana sose-sose, ya riƙeta yana tambayar miya ke damunta amma ba magana sai kuka tana ƙara shigewa jikin Najeeb kaman jikin sa ne zai ma ta magani.
Mom ta tafi da gudu ɗauko car key. Chak ya ɗauketa za su fita dai-dai nan Farida ta sa kuka itama tana wayyo cikina wayyo cikina.
Najeeb ɗauke da Sabreen ya juyo ya ga Farida har ta kai ƙasa tana riƙe da ciki.

Dad ya ce ajiyeta ka ɗauko matar ka.
Sabreen ba ta ji mi aka ce ba amma ganin Najeeb na shirin sauketa sai ta sake ƙanƙame wuyan Najeeb tana kuka.
Chan gefe ma Faridan kuka ta ke yi Mom ta yi kan ta tana ƙoƙarin ɗagata tana tambayar miya sameta.
Tunanin Najeeb ko dai ciwon cikin period ne amma kuma she was normal throughout yau, tunda yau kwana na uku kenan da farawanta.

Farida cikin kuka ta fara cewa "Mom ulcer, ulcer na ne ya tashi"

Bai san ko maganar Daddyn ne ta shige shi ba, ko kuma dai ya zaɓi tallafawa Farida ne akan Sabreen ɗin. Amma tsintar kan sa yai da sauke Sabreen ya nufi wajen da Farida ke murƙususun ƙarya a ƙasa. Daddy da Mom su ka tallafawa Sabreen su ka fita da ita. Daddy na cewa yai sauri ya ɗauko Farida. Faridan na hannun sa ya ce su tafi da Sabreen zai taho da Farida.
Ba tareda ya ji nauyin ta ba haka ya haura da ita sama dan ya ɗauko key ɗin motar sa, har da ce ma ta sorry.
Ya ɗauki key ɗin su ka fito still yana ɗauke da ita. Kafin su isa wajen motar sa motar su Daddy ta fice daga gidan. Sai da ya ajiyeta sannan ya zago da gudu ya shiga wajen zaman driver, yana ƙoƙarin tada motar ya ji ta ce "Sir Najeeb mu koma cikin gida, idan na sha Gestid ma zai lafa mun"

Kallon ta ya tsaya yi cike da mamaki da takaici, sai yanzu ya lura fiskarta ba ɗigon hawaye ko ɗaya. Lokaci guda zuciyar sa ta ankara da cewa lallai Farida na da hannu wajen abinda ya samu Sabreen, yanzu haka wani abin ta sa ma ta a ɗaki.

"You lied?" Ya faɗa da ɗan ƙarfi

"Sir Najeeb Allah Wallahi ina da ulcer, na ji alamun zai tashi ne shi ne ya sa na tareshi tun kafin ya zo"

Zaro ido yai waje lokaci guda kuma ya kwashe da dariya har da dukan steering.

"Now i'm very certain that you're crazy Mrs Jibo"

"Sir Najeeb da laifi idan mutum ya tari rashin lafiya ne?"

Sai da ya sha dariyar sa sannan ya ce " faɗamin gaskiya mi ki ka yiwa Sabreen?"

"Ni ba abin da na ma ta. Ance idan duka yai yawa na kai ake karewa. Da ka je kana dakon ɗaukar wata ƙatuwar banza ba gara ka ɗauke ni ba, har lada za ka samu a hakan fa"

"So, kin ƙirƙiri ciwo ne kawai dan na ɗauke ki?"

"Allankatafir ba haka ba ne. Ciwon a jikina ya ke tun asali"

" Ok ok, so yanzu mi za ki ce da su Dad? Su ma za ki gaya mu su taro ciwo ki ka yi?"

"Cewa zan yi na sha magani na warke"

"Ni kuma sai na kai ki asibitin, a taro miki ciwon da kyau"

Ganin yana ƙoƙarin ta da motar ne ya sa ta yi saurin buɗe ƙofa ta fita da gudu. Yana gani ta fita ya kwantar da kan sa ajikin kujera yana murmushi. Shi kan sa mamaki ya ke, a da ya tsani yawan surutun ta amma yanzu ya na jin nishaɗi idan tana yin wasu abubuwan.

Ya jima a cikin motar yana tuno wassu abubuwa da su ka faru a baya. Yana fitowa zai koma cikin gida Daddy ya kirashi yana tambayar ya aka yi ba su iso ba. Cewa yai cikin Faridan ya lafa ta ce ba sai anje asibiti ba.
Daddy ya ce "to Alhamdulillah, Allah ya ƙara lafiya"

Yana kashe wayar ya fara mamakin ƙaryar da yai saboda Farida.
Duƙunƙunewa ta yi ajikin bargo tana tsoron mi Sir Najeeb zai yi dan ta tabbata ya gane ita ta yiwa Sabreen wannan abu.
Yana shigowa ta sake duƙunƙunewa ta na rintse ido.

"Ki gayamin gaskiya mi ki ka sa ma ta?"

Ta yi shiru ba ta kulashi ba.
"Idan ba ki gayamin ba zan gayawa Dad ƙaryan da ki ka yi"

Ta ɗan buɗe idon ta ta leƙo shi yana tsaye yana kallon ta.

"Borkono ne, dakakken borkono na sa ma ta a bedsheet"

"You're a criminal Mrs Jibo, ya kamata a kama ki"

"Allah ya kiyaye"

Wucewa yai ya shiga banɗaki dan ya sake wanka...
Farida na ganin ya shiga banɗaki ta san ba fitowa zai yi da wuri ba ta yi wuff ta tashi ta fita daga ɗakin. Ɗakin Sabreen da ke ƙasa ta je ta cire bedsheet ta karkaɗe sannan ta juyashi baya ta shimfiɗa, filon ma ta ma sa haka sannan ta fito.

*(yau na ci yaji dayawa, hakan ya tada min ulcer na. That's d trigger for writing this scene😁. Ni ma daga yau irin na Farida zan na yi, zan dinga taro ulcer tun kafin ya tashi, saboda idan ya zo kar ya wahalar da ni😂)*

.......................

Su Daddy na zuwa aka duba jikin Sabreen wanda har ya feso da ƙuraje abinka da jar mace. Magani aka ba su aka ce ta shafa. Mom ta karɓa ta shafa ma ta. Likitan cewa yai allergy ne ba komai ba.
Mom ta ce da sun koma gida za a chanja ma ta ɗaki tunda ta ce daga kwanciya a gado ta fara jin zafi da ƙaiƙayin.

Lokacin da su ka dawo gida ƙarfe shabiyu na dare ya wuce. Ɗakin Najma da ta ke sauka idan ta zo su ka wuce da ita. Mom ta je ta ɗebo ma ta kaya a wancan ɗakin da ke ƙasa.
Sai da su ka tabbatar ta kwanta a wannan gado lafiya kafin su ka bar ɗakin...

Farida ta yi bacci kafin su dawo amma Najeeb ya ji dawowar su, sai dai ko leƙowa bai yi ba.


Yau da asuba Najeeb ya fito daga wanka yana sa kaya sai ga siririyar tusa ta fito. Farida da ke shirin shiga banɗaki ta leƙo inda ya ke dan sarai ta ji tusan.

"Sir Najeeb ka ji abin da na ji kuwa?"

Yai gyaran murya ya ci gaba da saka belt ɗin da ya ke ba tareda ya kulata ba.

"Sir Najeeb fitar tusa na ji fa, kuma ba ni na yi ba. Ba ma irin warin tusa na bane"

Ɗagowa yai ya kalleta ran sa a haɗe.

"Ke wai bakin ki ba ya iya yin shiru ne?"

Ɓiiiit sai ga tusan ta kuma fitowa.

Ta kama baki tana faɗin "Lahaula! Sir Najeeb ashe kai ne. Ina ga basir ke damunka, ka nemi magani"

Hannu ya kai zai buge bakinta ta ja baya da sauri tana dariya. Sai da ta shiga banɗaki ta leƙo da kan ta ta ce "Sir Najeeb tusan ka irin ta yara. Kasan ance tusa kala uku ne akwai Ɓiiiit na yara, booooot na manya, alanrankiɗibobot na tsofi"
Tana faɗin haka ta banko ƙofar banɗakin...

Ya na tsaye yana naɗa tie amma dariya ya ke ciki-ciki. Cikin zuciyar sa yana maimaita abin da ta ce. "Where on earth did she know all this" ya tambayi kansa.

Kafin ta fito ya riga ya shirya ya fita. Lokacin da ya kai ƙasa ya haɗu da Daddy.
"Morning Dad"

"Morning ya jikin Aisha?"

"Da sauƙi" ya faɗa yana tuno abin da ya faru jiya.

"Allah ya ƙara ma ta lafiya, za ka koya ma ta mota ne ko za ka enrolling na ta a driving school? Ka ga ba daɗi Najdah na hawa mota ita ba ta da shi"

" Ehm Ehm..." ya rasa abin faɗa.

"Shikenan duk abinda ka yanke ya yi dai-dai"...

...................

Saboda abinda ya faru ranan Sabreen ba ta fita ba. Lokacin da Najdah ta dawo ne ta ke jin abinda ya faru a bakin Sabreen ɗin, saboda ba ta kwana a gida jiya ba, gidan Uncle Sulaiman ta kwana.

Najdah ta tashi ta je ɗakin dan ta tabbatar da zargin ta. Sai dai Adama ta riga ta chanja bedsheet ɗin kuma an gyara ɗakin dan haka ba abin da ta gani.

Da ta dawo ta ce da Sabreen ta san wanda ya sa ma ta abu a gado. Sabreen ta zaro ido tana tambayar waye?...

...........

"Khalidah ban gane mi ya ke faruwa ba? Kin min alƙawarin zan samu wannan sakatariyar Najeeb ɗin amma daga dawowata ki ke min zancen banza wai Najeeb ya aureta. Ya aka yi haka? Ba kin tabbatar min plan ɗin mu zai tafi dai-dai ba. Zai koreta a aiki ni kuma na sameta"

" Alhaji matawalle ban san ya zan ma ka ba. Ba fa kai kaɗai ka ke jin zafin abin nan ba. Kai damuwarka ka kassara Najeeb ni damuwata na samu Najeeb. Kai buƙatar ka ta biya ka sa Najeeb ya rasa babban project wanda hakan ta jawo ma sa asara, ni kuma fa? Mai na samu banda ƙara haɗa Najeeb da sakatariyar sa"

"A'a Khalidah bayan kassara Najeeb kin min alƙawarin samun sakatariyar sa, Farida sunan ta ko?"

" Alhaji Matawalle ka fita a office ɗi na, ka bar ni da takaici da ƙuncin da zuciyata ke fama da shi"

"Kar ki kawomin zancen banza Khalidah, ba na neman abu na rasa"

"Ya zan ma ka ne? Ka je ka ɗauki Farida ma na idan ka isa"

"Haka ki ka ce ko" ya girgiza kai ya fita daga office ɗin.

Yakubu ya koma da baya lokacin da ya ga Alhaji Matawalle na shirin fitowa. Dama ya zo kawo wa Khalidah wa su takardu ne ya ji ƙarshen hiran na su. Jin sunan Farida ya sa ya fasa shiga office ɗin.

.......................

Wannan weekend ɗin da Aneesa ta zo ne ta lura da cikin jikin Maijiddah. Ba ta san lokacin da ta ce "Sweetheart yaushe wannan yarinyar ta samu ciki?"
AbdulWahab bai kulata ba ya cigaba da cin abincin da ya ke yi.

"Sweetheart magana fa na ke"

"So ki ke na bayyana mi ki abinda mu ka yi ta samu ciki? ko so ki ke ki san sau nawa mu ka yi kafin ta samu ciki?"

"AbdulWahab zai kai 4 months fa"

"Allah ya sauke min ita lafiya amin"

"Abinda ma za ka ce kenan? Bayan ka gama cin amana ta da yarinya ƙarama, wanda a haife ka haife ta har kana da bakin cewa Allah ya sauketa lafiya"

"Ya nuna ina da lafiya kenan, kuma kin ga ina da damar ƙaro irin Hauwerh biyu idan ina so, kin ga in shiga nan in shiga nan"

Aneesa ta cillar da cokalin hannun ta.

"Wallahi ba zai yiwu ba. Ba ka isa ba AbdulWahab"

"Ki cigaba da aiki a Abuja, zan cigaba da aiki a nan kuma da idon ki za ki dinga ganin sakamakon ayyuka na ma su kyau da tarin lada. Alhamdulillah da na kasance musulmi, na ke da damar auren mace fiye da ɗaya. Kin ga musulunci ya min rana"

Juice da ke glass cup a gaban ta ta ɗauka ta watsawa AbdulWahab tana zage-zage. Bai ƙara cewa komai ba ya tashi ya bar wajen.

"Ka dawo ma na, ka dawo mu ƙarasa maganar, macuci kawai"...

Wannan weekend ɗin gaba ɗaya cikin faɗa su ka yi dan AbdulWahab dena shiga sabgar ta ya yi. Tana komawa Abuja ta sanar da Mama Maijiddah na da ciki, ga mamakin ta sai Mama ta ce "Allah ya raba lafiya"

"Mama kin ji mi na ce kuwa? Su baby da Alizah su na gab da samun step siblings"

"Na ji kuma na gane, idan kina son haihuwan ke ma sai ki dena planning ki koma tara 'ya'ya rututu kamar Kaza"

Aneesa ta rasa bakin magana, dan inda ta dosa Mama ba ta bi nan ba.

A ranan da ta je office ta nemi a maida ita Lagos ko kuma ta ajiye aiki. Su ka ce za su duba.

.......................


Da ke tun ƙarfe ɗaya Najeeb ya fita kuma ya riga ya ce ma ta ba zai dawo ba sai yamma shi ya sa ta tattara ta fito dan ta koma gida. Tana fitowa ta hango Sabreen da wassu police biyu su na tahowa. Mamaki ya kamata ta ɗan tsaya dan ta yi gulman me ke faruwa.
Sabreen ta nuna ta tana faɗin "she's the devil, arrest her"

Farida ta zaro ido " arrest me for what?"

"Ran ki shi daɗe za ki bimu zuwa station mu mi ki wassu tambayoyi"

"Ƙwal ubanchan, na bi ku station a dalilin me. Kun san ko wacece?"

Ɗaya police ɗin ya kwantar da murya ya ce " dan Allah ki yi haƙuri mu je, mu ma daga sama aka samu"

Sabreen sai hararanta ta ke.

"Shikenan barin kira miji na" ta fito da wayarta daga jaka ta fara kiran Najeeb sai dai da ke inda su ke ba service sai bai shiga ba. Jikin Farida yai sanyi, ta tura ma sa text kawai ta bi police ɗin nan...


Bai duba wayar sa ba sai ƙarfe biyar da rabi bayan sun dawo kamfani. Yana duba missed call ya ga har da numbar Farida ga kuma text ɗin ta. Ya buɗe text ɗin ya ga ta rubuta *Sabreen ta arresting ɗi na*

"Arrest?" Yai saurin kiran numbar Faridan ya ji ta a kashe. Da sauri ya fara dialling numbar Anas ya na fita daga office ɗin da gudu...

Shi da Anas su ka isa gida dan numbar Sabreen ɗin da Najdah ta turo mu su an ƙi ɗaga kiran su.

Hankali kwance su ka samu Sabreen tana zaune a falo tana cin apple.

"Where's she?" Ya daka ma ta tsawa

" who?"

"Dont be stupid Sabreen, where is she?"

Juyar da kai ta yi gefe ba ta amsa ba.
Ƙarasawa yai wajen ya fincikota yai waje da ita Anas ya bi bayan sa...

............

Tun da su ka shiga mota ya ke faɗa abin mamaki Sabreen ta ce ba za a fitar da Farida ba saboda abin da ta ma ta...

'Yan station ɗin ma sai da su ka san sun taɓo matar babban mutum. Tun da su ka shiga Najeeb ke ta masifa. Anas ne ma ya ke ƙoƙarin bashi haƙuri dan kar a samu matsala a wajen.

Ba'a jima ba aka taho da Farida. Yana ganin ta ya ƙarasa wajen ta da sauri. Ya riƙe hannunta kawai sai ta faɗa jikin sa ta fara kuka.
Duk wani formalities Anas ne ya tsaya zai yi, dan Najeeb kan jan hannun matar sa yai su ka bar wajen. Sabreen ta bi bayan su tana faɗin ba zai yiwu Farida ta tafi haka ba bayan abinda ta yi ma ta. Najeeb bai kulata ba har su ka isa bakin mota. Zai taimakawa Farida ta shiga Sabreen ta riƙe ma sa riga, ta fara kukan munafurci.

"Noory she wanted to kill me, ita ta sa min yaji a gado jiya. I almost died Noory"

Bai yi yunƙurin yafce hannunsa daga riƙon da ta ma sa ba illa matsawa yai kusa da Farida ya ɗan sukuyo dai dai saitin fiskarta. Ba tareda wani tantama ba ya haɗe bakin su. Farida ta ƙwalalo ido saboda mamaki da shock da ta ji lokaci guda.

Sabreen ta sake rigan Najeeb tana kallon yadda Najeeb ke kissing Farida zuciyarta na tafarfasa, ji ta ke kamar zuciyar zai bulluƙo ya fito.

Farida ta yi saurin janye bakin ta saboda tunowa da ta yi a public place su ke. Da rinannun idanun sa da su ka ƙanƙance ya ce "kiss me" ba ta san ya akayi ta jefar da kunyar ba kawai ta tsinci kan ta da haɗe bakin su not minding a inda su ke...




*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*




0️⃣3️⃣0️⃣





Murmushi kawai ta ke yi tunda su ka fara tafiya. Idon ta na gefen titi amma hankalin ta ba a titin ya ke ba. Har yanzu tana jin taste ɗin zaƙin bakin sa a nata bakin. Ba ta taɓa sanin haka kiss ke da daɗi ba sai yau. Lokacin su na soyayya da Lukman ya taɓa kissing hannun ta da goshi amma banda lip to lip kiss. Shi kam Rayyan

Please Login or Register in order to submit comment